Batuol mamman complete novel - Chapter 24
Batuol mamman complete novel Chapter 24: Batuol mamman complete novel Chapter 24. "Tsokanata kuke yi ko? Nasan me zanyi muku" yace yayi gaba Ghazalatu tayi…
3,360 words
"Tsokanata kuke yi ko? Nasan me zanyi muku" yace yayi gaba Ghazalatu tayi saurin tarar dashi. [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Sun isa Sumaila karfe biyu na rana a gajiye saboda tashin wuri da suka yi. Emzee ne ya koma jagora da suka shigo garin shiyasa tasu motar take gaba. Awwab ba tsayawa Emzee din ya fita da sauri saboda magana da yake son yi wa Ummin tasu. Gefe ya ja ta ana kokarin fitowa da kayan da ita kanta bata san da zamansu ba a boot.
"Ummi wai kuwa sun san zamu zo da baki?" Yace yana rage murya.
"Na fadawa Innawuro da ta kira nace ta sanar dasu tunda kaga ba waya gareni ba. Menene?"
Da damuwa a fuskarsa yace "kada muje a rasa abinda za'a basu nasan bazaki ji dadi ba"
Murmushi Mairama tayi. Zayyan dinta akwai hankali da nutsuwa ga zurfin tunani. Rashin abin tarbar baki tabbas zai iya faruwa don tasan halin gidan nasu "to yanzu me ya kamata ayi?"
"Idan kina da kudi kawo naje na siyo gurasa da tsire kawai"
Karamar jakarta ta mika masa. Dubu uku ya cire cikin kudin da Ardo ya bata ne da zasu taho. Ya tafi tana ta masa addu'a a zuciyarta.
Radhiya kuma ta kama kofa za ta bude Awwab ya danna central lock. A zuciye ta juyo "bude min"
"Ko nima balotellin zaki yi min ne? Zai fi miki sauki akan wannan juya idanun" bayansa ya juya "Ghazalatu zauna magana zamuyi"
Murtuke fuska tayi itama ya kallesu ya tabe baki. Mata, mata halinku sai ku.
Su Zayyana duk sun fita sun bi bayan iyayensu cikin gidan. Basu san me yasa ya tsayar da su Radhiya ba amma ko ma meye tabbas basu ga alamun wasa a tare da yayan nasu ba.
"Kun gama fushin ko har yanzu da saura?"
Ghazalatu dama jira take yi "don na biyoka shine zaka wulakantani akan wannan yarinyar kamar wata kishiyata? Tunda muka zo sai kayi mata magana sau uku baka yi min daya ba. Sannan nazo shiga gaba ta shige duka ka kyaleta. Idan wani abu ne tsakaninku gara ka fada min da wuri na san matsayina. Amma bazai yiwu ta rinka jin kanta kamar wata a wurinka ba tana neman shiga tsakaninmu"
"Kin gama? To bari kiji in fada miki. Alheran wata ce a wurina Ghazalatu kuma bazan yarda kici mata mutumci ba. She is my sister kamar yadda na dauki su Zahra haka ita ma na dauketa. Idan ma kishi zakiyi ba da ita zakiyi ba. Ki bari sai kin hadu da wadda take da matsayi irin naki a wurina"
Dazu gani take wannan Ghazalatun take ko wa tayi mata rashin mutumci amma maganar Awwab ta yanzu tafi kona mata rai akan komai duk da cewa gaskiya ce ya fada. Ita din kanwa take a wurinsa amma meyasa kalaman nasa suka yi mata zafi haka.
Daga haduwa dashi kwana daya kawai take neman matsayi fiye da abinda zai iya bata. To me ma take nema ta tambayi zuciyarta. Ranta taji ya cunkushe gabadaya taji ta tsani zaman da take yi tare dasu a motar. Dago kai tayi kamar ba ita bace zuciyarta take kai kawo a abinda ta kasa gane zahirinsa ta kalli Ghazalatu.
"Matar Hamma kiyi hakuri don Allah. Haushi naji da kika kirani house girl. Ke da kishiya sai dai mota in sha Allahu"
Awwab kallonta yayi yadda ta nutsu tana magana kamar ba ita ba. Suka hada ido tayi masa wani murmushi da ya tsaya masa a rai yaji kamar ya dora hannunsa a kumatunta da ya lotsa.
"Kaima kayi hakuri bazan kara ba"
Tana kaiwa nan ta kama kofar zata bude sai ya cire lock din ta fita tare da duka tunaninsa kamar ta zare masa duk wani kuzari da yake jikinsa. A katon soron gidan ta ya da zango jikin wani dan tudun siminti da akayi domin zama. Abinda ya bata mamaki bai wuce kukan da ta fashe dashi sosai ba. Ji take idan bata yi ba ma zuciyarta zata iya bugawa. Kukan na meye? Oho, itama bata sani ba. Abu daya ne kawai ya tsaya mata a rai kalmomin Hammanta na karshe wai Ghazalatu ta jira sai ta hadu da mai matsayi irin nata a wurinsa sannan tayi kishi. Tsaki taja tana jan hanci "Mtswwww in kun ga dama ku cinye juna karewarta, aikin banza. Dadinta dai nima Kawu Zakari ina komawa zai ce yana sona. Mu za'a yiwa burga da wata soyayya? Maza na fita filin yaki ko su je ceton rai a asibiti kai ka makale a jirgin sama kamar tsuntsu wa zai so ka idan ba wannan mai kwalakwalan idanun ba dama"
Hannu tasa ta share hawayenta bayan ta gama rarrashin kanta ta shiga gidan da sallama. A can mota kuwa Awwab da Ghazalatu an bude sabon shafi sai dai a wurinsa babu wannan dokin jikinsa kamar wanda aka yiwa duka haka yake ji. Su ma tana shiga suna shigowa.
Tabarmi ne aka shimfida daga can gefe inda inuwa take don dakunan gidan babu mai girman da zasu zauna a wadace da su da kuma tawagar Malamijo da suka zo kallon 'yan gayu. Akan abin sallah yake zaune ya mike kafafu dawowarsu kenan daga asibiti an zuke fitsarin an hadosu da tulin magunguna. Sallamar baki yasa aka kawo masa babbar riga ya saka ya rufe kasusuwan kirjinsa.
Radhiya ya hango zai fara tsokanarta sai da ta matso ya kula idanunta sunyi ja sosai.
"Kukan me kika yi ke kuma?"
Kamshin turaren Awwab kawai ta ji a bayanta ta gane ya shigo shima. Gashi ana ta kallonta idanunta sunyi ja haka saman hancinta.
"Ji nayi kamar ana kuka ance ka tafi shine na fara nawa nima. Ashe ashe kana nan."
"Kaniyarki" Malamijo yace ya yi mata dakuwa "Mairama ki rasa da wa zaki zo gidan nan sai da wannan aljanar 'yar taki, ko wancan hutun da kika turo su ni banji dadin zama da ita ba. Sau biyu tana yi min barna a gona"
Awwab sam hankalinsa kasa kwanciya yayi da aka ce tayi kuka. Bayan ya gaisa da mutanen gidan da suke wurin fuskarta ya rinka lalube yana son hada ido da ita amma fafur taki. Baya so ya zama sanadin kukanta ko kadan. Muryarta ya tsinkaya tana cewa "wai me ya sameka ne Malamijo, ciwon me kake?"
Hajjo ta soma dariya za ta tona masa asiri a gaban 'yan gayu yayi saurin cewa "zazzabi ne mai zafi ya damkeni kamar bazan kai labari ba. Ai naci wahala ba kadan ba. Yanzu ma daga asibiti nake"
Sannu da adduar samun sauki suka yi masa. Yadikko ta soma cigiyar Emzee shine Mairama tace ya tafi sayen gurasa da tsire wai yana sha'awa. Hakanan Malamijo ya tsargu ya daure ya cije yace a kira guda cikin samarin gidan ya yanka kaji uku ayi musu farfesu.
Mami ce tace " Kada ka damu Baba muna sallah zamu juya akwai tafiya a gabanmu. Ibrahim idan Karami ya dawo ku shigo da kayan nan ciki"
Nan fa hankalinsa ya tattara yayi waje. Ba dadewa Emzee ya dawo da ledoji a hannu. Ya sayo gurasar da nama a wadace harda lemuka irin su cway, lacasera da maltina masu sanyi. Ashe 'yan matan yunwa suke ji. Kafin Hajjo ta gama dafa shinkafar da Malamijo ya aunar mata bayan ya koma daki daga buhu daya cikin wanda su Mami suka kawo don kwarewa a tsiya har sun koshi.
Sallah kasaru suka gabatar azahar da la'asar sannan suka ce zasu koma. Idan sun isa da wuri ma Katsina zasu wuce kawai saboda kada su yiwa Zainab yawa a gida.
Da sauri Radhiya ta dago kai rike da gurasa a hannu sai lokacin take ci ta kalli Awwab. Hada ido su ka yi shima tun dazu ita yake kallo. Kin kula shi da take yi shine yake damunsa. Kwana biyar Mairama tace zasuyi a nan sannan su wuce Rugar Barkindo. Sai bikin su Zahra ya rage sati daya zasu koma Katsina.
"Wannan dan samarin baici komai ba zaku tafi. Radhiya ko saurayinki ne kika kawo baki gabatar min dashi ba?"
Malamijo yace yana kallon Awwab. Yaron da gani akwai maiko maiko zai so ya auri jikar tasa.
Murguda baki tayi da ta ga Ghazalatu ta sha kunu "idan ma kishi kake yi to ka dena Malamijo, ka jira sai na sami mai matsayi daidai da naka amma ba wannan ba."
Yanzu ya gano bakin zaren. Da gaske maganarsa ce ta bata mata rai harda kuka don sai da ya gano ja da kankancewar da idanun nata suka yi. Da ya juya kalaman a bakinsu sai ya ga rashin dacewarsu a dazun.
Mami haka nan ta fara zargin ko Awwab din ya yiwa Radhiya wani abin ne ya bata mata rai. Bazasu so ayi aure basa son juna ba. 'Yar dabarar manya ta kirkiro wadda bata baude da yanayin Awwab din ba a yadda ta san shi "haka yake baya son cin abinci, ga tuki a gabansa mai nisa"
"Ke zuba masa abinci ki kai masa wajen soro tunda babu kowa a wurin. Kila kunya yake ji ko dan Ummi" Mairama tace tana murmushi.
Hakan yayi masa daidai har ransa. Abincin da Hajjo ta dafa da wanda Emzee ya siyo ta zuba masa a plates biyu ta dora akan tray tayi gaba batare da tayi masa magana ba. Ghazalatu kamar ta bisu sai ta tuna bayan fitarta dazu daga motar yadda ya jaddada mata son da yake mata. Tayi ta gama iyayinta ta koma kauyensu kowa ma ya huta.
Wurin yana da fadi daga kan tudun dazu ta ajiye abincin ta koma daukar tabarma suka yi kicibus. Wai sai tayi masa murmushi a zuwan komai lafiya shima ya maida mata. Da ta kawo tabarmar yana zaune a gefen abincin ta shimfida ta sauke masa a kasa.
"Hamma sauko kaci kada kuyi dare"
Kura mata idanu yayi sai da taji kallon ya hanata motsi sannan ya sauko ya zauna a kan tabarmar ya tankwashe kafafunsa.
"Zauna mu ci"
"Na koshi"
"Ban isa da ke ba ko?" Taji yace a hankali yana daukar cokali.
Bata so yana magana irin haka sai ta taji zuciyarta tayi wani iri. Zama tayi a daya bangaren tray din ta tankwashe kafa yadda yayi. Cokali daya ne a ciki ya debi abincin yaci ya mika mata. Satar kallonsa tayi ya dage mata gira da ido yayi mata nuni da taci. Sai da ta sauke numfashi tana kunyar wannan abu ta rufe ido taci da cokalin da ya fito daga bakin Hamma Awwab.
Karba yayi ya sake ci ya kuma mika mata. Za tayi magana yasa hannunsa a kan lebensa sai ta hakura. Duk loma daya sai ya mika mata har suka cinye abincin gabadaya.
"Wannan gurasar dai bani da inda zan cusa ta ki mayar ciki"
Dama ta kagu ta tashi ta kinkimi tray din za ta gudu ya danne gefensa.
"Ban gama magana ba"
Komawa tayi ta zauna ba don taso ba taji yace "I am sorry Alheran. Nazo ina ta yi miki laifi ba da niyya ba"
Sake karyar mata da zuciya maganarsa tayi. Shi kam bashi da girman kai. Wai ita dinnan kanwar bayansa 'yar kauye yake bawa hakuri.
"An daure harshen ne? Talk"
Rufe ido tayi sai hawaye sharrr kamar famfo. Ta rasa gane irin emotions din da suke yawo a zuciyarta yau dinnan.
Hankali a tashe yace "Ya Allah, me nayi miki kuma?"
"Nima ban sani ba Hamma" tace tana kara fashewa da wani kukan. Me ya sami zuciyarta ne a cikin kankanin lokaci? Rabonta da kuka tun farkon zuwan su Mami rugarsu da ana bada labarin abinda kawunsu Maikudi yayi.
Kuka tayi harda shessheka Awwab bai hanata ba har ta gama don kanta ya bata tissue irin ya ledar nan karama ta goge idanunta.
"Feeling better?"
Ta gyada kai tana kallon kwanukan gabanta.
"Good, yanzu ki fada min tsakani da Allah me ya same ki? Nine ko?"
Rasa me za ta ce masa tayi ta kare da cewa "ba kaine kake murna zaka tafi ba"
"Ke kuma ba kya so na tafi?"
Kada fa ya fassarata ta soma tunani "dena fada kada budurwarka taji. Duk baka tambayeni labarin komai nawa ba zaka koma kila bazan kuma ganinka ba sai an dade. Shine naji raina ya baci"
"Sai nake ji kamar dai maganata ta dazu ce ta baki haushi. Amma nima bana son tafiyar ko sabawa bamu gama yi ba ko" yayi yar dariya.
"Eh, ko askina ban fada maka me yasa akayi min ba"
Sai da yayi dariya sosai yace "an gaya miki ni bana tsoron kiyi min balotellin ne? Ina sane naki tambaya kada na janyowa kaina"
"Ashe kai matsoraci ne" ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ta gama kuka ba.
Sweet ya dauko daga aljihunsa irin mai mint dinnan ya bare ya jefa a baki yana dariyar matsoracin da ta kira shi.
"Dazu ka raba abin leda baka bani ba yanzu ma a gabana ka shanye alawar? Kuma nice karama ni ya kamata ka bawa"
"Sorry gashi in kina so" ya cirota daga bakinsa dama niyyarsa kenan.
Wata zuciyar tana kwabarta wata tana ingizata har ta mika hannu tayi saurin janyewa "wayo zaka yi min, na tuna me kace dazu"
"Ke dai kina kyankyamin abin bakina kawai"
"Haba dai..." bata rufe bakin ba ya saka mata sauran da ya rage har hannunsa yana taba lebenta. Saurin tashi tsaye yayi ita kuwa ta rasa me zata yi ma.
"Ki rage min kinga kadan na sha"
Lumshe ido tayi tana tsotsar alawar yana kallon yadda bakinta yake motsawa yana jin kamar ya taya shi. Girgiza kai yayi da sauri. Lafiyata kalau kuwa ya tambayi kansa.
"Ahhhh" Radhiya tace ta bude bakin ta mike tsaye yadda zai gano cikin bakin nata sosai. Ta shanye alawar saura yar kadan.
"Cewa nayi ki rage min fa"
"Nima bata isheni ba. Babu kari?"
"Zan gamu dake ne, muje ciki su fito bana jin zamu iya wucewa a yau sai dai mu kwana a Kano" tafiya ciki ya soma yi.
"Hamma gashi" ya juyo ta miko masa yar karamar sweet din ya karba yana kallon cikin kwayar idonunta ya saka a bakinsa. Bata sani ba ko shima yaji amma ita dai wani abu ne ya zarga mata har kasan zuciyarta.
[5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Mota suka nufa cikin sa'a Mal Da'u ya sanar dasu cewa ya fitar da mahaifar tinkiyar ta tashi. Radhiya sai murna kamar wata mutum. Kafin ta bar gidan ta kudiri niyar sai anci nama amma bazata so yau da babu hannunta a ciki ba Malamijo ya kare mata tanadi a bainar jama'a. Kowa wurin zamansa na dazu ya zauna jiki yayi ligib bare ma Ghazalatu da ta hado da tafiya daga Katsina. Suna isa gida sallar magariba suka yi.
Abin farinciki wurin Radhiya ashe bayan fitarsu Nene Marka ta iso. Danne tsohuwar tayi cikin murnar ganinta. Yau tsakar gidan ta san anyi baki kusan kowa anan ya zauna suna shan iskar Allah suna hirarrakinsu. Ana isha Ghazalatu ko abincin da ake yi mata tayi bata iya kallo ba tayi bacci ita kadai a dakin Zahra ma taji sauki ta fito wurin 'yan uwanta.
"Nene muje in nuna miki wani abu" Radhiya tace cikin rada. Dakin da zasu kwana ta ja ta. Ganin Ghazalatu bacci take yi ta cire dankwalin ta nuna mata kan ta "kinga abinda Innawuro tayi min" tace kamar zatayi kuka.
"Me zan gani ni Marka, aski akan budurwa saboda Allah"
Caraf a kunnen Ghazalatu. Da dabara ta juyo idonta ya sauka akan Radhiya dariya ta kusa kwace mata. Ashe ma babu wani dalili da zai sa ta dami kanta akan wannan namijin. Ji take kamar ta jawo gobe ta ganta a Katsina. Yau din taki karewa tunda tazo yarinyar take like da Awwab. Bata so ta nuna masa zahirin yadda take kin mutanen nan saboda yanzu dai a cikinsu take a cikin gidansu ma. Zata jira ko ma meye sai sun koma inda tafi wayo. Da wayo da dabara sai ta kawo karshen wannan alakar tun kafin rayuka su fara baci. Tana ji Radhiya tana yiwa Nene bayanin makeron da tayi da kwarkwata da suka janyo askin.
"Da kansa zai gudu makeron nan kinji 'Yar soja. Gobe da kaina zan shiga kasuwa akwai wani magani mai kyau idan nayi sa'ar haduwa da matar kanki har sai yafi na da in sha Allahu"
"Yauwa Nene" ta rungumeta tana murna.
Tuwo taje suka ci da su Zayyana. A dakin da mazan suke ma Emzee ya kai musu nasu ba kyama ko nuna gayu Awwab yaci nasa. Jakar kayansa ya duba bayan ya gama babu toothpaste ya manto shi a gidan Mama Zainab. Tun a hanya ya tuna bai damu ba tunda da niyar komawa gida suka taho. Bazai iya bacci baiyi brush ba. Ya ma tabbatar ko Emzee ya tambaya za'a bashi amma ransa yafi raya masa ya fita, fitar ma da Alheran bai gaji da ganinta ba.
"Emzee wane irin toothpaste gareku na manto nawa a Kano"
"Close up ne"
Da murna sabanin rashin jindadi da ya kamata ya nuna yace "kash bana iya amfani dashi, akwai inda zan iya siyowa nan kusa?"
"Kawo na siyo maka yanzun nan, da wane iri kake amfani?"
Shiru Awwab yayi zancen gaskiya bashi da wani zabi indai yana da kyau yana saya. Da dai sabulun wanka ne to baya tsallake pears masu mabambantan kamshi da sinadaren gyaran fata.
"Colgate nake so, amma zani da kaina kwatanta min"
Emzee da wayo ya gano Hamman nasu. Kallonsu yake daga shi har Radhiya ya ga ina za'a dire wannan abu.
"Ko in kira Adda ta raka ka ta fini sanin wurare. Idan ba'a samu a wani wuri ba baza'a rasa a wani ba"
Ido ya kafe Emzee dashi yana tunanin ko dai yaron ya fahimci yadda ya damu da ita ne. Ba ya son bawa kansa kunya a gaban yara ba. To amma meye a ciki don ya damu da ita ba kanwarsa bace? Yana can yana musu da zuciyarsa Emzee ya fice ya tafi nemanta. Tana dakin da su Mami zasu kwana sun je ita da Zayyana suna damunsa da hira. Fauziyya da Zahra suna nasu dakin kowacce tana waya.
"Adda kizo inji Hamma"
"Tayi masa me a daren nan tara saura?" Cewar Mami .
"Nima ban sani ba"
Mairama addu'a take Allah Ya daidaita kansu kada a sami matsala. Zama da Radhiya idan babu soyayya fa to akwai daru.
"Kai Hajiya yanzu bashi da ikon kiran kanwarsa?" Hajjo tayi maganar tana murmushi irin na ta fara gano manufar yaron.
"Radhiya tashi kije"
Sai dai tun suna magana Radhiya tayi gaba abinta. Nemanta suka yi suka rasa suka kwashe da dariya gabadaya.
Ta riga tayi wanka bayan magariba da suka rinka layi ita dasu Zahra kowa jiki yayi datti. Wata riga ce cotton mara nauyi take bacci da ita sai zani da ta daura da hijabi a kai. Shima Awwab can dakin da suke a bangaren samarin akwai bandaki wanda Emzee ya wanke musu shi tas suka yi wanka.
Lokacin da Awwab ya juya bai ga Emzee ba tunanin ina ya tafi ya fara yi sai gashi ya dawo yace Radhiya tana kofar gida inda ya turata yace ta jira shi. Yana fita shi da Ibrahim suka kwashe da dariya.
"Zeezee malamin soyayya. Nima na fara ganosu fa" Ibrahim yace yana mika masa hannu suka tafa.
"Idan ka sami ta ka kuma ka rasa yadda zakayi ka fada mata ka nemeni ka ga aiki da cikawa"
Daure fuska Ibrahim yayi da wasa "an fada maka na shirya ganganci ne. Idan na samu ma sai ranar kai amarya zan tura ka daukota"
"Dalili"
"Kada kaje kayi min kwace kana wannan lumshe idanun da shan kamshi tace ta fasa na fiye surutu"
Emzee sai dariya suka shiga tsokanar juna irin yadda dai matasa sa'o'insu suke yi.
Tun daga ciki ya soma hangota tana tsaye suna magana da wani da sau biyu yana ganinsa a cikin gidan. Me yiwuwa dai shima kanin Umminta ne. Sallama Awwab yayi masa suka gaisa ya shige ciki.
"Emzee yace kana kirana kuma wai a waje"
Hannuwansa ya zura a aljihu yana kallonta "aikenki zanyi dama amma na fasa dare yayi"
"Yo ni ina tsoron dare ne kamar ba soja ba"