Batuol mamman complete novel - Chapter 62
Batuol mamman complete novel Chapter 62: Batuol mamman complete novel Chapter 62. Bakin mota suka raka shi batare da ya sake neman wayar Radhiya ba ya…
3,361 words
Bakin mota suka raka shi batare da ya sake neman wayar Radhiya ba ya dauki hanya. Karfe uku yana cikin garin Abuja saboda ko mai bai tsaya sha ba yayi full tank a Katsina. Gidansu ya fara zuwa amma wurin Mama ya shiga. Bata nan sai Baba Hadir shi kadai wai Ummi tazo sun koma can gidan tare. Abinci suka ci tare da sallah sannan ya je yayi wanka ya tafi ganin Radhiya. Kananan kaya ya saka bakin jeans da bakar shirt mai maballai da collar ya dora rigar sanyi mai v-neck cream ta saman wuyan ya lankwasa kwalar shirt din ciki. Ba karamin kyau yayi ba yana ta kamshi ya shige mota.
Yana shiga ya tarar da motar Ibrahim dama Baba Hadir ya fada masa can suka tafi duba Radhiya. Ummi da Mama sunyi mamakin ganinsa sosai ya sunkuyar da kai da Mama ta shiga tsokanarsa wai amarya tayi kira.
Murmushi kawai yake yi Ummi ta tura mai aikinsu kiran Radhiya tasa Rahima kawo masa abinci. Bata yarda ba da yace a koshe yake sai da ya tabbatar musu a gidan Mama yaci.
Mai aikin ce ta dawo tace wai bacci Radhiya take yi. Ba dai haka yaso ba kuma fuskarsa ta nuna. Mama ta nuna masa dakin da take ciki a kasa inda suke gyaran jiki. Yau ba'ayi ba amma saboda rashin kwarin jiki can ta shiga bayan an matsa mata ta sauko dazu.
"Shiga tana ciki ka samu ka tursasata cin abinci me yiwuwa kai taji maganarka"
Ummi ta kalla ganin ko motsi baiyi ba "muje sama mu karasa don naga alama dan naki ba tashi zaiyi ba"
Awwab kunya Ummi kunya. Sai da su ka shige sannan ya tashi da sauri ya tafi dakin da aka nuna masa. Kwankwasawa yayi tana kwance da waya a hannu r muryar Hammanta amma kishi ya hanata kunna waya ta kira.
Tura kofar yayi a hankali yaji tace "Rahima karo min bargo a sama dakin nan akwai sanyi sosai"
"Gani ki yafa"
Muryarsa ce tazo mata a bazata ta dago kai ta tabbatar shi din ne yana tsaye da ga bakin kofa sai kawai ta ja bargo ta rufe har kanta. Murmushi Awwab yayi ya zauna a gefen gado sannan a hankali ya zura hannunsa ciki ya kamo nata tana ta kokarin kwacewa ya rike.
"Idan baki nutsu ba zanyi miki rawar 'yar amana"
Dena motsin tayi yana jiyo sautin dariyarta a hankali yayin da take jin dumin hannunsa yana ratsa ta. Shiru su ka yi duka su biyun na dan lokaci sai daga baya ya soma magana. Hakuri ya bata tare da bayanin ya akayi ma taji shi tare da Ghazalatu a lokacin.
"Ko kinfi so ace mun dena zumunci da 'yan uwana?" Tana cikin bargon ta girgiza kai yace yana dariya "ashe ma zakiyi saurin hakura duk kika tayar min da hankali"
Gefen fuskarta kadan ta bude amma bata iya kallon idanunsa ba tace "ba hakura nayi ba ka tashi kayi min rawar"
"Sai dai muyi tare" yace yana kashe mata ido.
Sake rufa tayi ya kwanto a jikinta tuni ta fara rawar jiki kuwa "ko ki bude in ganki tunda dubiya nazo ko na shigo ta nan" yace yana dan matsa hannunta da ya rike ta kasan bargon. Ja taji yayi ta bude kanta da sauri.
A kunyace ta ture bargon tana sanye da dogon skirt baki sai rigar sanyi da ta kamata mai high neck.
"Give me a hug" yace yana ware hannuwansa. Bata motsa ba sai kai da ta sunkuyar yace "now please" da wata irin murya. Ji yake kamar ya janyo kwanakin nan su kare da wuri ace an gama biki kowa ya huta.
Ba yadda ta iya ta dan matso kadan shi kuwa ya janyota jikinsa ya rungume yana shafa kanta.
"I love you Schatzi ki dena kokwonto akan hakan. Bazan taba yin abu don na bata miki rai ina sane ba"
Dama can bata gama kukanta ba sai yanzu ta sami damar yi masa yana ta rarrashi.
"Ni dai ko za ka yi min kishiya bazan zauna gida daya da ita ba"
Kanta ya dago yana murmushi "saboda me?"
Shagwabe masa tayi "Ni dai kawai bana so"
Goshinta ya yiwa kiss ta runtse idanu yace "saboda kina tunanin zanyi mata wannan?" Ya koma kumatunta hagu da dama "da wannan?" Sai kan hancinta "da wannan ma?"
"Ni dai ban ce ba"
"Ni nace baby...I miss you so much" yace yana kallon fuskarta idonta a rufe ya soma zana mata lips da karamin yatsansa "yau baki sa janbaki bane?"
Tamkar ta nutse a cikin gadon ta kawar da fuskarta "bani da lafiya fa"
Idanunsa a kanta yace "Ni kuma na taho all the way from Katsina shan janbaki ne fa"
Ciwo dama ya riga ya warke tunda ya iso da sauri ta tashi yana kiranta wai ko vaseline ne ta shafa ta bashi ya shanye ta gudu tana dariya. Bata sake bari sun kebe su kadai ba sai da zai tafi gida tayi masa sallama yana ta korafin bai sha janbaki ba tana dariya. Kafin dare ta ware tas sai karadi da dariyarta da ta cika mutane dashi. Zayyan yana ganin chanjin da ta samu kuma an fada masa Awwab yazo yayi dariya wai dama can ciwon soyayya ne.
"To saura ka fada a gabansu" Ummi tace fuska a daure don kada ya saka ta dariya.
Alamun zip ya yiwa bakinsa sannan ya tashi yana nade hannun rigar baccinsa "bari na gani ko ina da sauran karfi"
Mairama bata ankara ba ya dagata ya dire akan gado. Tana tashi ya danneta yana dariya "kwanta bitar karatunmu zamuyi muma"
**********
Yau litinin ya sati na gaba ya kamata a fara biki gidan gabadaya suka tafi Sumaila tare da Mama, Zayyan kuma ya tafi Sakkwato. Sun isa gidan na Malamijo ya cika da 'yan uwa da abokan arziki. Su Innawuro daga rugar Barkindo, Nene Marka da kishiyarta tare da 'ya'yab kishiyar da jikoki sai kuma 'yan uwan Malamijo da nasu iyalan. Ranar laraba zasu yi Kamu saboda da yawansu ba iya zuwa Abuja zasu yi ba. Emzee yana makaranta har lokacin sai wani satin zai taho. Sunyi waya da Rahima ta fada masa sun taho Sumaila sai dai har yau bai kawo komai ba. Sallah kawai Rahiman tayi ta fadawa Ummi zata je gida.
Envelop Ummin ta mika mata "ga kudadenki na kunshi ki kaiwa Baffanki"
Da tsananin mamaki Rahima take kallon Ummi saboda da idanunta ta ga Salame da aihinin wanda aka bata ranar da tayiwa bakin Mom Arifah. Sauran wanda tayi kuwa ba wani yawa gareshi ba to ta ina kudin yayi wannan kaurin. Kasa shiru tayi muryarta tana rawa tace "Ummi ba kin bawa Umma wancan kudin ba?"
Mairama ranta taji ya baci a tunaninta Salame ce ta fadawa Rahima ta karbe kudin. So tayi ta rufa mata asiri shine ta sake hada mata dubu dari da sauran kudin da ta samu.
"Wancan kyauta ce zanyi mata ranar babu kudi a hannuna shine na bata naki amma gashi na dawo miki dasu"
Tasan Ummin ta fada ne kawai ba yarda tayi ba. Kuka ta fashe dashi tana kara son kanwar Ummanta da danta Emzee. Cike da farinciki ta tafi gidansu. Baffanta yana kofar gida suna hira da abokinsa ya hangota. Bakinsa kamar gonar auduga ya tashi ya shige ciki da saurinsa yabi bayanta. A dakin Iya suka yada zango suna ta sakin murmushi ta je ta nanikewa Iya a jiki. Sunji dadi sosai yadda tayi fes da ita ta kara cikowa tayi kyau.
"Har kin gama hutun ne Rahima?" Iya take tambayarta tunda basuyi tsammanin dawowarta yanzu ba.
Bayani tayi musu ta cewa Iya don Allah ranar laraba tazo yinin Adda Radhiya. Labarin kirkin su Ummi tayi ta basu da yadda kasuwar kunshi ta bude mata. Da ta basu kudin ba karamin mamaki Baffanta yayi ba.
"Tare zamu je gidan Malamijon idan kin huta nayi mata godiya. Dubu dari harda sha uku a hannuna arzikin Rahimata" yace yana dariya.
Ta tashi taje bangaren matar gidan suka gaisa ba yabo ba fallasa ta dawo Iya ta mika mata kudi a leda "ga wannan Rahima nasa Baffanki ya raba kudin ki kaiwa Salame itama tasa albarka. Dubu talatin ne, Baffanki ma ya dauki talatin sauran kuma zan fara yi miki siyayya kinga ko maburgi baki dashi kada aure yayi mana zuwan bazata"
Ture kudin tayi kamar zatayi kuka tace "A'a Iya Baffa ya rike duka"
"Kul na kara ji mahaifiya ba abar wasa bace. Maza dauki ki kai mata ki dawo sai kuje can din da Baffanki ko"
Ba haka taso ba tunda zai zama Salame taci bulus harda kari amma bazata iya yiwa Iya musu ba. Daukar ledar tayi ta boye a cikin hijabinta ta kama hanyar gidan Alh Indararo.
A gidan Malamijo Radhiya bata san Rahima ta fita ba sai daga baya Ummi ke fada mata inda taje. Ta taho mata da kaya akwati guda masu kyau wanda bata yi wani amfanin kirki dasu ba kuma bata so dama ta bata a cikin gidan sai kawai ta nemi yaro ya rakata gidansu. Suna fita suka hangota tayi hanyar gidan Salame shine ta bi bayanta.
Da Rahima ta isa tsakar gidan kamar kaji sunyi dambe ko ina shinkafa ce tun wadda aka ci da rana da mai ta watse a wurin. Ga kwanuka a bakin kofofin dakuna wasu a tsakar wurin kadan ne aka ajiye a wurin wanke wanke. A mutumce ta gaishe da Maman Danmama tayi sallama a kofar dakin Salame.
Daga ciki ta amsa mata irin na gatse dinnan "Su Hajiya Rahima ne...shigo mana"
Gwiwa a sake ta shiga ta gaisheta. Bata amsa ba sai kunnenta da ta kama ta murde iya karfinta amma dauriya irinta Rahima bata yi yunkurin kwacewa ba sai hawaye da yake zuba kamar an bude famfo "dama jiranki nake yi ki dawo mai shegen kwadayi. Kin bi Mairama gidanta batare da neman izinina ba sannan da muka je akanki Hajjo da Yadikko ke yi min fada"
"Umma kiyi hakuri" tace idanunta a runtse zafin murdar kunnen tana ratsata sosai.
Salame bata raga mata ba saboda bakincikin yadda har take da bakin cewa dama Mairama ce ta haifeta. Rai a bace take fada "kinje kin sami duniya da bakinki kina cewa ni bana sonki ko? Akwai uwar da kika taba yi min ne da zan so ki? Banda kaddarar haihuwarki me zai kaini gidan fakirin mahaifinki ma. Sai ana magana kiyi ta zarowa mutane idanu"
Maman Danmama tana jinsu amma bata shiga ba saboda ko taje bazai hana Salame abinda tayi niyya ba. Bacin rai sosai Rahima take ji wanda ba don Salame ce ta kawota duniya ba yau da tayi mata fitsara da rashin kunya irin wadda bata taba sani ko ji ba.
Sauran yaran suna dakin suna dariya Salame ta cigaba ido a rufe "daga yau na sake jin kinbi Mairama gidanta sai na saba miki. Har wani arziki garesu da zaki je kamar almajira kina 'yar cikina ana baki kafa da hannu kina kunshi wai ke mai sana'a"
Kasa magana tayi sai gunjin kuka. Babu abinda ke damun Salame sai frustration da tsantsar hassadar Mairama. Yanzu kowa ya bude baki a gidansu ita yake kira a yabeta a yabi 'ya'yanta. Rayuwa tayi mata ba daidai ba ace ita ce yau a kasan kanwarta wadda a da can baya take cin arzikinta. Ga Alh Indararo tayi haukan tayi hankalin duka a banza yaki sakinta. Halifa shima kuma ya koma jikin Mairaman shine itama da ubanta ba kowan kowa ba take neman bijere mata.
"Ba dake nake ba?" Ta hayayyako mata sai ji kake tas ta dauketa da mari saboda taki amsawa. Hancin Rahima sai jini Salame niyarta ta sauke duka bacin ranta yau a jikinta ta kuma daga hannu don ko jinin bata kula dashi ba Radhiya ta damke shi ta watsar dashi gefe. Kusan tare suka shigo gidan da Rahima duka abinda suka yi taji. Zuciyarta har wani daci take yi ganin yadda ake yiwa Rahiman da take kamar kwai yanzu a wurin Ummi. Ashe shiyasa Ummin ta kara janta a jiki don ta maye mata gurbin uwa.
Tayar da ita daga durkusun da tayi a gaban Salame taso yi amma taki tashi sai ma ture hannunta da take yi.
"Ki barta ta kasheni....Umma ki kasheni ki huta indai hakan zai sanyaya miki zuciya ki dena tsanata"
Zuciya a wuya Salame ta janyo wayar rediyo "kina zaton ina wasa dake ne Rahima? Kin tashi a nan ko sai naci ub...."
Wayar ta sauke mata a jikinta ya sami fuskarta sannan ta sake dagawa a kufule sai ta sauka a gadon bayan Radhiya saboda saurin kare Rahima da tayi. A zabure Rahiman ta mike ta kawo hannu za ta riketa ta nuna mata kofa "ki fita ki tafi gidan Baffanki gani nan zuwa"
"Adda ...." tace jikinta sai rawa yake yi kukan ma ya dauke mata.
"Nace ki fita ko sai ranki ya baci" Radhiya tace cikin fada.
Da sauri kuwa ta fita tana hawaye. Radhiya ta juyo tana yiwa Salame wani irin kallo da ya tsirga mata ciki. Idanu ne na Zayyanu Tureta take gani cikin tsananin bacin rai da zafin zuciya. Kujera Radhiya ta janyo ta zauna bayanta yana uban zugi saboda dukan ya shigeta sosai. Yaran ta kalla ta daka musu tsawa tace su fice kafin ta kirga uku. Ko biyu bata kai ba suka kama gabansu a guje ya rage daga ita sai Salame.
A rayuwarta bata taba tsorata irin na yau ba. Gani take kamar an hada mata Zayyan da Mairama a jikin mutum guda ne. Boye tsoron tayi tace "zaki rama dukan ne?"
"Zan so na rama Gwaggo Salame sai dai kinci arzikin Malamijo kuma dukanki zai janyo min fushin uwa. Yau ne na biyu da naga irin abinda kike yiwa Rahima saboda Baffanta talaka ne. Sai dai mijin naki na yanzu ma bana jin zai iya kwatarki daga hannun hukuma ko yaso"
A tsorace ta nunata da yatsa "Ke ki kiyayeni bana son rashin kunya don ko uwar da ta haifeki tayi kadan"
"Ki dena zagar min Ummina, bansan me tayi miki kika tsaneta ba amma inda ta kai bazaki taba zuwa rabinsa ba har abada da wannan algae (gansa kuka) din na bakinki"
"Wato dai turoki tayi ki fada min magana saboda baku da tarbiya ko?"
"Baki ga rashin tarbiyata ba amma yanzu zan nuna miki"
Emzee ta kira ya dauka zai fara janta da hira tace ya saurareta "motar sojoji nawa zaka iya turowa a kama Gwaggo Salame batare da kowa ya sani ba"
Cikin Salame yace tsuuuu da taji muryar Emzee kuma ana zancen motar sojoji. Ko tunanin cewa shi dalibi ne bata yi ba tsoronta kawai kada a kama ta.
Abinda tace ya saka shi tunani "Adda kada kice min kema kin gano ita ta makanta Ummi"
"What???" Radhiya tace jikinta na bari Salame kuwa sulalewa tayi a kasa saboda ba karamin tsoron hatsabibancin Radhiya take yi ba tuntuni. Yarinya ce kamar aljana bata da tsoro ko kadan.
"Kuna tare ne?" Ya tambayeta saboda bai fahimci zancen ba.
"Ina gidanta yanzu haka. Emzee kayi min bayani sosai"
"Adda dalilin da yasa ta tsani Ummi saboda tana son Daada ne, sannan ita ta yiwa Ummi asiri don ta auri wannan Alhajin da take gidansa yanzu"
Kuka yaji Radhiya ta fashe dashi jikinta yana wata irin rawa sanyi na ratsata. Tsorata Salame da taso yi akan Rahima sai ya koma bakincikin muguntar da ta yiwa mahaifiyarsu.
"Makantar shekara goma Gwaggo Salame na rantse bazamu yafe miki ba" tace tana wani irin kuka.
Maman Danbaba tana jin abinda ta fada ta garzaya ta kirawo Alh Indararo ashe yana cikin daki ya dawo da wuri.
Jikin Salame na rawa ta mike da dafa bango "kizo ki fita daga gidan tunda abin naku ya koma sharri" tana rarraba idanu kada wani ya shigo.
"Adda" Radhiya taji Emzee ya kirata "me ya kaiki gidanta ba dazu kuka iso ba?"
"Rahima na biyo" ta amsa cikin kuka.
Kansa ne ya daure sosai "Rahima kuma?"
"Eh Emzee, don baka ga irin dukan da take yi mata ba"
"Me ya hadata da Rahima kuma? Ko wacce kike nufi na kasa fahimta" yace jikinsa a sanyaye yana tsananta addu'a kada abinda yake zargin tana nufi ya tabbata.
"Rahima dai mana"
"Wadda nake gani tare da Zayyana?" Yace a tsorace.
"Eh" ta soma gajiya da tambayoyin ga serious maganar da ya kamata suyi.
Muryarsa taji kamar zaiyi kuka a raunane "Adda kina nufin Rahima 'yar Gwaggo Salame ce?"
"Kanwar Halifa ba..."
Wayarsa ce ta subuce daga hannunsa batare da ya sani ba yaji kansa yayi mugun sarawa. Hawaye sosai Muhammad Zayyan Tureta ya soma yi a garin yaya Rahima ta cuce shi haka? Meyasa bata taba fada masa ba? Shiryawa suka yi ita da babarta ko kuwa shima asirin aka yi masa tunda ta saba? Ko kuwa ta turota ne domin ta sake bakantawa mahaifiyarsa saboda tsanar da tayi mata?
Duka wadannan tambayoyin basu rage daidai da cikin cokali na soyayyar da yake yiwa Rahima ba sai dai wani irin zafi da yake ji a zuciyarsa domin ko sonta zai kashe shi bazai taba auren irin Salame ba.
"Why Rahima???" Ya durkushe a kasa yana kuka kamar karamin yaro. [5/22, 11:03 PM] Sis Ruky: *KUYI HAKURI DA RASHIN YAWANSA BANA JINDADI NE YAU. NAGODE*
Idanun Salame sunyi zuru-zuru saboda asirinta da wadannan 'ya'yan na Mairama suka sani. Daga nan kuma bata san yaya za ta kare ba. Radhiya kashe wayarta tayi bayan ta gama magana da Emzee ta koma kallon Salame tana ta hawaye.
"Me Ummi tayi miki Gwaggo? Mata nawa ne suka taba son wani Allah bai kaddari zamansu tare ba kuma suka hakura?" Matsowa ta rinka yi inda Salame ke tsaye gumi na karyo mata. Wannan shi ake cewa kada Allah Ya kaimu ranar da za'a tsare mutum ana masa tambaya akan laifukan da ya binne. Ya Allah Ka rabamu da hisabi irin wannan da za'a tono komai da komai da muka taba aikatawa a rayuwarmu domin WALLAHI da matukar wahala mu haye.
Kuka Radhiya take yi amma muryarta kowa naji a cikin gidan saboda karshe ranta ya kai kuloluwar baci "Kinsan tsananin da yake tattare da makanta kuwa? A lokacin Ummi ta rayu ba miji ga marayu sannan babu wadatar abincin da zata ci ta ciyar da yaranta. Gwaggo kina kallo sai da ta sayar da duk wani abu da ta mallaka muka dena karatu saboda neman magani." Kukanta ya kara tsanami ta matse kirjinta "sau nawa....sau nawa ina rokon Ummi ta barni nayi bara ko talla saboda bama koshi da abincin gidan Malamijo tana hanawa. Ba don Allah Ya dube mu su Innawuro sun zo ba kina jin da watarana bazata amince ba ko don kada yunwa tayi mana lahani. Sai Allah Ya sakawa Ummi Gwaggo" ta kare da fashewa da wani irin kuka. Rabonta da kuka sosai irin haka tun ranar da Ummi tace kada ta amsa cewar tana son Awwab. Yau ga abinda yafi rabuwa da Awwab kaji ko ka ga mutumin da baya kaunar mahaifiyarka kuma yake neman ganin bayanta.
Jiki na rawa ga tsoro amma Salame bata so ta nunawa Radhiya sai cewa tayi "idan kin gama sharrin sai ki fita ki tafi in kuma zaki rama mata ne to na fara jin didif a jikina sai na san cewa kin haifu"
Kallon da Radhiya tayi mata da jajayen idanunta kallo ne mai firgitarwa da nuna kwarewa wurin fitina da sanin yadda zaka rama abu cikin ruwan sanyi.
"Ummi tayi mana tarbiya wadda ni ko Emzee bazamu taba watsa mata kasa a ido ba in sha Allah. Gwaggo Salame ke ba sa'ar yi na bace domin kin girmi mahaifiyata ma...amma.... zan hadaki da wanda yafi cancanta ya hukunta ki" tana kaiwa nan ta daga waya ta soma kiran mahaifinta Zayyan Tureta.
Duk wannan abu da suke yi Alh Indararo da Maman Danmama suna kofar dakin sai dai su basu kula da tsayuwarsu ba sannan shima yana so ya gama gane kan zancen kafin ya afkawa Salame.
A can hostel dinsu kuma Emzee bayan ya gama nasa kukan shima babu wanda yake so da burin saukewa nauyin zuciyarsa sai mahaifinsa. A take shima ya soma kiran wayar Zayyan din.
**********