Boyayyen mutun complete - Chapter 24
Boyayyen mutun complete Chapter 24: Boyayyen mutun complete Chapter 24. Ahankali Muhsin ke bude ido da asuban fari wuraren karfe hudu, sosai yaji kanshi…
2,757 words
Ahankali Muhsin ke bude ido da asuban fari wuraren karfe hudu, sosai yaji kanshi namai nauyi da kyar ya iya bude ido duka ya kalli gefenshi Ahmad ne zaune kan kujeran ya kifa kanshi akan gadon yana bacci, dan ajiyan zuciya ya sauke komi na dawomai wani irin hawaye mai zafi ya gangaromai hakan yasa ya runtse ido da sauri yanaji kirjinshi namai zafi sosai kaman an zuba garwashi, hanunshi yaji an kankame ana shafa gaban goshin shi hakan yasa ya bude ido Mum yagani tsaye akanshi sanye da hijabi idanunta sunyi jajir sun kumbura kana ganinta kasan kuka tasha sosai, hanunta yarike gamgam murya chan kasa irin na mara lafiya nan yace "Mummy Nadeera, I want to see her" ahankali Mum takai kanta ta sumbaci goshinshi tareda rungume kanshi tsam a kirjinta wani irin tausayin shi na shigan ta bana wasaba takai kusan 3min ahaka sanan ta dago kai ta sakeshi tanamai murmushi dukdan ta danne abinda ke cinta tace "how are you feeling Son? Bari nakira Dr yaduba ka" ta mike zata wuce da sauri ya riko hanunta hakan yasa ta juyo ta lumshe idanunta dan bataso tai kuka tai breaking heart dinshi dan dago kai yayi zai tashi da sauri tace "no, no no no karka tashi" tai maganan hawaye na gangaro wa daga idanunta, cikin raunanniyar muryan shi yace "wat is it Mum maiya faru wen I was unconscious?" zata girgiza mai kai ya riketa ahankali yace "please tell me Mum naji sauki, I can handle anything" shiru tayi kafin ahankali ta zauna kan kujera ta rike hanunshi gam takira sunanshi tace "Muhsin" kallonta yayi kafin ahankali yace "Na'am Mum" dan murmushi tamai sanan tace "inaso kamin wani abu da jarumi kadai zai iyamin shi kuma nasan d'ana jarumi ne, jarumin namiji nahaifa dan haka zaka Iya" shiru tayi takara kallonshi sanan tace "inaso ka yakice son Nadeera daga ranka Son, cus your father have ruined everything for you, tayaya zan bari ka auri yarinyar da mahaifinka keso, to bayan auren dawani ido zai dinga kallonma mata? Muhsin understand me am saying all this for your own good daga kai har princess din, koda ace yau babu aure akan princess wlh mahaifinka bazai taba barinmaka itaba ayanda yake jinta aranshi dinan nashi, mahaifinka dabai taba daga hannu ya nunamin ba for 33 years da aurenmu akan princess yadakeni Muhsin" ta share kwalla tacigaba tace "mahaifinka dake sonku kaman ranshi yabude baki ya tsinema Ahmad jiya akan Princess, mahaifinka da his family is number one yanzu bama gabanshi he's only after princess" shiru tayi tana kallon Muhsin dake kallonta asanyaye yana sauke wani irin ajiyan zuciya ahankali ta kama hanunshi tace "Son! I know, I know, I know nice to be blamed for everything that happened, I know am responsible for koma me Baban ku yadawo ayau, but wanan difficult phase dinan damuke facing kaddara ce da dole zai faru, yanzu abinda yakamata muyi shine mu yarda da kaddarar, mukuma nemi taimakon Allah, son zakaso ka auri yarinyar da baban ka try to rape? Try to molest? Zakaso ka auri yarinyar data gama gane sirrin ubanka? Zakaso ka auri yarinyar da mahaifin ka yagama gane sirrinta ne? Zakazo ka auri yarinyar da baban ka is going gaga for, zaka so ka dinga takaran kishi da mahaifinka? Wani zubin ana barin halaliya dan kunya da kawaici dakuma yakamata, and besides Princess dinma yanzu matar aure ce, banaso tasan we are not her parent abun zasu mata yawa, bantaba tunanin akwai rana dazata zo da zaisa mufada ma princess we are not her parents ba, ubanka yariga ya aurar da ita dudda guy din gangster ne, but naga affection dayake having mata, and wherever there's affection love definitely exist there, and inhar akwai So! to their Love can conquers everything, karkai mamaki kaga sanadin princess ya shiryu yadawo good man sunyi building family maiban sha'awa, addu'a zamu mata da fatan alheri kaji Muhsin, kahakura da Nadeera dan matar wani ce and babu kyau kana son matan wani" ta karashe maganan tana kallon idanunshi dasuka ciko da kwalla sosai ya tsaya yana kallonta kaman wata madubi, gyadamai kai tayi ahankali tana kokarin mayar da kukan datakeji ta shafa kanshi tace "talk to me Son wanan look din na breaking heart dina, yimin magana Umm my Muhsin, are you okay" wani irin tashi yayi daga kan gadon yafada jikin Mum ya kankameta yafashe dawani irin kuka sosai mara kara sosai hawayen na diddiga ajikin Mum, kankameshi Mum tayi tana patting bayanshi tace "cry, cry kaji ko zuciyarka tarage nauyi, I know how much you love princess, nasani, nasani son, kuma naso nabaka ita, I love you so much Son and am sorry is all my fault, duk laifi nane" sosai yake kuka jikinshi na rawa zuciyarshi namai wani irin zafi, daci, cikin kuka sosai yace "I love her, Mum wlh I love her so much, Mum bantaba yin budurwa aduniyan nan ba sabida I have Nadeera, Mum I love her so much, Mum I love her, Mum I love her, Mummy I love princess so much wlh" yanda yake kukan kaman zai shide ajikinta yasa ta ciro shi daga jikinta tana sharemai fuska da hijabin dake jikinta, ahankali Ahmad da kanshi ke kife dan duk maganganu dasuke yanaji ya goge hawayen dayake yi na tausayin wanshi, batun yau yasan Muhsin nason Nadeera ba dudda bai fadamai ba amma yaga sonta a idanunshi, sharemai hawayen dasuka kasa dena zuba mum tayi tana girgiza mai kai idanunshi sunyi jajir jikinshi yadau zafi, ahankali yarike hanun Mum da muryanshi data dishe tsabagen kuka yace "Mum zanbar kasar, lemme just go back to Toronto inda nai karatu idan na cigaba da zama anan ina ganin Abba I can die wlh" daidai nan Ahmad shima ya daga kanshi yana goge kwalla yace "am going with u" kallon yaran nata Mum tayi jitake kaman ta kurma ihu da kyar da taimakon ta dana Ahmad Muhsin dake ganin jiri sosai yatashi suka kaishi bayi ya dauro alwala yafito sai yahau kan dadduma yana salla yana share hawaye zuciyarshi na tafarfasa, a raka'a na biyun kawai ya yanke jiki yafadi sabida wani irin duhu daya gani dakuma kunenshi dasukai dummm!. [10/17, 6:01 PM] Aishat Muhammad: *in kinason karanta book dinan Zaki tura 300 kota card kota bank sai nai adding dinki a group din danake posting kullum* _Acc no : 3107021073 first bank aisha Muhammad_ *Saiki turamin evidence ta watsapp number na kaman haka 07012181461 saina saki a group din danake posting* *For any enquiry ku tuntubeni ta watsapp number na kaman haka 07012181461*
*AX*
Arude Mum da Ahmad sukai kanshi, juyo dashi Ahmad yayi yadaura kanshi akan cinyarshi yana jijjigashi yana kiran sunanshi "Yah Muhsin, Brother, Brother" dawani irin gudu Mum tamike tsaye tai wajen gadon ta danna alarm din kiran Dr da Nurses kaman zata fasa tsabagen yanda take pressing din alerm din tadawo kanshi tana goge hawaye tana kiran sunanshi "Son" daidai lokacin wani babban Dr da wasu nurses suka shigo dakin da gudu sukayo wajen Dr na musu masifa yace "meyasa kuka bari ya sauko daga gado? Yaron nan jinin shi yahau sosai in kuna bari yana yanke jiki yana faduwa haka za'a samu matsala fa" da taimakon Ahmad dasu suka daukeshi suka daurashi akan gado, da sauri Dr yasa nurse tamai fixing drip shikuma yana hada alluran dazai mai, saida yamai alluran daban daban kusan uku sanan suka samu numfashin shi yadawo amma yay wani iri, dagowa Dr yayi yana goge sweat din daya hada agaban goshi yawuce yafita daga dakin da sauri Mum tabi bayanshi har zuwa office dinshi nuna mata kujera yayi ta zauna kafin ma yay magana tai maza ta share hawaye ta goggoge fuskarta tsaf tareda sauke ajiyan zuciya cikin wani irin murya datai kaman na zararra tace "my son is about to have stroke ko Dr karka boyemin komi" tai maza ta share hawayen daya zubo mata inda zakaga mum zaka Iya mata kuka, baki Dr yabude tai maza ta tari numfashin shi tace "I want transfer, inaso in fitar dashi daga Nigeria muje Canada munada komi dan Canada wajen zuwan mune sosai, inhar yana Nigeria bazai taba warkewa ba, kabamu transfer I will sort everything out and contact d hospital sabida in akwai any available flight yau mu tafi shida brother shi" yanda take magana tana breathing heavenly yasa likitan yace "calm down hajiya, zan baku amma gaskiya ku guji abinda zai dinga batama yaronku rai da dagamai hankali sanan dazaran kunga yafara tunani kuhana shi" gyadamai kai tayi yace "kije zan kawo miki anjima kadan" gyadamai kai tayi ta tashi tafita daga office din bata koma dakinba motar ta dake pake a parking space din asibitin taje ta shiga ta zauna sosai tai kuka zuciyarta na mata kaman dutse ta share hawayen tai kuka ta koshi sanan tadau wayarta ta kunna ahankali tana share hawayen dake zubo mata ta nemo number Marwan tadade tana kallon number kafin ahankali tai dailing number.
Sosai yake wani irin kissing dinta kaman zai cinyeta sai kuka take ko karfin daga yatsa batadashi, ahankali hanunshi ke yawo a gefen cikinta yana kokarin kamo kirjinta yana nishi yana lumshe ido, karan wayanshi ne yacika dakin alamun kira na shigowa. Fashemai da kuka sosai tayi dan mugun gaji tana kokarin tureshi danya saketa ta kwanta dan wani irin bacci ke fizganta amma yawani irin matseta kaman za'a kwace mishi ita, mamaki yayi wake kiranshi da safen nan batare daya saketa ba yacigaba da abinda yakeyi yana girgiza mata kai jin yanda take mai kuka sosai da baya fitowa sosai saidai hawayen ta daketa gangarawa kirjinshi ko kadan batada karfin kwatan kanta, jin wayarshi nata ringing yasa yay tunanin kosu Abdallah ne ke kiranshi maybe jikin Abdallah ne dan yaji yana running temperature dazu dasafe, ahankali ya janye bakinshi ya saki nata yana wani irin kallonta yanda lips dinta sukai jajir harda sun kumbura, kwantar da ita yayi ahankali kan gadon yana kallonta lumshe ido tayi tana sauke ajiyan zuciya jikinta na bari har lokacin tana kare kirjinta bargo yaja ahankali ya rufa mata sanan yay pecking forehead dinta ya sauko daga gadon yanadan lumshe ido dan jikinshi ya mutu sosai ya tsaya agaban kujera tareda daukan wayan nashi yajuyo ya kalleta yanda take rawan sanyi ta lumshe ido hawaye na zuban mata, sosai shagala ya da kallonta wayarshi tadauki ruri da sauri ya juyo ya kalli wayan, kafe number yayi da ido har wayan ta katse another kira yasake shigowa juyowa yayi ya kalli Nadeera dayaga jikinta yarage rawa tana saukar da numfashi ahankali kaman bacci yasoma fizgar ta, picking wayar yayi yakara a kunenshi batare dayay magana ba.
Daga tachan bangaren Mum tace "Marwan sorry am calling da sassafe haka, ya jikin Princess? Tasha magani kuwa dan batason shan magani ko kadan u have to force her to take it" ta share hawaye da sauri dataji ya zubo mata, yanda yaji muryanta na rawan kuka yasa ahankali ya zauna kan kujera har lokacin kallon Nadeera yake, ahankali yace "tasha she's sleeping" gyadamai kai Mum tayi tace "thanks for taking care of my babygirl, please inada request" tai shiru tana sauraron shi ganin baice komiba yasa tacigaba tace "I want to come to your place, inaso nazo naga Princess am leaving the country probably tommorow or next yayan su Muhsin is seriously sick zamu fita dashi I want to come muyi sallama da Princess, akwai important magana danake so nayi dakai, akwai wasu documents danake so nabaka na Princess, i told you yesterday we are not her biological parents ko inaso nafada ma everything about her, please ka rikemin baby girl amana, wlh dudda bani na haifeta ba but I love her from d bottom of my heart, namafi son princess kan yarana maza biyu dana Haifa, please karkace bazaka bari na ganta ba I want to see her inaso nataho mata da some of her things datake so sosai okayyy" takara she maganan ahankali kaman zatai kuka shiru yayi yana kallon Nadeera yanda tai nisa sosai cikin bacci, murya chan kasa adake yace "text me the address of your location anytime you are ready zansa azo a daukoki" da sauri tace "thank you so much, yanzu ina hospital amma zan barshi da kaninshi idan nakoma gida na shirya nahada komi I will let you know" katse wayar yayi batare daya kara cewa komiba hakan yasa tafashe da kuka sosai, kiran wani ma'aikacin ta tayi tasa yamusu booking flight na tafiya Canada kafin ta bude motar tafito ko kadan batama son tunanin Abba, wucewa cikin hospital din tayi ta shiga dakinsu ta zauna tana kallon yanda Muhsin ke bacci yawani irin rame Ahmad na gefe kan kujera yana shan coffee a cup shafa kan Muhsin tayi tareda mai peck ta kalli Ahmad dake kallonta cike da tausayawa tace "bari naje gida zan aiko muku da abinci if anything come up call me" gyadmata kai yayi batare dayace komiba tawuce tafita ta shiga motar ta taja tabar hospital din.
Tana kaiwa gida dakinta ta wuce ta tai wanka shirya cikin hadadden soft lace orange color tai kyau sosai sanan ta dauko wani babban jakan trolley ta bude ta ijiye akasa, sababbin kayan data siyoma Nadeera daga tafiyan na Dubai da tayi ta kwasan mata tana zubawa sunada yawan gaske harda english wears, tadau wasu magungunan mata tahada mata su ciki sanan ta wuce dakinta ta kwaso mata novels dinta dayawa ta zuba ajakan da kayan makeup dinta, tafito waya tayi super market dinta tasa aka hado mata snacks dayawa sanan akai a su Ahmad abinci hospital, aka kawo mata snacks din gida duk tahada komi jakan yacika sanan ta zauna abakin gado ta turamai text na address din gidansu, bai wani dau lokaci ba yamata reply yace "nan da hour za'a zo daukan ki" OK ta turamai sanan tawuce dakin Abba chan safe dinshi ta bude ta tattaro documents din Nadeera na gidan marayun dasukai adopting dinta, da hotunan ta da aka basu na tana jaririya daga gidan marayun tahade su tass tasa a file ta fito daga dakin ta rufemai kofa tadawo dakinta tahade komi a hadadden handbag dinta sanan tariko handbag din da da babban mayafinta sai kamshi take tafito gateman takira yazo yaja akwatin fito da akwatin sukayi tsakar gida text ya shigo wayanta da sauri ta bude ganin Marwan ne taga yace "ki fito waje" ok ta turamai tama gate man magana yaja akwatin zuwa waje, ta yafa mayafinta tafita awajen ta nunamai ya ijiye akwatin sanan tamai godiya yakoma cikin gida ta tsaya tana kallon anguwan nasu ganin bataga mota ba, kaman daga sama taga wani bakin jeep yataho da arnen gudu saida gabanta yafadi agabanta akai parking aka bude gaba aka fito wani ne yafito fuskarshi a boye da mask, baya ya bude mata ta shiga ahankali kirjinta na bugawa sosai yarufe motan ya bude boot yasaka akwatin aciki ya rufe ya zaga ya shiga gaban motan ya zauna ya kunna motar batare daya kalletaba yace "hajiya dau bakin abun kusa dake kisaka ki rufe fuskar ki dashi" arude Mum ta kalli gefenta sai a lokacin taga abin hanunta har rawa yake ta dauka ta saka juyowa Omari yayi ganin ta rufe ko ina yasa yatada motar yabar anguwan dawani irin arnen gudu.
Tafiya sukayi na kusan minti 30 kafin yay horn kamal yabude musu gate suka shiga gidan ya bude motar yafito sanan yabude ma Mum baya tareda cewa "you can take it off now" zare bakin abin tayi ta ijiye tafito ahankali ta tsaya tanabin dankareren hadadden gidan da kallo, boot ya bude ya dauko babban jakan yaja sai kallonshi take yay hanyar shashin su yace "follow me" binshi tayi abaya tanabin ko ina na gidan yanda gidan keda fili har da play ground da abubuwan basketball ajiki ajiki ga football zube kusan shida akasa, bude kofan shashin su yayi tana biye dashi abaya gabanta na faduwa sosai agaban kujera ya tsayar da jakan ya nuna mata kujera, zama tayi ahankali tana kallon hadadden falon bana wasaba gashi sai kamshi yake ko ina tsaf tsaf dashi ga sanyin AC daya cika koina, kitchen ya wuce bai wani jimaba yadawo dauke da tray da drink da ruwa ke kai sai glass cup yaja yar karaman stool ya daura mata akai batare daya cemata komiba yay hanyar stairs yahau yawuce sama dakinsu ya shiga yana tuge mask din fuskarshi ya kalli Abdallah dake kwance kan gadonshi yana kallo da laptop dinshi ya makala earpiece akununshi zama yayi kan kujera sanan yatura ma Marwan text tana falo.