Batuol mamman complete novel - Chapter 28
Batuol mamman complete novel Chapter 28: Batuol mamman complete novel Chapter 28. "Wwwwhat?" Ya fada idanunsa akan filon da babu kyaun gani. Bai rufe…
3,307 words
"Wwwwhat?" Ya fada idanunsa akan filon da babu kyaun gani. Bai rufe bakinsa ba mutumin nan ya tura masa filon lokaci guda kuma ya danna wukar cikin hannunsa saitin inda yake iya ganin alamun bullet din ya shiga. A maimakon kara Zayyan cizo ya kaiwa filon har hakoransa suka kusa hadewa ta ciki don azaba. Juyi biyu mutumin yayi da wukar sai ga bullet ya fado kasa.
Zayyan yayi gumi ba kadan ba idanunsa sunyi jazur sai jijiyoyin kansa da suka mike. Kwanciya yayi mutumin yana masa sannu. Babu bakin amsa sai kai yake gyadawa. Daga wannan lokacin bai kara sanin me ya faru ba sai farkawa yayi yana jin kamar ana dukan wani ga dare. A take ya wartsake ganin mutumin da ya taimaka masa ne ake yiwa dukan kawo wuka. Mantawa yayi da ciwon jikinsa ya tashi a fusace yayi kansu. Ransa ya kara baci ne da ya fahimci dalilin taimakonsa da mutumin yayi ne ake masa haka. Dukan ya koma su biyo ake yiwa amma Zayyan bai hakura ya janye jikinsa ba. Sai da suka gaji don kansu suka fita aka barsu a kasa kowanne jiki yayi laushi.
"Allah Ya isanmu tunda kunfi karfinmu....ashhh bakina" hannu ya dora daga gefen kumatunsa bangaren da hakoran suka zuba. Wahalalliyar dariya wancan mutumin yayi daga inda yake. Zayyan ya dinke fuska don ya jigata sosai yace "baka daku bane kake dariya, ni yanzu suka sake dawowa suman karya zanyi"
Dagowa mutumin yayi da kyar Zayyan sai ya koma turanci "are you okay?"
Dariya mutumin ya sake yi sai abin ya dan bashi tsoro ya ja jikinshi kadan ba dai mai matsalar kwakwalwa bane ko.
"Duk wannan dukan da muka sha ka sani dariyar dole" kallon mamaki Zayyan yayi masa yana jingina bayansa da bango ya dora da cewa "ina kallonka nayi tunanin kaima bahaushe ne"
"Kaima dan Nigeria ne?"
"Soja kamarka" yace da muryarsa da take a kausashe kamar wanda ya tashi daga bacci ko aka shake masa wuya.
Zama Zayyan ya gyara yana kallon mutumin sosai. Wannan zai girmewa Major Mustapha sai dai rashin khaki a jikinsa yasa a haka bazai iya gane mukaminsa ba.
"Lt Zayyan Muhammad Tureta, Giginya Army Barrack Sokoto"
"Colonel Nasiruddeen Aliyu, Bukavu Army Barrack Kano"
Soja ya ga ubangidansa, da ciwon hannun nasa haka Zayyan ya yunkura ya mike yana dafa bango ya dan kame jikinsa yayi masa salute.
Kai Col. Nasiruddeen ya kada yana dariya "baka daku bane shiyasa kake iya tashi, ni yanzu suka dawo cewa zanyi mace ne ni da kayan maza"
Ga wahala ga ciwo Zayyan sai da ya bushe da dariya. Sun dan zauna shiru kafin Col. Nasiruddeen ya soma bashi labarin dalilin zuwansa wurin.
Col. Nasiruddeen Aliyu mutumin karamar hukumar Wase ne ta jihar Plateau. Likita ne na sojoji wanda yake kwararren consultant a asibitin sojoji na Bukavu barrack a Kano inda yake base dinsa. Rabon wannan wahalar da kansa ya nemi a sanya sunansa cikin masu tahowa Liberia saboda burinsa na taimakawa sojojinsu. Sai aka shi turo a matsayin Cheif Medical Officer tare da wasu mutum uku su ma duka sojojin ne kuma likitoci. A lissafinsa yayi a kalla wata biyar tare da mutanen nan. Watarana sun sami rahoton rigima tsakanin sojojin kasar da abokan rikicin nasu inda mutane da yawa suka jikkata ana bukatar likitoci domin taimakon gaggawa. Shi da sauran da suke sansani guda inda yake a matsayin wurin kula da masu rauni suka dunguma da kayan kula da marasa lafiya da magunguna. Rabin tafiyar suka yi kamar yadda aka shammaci su Zayyan su ma haka aka yi musu. Bayan musayar harsashi an kashe mutum biyu cikinsu sauran kuma aka kadasu aka tafi dasu. Akan idanunsa saboda sun san shine babba a cikinsu aka rinka kashe na kasa dashi don sunki bada bayanan da ake bukata. Akwai takardu a jikinsa na bayanin sojoji masu tahowa, ranar isowarsu da ma adadin makamai, abinci da magunguna da zasu taho dashi. Tsoron kada a cutar dasu ya sanya ya fakaice su ya dunkule takardar ya cusa a bakinsa ya hadiya farat daya. Stapler din da take jiki wadda aka mannesu tare ita ce a lokacin hadiyar yana ji tana kartar masa wuya har ta wuce. Bai fahimci mugun rauni tayi masa ba sai da aka zo yi masa tambaya yana bude baki sai jini ya rinka zubowa ga uban radadi daga cikin wuyan nasa. Ya sha wahala sosai karshe muryarsa ta koma haka bayan wani lokaci. Babu ko mutum daya saura cikin abokan tafiyarsa duka an azabtar dasu an kashe. Shi kuma sun mayar dashi likitansu. Abubuwan da ya gani da idanunsa mutanen suna yiwa bayin Allah ba kadan bane, jiran amfaninsa ya kare kawai yake yi shima su kashe shi.
Zayyan ya tausaya masa shima ya fada masa yadda ya fado hannunsu. Ranar hirar da suka yi kenan kafin wahala ta sa suyi baccin dole.
Wurin da suke ba cikin daji bane hasali ma a cikin gari ne mutanen suka samu wani tsohon gini da rigima ta kori masu shi suke dabdalarsu a ciki. Tsaron da suke masa yasa har yanzu ba'a gano suna zuwa wurin ba. Sanyin asuba ne ya farkar da Zayyan ya tashi ya ga Col Nasiruddeen shima ya farka. Gefe yaja jikinsa ya bubbugi kasa ya dawo.
"Rabona da sallah tun la'asar ta ranar da muka fito"
"A haka zaka yi sallar babu alwala ko tsarki?"
"Akwai ruwa ne a kusa?" Zayyan ya tambayeshi yana leka lungunan gidan.
"A'a sai dan wanda suke kawo min tare da abinci. Idan yana da yawa dashi nake yin alwalar nayi sallolin da suka samu"
Murmushi Zayyan yayi masa "shiyasa Allah Ya hore mana taimama domin saukakawa a inda ruwa yayi karanci."
Col. Nasiruddeen bai nuna girman kai ba ya bari Zayyan ya koya masa. A zaune duka suka yi sallah jiki ya kara tsami. Zayyan ya dade yana yi saboda yasan wanda suke kansa da yawa. Addu'a yake ta yi Allah Ya tseratar dasu, Yasa su Hadir sun tsira kuma Ya maida shi ga iyalinsa.
Sai da rana tayi sosai aka miko musu plate da wani abu da Zayyan bai gane shinkafa ce, gero ko wake ba. Gashi nan dai a cure wuri guda. Col. Nasiruddeen yunwa ta galabaitar dashi ya rinka turawa kawai. Shima Zayyan sai ya ga bashi da zabin da ya wuce ya taya shi ci. Ba dadi ba dadadawa amma haka ake basu wannan abincin suna ci.
Sabo ne ya rinka shiga tsakanin wadannan bayin Allah da suke rayuwa a inda iyalansu da kowa nasu yake tunanin sun mutu. Kullum dare bayan 'yan tawayen nan sawunsu ya dauke daga dakin hirarsu sai ta karkata ga iyalansu. Dukkansu har jiran dare suke domin su saukewa juna nauyin zukatansu. Matsananciyar kewar iyalansu tana damunsu tana ci musu zukata. Yau ma bayan wata daya da kama Zayyan suna hira Col. Nasiruddeen yake cewa.
"Idan Allah Ya fitar dani daga wurin nan ina komawa abu na farko da zan fara yi shine yin ritaya. Zayyan na bar aikin soja har abada wallahi"
"Ka dena fadin haka Sir. Ni ka ga a duniya ban taba gani ko sha'awar wani aikin ba bayan shi."
"Da kuruciyarka ni kuwa girma ya soma zuwar min. Sa'annina da kannena suna kwance comfortably da iyalansa a wannan lokacin ina zaune a inda Allah kadai ya sani cikin wari da kazantar najasata. Babu wanka babu abinci mai kyau sannan duk abinda zamuyi sai dai mu yi shi a inda muke kuma mu kwana a ciki"
"Saboda abinda Allah Ya zaba maka kenan. Ya halicci mutane bayan kariyar da yake bamu da IkonSa kuma ya sanya mu garkuwa a garesu masu taimaka musu. I believe we soldiers are not made...we are born to protect (na yarda mu sojoji ba yinmu ake yi ba....haihuwar mu ake yi domin bada kariya)"
"We are special, nima na yarda...." Col. Nasiruddeen ya amsa da murmushi a fuskarsa "amma bazan cigaba da sacrificing rayuwata ga mutanen da basu san nayi musu ba. Ni da wannan aikin sai dai idan mutuwa nayi a wurin nan"
Dariya ya bawa Zayyan yadda ya hade rai da gaske ya gama da aikin soja "wannan magana fa kamar a kunnen Arifah. Nasan zata so ka cigaba da aiki muna biye daku"
Kafada ya noke kamar yaro "ko me zata yi sai dai tayi kuwa. Idan na mutu bakin aiki wa take dashi da zai kula min da ita? Burina kawai na koma gida na cigaba da bata kulawa. Shekara da shekaru ina neman haihuwa amma don ganganci ban tashi barin gida ba sai da na sami 'yar. Idan na mutu fa duka duka shekara hudu muka yi tare. Kila ma ta manta dani gabadaya"
Sai kuma ya bawa Zayyan tausayi. Col ya fada masa yadda ya kwashe shekaru shabiyar da aure tun da kuruciyarsa babu haihuwa sai akan Arifah. Yana son tilon 'yarsa kamar rai. Ranar da zai taho Liberia da kansa ya kaita makaranta nursery da take ta rinka kuka sai ta bishi. Zuciyarsa ta karye, ya baro mamanta tana nata kukan a gida itama tana yi kuma daga nan Lagos zasu wuce. Da kyar ya rarrasheta aka karbeta daga cikinsa tana ihu ya bar harabar makarantar.
Ranar da yaji labarin iyalin Zayyan ya tausaya masa matuka. Cewa yayi kada Zayyan ya kuma kiransa da wani abu da zai alakanta shi da soja sunana Baban Arifah shi kuma yana kiransa Baban Alheran.
Kwana uku a tsakani Zayyan ya soma tunanin hanyar guduwa. Sai da Col. Nasiruddeen yayi ta bashi shawarar kada ya fita ya fishi dadewa kuma shima ya gwada babu sa'a amma yaki hakura. Ta yaya zai hakura bayan kullum sai anzo an bashi wahala domin ya bada bayani shi kuma yaki. Sai ma zancen kashesu da aka fara wai zasu bar wurin an kusa gano su. Shiyasa yaga ya dace dole su nemi hanyar tsira.
Lallabawa yayi yana neman hanyar fita ya hango tawagar 'yan tawayen sun shigo wurin a guje. Masu gadin nasu da wasu kowa hankalinsa ya tashi. Cikin ikon Allah ya hango mutum biyu da kayan sojojin kasar amma umarni suke badawa a tabbatar babu wanda ya tsira a cikinsu. Su duka masu laifi.
"Shot on sight" (a harbe duk wanda aka gani) yaji ana bada umarni daga waje.
A guje ya koma ciki ya gano wani bari na katangar da ya dade yana tunanin haurawa sai kuma ya fasa ya shige inda suke ya tada Col. Nasiruddeen da yake bacci.
"Baban Arifah we need to run"
"Baban Alheran nace..."
Harbi suke ji da ihun maza da alamun guje guje. A gaggauce shima ya mike suka nufi wannan katanga. Zayyan ya haura saman ya miko hannu domin taimakawa Col. Nasiruddeen amma ya kasa saboda bashi da tsaho sosai. Ga tsira yana gani amma ya gaza. Idanunsa hawaye fal suna jin harbin yana kusanto inda suke yayi saluting Zayyan.
"It was nice meeting you Lieutenant. Take care"
Zukatansu sun karya su duka. Zayyan sai tuno Major Mustapha da dan uwansa Hadir yake yi. Soja shi kadai yasan ciwon soja. Durowa yayi kasa kafarsa tayi kara duk da haka ya kama Col. Nasiruddeen da mamaki mai tsanani ya kama shi na karamcin wannan yaro. A kafadarsa ya dora shi ya mike tsaye.
"Baban Arifah haura"
Col. Nasiruddeen ya mika hannu ya haye katangar bai sauka daya barin ba ya gano sojojin kasar da 'yan tawayen sun taho wurin gadan gadan. Su ma 'yan tawayen katangar suka zo haurawa. A gigice yace "yi sauri Zayyan"
Zayyan ya mika hannu ya hau katangar bai haura da kafafunsa ba bullet ya shiga kafadarsa. Col Nasiruddeen ya ga sanda aka yi harbin ya sa hannu zai janyo shi wani bullet din ya sami Zayyan a baya. Jikinsa ya saki duk yadda Col. Nasiruddeen yaso ko da gawarsa ce ya fitar daga wannan tsinannan gida bukata bata biya ba domin fadawa yayi baya aka cigaba da harbe harbe.
Col. Nasiruddeen ya sauka ta daya barin yasa gudu yayin da aka duba masu rai cikin 'yan tawaye harda Zayyan aka yi awon gaba dasu.
Taimako daya aka yi musu shi da sauran masu ran an cire musu bullets din jikinsu. Amma an gwada musu izaya da azaba nau'i daban daban domin su fadi inda sauran suke abu yaci tura. Sauran uban taurin kai ne yake damunsu shi kuwa Zayyan banda rashin sanin komai ya dage shi dan Nigeria ne. Da suka ga ya dage sai suka yi bincike akan unit da yace a cikinsu yake. Tashin farko akace wani mai suna Hadir Murtala ne kadai ya tsira a cikinsu tare da mutum daya daga wani unit din wato Major Mustapha.
Abu na ceton rai sauran ma kowa ya fara cewa shima wani ne baya cikin wadannan 'yan tawaye. Zasu fara dogon bincike aka kaiwa wani babban barikin sojojinsu mummunan hari wanda ya janyo gabadaya mutanen da aka kama harda 'yan wani kauye da tsautsayi ya ritsa dasu duka aka maka su a kurkuku.
Da fari Zayyan kusan hauka yayi a wurin. Tunanin iyalinsa yake yi. Mairama da Alheran da cikinta da yake tsammanin ta riga ta haife shi yanzu. A wane hali suke koma waye yake duba iyalansa? Yakan dauki tsahon lokaci yana zubar da hawaye masu zafi da kona zuciya. Uzurinsa na cewa shi ba dan tawaye bane bai karbo ba domin mutanen da ake kamowa sun hada da magidanta da matasa bisa tsautsayi. Kowa cikinsu kuma ya dage shima ba dan tawaye bane. Sai ake rasa gane waye mai gaskiya da makaryaci. Dadin matsakar kasar babu zaman lafiyar da zai bada damar a bata lokaci wurin sauraren korafinsu. A irin haka sojojin kasashe da dama suke riskar kawunansu a kurkuku daga zuwa kai dauki ga kasashen da suke cikin rikici.
Sannu a hankali ya karbi kaddararsa da hannu bibbiyu ya fawwalawa Allah lamuransa. Baya shiga harkar kowa a wurin sai ma shi da akan sami masu shiga tasa. Sai ayi masa duka bai ko daga yatsa. Rayuwarsa ta kuntata komai ya fice masa a rai. Daga baya ne ya sake rungumar addini fiye da baya har kusan kowa ya sallama masa hadda wadanda ba musulman ba kuwa. Zaman lafiyarsa da yanayin mu'amala yasa ya shiga zukatan jama'ar wurin. Zayyan Muhammad Tureta tun asalinsa mutum ne mai shiga rai shiyasa a nan din ma ya zama na kowa. Babu wanda zai yi yunkurin taka Zayyan wasu basu saita masa zama ba.
Col. Nasiruddeen yayi nasarar komawa gida ga iyalinsa. Satinsa guda da komawa yasa aka binciko masa barikin su Zayyan. Daga can ya sami kwatancen gidan iyayensa. Da kansa yaje Sakkwato ba sako ba har kofar gidansu. Da yake wahala bata yankewa su Mairamu ba a wannan lokaci da yasa ayi masa sallama da dan uwan Zayyan ba wanda ya fito sai Maikudi. Ya ga mutum a fige saboda tsabar wahala sai hanci dan firit. Yanayinsa gabadaya kama yayi masa da mutanen Nijar yayi zaton aiko shi akayi saboda basu yarda da bayanin da yayi musu ba. Rufe ido yayi ya maimaita masa cewa Mairama ta haifi da ba rai, ita da 'yarta kuma sunyi hatsari sun mutu. Col. Nasiruddeen yaji babu dadi jikinsa yayi mugun sanyi ya koma Jos wurin iyalinsa cike da damuwa. Zayyan ya rasu a dalilin ceton ransa kuma iyalansa ma duka babu su. A satin yaje ya kai takardarsa ta barin aiki. A wurinsa rayuwar soja ba tasa bace. Asibiti ya koma neman aiki sai dai lokuta da dama idan ya ga yawaitar jini musamman idan hatsari ne jikinsa ya rinka rawa kenan. Likita da tsoron jini aiki bazai taba yiwuwa ba bisa dole ya hakura ya tsunduma cikin harkar siyasa ka'in da na'in.
***********
SABON SHAFI [5/22, 10:52 PM] Sis Ruky: "Kukan ne har yanzu baki dena ba?" Yace a hankali yana jin farinciki na shigarsa saboda jin muryarta.
"Ni ba kuka nake ba"
"Shine daga tashinki kika soma damun mutane da waya ina jin ko wanka bakiyi ba"
"Ba kune ba sai kuka tafi bakuyi min sallama ba"
Siririyar dariya taji yayi "Silly girl. Cewa zakiyi nine na tafi banyi miki sallama ba ko ba haka kike son fada ba zaki basar?"
"Inji wa? Ni da munyi fada da kai"
"Ke abu baya wucewa a wurinki ne? Kuma ba na goge ba. Wai ma in tambayeki fushin na meye?"
Daburcewa tayi ta rasa me zata ce masa har ya sake maimaita tambayar "uhmm to ai zaka janyo mana ace yayanmu ne kai kuma kaje ana baka abu a baki"
"Ba ma ki da kunya, kema fa na baki har sau biyu"
"To ai ni kanwarka ce" tayi maganar da wasiwasin iya matsayin da take so daga gareshi kenan ko kuwa.
"Tunda dai bakya so na dena. Da Ghazalatu kadai zamu rinka yi"
Kit ta kashe wayar zuciyarta na tafarfasa. Ai sai yaje su karata ita dama meye ya dame ta dasu.
Kallon wayar hannunsa yayi yana tambayar kansa meye tsakaninsa sa Alheran. Ta wuce kanwa shi kansa ya sani amincewa ta rage. Lokaci yayi da zai dena yaudarar kansa don bazai iya ba. Bashi da karfin zuciyar jurewa. Kallo daya yayi mata ranar da ya fara ganinta a gidan Mama aka kwance duk wani notin jikinsa. Sake kiranta yayi wayar na hannunta dama tana nadamar kashewar da tayi kada yaki sake kira.
"Ke da na hana tashi idan muna magana shine kike katse min waya."
Baki a kumbure tana fushi tace "kayi hakuri"
"Bakin naki zan like tunda baya son yi min magana bashi da amfani"
"Ashe rabon wani ma zai nemi nasa ya rasa ne" tace tana dariya da tayi tunanin abinda ta taba son yiwa Gwaggonta Salame wata rana da taji ta zagi Umminta. Wurin Hanne taje lokacin tana auren Malamijo da niyar karbar super glue ta saka mata a kunu tayi rashin sa'a ya kare.
Jin kansa yake cikin nishadi yace "Ki gwada ki gani idan Ghazalatu bata zane min ke ba"
" 'Yar soja ce fa Hamma ko ka manta ne"
"Na dai ce bazaki yi sojan nan ba kuma kin yarda"
Bata sanin tana shagwaba sai maganarta ta fito kamar yanzu da tace "to gaskiya ka dena cewa bakina bashi da amfani"
Fuskarta kawai yake haskowa tana magana. A kasalance yace "fada min amfaninsa guda daya sai na kyale shi"
"Shan sweet in rage maka" tace da sauri ta dora hannu akan labbanta ta rufe bakin tana jin matsananciyar kunyar kalamanta. A karo na biyu ta sake katse kiran tare da kashe wayar. Kan katifar ta hau tana shure-shuren kafafu kamar zata yi kuka tana mai kunyar maganar da tayi da yanayin da tayita cikin wata irin siga mai tsayawa a rai.
Wani irin dumi yake ji yana ratsa shi tun daga tsakiyar kansa har kafa. Ya runtse idanunsa yana hangota cikin zuciyarsa. Abin takaici bashi da hotonta ko daya a wayarsa. Bazai iya sati biyu bai ganta ba shiyasa ya fara neman abinda zai fake dashi ya koma Sumaila cikin kwanaki kadan.
**********
Mal Aminu yayi bakinciki mara misaltuwa da jin yadda Maikudi ya yi da dukiyar marayu bayan Captain Onomza ya fadawa Major.
Gidan Zayyan na Kano yana nan tsahon shekaru ya zuba 'yan haya a cikinsa. Kudin da ya rinka aikowa da kudin hayar dasu ya tamfatsa katon gida mai bene a nan Sakkwaton a cikin wata sabuwar unguwa da yanzu ta fara cika. Bai kuma yi jayayya ba saboda dukan da yaci ya fada musu cewa yan uwan Zayyan na Nijar sun dauka iyalinsa duka sun rasu kamar yadda ya fada musu. Mal Aminu jikin girma bazai iya doguwar tafiya ba amma ya baiwa Major cikakken sunan gidan da zai nema da garin da suke.
Harka ta zamani da kwarewa Major ya bayar da cigiyarsu ta hanyar amfani da sojoji ta bangaren Captain Onomza. Zasu koma Katsina su bayar da sati daya ko biyu idan babu wata nasara da kansa zai je Nijar din nemansu. Ko a haka baya jin ya biya Zayyan fansar ransa.
**********