Kenza eBookz

Batuol mamman complete novel - Chapter 40

Batuol mamman complete novel - Chapter 40

Batuol mamman complete novel Chapter 40: Batuol mamman complete novel Chapter 40. Fadan su Farida akan daukar yara har waje Radhiya tana alkalanci. Jeans…

3,301 words

Fadan su Farida akan daukar yara har waje Radhiya tana alkalanci. Jeans ne baki a jikinta da top sai da dora hijab mai hannu da ya wuce gwiwarta kadan. Suna shigowa ta koma tana sulhun daga zaune.

Halifa ya kalleta ya kara duka akan idon Awwab yana mamakin yadda ta zama. Da kuruciya basa shiri saboda Salame ta koya masa kinsu haka itama bata son shi tunda dan Gwaggo Salame ne wadda bata son Umminta.

"Radhiya bazaki gaisheni ba" yace bayan ya zauna.

Murmushi tayi tace "Ka rainani Halifa ko don kana ganin ka zama basamude"

Yadda take magana ya sashi dariya "ance Emzee yana NDA ko, ke kuma me kike yi yanzu? By the way you look great and ...beautiful"

Turnuku, ya kai Awwab wuya Yousuf ya koma kallon Awwab din yana dariyar mugunta.

"Thanks" tace da murmushinta.

Bai da son hayaniya amma yaji yana son tsawaita hira da 'yar uwar tasa da ya jima basu hadu ba.

"Da gaske fa da a waje muka hadu bazan ganeki ba. Nafi gane wannan terror din abokiyar fadana...tsoronki fa nake ji da"

Fauziyya sai ta tattara 'yan matan da yaransu suka koma daki saboda kada Awwab ya fashe musu a wurin. Da Halifa zai ga irin kallon da yake masa kila da yayi shiru. Radhiya ta gani sarai ko zama ya kasa yi amma ta biye masa.

"Ta da dinma tana nan sai dai idan ba'a tabota ba"

"Halifa mu bazaka yi hirar damu bane sai 'yar uwarka?" Yousuf yace domin ya kawo karshen hirar. A fusace Awwab ya juya ya fita. Kalmar great and beautiful ta tsaya masa. Jikin mota yaje ya tsaya sai ya sami kansa da kiran layinta.

Su uku suka rage a falon saboda Zahra tana can dakin Awwab da mijinta tunda ya leko suka fice. Yanzu hirar da Yousuf ake yinta yawanci akan makarantar da ya gama a Dubai da kuma wadda take yi yanzu.

Allah Yasa wayar na gefenta ta ga kiran ta dauka.

"Fito" kawai yace mata ya kashe.

Tashi tayi tsam ta saka wasu flat shoes dinta masu kyau ta fito wajen ta hango shi zaune cikin mota. Kallo daya tayi masa tasan ransa ne a bace sai taji babu dadi kuma.

"Hamma" tace a dan tsorace.

"Get in" ya umarceta. Bata ce komai ba ta shiga gaban ya daga waya ya kira Ummi yace mata Alheran zata raka shi siyan magani ba jimawa zasu yi ba.

"Hamma baka da lafiya ne?" Idonsa akan titi yaki kulata.

"Ko mu koma gida a taho da namiji ka ga idan lalurar tayi tsanani sai an daukeka ni ba karfi gareni ba Allah."

Bai san lokacin da ya soma dariya ba tun yana yi a hankali har ta fito.

"Yanzu fushin ma bazaki bari nayi ba?"

"Fushin me?" Tace kamar bata sani ba

Murmushi yayi "Ya wuce"

Daidai nan ya wuce wani kanti ta hango katan din lemuka an jere a waje harda na maltina. Kwadayin ne ya motsa ta dube shi.

"Hammaaaa" muryarta ta doki kunnensa da shagwabarta da take bashi sha'awa yanzu.

"Uhmm"

"Ka saya min maltina don Allah yanzu ka wuce shop din a can" ta nuna da hannu.

"Kinyi dinner ne?"

"Sai anjima"

"Bazan saya ba, na kula ba kya son cin abinci kema"

Sake narke masa tayi sai da ya dage ya iya controlling kansa daga barin janyota jikinsa.

"Hamma manaaa..."

Bashi da zabin da ya wuce juya kan motar ya barta a mota yaje ya siyo. Katan uku aka saka masa a booth sai guda hudu masu sanyi a ledar hannunsa. Yana zama ya mika mata ta balle saman gwangwanin tana sha tana lumshe idanu.

Rabi tasha ta mika masa ya karba sai da ya kalleta ya dora bakinsa a kai ta kawar da kanta gefe.

"Tell me about your project tunda jira kike na roka"

Sun kusa gida lokacin ta soma yi masa bayani dalla dalla kamar ba Radhiyan da ya sani ba. Shirmen yana nan amma ta fannin karatun bata wasa. Wannan ita ce Alheran din da ya fada soyayyarta.

"Impressive. I am proud of you. Amma why mass comm? Meyasa baki zabi wani course din ba?" Ya tambayeta bayan yayi parking din motar.

Gwangwani na biyu take shirin budewa ya karba ya bude mata. Kafin ta karba ta nuna masa wannan zoben nasa.

"Ka ga wanda ya zaba min nan. A hannuna sunansa Awwab shi yace yafi son nayi mass comm"

Duk kalma daya dake fita daga bakinta tana kara hura masa wutar soyayyarta ne. Bazai sake yarda da wasu dalilai ba da zasu sa yaki aurenta wannan karon. Baya ma tunanin komawarta school babu igiyoyinsa a kanta. So yake yaje ya kammala abinda Mama ta katse masa ya dawo ayi komai a gama kafin ya koma aiki.

Kwantar da kansa yayi baya a jikin seat yace "Kin shirya aurensa yanzu"

"A'a"

"Reason?"

"Sai ya dena fushi dani"

Gwangwanin hannunta da ya bude mata ta mika masa "rage min".

Kurba daya yayi ya bata ta dauki ledar ta fita batare da ta sake cewa komai ba. Yana kallonta har ta shiga gida ya fiddo wayarsa da niyar kiranta ya fallasa mata duka sirrukan zuciyarsa ya ga kira da bakuwar namba. Yana karawa a kunnensa ya gane muryar mai maganar mahaifin Arifah ne.

Tambayar farko da ya fara yi masa shine yana son sanin idan shi kadai ne a inda yake. Idan ba shi kadai bane kuma ya tashi ya kebe akwai maganar da yake so suyi.

Awwab ya tabbatar masa da cewa shi kadai ne sannan yace masa yana bukatar passport dinsa a daren saboda gobe da sassafe za'a zo a karba. Dakinsa yaje da sauri ya dauko yanayin muryar Excellency yasa shi jin cewa akwai abinda yake faruwa. Bai sanar da kowa ina ya tafi ba yaje gidan wanda kamar jiransa suke masu gadin aka bude masa gate.

Wani falo PA dinsa ya jagorance shi suka je ya same shi tare da bakon da bai sani ba. Duk da haka ya mika masa hannu suka gaisa bayan ya gaisa da gwamnan. Da turanci domin kowa ya fahimta ya soma magana.

"Awwab wannan sunansa Chibuzor Kalu"

Murmushi ya sake yiwa mutumin wanda ya dauke a lokacin da yaji Excellency ya fara fada masa abinda ya kawo Chibuzor garesu.

"Zayyan is alive and in prison"

Mikewa yayi tsaye yaji kansa ya kulle. Gaban Chibuzor yaje ta idanunsa suna nuni da rauni matuka "is this some kind of a joke?" [5/22, 11:03 PM] Sis Ruky: "Nima haka nayi tunani. Zauna Awwab. Duka wani protocol da ya kamata nabi domin sanin gaskiya nabi. Yanzu haka ina jiran kira daga Mr President ya bamu go ahead mu nemi ganawa da gwamnatin kasar domin a sake shi"

"Kana nufin Babana Zayyan yana da rai duka tsahon shekarun nan a prison" hawaye ne mai zafi ya zubo masa baiyi yunkurin dakatar dashi ba.

Dukkan bayanai Excellency da kansa yayi masa yaci kuka tamkar kankanin yaro. Zancen da girma kuma da nauyi. Gashi yace yayi shiru har su dawo saboda yana tsoron sakawa iyalinsa rai da abinda ba gaskiya ba.

"Ka samo min hotonsa, na matarsa dana 'ya'yansa. Idan da hali harda copy na national identity card dinsu ko international passport domin mu tabbatar musu bashi da alaka da Liberia"

Kamar anyi masa duka haka ya koma gida zuciyarsa tana ta bugu da karfi. Zahra bata dakinsa a nan ya kwana sai dai ko digo bai iya runtsawa ba. Kwana yayi yana tunanin ta yadda zai samo hotunan da ake bukata. Duk da yace kada kowa yaji dole ne ya nemi mai taya shi. Jira yayi sai da su Yousuf da Tante suka tafi airport zasu wuce Nijar, shi dai bai bisu ba su Radhiya ne suka tafi rakiya ya shiga bangaren Mama. Baba Hadir yana falo sai ya wayance da ganin Daadaa ya tafi. Mintu talatin bai cika ba ya kuma dawowa har yanzu yana falon ita ta tashi. Zama yayi kamar akan kaya yana jiran Baba Hadir ya fita ko ya koma daki shiru. Mama tun da ta dawo take karantarsa daga karshe tace wa mijinta ya basu wuri zasu gana da danta ta ga alama son aure yake yi.

Baba Hadir ya girgiza hannuwa wai babu ruwansa ya tashi ya shiga ciki. Sai kuma ya kasa cewa komai.

"Awwab ka fara bani tsoro. Akwai abinda ke damunka fa"

Siririn hawaye ta gani ya ziraro daga idonsa ta soma tafa hannuwa "Radhiya ta sake cewa bata shirya auren bane?"

"Ni ai na shirya so bana bukatar amincewarta" yace yana kakalo murmushi.

"Good, me kake boye min?"

Yanayin da ya shiga da Excellency yake masa bayani har tafi shi. Zainab kuka take rikewa Awwab yana bata baki da ta daure saboda kada a gane. Abubuwan da yake bukata ya zayyane mata tace zata yi masa kokari zuwa dare. Daurewa kawai ta rinka yi kada ayi saurin ganota musamman da Ibrahim da Emzee zasu dawo yau gidan zai kara cika.

Dakinsu ta shiga cikin kayan Baba Hadir ta dukufa bincike. Bata yi mai yawa ba ta samo hotunan Zayyan da khakinsa shi da Hadir. Da wayo da dabara tasa Radhiya ta kawo mata passport dinta wai zata gani. Hadawa tayi da hotunan ta bawa Awwab cikin wata leda wai sako ne. Yana karba yaje yayi photocopy na passport din ya dawo mata dashi. Sauran hotunan ta waya ta tura masa duka yayi printing ya kaiwa Excellency. A hanyarsa ta komawa gida ya kira shi ya sanar dashi shugaban kasa da kansa ya nemi shugaban kasar Liberia zai bada umarnin a duba masa mai wannan suna a prison din.

Wannan dare ma bacci barawo da kyar ya dauki Awwab, Mama Zainab da Col. Nasiruddeen. Dare ne mai tsayi a garesu wanda a safiyarsa ne zasu ji dahir. Ayi ba ayi ba sai gabanin magariba wayar Excellency ta shigowa Awwab.

"Karfe tara na safe zamu tashi gobe, Zayyan has been found"

"Alhamdulillah" Awwab yace idanunsa na cika da kwalla. Baya jin komai don yayi kuka saboda abin kukan ne ya same su.

A daren ya sanar da su Mami tafiyar gaggawa ta kama shi Lagos wai kamfanin jirgin da yake aiki zasu gabatar da wani shiri. Ita kadai ce karyar da ya iya nema ya fada musu. Rashin zamansa a gida yasa bashi da lokacin neman Radhiya abin har ya soma damunta. Tun daren da akayi masa wayar sai yau yaje wurin Ummi saboda yana gudun ta fahimci wani abu a tare dashi kamar yadda Mama tayi. Zancen tafiyar yayi mata tayi masa fatan alkhairi. Yaso ganin Radhiya sai dai tayi bacci da wuri period pain ya kwantar da ita. Da safe kafin ta tashi ya tafi sai labari taji wai ya tafi Lagos. Fada ta soma yiwa kanta na saurin bada kai da taso yi bata san babban aikin da yasa a gaba domin iyalansu gabadaya ba.

Da yaje airport yayi mamakin ganin official plane din shugaban kasa aka bayar dungurungum domin dauko Lt Zayyan Tureta. Su tara ne duka a tawagar. Shi, gwamnan Plateau, Deputy chief of army staff, Chibuzor da wasu sojoji guda biyar. Gani yake kamar da shi yake tuka jirgin sai yafi haka gudu amma sannu sannu bata hana zuwa sai gasu sun sauka a filin jirgin Monrovia babban birnin kasar.

Su ma sojoji suka turo domin daukarsu ana musu zancen tafiya hotel Excellency yace ko ruwa bazai iya sha ba sai ya ga Zayyan tare dasu.

**********

Kararrawa aka buga lokacin cin abincin dare yayi 'yan prison din suka soma fitowa daga dakunansu da aka bude. Kusan kullum cin abincin tamkar yaki ake yinsa kowa na sauri ya sami abin arziki.

Tafiyar nan tasa da dogayen kafafunsa yake yi cikin nutsuwa ya isa layin ya tsaya kenan wani kato yazo ya sha gabansa. Sai ya ja baya ya bashi wuri saboda gudun rigima. Sati uku da kwanaki da tafiyar Chibuzor dan guntun hope din da yake dashi gabadaya ya tafi. Fadawa kansa yake yi ya cigaba da hakuri da kaddarar rayuwarsa me yiwuwa shi da iyalinsa sai a lahira. Shi da kasarsa kuma sunyi bankwana kenan. Rikici ne ya kaure daga gaban inda ake rabon abincin garin dambe aka zubar da kulolin abincin a kasa. Mutane kuwa suka dira akansa suna wawaso ga gandirobobi suna ta kokarin raba su.

Yau ma bashi da abinci kenan zaiyi kwanan yunwa ya juya a nutse zai koma dakinsu. Da rana wani tsoho ya barwa nasa saboda ya taho zai zauna irin shakiyan nan wani yasa masa kafa yayi tuntube ya fadi. Yanzu kuma abincin duka an zubar. Ya kusa isa dakinsu yaji da karfi ance.

"LIEUTENANT ZAYYAN MUHAMMAD TURETA"

Tunda ya shiga kurkukun nan sunansa 3810 sai ko mutanen da suka san sunansa kalilan amma su dinma numbar tasa suke kira. Gabansa ne yayi mugun faduwa ya juyo da sauri. Babban prison Warden dinne da kansa ya shigo wurin. Wannan salon tafiyar tasa da shi kadai ya iya kayarsa yayi zuwa gaban mutumin. Ga mamakinsa sai ya ga ya cire hularsa ya maketa a kasan hannu daya sannan ya gyara tsayuwa ya sara masa.

Habawa sai idanu suka tattaru a kansu shi ma sai yayi saluting mutumin yana jin idonsa ya soma ruwa domin hasken da ya fara hangowa na rayuwar 'yanci

"This way Sir" Chief Warden yace masa ya bi bayansa. Sun fara tafiya ya juya ya kalli prison din da jama'ar cikinsa sai ya tsaya at attention ya kame yayi saluting dinsu. Da yawansu su ma sai suka yi masa wadanda suka taba jin cewa soja ne suna taya shi murna.

Wani office aka kaishi Chief Warden ya bashi takarda ya saka hannu a kai sannan ya kuma gyara tsayuwa.

"Kai jarumi ne da ban taba ji ko ganin kamarsa ba. Kasarka bata san kana raye ba tsahon shekaru ashirin da biyu sai yau zaka koma gida. Ba kai nake tausayi ba sai ire irenka da dama da suke da rai a hannun abokan gaba ko kurkuku irin wannan batare da an sani ba. Goodbye Lieutenant"

Musabaha suka yi sannan ya kuma nuna masa kofa suka fito tare. Wani gate da bai raba sanin akwai shi ba duk tsayin zamansa a wurin suka bi sai ga motoci biyar a jere na Nigerian Embassy dake Liberia a baya kuma wasu uku ne na sojojin kasar.

Motar tsakiya aka nuna masa ya shiga yana jin kansa kamar a ire iren mafarkan da yake yi na komawa gida. Cikinta ma sojoji ne da sai suka yi saluting dinsa suka shiga aka tayar. Jiniya ce tun daga prison din har babban ofishin jakadancin Nigeria dake Liberia.

Awwab ya kasa zaune ya kasa tsaye haka ma Excellency. Duka a waje suke daidai kofar shiga tare da Ambasadan suna tsaye zugar motocin nan suka jeru a gabansu.

Kafin ya yunkura an bude masa kofa ya sako kafarsa waje sanye da takalmin roba da ya mutu murus. Kayan jikinsa a kode suke sosai. Fatarsa kuwa bai san cewa ta shiga wani yanayi ba sai da ya ga mutanen dake tsaye a wurin sun zuba masa ido.

"Uncle" yaji ance da muryar da ya sani. Chibuzor ne ya taho wurinsa da hawaye yabe yabe a fuska. Zayyan ya rungume shi.

"My son I owe you my life"

"And I owe you mine" yaji wani ya fada daga bayansa.

Sannu a hankali ya juya yana kallon mutumin dan lukuti ga tumbi amma komai nasa yana nuni da cewa ba karamin mutum bane. Ina yasan fuskar nan yake ta tunani.

"Baban Alheran kayi hakuri banzo da wuri ba"

Zuciyarsa ta nemi bugawa don bai manta mutumin da yake kiransa da wannan sunan ba. Sai yanzu yaso ganin kama. Bakinsa yana rawa yace "Baban Arifah? Col. Nasiruddeen?"

Rungume shi yayi suka fashe da kuka a tare mutane na kallonsu wasu suna yi.

Ga Awwab kuwa babu inda baya rawa a jikinsa. A yau ya yarda soja daban namiji daban. Duk yadda yake son ya dake kwanansa nawa yana kuka saboda jin cewa Babansa Zayyan yana nan amma babu tabbas sai ido ya gani. Shekarun da yawa amma tabbas shine wannan mutumin da ya ga duniya kuma duniya ta ganshi.

Muryarsa tana rawa yace "kaine Tureta?" Yadda ya taba yi masa farkon haduwarsu.

Zayyan ya dago kansa daga kafadar Excellency yayi masa murmushi "nine yaro. Ka sanni ne?"

Tsigar jikin Awwab har tashi tayi a lokacin da ya kamo hannuwan Zayyan duka biyun "sunana Muhammad Awwab Mustapha...ka tuna ni?" Ya kare tambayar da kuka.

Wasu sababbin hawayen suka sauko daga idanun Zayyan jikinsa shima yana rawa ya sanya hannuwansa biyu a gefen kumatun Awwab da suke tsayi kusan daya.

"Awwab din Mairamata?"

Awwab ya gyada kai nasa hawayen suna gudu kamar famfo baya tunanin yin komai domin tsayar dasu.

"Major da Hadir fa?"

"Suna cikin koshin lafiya"

"Mairama?"

"Na barota lafiya"

"Alheran dinka?"

"Tana jiran Daadaa yazo ya aura mata Awwab" yace yana murmushi mai hade da kuka. Zayyan ma sai ya fadada murmushinsa.

"Cikin jikin Umminka?"

"Alive and well sai munje gida zaka ga ko mene"

"Awwab?"

"Daadaa"

"Nayi kewarku, nayi kuka, nayi hakuri nayi hauka duka a rashin sanin makomar rayuwata. Ku kaini gida...ku kaini wurin iyalina"

Kankameshi Awwab yayi suna kuka sosai abin tausayi da tsinka zuciya.

[5/22, 11:03 PM] Sis Ruky: *SAKAMAKON ALKHAIRI...ALKHAIRI NE*

Awwani hudu bayan dauko shi Awwab da Excellency suka saka Zayyan a tsakiyarsu suna zaune a cikin jirgi domin komawa Nigeria. Sai da aka hadu so da takardun neman afuwa kuma mataimakin shugaban kasa yace zasu zo Nigeria officially bada hakuri. Sun kama hanya cikinsu babu wanda zai iya bacci a wannan kasar idan basu ga kafafun Zayyan sun sauka a kasar haihuwarsa ba. Babu wanda ya damu da wata tafiyar dare ko nisa. A lokacin da suke hawa jirgin Zayyan ji yake kamar ana zare masa wata kaya mai tsini daga cikin zuciyarsa.

"Baban Alheran" Excellency ya kira shi ganin idanunsa sun kasa daina zubar hawaye. Kukansa kuwa kara raunana Awwab yake yi suke ta yi tare. Kallonsa yayi suka hada ido yaji mugun tausayinsa ya mamaye masa zuciya.

Har yanzu kyakkyawan mutum ne da ya wadatu da arzikin kyakkyawar zuciya, amma yasha wahalar rayuwa fiye da zato da tsammani. Ciwon da yake tattare da rabuwa yafi karfi a gareshi domin shi yasan ya baro iyalinsa da rai ya azabtu da begen sake ganinsu sabanin su da suka dangana saboda tunanin ya rasu. Akwai lokutan da yake jin kamar zai zauce saboda kewarsu. Wani zubin kuma hakuri yake sakawa ransa, wasu lokutan kuma yayi kuka har sai yaji kamar bashi da sauran hawaye.

"Baban Alheran kayi hakuri shine abinda zanyi ta fada maka har muje gida. Ni dasu Hadir da Mustapha duka zaton mutuwa muka yi maka"

"Ka dena bani hakuri domin Allah Ya riga Ya warware min ciwon da yake raina. Ku bani labarin me ya faru daku da matata"

"Bazaka jira mu koma ka nutsu ka huta ba?"

"Labarin ne kadai zai sa na cigaba da dauriya har mu sauka. Idan ban manta ba ana cewa aski idan yazo gaban goshi..." yayi murmushi.

A takaice Excellency ya labarta masa dalilin tunaninsu na cewa ya rasu, ya kare da cewa "sauran bayani zaka ji idan mun isa gida ka huta yanzu"

Ruwa da abinci aka kawo musu amma shine ya fara daga hannu domin dakatar da air hostess din daga ajiye masa.

"Daadaa kaci wani abu mana. Kafin mu taho ma ko ruwa baka sha ba duk wannan lokacin da aka bata" Awwab yace yana rokonsa.

Murmushi yayi sai ka rantse Emzee ne a wurin yace "babu abinda zan sake ci ko sha sai naje gida in sha Allahu Mairama ta bani."

Yana so ya tambayi Awwab ko tayi wani auren amma baya tunanin zuciyarsa zata iya daukan nauyi irin wannan komai kankantarsa a yanayin da yake ciki shiyasa ya ja bakinsa yayi shiru suka cigaba da tafiya kowa yana murmushin farinciki da jindadi.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull