Kenza eBookz

Buzu book 3 complete - Chapter 1

Buzu book 3 complete - Chapter 1

Buzu book 3 complete Chapter 1: Buzu book 3 complete Chapter 1. 78

4,365 words

78

78 Gaban Nana ya faɗi, cikin tsoro da razani ta ce "Waye? Waye a nan?" Sai dai shiru ba a yi mata magana ba.

Ta kunna fitilar kawai ta ga Imam Hammad a tsaye a cikin ɗakin. Ja da baya ta yi a razane tana toshe bakinta saboda ihun da take shirin kurmawa saboda razani da tsoro. "Idan ki ka yi ihun da Asal ta ji ki, za ki yi mata bayanin abin da ya kawo ni ɗakin nan, kuma duk hukuncin da ta zartar a kan ki sai an yi miki shi, komai tsaurin sa."

Ta marairaice ido tana kallon sa cike da tsoro. Ya tako a hankali ya ƙaraso gabanta, ya zuba mata idanunsa da suka ƙara rikita ta, jikinta har tsuma yake yi.

"Wace ce ke?" Ya yi maganar yana kafe ta da idanunsa.

"Ni ba kowa ba ce" Ta furta jikinta na tsuma cike da tsoron ko yana hayyacinsa jiya da ta je turakarsa.

"Ki gaya mini wace ce ke? Kuma da wace manufar ki ka zo gidan nan?"

Ta rintse idanunta tana girgiza masa kai ta ce "Wallahi ni ba kowa ba ce ba, Matarka ce ma ta kawo ni nan"

"Kin sanni a wani gurin kafin nan?" Ta ɗago kai ta kalle shi, ta girgiza masa kai a hankali, idanunta na cika da hawaye.

"Kin hana ni cin ayaba, kin ci kin yi rashin lafiya, kin hana ni hawa kan taguwa, na hau na faɗo. Idan na ganki ina jin wasu abubuwa da ba na ganewa a jikina, tamkar ke ba ɗan Adam ba ce. Ɗanɗanon Abincinki na yi mini kama da wani Abinci da nake ci a wani guri da ba zan iya tunawa ba, idan ba Abincin da ki ka dafa ba, ba ya yi mini ɗanɗano a bakina. Ki na shafa irin turarena kin ba ni madara da habbatussauda, wani abu da ba kowa ya san ina sha ba. Ki gaya mini wace ce ke, kuma a ina ki ka sanni?" Ya yi maganar yana ƙara matsawa daf da ita yana ƙara ɗaga mata murya.

"Ni ban sanka ba, ban taɓa zuwa Agadez ba sai a wannan karon, ni babu abin da na sani game da kai" Ta yi maganar hawaye na ta sintiri a kan fuskarta.

Ya numfasa ya ce "Idan wani ne ma ya turo ki, ki ke yi mini wasa da hankali, ki ji tsoron Allah, jarrabawoyin da suka yi wa rayuwata ma ƙawaanya sun ishe ni. Kar ki bari na kama ki da kowane irin nau'i na rashin gaskiya" Ta yi shiru tana sunkuyar da kanta ƙasa.

"Nana ko?" Ta jinjina masa kai cikin tsoro.

"Ki yi haƙuri na tsorata ki, ba na son Asal ta gane wani abu, za ta ƙara tsanar ki ne." Daga haka ya juya ya bar ɗakin nata.

Neman guri ta yi ta zauna tana mayar da numfashi, saboda yadda ta tsorata.

*****

Sagir ne ya ɗauki Yusra suka tafi gidan su Shukura, domin ƙara jajantawa juna tare da su Hajiya Amina, ta kuma tabattar da iyayen Shukura ba sa zarginta da ɓatan Yusra kamar yadda take faɗa.

A babban falon gidan suka zauna, Hajiya Amina duk ta rame saboda tashin hankali da kuma damuwa. Gefe ga Yusuf yayan Shukura, da shi ma fuskarsa take ɗauke da damuwa. Bayan sun gaisa Hajiya Amina ta ce "Sagir har yanzu babu wani labari game da ɓatan Shukura ko?"

"Wallahi Mami babu, na yi sintirin gurin jami'an tsaro amma babu wani labari, kullum sai dai su ce mini a kan bincike. An kasa tracking ɗin in da wayarta take, abin dai sha'anin binciken na rasa gane wane iri ake yi"

Hajiya Amina ta ce "Babu komai, akwai Allah mu ci gaba da gaya masa, in sha Allah za ta kuɓuta"

Alhaji Zailani ne ya fito da shirin fita, Cikin girmamawa.

Bai amsa ba ya ce "Yaya ake ciki da batun Shukura haryanzu babu wani labari?"

"Eh Daddy, amma mu na ta addu'a in sha Allah za a gan ta"

"Ka ga ni fa na gaji da wannan kwana-kwanar, ta ɓangarena zan ƙara saka wa a tsananta bincike, dan kai kan ka ban yarda da kai ba. Ta yaya za a ce rana tsaka a nemi yarinya a rasa ga tsohon ciki, kai me yasa ba a neme ka an rasa ba ko matarka sai ita?"

Hajiya Amina ta ce "Haba Alhaji, ya za a yi Sagir ya sanya a sace Shukura a sace ya kai ta ina?"

"Ni ki yi mini shiru, babu abin da ba zai iya faruwa ba" ya gama bambaminsa ya fita.

Hajiya Amina ta ce "Ka yi haƙuri Sagir, kawai yana cikin tashin hankali da damuwar ɓatan Shukura ne. Dan Allah kar ka damu za a gan ta da yardar Allah"

Yusra ta ce "Da ƙawata tana nan wataƙila da tuni ta gaya muku inda Shukura take".

Gaba ɗaya suka kalli Yusra, ta ce "Eh Nana mana, ai kin tuna ta ko?" Ta yi maganar tana kallon Hajiya Amina.

Ta jinjina kai. Amma Sagir ya ce "Mami bari mu tafi, kin san ba ta da cikakkiyar lafiya ne"

Mami ta ce "Allah sarki, amma ta yi gaskiya na san Nana, a ina ki ka santa?"

Yusra sai ta yi shiru, saboda ba ta son ta ji an ce ba ta da cikakkiyar lafiya, amma tun da suka shigo gidan, ta ji ƙamshin Nana.

***** Nana kuwa bayan sallar asuba, ta kashingiɗa tana ta zancen zuci, tana tunanin mece ce mafitarta ta ƙarshe, ta fuskanci kullum al'amuran cikin ƙara rikice mata suke. Wayarta ta ɗaukko tana kallon hotunan Muhsin, kewarsa take yi sosai da sosai, har sai da hawaye ya cika mata ido. Sai ta yanke shawarar neman izini daga gurin Imam, ta je gida, dan ta ga ya fi Asal kan gado.

Sai dai wani abu mai kama da bacci ya ɗauke ta, sai dai ta iya kiran shi da dannau, wato sleep paralysis, da wasu kan ce aljani ne yake danne mutum, ya yi iya ƙoƙarinsa gurin tashi amma ya kasa. Iya ƙoƙarinta take son ta yi addu'a, amma ta kasa. Inuwar mutum ta gani ya shigo ɗakin, amma ba ta iya tantance wane jinsin ba ne ba, mace ko namiji. Inuwar na zuwa aka zare wayar da ke hannunta, aka fice. Cikin razani da tsoro ta farka a galabaice tana ta haki tana rarraba ido, amma ba ta ga kowa a ɗakin ba, ta laluba ta nemi wayarya ta rasa. Hankalinta ya yi mummunan tashi, ta ɗaga fulon, ta zazzage inda take zaune, amma babu waya babu dalilinta. Ta tashi cikin azama ta hau buɗe kayanta, ko wayar tana ciki, amma wayam babu waya babu dalilinta. Ta fita da sauri ko za ta ga alamar wanda ya shigo sashen amma ba ta ga kowa ba. Hankalinta ya yi mummunan tashi, saboda rashin sanin wanda ya shigo ya ɗauke mata waya.

Gudun masifar Asal idan ta makara gurin hattama abinci ya sanya ta shiga ɗakin girki. Ta fito jiki a sanyaye tana gyaran falon Asal ta fito, kamar Nana ta share ta sai kuma ta ce mata "Barka da wannan lokaci"

"Yauwwa. Amm kar ki damu da ajiyewa Imam abinci, tun asuba baya nan, za su yi zaman majalisar Sultan." Nana ta jinjina kai. Idan haka ne ba shi ne ya sake shigar mata ɗaki ba kenan, to ko Asal ce?

Da sauri ta ce "Amm ranki ya daɗe, na ce dan Allah.. sai kuma ta yi shiru kar ta tambaye ta, ta canza mata fassara.

Asal ta ce "Ina sauraren ki"

"Amm shikenan ba komai" Asal ta yi gaba ta yi waje abin ta.

Gaba ɗaya hankalin Nana ya ƙi kwanciya, ba ta san a hannun wa wayar take ba, ba ta san ta ina balli zai tashi ba, tun da wayar babu security a kai. Ba kuma ta tunanin ma'aikatan gidan, saboda ba su da ikon shiga wannan sashen.

***** Gaba ɗaya su ke zaune cikin shiga ta alfarma ana tattaunawa, Sultan ya ce "Ina mai farincikin sanar da ku cewa kamfanin masarauta na zinari, zai shiga wata yarjejeniya da ƙasar faransa a kan zinari da kuma sindarin uranium da muke haƙowa. Dan haka ina ganin sai mu tura Imam Hammad da Omar, su je su karanta tsarin yarjejeniyar. Sai kuma a nan gida mu na da taro shi ma, a kan yadda zamu bunƙasa harkar safarar raƙuma da muke yi zuwa ƙasashen ƙetare. Akwai buƙatar fito da sabbin hanyoyi na ƙara faɗaɗa kiwon su da kuma shige da ficen su. Ina ga wannan da kaina zan je taron tare Imam Asad, Zahradeen"

Tafawa Maleek ya ce "Wai dan Allah Jalaludeen ba ka jin nauyinmu da ka ke fito da son zuciyarka da son kan ka ƙarara a gaban jama'a?" Gaba ɗaya suka ɗaga kai su na kallon Tafawa.

"Za ka tura ɗanka yarjejeniyar Zinari da sinadarin uranium, mu kuma ka haɗa ka 'ya'yanmu da harkar raƙuma"

Abduou matawalle ya ce "Tafawa, yakamata ka san abin da ka ke faɗa fa, Sultan ka ke yi wa magana"

"Ban saka da kai ba, da ɗan uwana nake magana" Tafawa ya yi maganar yana dakatar da Matawalle.

Sultan ya yi murmushi ya ce "Ba abin da ka ke zargi ba ne Tafawa. Hammad ai ɗanka ne, kuma ni duk matsayinsu ɗaya a gurina."

"Ba matsayinsu ɗaya ba, me yasa ba ka tura Zahradeen ba sai shi, mutumin da ko cikakkiyar lafiya ba shi da ita?"

Imam Zahradeen ya ce "Mai girma Tafawa, da ni da Imam Hammad ai duk ɗaya ne, ni dan ya je masarautar Agadez ya wakilta babu wani abu a ciki"

"Yi mini shiru, kai har ka na da zarafin da ina magana da babanka ka din ga sanya baki? Ni na gaji da wannan bambanci da ka ke nunawa, sai ƙoƙari ka ke lallai sai ka tura ɗanka kan kujerar Sultan ta ƙarfin tsiya, bayan bai cancanta ba. Shi ba cikakkiyar lafiyar zuciya ba, ga rashin lafiyar ƙwaƙwalwa, kalli yatsunsa babu zobensa na tambari, ga shi tsawon shekaru da aure ba shi da magaji, ta yaya ka ke tunanin makaho ya jagoranci mai idanu? Ta yaya mutumi da shi kansa ba zai iya tsayuwa da ƙafarsa ya yi rayuwa ba za a ce ya wakilci masarauta kamar Agadez a harkar kasuwanci"

Cikin tsawa Sardaunan Agadez ya ce "Wane irin lafazi ne wannan ka ke yi Tafawa? Kar ka manta da wanda ka ke magana, babu ruwan masarauta da gaba ka ke da Sultan, zamu iya sanyawa a warware rawaninka a hukunta ka. Hammad ba ɗanka ba ne kai ma? 'yar ka fa yake aure, kuma ɗan ɗan uwanka ne, kai ba mai rufa masa asiri ba ne idan ma hakan ne? Batun zoben sa zamu yi bincike a kai, haihuwa kuma Allah ne yake bayar da ita, bai zama hujjar da za a ce an hana shi wata dama ba. Ko yana da ɗa ko babu idan Allah ya nufi ya yi mulkin Agadez wallahi sai ya yi" Gaba ɗaya gurin suka yi tsit.

Ya mayar da idonsa ga Sultan cikin girmamawa ya ce "Ina neman afuwa ya shugabana bisa ɗaga murya da na yi a gaban sarki"

Hammad ya dubi Sultan a tsanake ya ce "Ina neman a yi mini izini, zan ɗan fita" Da ka Sultan ya yi masa alama, ya yinƙura ya tashi ya fita. Zuciyar Sultan tamkar ta kama da wuta saboda damuwa da jin zafin kalaman ɗan uwansa ga ɗan nasa.

Kai tsaye Imam Hammad ya koma gida, zuciyarsa na yi masa wani irin zafi na maganganun da Tafawa ya faɗa a kansa. Ɗakin saukar baƙinsa ya wuce, da nufin ya zauna ya kaɗaice a ciki. Kawai ya tarar da Mahmoudu a ɗakin. Bai kula shi ba kawai ya nemi guri ya zauna idanun nan jawur. Mahmoudu ya tashi ya koma kusa da shi, ya kalli yadda idanunsa suka yi jawur ya ce "Imam, lafiya kuwa?" Yayi shiru kamar ba zai yi magana ba, sai kuma ya ce "Mahmoudu, ina son na roƙi Sultan ya cire ni daga duk wani abu da ya shafi harkar mulkin nan ba na so"

Mahmoudu ya waro ido ya ce "Saboda me? Kai ma ka san abin da ba zai yiwu ba ne ai. Ka riga ka kai matsayin Imam kuma ka san me hakan yake nufi"

"A cire ni a maye gurbina da wani, tun da akwa masu so. So nake na yi nesa da gidan nan, na samu nutsuwa na yi rayuwata cike da 'yanci yadda babu wanda zai dame ni ya takura mini. Gidan nan ji nake yi tamkar a kan wuta nake. A kan abin da bai taka kara ya karya ba an ci mini mutunci ana ce mini juya. Ni Tafawa yake ci wa mutunci saboda kawai Sultan ya ce na je faransa na wakilci masarauta? Wallahi wataran za su neme ni su rasa" "Mahmoudu a ransa ya ce wancan karon ma da ka gudu ni ka saka a bala'i'

A zahiri ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri, duk inda ka je ma ba zaka iya zama ba sai ka dawo, dan Allah ka yi haƙuri"

Ya yi wa Mahmoudu shiru, ya lumshe idanunsa.

Yana kwance a kan cinyarta, ya zuba mata idanu yana kallonta. Sai shafa gashin kansa take yi tana yi masa murmushi mai ƙayatarwa. Bai yi mata magana ba, ita ma ba ta yi masa ba, amma yanayin ya yi masa daɗi sosai da sosai.

Wata babbar mace ce a zaune, tana ta huci tamkar za ta fashe, cikin takaici da ƙunar rai take kallon matashin saurayin da yake gabanta. "Zahradeen wai kai wane irin mutum ne mara kishin zuci da bai san ciwon kansa ba? Ina nan na samu labarin ka na cewa Sultan wai a tura Hammad wakilci kai da shi duk abu ɗaya ne, a gidan uban wa ku ke abu ɗaya, ana ƙoƙarin nemo muku 'yanci, amma kai kana shirme da shiririta?. Ƙarara Sultan yake nuna bambanci a tsakaninku ammma kamar ya yi maka asiri ka zama nusari. To wallahi ni ba nusara ba ce, ban tsaya tsayin daka ka zama Imam ba, sai dan ka zama Sultan ɗin Agadez. Dan haka ba zan zuba ido shashancinka ya ɓata mini wahalata ba na gaya maka". Zahradeen ya yi shiru bai ce komai ba, shi sam bai ga wani abu da Sultan yake yi na nuna fifiko a kan Hammad ba, kawai yana ba shi kulawa ta musamman ne, saboda yanayin matsalar hawan jini da yake da ita, da kuma rashin mahaifiya. Aka ci gaba da dambarwa, a kan tafiyar sa Faransa. Ko da aka koma zaman tattaunawa, Mayan 'yan majalisar Sultan ra'ayinsu ya kasu biyu, wasu su na goyon bayan a tura Hammad, saboda nagartarsa da jajircewa ya cancanta mussaman da duk ya fi sauran Imam Imam ɗin ilmi da mu'amala, ga yarurruka da yake ji. Ya yinda wasu suka goyi bayan Tafawa a kan Hammad ba zai ce wakilci Agadez ba, sai sun ji ba'asin zobensa, sai kuma sun ji matakin lafiyar ƙwaƙwalwarsa. Da rahoton lafiyarsa na tsawon shekarun da ya yi a faransa. Wannan ƙa'idoji da suka shimfiɗa ƙa'idoji ne da sai an kwashe lokaci kafin cika su, wanda har lokacin taron ya zo ya wuce, ba a kammala cika su ba.

Ganin gurin zai sake yamutsewa, ya sanya Imam Hammad yin gyaran murya. Cikin girmamawa ya ce "Ina godiya matuƙa da wannan dama da aka so ba ni, amma zaman lafiya da kwanciyar hankalin Agadez shi ne a gaba da komai. Ina roƙon a yi mini alfarmar yi mini afuwa, ba zan samu damar yin tafiya wakilcin nan ba, sakamakon hali na rashin lafiya da nake fama, ciwo zai iya kama ni a ko ina, dan haka Tafawa ya yi gaskiya, ina buƙatar hutu"

Cikin tsawa Sardauna ya ce "Ba kai ka ke da wannan hurumin ba."

"Mai girma Sardauna, gaskiya Tafawa ya faɗa, ban cancanci duk wannan abubuwan ba, shugabancin Imam ma zan sauka na nemi lafiyata"

"Mun san ba ka da lafiya, amma ka ka na kan magani, dan haka larura ba za ta hana ka aiki ba"

"Larurar ƙwaƙwalwa, mahaukaci ba zai wakilci masu hankali ba, ina neman afuwarku"

Daga wannan maganar ya yi waje, saboda yadda idanunsa suka yi jawur, jikinsa ya fara tsuma.

Tsit gurin ya yi aka hau kallon-kallo.

Sardauna ya ce "Ka ga abin da ka janyo ko?"

"Ai ba ƙarya na yi ba, shi ya faɗi cewa ƙarya nake yi ɗan sa ba mahaukaci ba ne?" Ya yi maganar yana kallon Sultan.

AREWABOOKS

Har wani duhu yake gani a idanunsa, saboda matsanancin ɓacin rai da tashin hankali. Mutumin da yake uba a gare shi, shi ne ya yi masa wannan kausasan laffuzan a gaban jama'a. Ya daɗe yana nuna masa ƙiyayya, amma lamarin bai fito ƙarara ba sai bayan da ya zama Imam. Mussaman wannan dswowar da ya yi, dan ya matsa a kan lallai sai ya ji wani ciwon ne ya zaunar da shi a ƙasar waje har shekara biyu, kuma aka hana kowa zuwa duba shi? Ya kawo kai cikin falo, Nana tana ta aikace-aikacenta. Ɗan turus ta yi bayan da ta tuna Asal ta ce mata ba yanzu zai dawo ba. Fuuu ta ga ya nufi uwar ɗakinsa. Ta ɗan taɓe baki ta ci gaba da aikin gabanta. Sai dai zuciyarta na kan abin da ya sanya shi cikin fushi da tashin hankali haka. Duk da ba ta da wani kusanci da shi a wannan Duniyar tasa, amma mutum ne mara magana, amma yana da yawan fara'a.

Asal ta fito daga wanka ta gan shi kwance a kan gado. Ta kalle shi ta ce "Amour ya na ga ka dawo kuma? Lafiya kuwa?" Muryar Asal kawai ta fusata shi, saboda abin da mahaifinta ya yi masa a fitarsa. Dan haka ya yi mata banza. Ta nufi gaban mudubi ta amsa wayar da take ta ringing, ta ajiye ta dawo ta dube shi ta ce "Sultan yana neman ka a sashen sa yanzun nan" Ya yi mata shiru, bai yi magana ba, ta nufe shi ta zauna a kusa da shi, ta ɗora hannunta a kan kafaɗarsa. Ya tashi zaune a fusace ya ture hannun Asal, ya tashi ya fita. Sororo ta tsaya tana mamakin me yake damunsa haka? Gaba ɗaya ya fita ya bar sashen.

**** Cikin matsananciyar damuwa Mama take kallon Jamila da ta yi wata irin rama mara fasali, duk ta bushe ta yi haske sai uban kai ɗauke da gashi.

"Jamila ni fa na rasa gane kan ki gaba ɗaya, kalli yadda ki ka koma, dole ki shirya mu je gurin masu magani ko mayu ne suka kama ki, ki ke ta wannan wahalar duk kin ƙi lafiya"

"Ni babu wasu mayu da suka kama ni"

"To idan ba mayu ba wannan ciwon na mene ne haka? Fitar nan ma da ki ke yi gurin kasuwancin naku kin daina gaba ɗaya"

"Ki ƙyale ni zan warke ne" Ta yi maganar cikin ƙosawa da maganganun Mama.

Su na haka Yaya Atine ta yi sallama, Mama ta amsa tana yi mata maraba.

Mama ta ce "Ke ki ke tafe a yammacin nan?"

Ta ce "Wallahi kuwa, na ga kwana biyu ban leƙo ba, na ce bari na shigo, Isan ba ya nan ne?"

"Eh ya fita baya nan"

"Ita kuma wannan fa?"

Cikin damuwa Mama ta ce "Ba ta da lafiya ne, nayi-nayi da ita, mu je gurin mai magani ta ƙi yarda, ga na Asibitin an yi ya ƙi jiki kullum ƙara rikicewa yake yi" "To me yake damunta ne har haka?" Mama ta ce "To gata nan dai, kullum zazzaɓi ba ta kuma son cin abinci ko fita ba ta yi, na Asibitin ya ƙi yi mata, mu koma na gargajiya ta ƙi"

Yaya Atine ta ɗan zura wa Jamila ido, har sai da haushi ya kama Jamila, ta tashi ta bar gurin. Yaya Atine ta ce "Mhmm" Ta ɗaukko wata hirar daban.

Ba ta wani jima ba ta yi wa Mama sallama ta tafi, sai dai cikin sa'a ta haɗu da Baba a ƙarshen layin, dan haka ta zauna suka dasa hira a hanya. Ta ce "Ashe Jamila babu lafiya?" "Eh wallahi ana ta fama, an kasa gane abin da yake damun ta"

"Lallai, to gaskiya yakamata ku zurfafa bincike dan kuwa ɗan yau ka haife shi ne, amma ba ka haifi halinsa ba" Cikin rashin fahimta ya ce "Me ki ke nufi?"

"Ni babu abin da nake nufi, balle a ce na ce, ni dai kawai na ce a zurfafa bincike ka ga tafiyata" Ya yi shiru yana nazarin maganganun 'yar uwattasa.

****

Cikin fushi Sultan yake kallon Imam Hammad, ji yake yi tamkar ya kwaɗa masa mari ko ya huce. "Sai yanzu ka ga damar amsa kiran nawa?"

Ya girgiza kai ya ce "A yi mini afuwa, jikina ne ya so motsa mini shi ya sanya ban samu fitowa ba"

Sai kuma ya sassauta murya ya ce "Wani abin ne ya faru da kai bayan tafiyar taka?" Ya girgiza wa Sultan kai.

Cikin rarrashi ya ce "Hammad, ba a cin nasara da karaya da kuma miƙa wuya farat ɗaya. Kuma Tafawa Maleeka bai yi ƙarya ba, ina son ka gaje kujerar Sultan ba dan komai ba sai domin ina buri da fatan ka gyara kura-kuran da na aikata a baya. Ni ba ina burin ka zama Sultan domin son zuciya ko wani abu ba, ko iya haka Allah ya yi maka mai kyau a duniya, ina yi maka fatan mai kyau a Lahira. Ka ma da ilimi, ka na da dukiya, ka na da mulki iko ka ke buƙata gurin aiwatar da wasu abubuwan. Kai kaɗai ne kujerata ba ta gabanka, kuma ka fi ni jajircewa da tsayawa a kan ra'ayinka da aƙidarka, burikanka a kan Agadez da ƙudure-ƙudirenka abubuwa ne da za su sauya rayuwar mutane da dama, saɓanin sauran da hawan kujerar ne kawai a gaban su, ba ƙalubale da abubuwan da suka kamata ba. Dan Allah ka yi haƙuri ka jure kar ka watsa mini ƙasa a ido. Wannan nagartar taka ya sanya manyan nan na majalissata suka ƙara tsanarka ba wani abu ba"

Imam Hammad ya numfasa ya ce "Abie na ji duk bayananka. Amma ka yi haƙuri na riga na karaya, kalaman da ake jifa na da su sun yi tsauri da muni, su na taɓa zuciyata da yawa"

"Na sani, ba na buƙatar ka musanta abin da na zo da shi, ka yi mini biyayya kawai. Kuma majalisa sun zartar da hukunci a kan Tafawa bisa abin da ya aikata"

Hammad ya kalli Sultan ya ce "Ina fatan ba wani abin mai tsauri suka yanke a kansa ba, kar alaƙa tsakanina da shi ta ƙara yin tsami, ga 'yar sa ina aure. Ko ba komai uba ne a gare ni, kuma Asal ƙanwata ce kuma matata"

Sultan ya girgiza kai ya ce "Kar ka damu, hukuncin ba zai shafi nasaba da dangantaka ba, ka je ka samu ka huta" Ya risuna cikin girmamawa ya yi godiya ya fita.

Bayan fitarsa Sultan ya zauna, zuciyarsa cunkushe da damuwa, tunani yake yi yaya aka yi Tafawa ya san batun larurar Hammad. Ya yi tunanin ko Asal ce ta gaya masa, amma ko Asal ba ta san taɓin hankali Hammad ya yi ba, kawai dai ciwo ne yake kama shi, gangar jikinsa ta sauya, ya din ga wannan jijjigar da kakarin. ***** Kaiwa da komowa Tafawa yake yi a cikin falonsa, zuciyarsa a cunkushe da baƙin ciki, bayan tuna yadda wasu daga cikin majalisar Sultan suka ƙaryata shi, bayan da ya faɗi cewa Hammad yana da taɓin hankali. Ya yi ƙwafa ya ce "Da ni ku ke zancen, sai na tabattar wa da Duniya ɗan ka mahaukaci ne, sai ya yi hauka tuburan Duniya ta gani ta shaida, kujerar da ka ke ƙoƙarin cusa shi ya hau, sai ta zama haramiyarsa ta har gaban Abada. Mulkin ai ba da shi aka haifoka ba, da za ka ce lallai ka yi shi ma sai ya yi ba. A wancan karon mu na ji mu na gani, aka ɗora ka aka ce bamu cancanta ba, a wannan karon dole sarauta ta bar gidanka ta dawo gidana, Asadullah sai ya hau kujerar Sultan, ko ka na raye ko ka mutu".

***** Tun da ya koma gida Asal ta share shi, shi ya manta ma abin da ya yi mata, ya ga tana basar da shi ga damuwa da yake ciki.

"C'heri'"

Ta ɗago ta kalle shi. "Me yake faruwa ne?" Ta girgiza masa kai alamar babu komai. "Idan na yi miki laifi ne, ki yi haƙuri, ina cikin damuwa ne kwanakin nan, ki din ga yi mini addu'a" Ya yi maganar yana hargitsa gashin kanta da ta gyara. Ya nemi guri ya kwanta ya lumshe idanunsa, yana fatan bacci ya ɗauke shi, ko ya samu sauƙin wannan damuwoyin. Yana jin ta ta kashe fitilar ɗakin, sai hasken fitila na gefen gado wanda ba mai takura ba ne. Ta hau kan gadon ta kwanta a bayansa, ta zura hannunta ƙirjinsa. A hankali ya juyo, ya rungumeta sosai a jikinsa yana shafa bayanta, duk da ta ji haushin abun da ya yi mata ɗazu, amma da yake ya ƙware a iya mantar da mutum laifin da ya aikata masa, dole ta ba da kai bori ya hau. A hankali ya ji jikinsa ya fara ɗaukar zafi. Ya raba Asal da jikinsa saboda yadda yake jin san tamkar an saka masa fetur an kunna wuta a jikinsa. Ya miƙe ya din ga kaiwa yana komawa a ɗakin, yana maimaita ya hayyu ya ƙayyum. Ya shiga banɗaki ya haɗa ruwan ɗumi ya yi wanka ya fito. Kasa jurewa ya yi jin yana neman ya fita daga hayyacinsa, ya fita falo. Yana fita ya ji wannan dadaɗan sanyin ya ratsa shi. Kan sa tsaye ya nufi inda yake jin sanyin na fitowa wanda hanyar ɗakin Nana ne. A corridor din gurin ya yada zango, ya samu guri ya zauna, ya jingina da jikin bango yana numfarfashi.

*****

Kwanaki biyu a tsakani, aka kuma zama, sai dai a wannan karon ba da duka Imam ɗin aka zauna ba, Hammad ne kawai, sai manyan masu faɗa a ji na kusa da Sultan, wanda an yi zaman ne saboda abin ya shafi Hammad ɗin.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull