Batuol mamman complete novel - Chapter 67
Batuol mamman complete novel Chapter 67: Batuol mamman complete novel Chapter 67. A kafa su ka tafi gida babu mai cewa wani uffan kowa da nasa tunani. Sun…
3,353 words
A kafa su ka tafi gida babu mai cewa wani uffan kowa da nasa tunani. Sun kusa kofar gidansu Malamijo ya yanke jiki ya fadi tunani yayi masa yawa saboda ko ba'a fada ba ya sani cewa shine musabbabin lalacewar duk wani bara gurbi ciki 'ya'yansa kamar yadda yasan cewa duk wanda ya shiryu a cikinsu daga Allah ne da taimakon Yadikko matar da bata haifi ko tsinke ba amma taci kashi da fitsarin kusan duka 'ya'yansa.
Allah Yasa Baffan Rahima yana biye dasu saboda son ya ga halin da 'yarsa take ciki ya tafi da ita gida. Hankalinsu duk ya tashi musamman Mairama da take yiwa yau din kallon bakar rana ya ciccibe shi ya saba a kafada ya karasa dashi gidan. A kidime Mairama ta kira Radhiya ta turo musu Lucas tace ai sun kusa gida an duba su.
Da sauri sauri suke shirin saka shi a mota ya farfado yace babu inda zashi.
Hajjo tun tana lallaba shi har ta koma fada "so kake ka cuceni kawai. Cikin shekarar nan na dana zaman iddah yanzu kuma takaba kake son kakaba min don mugunta daga dawowata"
Duk da yana jin jiki bai hana shi galla mata harara ba "ina jin har kin gama lissafin tumunin takaba to ta Allah ba taki ba. Ina nan garau ba mutuwa zanyi ba. Ke in bakiyi wasa ba fa Hajjo sai na kaiki zan taho daga baya"
Cinya ta buga tana dariyar jindadin ya tashi amma duk da haka bata barshi haka ba "ashe da rabon ayi suna da kai"
Sam ya manta a waje suke ya kalleta a tsorace yana hadiyar yawu da kyar "wace take da ciki kuma ni Ali wai ku baku da tausayi ne bazaku barni na huta ba"
Radhiya, Rahima da Mama basu san lokacin da suka sa dariya ba Ummi ta tallewa Radhiya da Rahima keya tana murmushi suka shige cikin gidan. Manyan daki suka shiga suna cigaba da tattaunawa Mama da Ummi kuma su ka tafi dakin da aka basu. Radhiya ma da Rahima daki daya suka shiga nan Rahima tana hawaye ta soma cewa Addarta tayi hakuri da abinda Ummansu tayi mata. Daure fuska Radhiya tayi tana harararta da wasa
"Rahima bana son kina sake tada wannan maganar. Nasan ko ma meye su Ummi sun gama daidaitawa a junansu babu ruwanki"
Wani kukan ne ya taho mata ga idonta daya yana zugi kamar zai fado "Adda ni shikenan Umma bata sona, me nayi mata ta tsaneni?"
Tausayi da kaunar kanwarta ya sake kamata ta zauna a kusa da ita ta rungumeta haushin Salame yana kara kamata. Allah Yasa kada Rahima taji sauran maganar game da Gwaggo Salame don tasan it will break her heart fiye da yanzu. A tausashe tace "Ummi tana sonki kinji kuma bazata sake bari ta dakeki ba"
"Mu ga bayanki" Rahiman tace a kokarinta na nemo nutsuwa ta yafawa kanta a dole. Radhiya kwanciya tayi Rahima ta dage rigarta wurin yayi wani iri da yanzu ita za'a sake saukewa wannan bulala bayan wadda ta sauka a fuskarta. Maganin da aka basu tace za ta shafa mata Radhiyan tace ta bari suyi wanka sai su shafa.
A dakin da su Ummi suke kuwa suna shiga ta haye gado ta kwanta tare da juyawa kofa baya. Kuka take yi sosai jikinta har wata irin karkarwa yake yi. Abin na Adda Salame har ya kai haka ashe. Ita kuwa banda auren Zayyan me kuma tayi ta konawa 'yar uwarta rai haka. Mama jikinta duk yayi sanyi a hankali ta zagaya gabanta ta zauna daga gefe.
"Mairama" tace cikin sigar rarrashi.
Sake juya mata baya tayi muryarta har tana sarkewa tace "ki barni inyi kuka Zainab, ashe a duniya akwai wanda zai tsaneni har ta kai ga yi min asiri na makance. Ina nan ina yiwa kaina kallon wadda bata shiga gonar kowa ba ashe na kure yayata kiyayar tayi tsamari" dago rinannun idanunta tayi suka hada ido tace "Allah kadai Yasan mutum nawa ne suka tsaneni"
Hawaye Mama ta soma yi itama "mijinki yana sonki Mairama. Ni da Mami muna kaunarki kamar ciki daya muka fito kuma ga Malamijo da sauran mutanen gidan nan, banda su Radhiya rabin rai" ta dage mata gira.
Murmushi Ummi tayi kamaninta da Radhiyan suka fito sosai "nagode Zainab Allah Ya kara mana zumunci. Inama Mami tana nan da nasan bazata gudu ta barni yadda kika yi ba dazu kawai ina cikin fada na juya neman support na ga wayam"
Mama sai da tayi dariya sannan ta kira mata Mami. Tana dauka bayan sun gaisa take basu labarin yadda suka yi da Alh Baba wurin shiryasu ita da kannenta.
"Nan ma fa fama muke ina jin shirin ne za'ayi idan an gama hawa saman" cewar Mama.
Ummi cikin kuka take yi musu bayanin abubuwan da suka faru. Su duka ukun kuka suke yi musamman Mami da tayi nisa tana jin kamar tayi tsuntsuwa tazo ta wanke Salame irin wankin babban bargon nan. Zumuncin da yake tsakanin su uku abin burgewa ne da sha'awa domin kowacce da zuciya daya take son sauran.
Bayan sun gama Mama tace "to saura Oga tun dazu wayarki ke haske nasan shine"
Murmushi na musamman Ummi tayi ta mika hannu ta dauko wayar wanda yayi daidai da sake kiranta da Zayyan yayi. Tana dauka ko sallama bata yi masa ba ya kira sunanta a kagauce saboda yadda hankalinsa ya tashi. Jin muryarsa kadai ya sake tado mata abinda Salame tayi sai kawai ta fashe masa da kuka. Yi take yana sauraronta yayin da Mama ta dauke DK tayi waje don ta basu wuri. Sai da tayi mai isarta tayi shiru don kanta. Hakuri ya bata tare da kalmomi na kwantar da hankali sannan ya nemi jin ba'asi.
"Ki kwantar da hankalinki gobe in sha Allahu jirgin safe zan biyo"
"Sojana" yaji ta yi masa kiran da dole ya amsa.
"Mairama Fillon Zayyan me kuma akayi?"
Kukan yaji ta cigaba da yi "Don Allah ka fada min ni muguwa ce ko naso kaina ne da yawa da na aureka har ya janyo min kiyayyar Adda Salame?" Ta fada da wata irin murya abin tausayi.
Kwafa yayi kawai yana jin kamar ya baro garin Sakkwato a lokacin saboda yazo ya nunawa Salame kurenta.
"Ki bari inzo goben sai na baki amsar da ta dace. A haka babu abinda zaki fahimta"
"To don Allah ka taho da wuri sosai, yau ina jin ko bacci bazan iya ba"
"Saboda kewata ko saboda Salame ikon Allah?"
Dariya ya bata "bani da sauran abinda zance mata na bar maka komai Daadan Alheran" ta kare cike da kunya.
"Ki cire komai da kowa a ranki ki barni ni kadai yau dinnan bana son tunani ya dameki. Ina nan tare dake babu wanda zai taba min ke batare da na nuna masa mijinki yana sonki ba"
Sannu a hankali ya mayar da akalar hirar ta soyayya inda yayi nasarar rabata da duk wata damuwa.
**********
Hawaye kafewa yayi a idanun Salame tun bayan fitarsu Mairama ta koma ciki tana tafe kamar kwai ya fashe mata a ciki ta shige dakinta. Mayafi ta dauko ta fito Alh Indararo yayi wuf ya fito daga falonsa.
"Ina zaki je?"
Bata da wani kuzari bare tayi masa rashin kunya "ka yiwa Allah ka barni inje gidan Ta Madina"
Baki ya rike saboda tsabar mamaki kamar wata mace "Ta Madina dai mahaifiyarki?"
Kai ta gyada masa kai kace kadangaruwa ce.
"To sai kin dawo yau nasan zata ce tayi gamo. Idan kin fita ki turo min 'ya'yana. Kuma Yasin kika kuskura isha ta riskeki a waje ko a ina ne har can zani na sabunta miki kamanni muguwa mai muguwar zuciya"
Bata iya tankawa ba ta fita tayi sa'a kuwa jikin gidansu yaran suka shiga. Gida tace su koma sannan ta wuce gidan babarta a kafa tafiyar minti sha bakwai ta kaita. Da sallama ta shiga jama'ar gidan su ka rinka kallonta kamar an ga wata sabuwar halitta. Babu wanda ta kula ta kunna kai dakin Ta Madina ta sameta zaune akan tabarma tana gurza goro. Da mamaki ta dago tana kallonta kafin ta soma magana.
"Iko sai Lillahi...Salame ke nake gani ko kuma gizo kike min. Tohhh ni dai ban kwana dake a raina ba bare ace saka ki nake a zuci har kika fara min gizo"
Daga bakin kofar Salame ta zube saboda ganin uwa mai dadi ta shiga kuka tun daga kasan zuciyarta. Ta Madina kamar mai kallon film haka ta kare mata kallo ta gama kukan bata ce komai ba. Sai da ta fuskanci kamar tayi shiru ta tabe baki tace "alhaki kwikuyo ya biyoki kenan. Ina kyautata zaton wannan hawayen na Rahima ne ko hakkinta. Ko ma wanne ne a dakin nan nace miki da sannu zaki ganewa idanunki illar abinda kike matar Alhaji"
Da kyar ta iya cewa "Ta Madina baki kika yi min gashi ya kamani"
"Karya kike" ta nunata da yatsa a harzuke "ke idan nayi miki baki buzunki ma bazai ganu ba in fada miki."
Kai ta sunkuyar tana ji Ta Madina ta cigaba da fada "wai ni Salame zaki nunawa kina auren maikudi ban isa dake ba. Nan inda kike zaune lokacin kika tsaya kina fada min maganganu saboda Rahima tazo ta roki in baki hakuri ki yafe mata ko ma menene tayi ki dena dukanta. Saboda kinci maiko kin tada kai kika kada baki kika ce mata idan ta kuma zuwa wurina baki yafe mata nononki da tasha ba. Ni...ni Salame kika yiwa wannan rashin arziki"
Ta sani ita din mai laifi ce sosai a wurin mahaifiyarta. Idan bata ga ba daidai ba a dalilin kowa dole ne ta gani a dalilin Ta Madina. Muryarta ta ji tana ta koro bayani kamar yau akayi.
"Yarinyar nan tayi kuka kamar me tun daga ranar idan tazo daga waje take kwada sallama na fita mu gaisa. Yau shekara biyu rabona da ita saboda kaninki Sa'adu rannan yayi fushi ya daukota a ka ya dire min ita yace idan kin isa kizo gabansa ki tabata. Da yake ta gaji halin kwarai wurin babanta a guje ta fita tana tuna kalmar rashin yafiya da kika jefa mata...shikenan ta dena zuwa"
Ajiyar zuciya ta saki ta gurfanar da kai "Ta Madina ki yafe min amma yau abinda ke damuna yafi karfin Rahima"
"Wa kuma kika tabo kuma?"
Cikin kuka ta zayyane mata komai batare da ta boye wani abu ba. Bacin rai sosai take gani akan fuskar Ta Madina kafin ta nuna mata kofa "ga hanya nan idan kika sake shigo min gida nima ban yaf...."
A guje Salame ta tashi "kada ki karasa zan tafi"
"Baki ga komai ba ma indai bazaki dena wannan shashancin ba. Duk kinbi kin tsangwani kanki kin lalace kamar alayyahu yaji rana" Ta Madina ta daga murya yadda zata ji. Sai da ta tabbatar ta tafi kuma hankalinta ya tashi kawai sai ta kira wata jikarta 'yar kanin Salamen ta saka ta kiran Halifa a waya. Cewa tayi ya gaggauta zuwa Sumaila indau yana Kano yace to. Rahima ya kira tana dauka ta fashe masa da kuka sai ya kara jin hankalinsa ya tashi. Gashi ta kasa cewa komai. A ranar ya dauko hanya kai tsaye gidan Ta Madina yaje. Matsa mata yayi da tambaya ta kasa cewa komai kawai ya wuce gidan Alh Indararo gashi dare yayi. Alhajin da bai san ina Salame ta makale ba ya fyede masa biri har bindi....bai karasa bindin ba dai tunda kuwa iyaka abinda ya fada masa bayan dukan Rahima da 'yae uwarta wadda ya gano Radhiya ce daga kwatancen da yayi masa sai kuma baton makanta Mairama. Bai kai ga fada masa soyayyarta ga Zayyan ba Maman Danmama tayi saurin dakatar dashi. Halifa idanunsa kamar garwashi sai jijiyoyin kansa da suka tashi kamar zasu fasa fatar su fito.
Cije lebensa na kasa yayi har yana jin dandanon gishiri yana magana da kyar yace "yanzu kowa ya sani?"
"Ina maganar kowa Halifa, wannan zance fa yarinyar Mairaman ce ta kira waya wani yake fada mata muna ji mu kuma. Da su Malamijo suka zo kowa yaji mana."
Hawaye Halifa ya soma abin tausayi "Rahima ma ta sani?"
"Eh tohhh...lokacin da muke zancen dai bata gidan sun tafi asibiti amma ban sani ba wala Allah ko a can gidan an fada mata." Alh Indararo yace bayan guntun tunani.
Jiki a sanyaye kamar wanda yasha duka ya kira Mairama. Tana ganin kiran hankalinta ya tashi. Kuka Halifa ya saka mata muryarsa tana rawa yake mata magana.
"Ummi ki yafe mata ba don ita ba don Allah..."
"Halifa kana ina?"
"Gidanta"
"Waye ya fada maka?" Tace tana taya shi kukan.
"Yanzu zan zo gidan Malamijo amma don Allah don sonki da Annabi Ummi kada ki bari Rahima taji don bansan yadda zata dauki abin ba"
Kwantar da murya tayi tace ya taho tana jiransa. Babu wanda ya san ya shigo ta kaishi dakin Malamijo inda ya sha kukansa kamar ba gobe Malamijo yana ta bashi baki.
Ranar babu wanda yayi baccin kirki cikin manyan ba don komai ba kuwa sai tausayin Halifa da yadda ya dami kansa. Radhiya sai da ta ga Rahima ta kwanta ta soma nata kukan itama. Tana tausayin 'ya'yan Gwaggon tasu sannan a gefe daya ta tsaneta saboda wahalar da ta sanya Umminta fuskanta. Awwab ba karamar damuwa ya shiga ba da yayi ta kiranta babu amsa ashe ta yar da wayar a dakin Salame. Itama bata tuna ba sai daga baya sai dai bata son yaji muryarta a yadda take gashi kowa da tasa damuwar shiyasa ta kasa aron waya.
Cikin bargon kuma Rahima ce ta boye kanta tayi kuka har sai da taji kanta yana neman rabewa biyu don ciwo. Bata san me Ummanta tayi ba amma yanzu ace mahaifiyar mutum tayi masa tsanar da sai wasu ne suke tare masa? Wace irin kiyayya take gwada mata da har ta kasa ko da sau daya yi mata kallo irin wanda take yiwa sauran 'ya'yanta? Da wannan tulin tambayoyin bacci a kwasheta. Gashi ta kira Emzee yafi sau ashirin sai dai wayar ta tsinke don kanta batare da ya dauka ba.
*********
A bangaren Emzee wutar kiyayyar Rahima ke cin ransa kamar gobara yayin da ya kasa gane a wane matsayi ya barta a cikin zuciyarsa. Kunci da bacin ran da ya shiga a wannan dare bazai misaltu ba. Da abin ya ishe shi Daada ya kira ya rasa yadda zaiyi ya fada masa halin da zuciyarsa take ciki. Ya dai yi masa kuka abinda ya daurewa Zayyan kai sosai. Kallon jarumi mai dakakkiyar zuciya yake yiwa dan nasa ashe akwai abinda zai kawo hawaye a idon mazaje.
"Ba kace dama an baka leave har zuwa bikin Alheran ba?" Ya tambaye shi bayan ya samu yayi shiru.
"Eh Daada"
"Gobe da sassafe ka sameni a Kano Janguza barrack wurin Captain Onomza zamu je Sumaila tare. Akwai jirgi karfe bakwai da rabi shi zan biyo in sha Allah"
Suna gama wayar ya kira Captain Onomza ya sanar dashi yana bukatar mota guda ta sojoji. Allah Yasa da uniform dinsa a mota sai dai tunda ba da dreban zai tafi ba zai dauki jakar ne kawai. Akwai mutum uku da suke tare a daya motar masu bashi kariya duka dasu zai tafi Kano. Ziyarar tasa ba official visit bane amma ya kamata a tauna tsakuwa domin aya taji tsoro. Yau daya banda Mairama, Alheran da Zayyanunsa da yayi ta aikin rarrashi daga nan Allah kadai Yasan mutum nawa Salame ta sa zubar da hawaye. Ita mace ce mai rauni bazai dauki hukunci irin wanda aka yiwa Maikudi ba akanta amma tabbas zai nuna mata ta taba masa mutane mafiya suyowa a ransa. [5/22, 11:05 PM] Sis Ruky: Tare suka yi girkin amma Rahima ce karfin aikin. Yaran gidan sai binta suke da kallo ita dai kanta na kasa har suka kammala. Baffanta ne ya kira Ummi ya sanar da ita inda zata kwana kada suji shiru. Addu'a ta rinka yi Allah Yasa kada wani abu mara dadi ya biyo baya.
Lura Salame tayi da yadda Rahima take tsakurar abincinta. Tuwon masara ne da miyar karkashi sai tashin daddawa take yi ga sukunbiya an saka saboda ita. A cikin kwanon silva ta zubawa Rahima ta kwarara miyar a kai.
Sai da ta gama lashe hannunta ta bi irin abin miyar nan da ya kan makale a tsakanin hakora da harshe tana sakato shi sai ji kake tana tsk-tskk da baki ta kora da ruwan rijiya sannan ta tabe baki.
"Abincin namu bai kai na 'Yan Abuja dadi bane naga kina ta yafita kamar bakya so?"
Kafin ta kai karshen maganarta Rahima ta zunduma wata katuwar loma wadda ta kasa hadiyewa saboda bata kaunar karkashi ko kadan. Da gudu taje bakin rariya ta zubar ta dawo tana jiran Salame ta soma fada sai taji tayi mata magana babu wannan fadan.
"Ba kya cin tuwo ne?"
"Miyar...miyar ce dama...dama karkashi ne....bana sha"
"Yo maimakon ki fada nayi miki hadin mai da yaji sai ki cuci kanki? In kin fada min ai ba dukanki zanyi ba" tace da ita amma idan kaji yadda muryarta ke fita sai ka dan tsorata. Takaicin yadda yarinyar ke zabura duk motsinta ne yake damunta. Kwanon ta dauka ta mikawa sauran yaranta da gudu suka far masa dama sun cinye nasu ita kuma taje kitchen ta dibar mata wani cikin sauran da zasuyi dumame dashi da safe. Mai kwantirola ta yaryada mata da gishiri ta dauko yaji da rabin maggi a dakinta ta saka sannan ta bata. Ko kadan wannan hadi bai yiwa Rahima dadi ba saboda man danye ne sai karni ke tashi amma kyautatawar da mahaifiyarta ta gwada mata karon farko tun wayonta yasata yin kwalla ta janyo farantin ta cinye shi duka.
Basu wani jima da gamawa ba Alh Indararo ya dawo gida Salame ta kai masa nasa abincin. Kayan jikinta tun na jiya ne babu zancen wanka a ajandarta duk kuwa da cewa da murhu tayi girki ga kauri ga datti. Tunda ta shiga banda harara da habaici babu abinda yake mata ya gama cin abincin yace ta fita kada ta sake zuwa turakarsa da sunan kwana sai idan da kansa ya nemeta. Abu na biyu kuma ya bata lokaci kankani ta san yadda zata yi su daidaita da Mairama a basu ko da mutum biyu ne cikin yaran shi ma a rage masa nauyi.
Kallon raini ta bishi dashi "wannan shi ake kira karfin hali barawo da sallama."
Hannu ya kawo da sauri zai sauke mata ta fita ba shiri yana ta fada kuma wai kashin tsiya gareta kada ya kuma ganin kafarta a dakin. Dama waye ya aiketa bayan jiya ya mata dukan nan jiki yayi tsami. Dakinta ta koma aka yiwa yara shimfida Khadi tana gado tace da Rahima.
"Kwaba lallen kizo ki yayyaba min dashi zan kwana saboda ya kamu sosai"
"Kada ya cabe ko ba mai ado kike so ba?"
"Ado kai 'yan nan. Kada ki damu zan iya kwana dashi."
Duk yadda idonta yake damunta bata nuna ba ta kwaba lallen nan ta zauna. Wayarta ta soka a gaban dankwalinta bayan ta kunna torchlight saboda rashin wuta sannan ta kamo kafar. Dandakuwa sunan wani abu. Ga datti da wani maiko maiko ga yalwataccen kaushi yabi ko ina a cikin kafar babu inda babu. Kamar ta ce mata ko zata wanke kafar amma babu fuska sai uwar hamma da Salamen take yi. Ba yadda ta iya haka tasa kasan zaninta ta goge kafar sosai sannan ta baje basira ta soma zane. Goma ta wuce ta gama Salame tace mata ta kwanta a daya gefen ya zamana Khadi na tsakiyarsu. Da kyar ta iya bacci saboda rashin sakewa da sabo. Asubar fari kuwa ta mike ciwon ido yayi sallama ya kara nauyi tana ruwa. Alwala ta dauro ta zo ta tashi Salame ta kwashe mata lallen ta goge hannuwan da kafafu sannan itama tayi alwalar. Tun a lokacin tana iya ganin yadda lallen nata ya fito radau yayi kyau musamman hannuwanta. A sannu sannu gurbin da ta danne Rahima a zuciyarta ya fara neman nuna kansa ga duniya. Sai take jin wani takaici da haushin kanta na kin sakarwa yarinyarta tun farko.