Cutarwa complete by ayshercool - Chapter 18
Cutarwa complete by ayshercool Chapter 18: Cutarwa complete by ayshercool Chapter 18. Da sauri ummi ta ɗauke kanta tare da cewa "Yi haƙuri"
3,337 words
Da sauri ummi ta ɗauke kanta tare da cewa "Yi haƙuri"
"Da haƙurin ta mutu sadakar nawa ki ka bayar? Bana son kallo"
"Ai na ce kiyi haƙuri" ta faɗa a sanyaye.
A ranta ta ce 'Dama nima fara ce, wataƙila da ba za a tsane ni ba. Amma ai akwai baƙaƙe da yawa da ake son su, ni meyasa ba a sona?' ta tambayi kanta, wasu hawayen na rige-rigen zubowa.
Maryam ta zauna a kusa da ummi, ko a jikinta ganin ummi ta kifa kanta.
Sai da malami ya shigo ajinsu sannan ta ɗago kanta, ya yi musu karatun da zai yi musu, sannan ya basu class work.
Sai dai fa maryam ba ta iya komai ba, ta din ga rarraba ido, ga malamin ya jaddada cewar duk wanda ya faɗi sai ya zane shi.
Ganin lokaci ya kusa cika, ya sanya ummi buɗe mata takardarta ta ce "ki kwafa ya kusa karɓa" babu kunya maryam ta kwafe duk abun da ummi ta rubuta.
Lokacin sallar la'asar yayi, ɗalibai na ta ƙoƙarin fita daga ajin, ba tare da tuna alkhairin ummi ba, maryam ta hankaɗeta zata fita, bisa tsautsayi ummi ta faɗi ta fama ƙonuwar da take cikinta.
Ƙara ta saki, tana girgiza kanta, duk ɗaliban suka tsaya suna kallon ummi, ganin jini yana tsatstsafowa a rigar uniform ɗin ta.
Maryam a tsorace ta ce "Na shiga uku" ta durƙusa ta ɗago ummi, a zaton ta ko cikin ummi ne ya ɓule.
Ummi sai yarfe hannu take yi tana kuka, ɗalibai suka taru a wurin, malamin da ya fita daga ajin ya dawo ganin ɗalibai a wurin yana tambayar meyafaru, aka gaya masa maryam ce ta hankaɗeta ta faɗi.
Cikin tashin hankali ya ce a kai ummi ofishin malamai, ita ma maryam ta bisu sai an hukunta ta.
Cikin tashin hankali malamai mata suka ɗaga rigar ummi, ana ƙoƙarin gano menene yake jini a cikinta, sai dai ba kyan gani, suka tarar da ƙonuwar ta jagwale, ga ruwa ga jini ya dame da zumar da take sakawa.
Maryam na ganin haka ta fashe da kuka, ta zata duk faɗuwar ce ta janyo haka.
Shugaban makarantar ya dubi Maryam ya ce "Wato maryam ba kya ji ko? Zaki gane kuskurenki, sai kin daku yau ɗin nan, makauniya ce ke da zaki tureta ta faɗi".
Malamin ya dubi ummi ya ce "Ke ya aka yi ki ka zo da wannan ciwon makaranta, meya sameki haka?"
"Ba maryam ce ta ji mini ciwon ba, dama na ƙone a gida"
"Da me ki ka ƙone, kuma an kai ki asibiti?"
Ta ce "Eh an kaini"
"A'a wannan da an kai ki asibiti, da ba ta jagwale haka ba, kuma da ba a bari kin saka kaya ba, ki gaya mini gaskiya da me ki ka ƙone?" Malamin yayi maganar cikin zare ido.
"Da ruwan zafi"
"Mamanki ta san kin ƙone?" Ta girgiza kai alamar a'a.
"Meyasa baki gaya mata ba?"
Cikin kuka ta ce "Ai ban san in da take ba"
"A'a to ina mutanen gidan da ki ka ƙone ɗin, ba ƴar gidan dr. Yahaya bace ne?" Ta ɗaga kai alamar eh.
"Malama zuhra, a nemo abun hawa a kai yarinyar nan asibiti a dubata, ke kuma maryam mu je office ɗina sai na hora ki"
Maryam ta fashe da kuka tana magiya, cikin ƙarfin hali ummi ta ce "Malam dan Allah kayi haƙuri, ba ta san ina da ciwo ba, na yafe mata ai"
Ya ce "To zan duba, tashi a kai ki asibiti, daga nan a mayar da ke gida".
A asibitin ma, ma'aikaitan sun yi faɗa sosai a kan sakaci da lafiyar ummi, dan da ƙunar zata iya zama infected ta taɓa sauran sashin jikinta, bayan ta zama gyambo.
Suka ce lallai a kula da ummi, a samu ƙunar ta warke, kuma a zurfafa bincike dan wannan ƙunar ba tayi kama da ta ruwan zafi ba.
Ummi ta sha kuka, saboda yadda aka dirje ƙunar nan tas, aka saka magani, aka bata magungunan sha.
Sai dai da malama zuhra ta ce ta kwatanta musu gidansu a mayar da ita ta ce "A'a a mayar da ni makaranta, idan aka tashi zan ɗaukko ƙannena daga islamiyya"
"A haka da wannan ciwon" malamar tayi maganar tana kallon ummi.
Ummi ta jinjina mata kai.
"A'a ba zai yiwu ba, mu je gidan naku, a saka wani ya ɗaukko su".
Kuka ummi ta fara tana yi wa malamar magiya, a kan ta ƙyaleta a tashi ta ɗaukko su daga makaranta.
Ba ta da zaɓi, suka koma islamiyyar ta gaya wa shugaban makarantar duk abun da ya faru.
Suka yi waya da kawu yahaya, suka tattauna, ya ce a mayar da ummi gida, zai yi waya makarantar yaran, su jira yayansu sai su taho tare.
Da ƙyar ta yadda da hakan, saboda tana tsoron abun da ka iya biyo bayan rashin ɗaukko su daga makarantar.
Cikin sa'a malamar ta fuskanci yanayin da ummi take ciki na tsoro, dan haka a ƙofar gida suka yi sallama ummi ta shiga.
Har ta tafi ɗakinta ba wanda ya san ta dawo, saboda ana ta hada-hada a gidan, ƴan barka na shige da fice.
Ta kasa fitowa daga ɗakin, saboda tsoron kar su kuma dukanta.
Sallamar kawu yahaya ta ji a ɗakin, ta tashi da sauri, tana gaishe shi.
"Ya jikin naki?"
"Da sauƙi"
"Mu ga ciwon" a hankali ta ɗaga masa cikinta ta ƙonu sosai da sosai, ya zubawa ƙunar ido sannan ya kalleta ya ce "ya aka yi ki ka ƙone?"
"Da ruwan zafi" ta faɗa tana ƙiƙƙifta ido, saboda ta san ƙarya tayi.
"Meyasa baki gaya mini ba?" Tayi shiru ba ta ce komai ba.
Wannan ƙunar ba ta yi kama da ta ruwan zafi ba, ki gaya mini gaskiya.
"Da gaske nake..." Ba ta ƙarasa ba ya ce "Shaidar iron tayi, kalli yadda shape ɗin ƙonuwar ya tafi, ki gaya mini gaskiya".
Ta ɗan yi jimm sannan ta ce "Idan na gaya maka ba zaka gaya wa maman su Abdul ba?"
"Ba zan gaya mata ba"
"Ina guge Abdul ya ce zai tayani, ya ƙonawa mamansu riga, ta zata nice shi ne anty rahama ta danneni, suka ɗora mini iron. Dan Allah Abba ka gaya musu bani na saka anty farida ta faɗi ba, sun ce ni na kusa kasheta wallahi ba ni ba ce, fitsari na yi da na ji zafi, shi ne ta zame ta faɗi" tayi maganar tana sheshsheƙar kuka.
Ayshercool 08081012143 What's app only please 🙏 *CUTARWA*
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
BRIGHT PENS (FREE BATCH)
P16
PAID ADVERT!.
Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi. Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku
Oll types of Turaran wuta Sandal Halut Irik Difur Gab Gab Kajiji Habil Nabak Humra Kulakcha Dilke da kalta Kayan Garan jiki Muna turara Kaya Kujerar garan jiki Kannada Madarorin turare masu kamshi Man garan gashi Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921
*TALLA!TALLA!TALLA!* *INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*. *BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU* *MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*
BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI
P16
Ƙurriii kawu yahaya ya yi wa ummi da ido, abun ya girmame shi, bai taɓa zaton mugunta da zaluncim da farida za ta yi wa ummi zai kai haka ba.
Ya sauke numfashi da ƙyar ya ce "Ya isa haka ki share hawayenki, ki daina kukan ya isa ba zan gaya mata ba, kuma na san ba zaki taɓa iya cutar da kowa ba, duk wanda ya cutar da ke, shi ma Allah ba zai bar shi ba, ki yi haƙuri ummi, in sha Allah gobe in Allah ya kaimu zamu koma asibiti, tun da yau an yi dressing ɗin.
Mun yi magana da malaman islamiyyar ku, na biya kuɗin maganinki, sannan sun ce ki zauna a gida sai kin warke".
Ummi kamar ta ce masa gara ta cigaba da zuwa a haka, dan ta san zamanta a gidan nan ba hutawa za ta yi ba, amma ta dake ta ce "To kawu na gode sosai"
"Kar ki damu, Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana ummana"
Murmushi ummi tayi, tana so ta ji ya kirata da ummana ko ummina, hakan yana yi mata daɗi, kuma yana tuna mata da maman da babanta.
Ya ce "Au, na manta ban gaya miki ba, mun kusa komawa sabon gida fa, bamu taɓa zuwa kin gani ba ko"
Ta faɗaɗa murmushin ta ta ce "Allah ya nuna mana, wannan wa za a barwa, na ga shima mai kyau ne"
"To ko in bar miki, tun da kin fi son nan?"
Murmushi ta yi ta ce "Ai ni macece ba zan iya zama a gida nikaɗai ba, amma ina son gidan nan"
"Can yafi kyau ai, idan muka koma zaki gani"
"To Allah ya sanya albarka, to nan su iya ne za su dawo su zauna?"
Sai da ya ƙara kallonta da sauri, ya ce "Su iya kuma?"
Ta ce "Eh, su baro ƙauye su shiga makarantar islamiyya, makarantar mu har da matan aure da tsofaffi suna zuwa asabar da lahadi"
Bakomai a ranta ta faɗi hakan, kawu yahaya yayi murmushi saboda magana tayi cikin magana mai ma'ana, ba zaka san ummi na magana ba, sai ka zauna da ita, a haka kamar ba ta magana.
Sai kuma ta sake cewa "Kawu, kaga da ka san in da mama take ita ma zaka ɗaukkota ka dawo da ita nan? Sai mu zauna ni da ita a gidan nan sai ku koma sabon gida"
Tausayin ummi ya kama shi, ya ce "Ki na kewarta ko?"
Ta jinjina masa kai alamar eh.
"In sha Allah zan nemo in da take, zan haɗa ki da ita, sai dai ba zan so na kawo ta nan ita ma ta din ga shan wahala kamar yadda ki ke sha ba"
"To ai ba zan bari ta sha wahala ba, ni zan din ga yin duk wani aiki, idan na iya sana'a na din ga saya mata abubuwa, idan ka gano ta dan Allah kar ka kai ta wurin Iya, Iya ta ce ba ta son ta, wai mama mayya ce..."
"Ummi ya isa haka, ki daina tuna abubuwan da suka shuɗe wanda za su dinga ɓata miki rai, ki yi karatu sosai yadda maman idan ta gan ki za ta yi alfahari da ke"
Ta gyaɗa masa kai ta ce "In sha Allah" kai da ganin yadda ta ɗan kwaɓe fuska, ka san akwai tarin abubuwa cunkushe a zuciyarta da take burin amayar da su, sai dai babu wanda zai tsaya ya saurareta, to wa ma ya damu da ya zauna da ita balle aji matsalarta.
Cikin son kawar mata da wancan tunanin, ya yi murmushi ya ce "Ki na buƙatar wani abu ne ummana?"
"A'a bana son komai"
Ya ajiye mata ɗari bibbiyu guda biyar, ya ce "Gashi idan kina buƙatar wani abun ki yi amfani da shi".
Kallon kuɗin ummi take yi dan da yawa a wurinta, kan tayi magana ya tashi ya fita, zuciyarsa na yi masa zafi.
Ɗakin farida ya wuce kai tsaye, ya tarar da ita tana saka kaya a gaban mudubi, ta ɗago ta kalleshi ta ce "Ya dai?"
A take ya nemi karsashinsa da zafin zuciyar da ya zo da ita ya rasa, duk yadda ya so yi mata magana a kan ummi, sai ya kasa kawai ya tsaya yana kallonta.
"Kana buƙatar wani abu ne?" Kawai ya girgiza mata kai ya juya ya fice, yana jin baƙin cikin kasa yi mata magana a kan cin zarafin da ta yi wa ummi.
Duk da ƙonuwar cikin ummi, haka ta cigaba da yin aikace-aikacen gidan, kuma muddin ta fito ƴan uwan farida suka ganta, sai sun ci zalinta, ko sun aibata ta.
Hatta makarantar boko, kawu ya hanata zuwa, ya ce sai ta samu sauƙi tukuna.
Dan haka, a hakan take naɗe rigar ta, ta bar wurin ƙunar a waje tana shan iska, tana aikinta.
Abdul ne kawai yake tausaya mata yake yi mata sannu, dan shi har ga Allah yake jin matuƙar tausayinta.
Mopping kuwa a rana a gidan nan, sai tayi sama da sau sha biyar, wanke-wanke kamar gidan da ake rabon sadaka, banda ɗorawa da saukewa da kula da yaran baƙi, tana yi ana zaginta.
Wani lokacin haka zata fama ƙunar tayi ta kuka.
Kawu yahaya ya din ga kai ta dressing, Allah ya taimake ta ƙuna ta fara warkewa. Tana matuƙar son ta ɗauki jaririyar da antyn ta haifa, sai dai an ƙi bata damar hakan, daga nesa take hangen ƴar, zuciyarta har raya mata take ta ce a bata ta ɗauketa, amma da ta tuna hakan na iya haifar mata da cin mutunci, sai ta haƙura.
Farida ta je ta tarar da mijinta a bedroom ɗin sa, yana ta aikin takardu.
Ta zauna tana cika tana batsewa ta ce "Dr. Wurinka na zo"
Ba tare da ya ɗago ba ya ce "Ina jin ki"
Ta ɗan taɓe baki ta ce "Jibi in Allah ya kaimu ne fa suna, haryanzu baka ce mini komai ba, baka bayar da kuɗin hidimar suna ba, kuma wuri nake so a kama ka sani, amma ka ƙi magana".
"A wannan karon babu suna, sauran ukun da aka yi Allah ya amfana, idan Allah ya kawo wata a gaba ayi".
A fusace ta ce "Ban fahimta ba?"
"To ki jira daga lokacin da ki ka fahimta, sai ki tashi ki bani wuri"
Ta miƙe tsaye ta ce "Yahaya ni zaka wulaƙant, na gama gaya wa mutane da taron suna ka ce ba za ayi ba"
"Hakika kawai zan yi, za a kawo raguna biyu manya, ayi hakika na sanyawa yarinya mariya, sai ki koma ki gaya wa mutanen babu suna"
"Mariya kuma? Wace irin mariya ana zaune ƙalau, sunan uwar waye mariyar da zaka sanya wa ƴa ta, haka muka yi da kai? To ba gara Salman da na ce bana so ba, a kan wata mariya, kamar dattijuwa"
Ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "To ki koma ki bibiyi tarihin fiyayyen halitta, zaki gane suna ne mai daraja da ma'ana".
Aikuwa ta hau ta din ga surfa bala'i, duk yadda ya yi ƙoƙarin sanar masa da cewa, hukuncin zaluncin da ta yi wa ummi ne, ya sanya ya hukunta da haka ya kasa, saboda tuni ta kai sunansa wurin malamai, a kan ko ya mayar da ummi, ko kuma duk izayar da zata yi mata ba zai iya magana ba, yarinyar ta gaji ta bar gidan.
Tun a haihuwar inteesar, ya so saka mata sunan mahaifiyarsa Salma, farida ta ce ba ta san zancen ba, ba ta so, aka saka sunan ta ta uwar, haihuwar khausar ma, ta ce sunan yayarta da ta rasu za a saka, wannan ma suna ta kai ruwa rana a kan ita gaskiya ya bari sai wani lokacin a saka Salman, tun da sanyan wa ƴaƴa sunan iyaye ba wajibi bane ba, wai Jidda za a sakawa yarinyar, tana son sunan.
Shi kuma ya sanyawa yarinyar mariya, sunan mahaifiyar ummi, wanda ita Farida sam hankalinta bai kai kan cewa sunan babar ummi bane ba.
Ya fice daga ɗakin ya bar ta tana ta sababi da kumfar baki, ya zo falo ya tarar da ƴan uwan farida na ta cin abinci da lemuka da nama zuƙu-zuƙu.
Ga ummi da ɗagaggiyar riga, tana ta mopping, tare da haɗa kwanukan da suka ɓata, sai ta kwashe zata tafi, sai a kirata a jefa mata wani kwanon.
Gyaran muryar da yayi ne ya sanya duk suka juya, mai neman gyale nayi su rufe jikinsu, masu gyara zama na yi.
"Yauwwa, ina godiya ga Allah subhanahu wata'ala, da kyautar haihuwar mace da ya bani, ina kuma godiya a gareku wurin tsayawa tsayin daka, wurin kula da ƴar uwakku, duk da hakkina ne. Ina godiya sosai, dan Allah idan kun gama cin abincin, zaku iya tafiya gida, rahama zata iya cigaba da kula da ita. Ba za a yi taron suna ba, ga yanayin rayuwa, gara a tattala kuɗin tayi jego mai kyau, kuna iya tafiya idan kun gama kan magariba dan Allah, sunan jaririya mariya, za a dinga kiranta da noor"
Gaba ɗaya turus suka yi suna kallonsa, tun da suke zuwa gidan, su yi duk hauka da rashin hankalin da suke so, bai taɓa yi musu magana ba, sai yau, dan maganar tasa ta wani fannin kamar cin fuska.
Ummi kuwa washe baki tayi, jin an sakawa jaririyar mariya, duk da ba ta san dan sunan mahaifiyarta ya saka sunan ba, amma wani irin daɗi da farinciki ya ratsa ta.
A hankali ta ce "Allah ya raya noor takwarar mama"
Daga in da yake ya hango farinciki a kan fuskar ummi, yayi murmushi ya fice, yana tawasalli da farincikin da ya sanyata yana neman biyan buƙatunsa a wurin Allah.
Farida ta sha kuka, da yin alwashi kala-kala a kan yahaya, saboda yadda ya wulaƙanta ta, ya tozarta ta a gaban ƴan uwanta.
Suka din ga rarrashinta, tare da bata shawarwari daban-daban.
Babbar yayarsu ta xe "Duk sakacinki ne, waye ya gaya miki ana barin namiji haka, kyakywar mallaka zaki nema, ta mai da ɗan gida bawa, ki juya shi yadda yake so, kar ki yi bori da yawa, ki girgiɗe auren, duk cikinmu babu wanda yake cikin rufin asiri da kwanciyar hankali kamar ke, kar ki yi mana sagegeduwa, amma dole mu zage damtse".
Suka din ga zigata, ƙarshe kan sallar magariba suka watse daga gidan sai rahma, rahama kuma ba wani abun kirki take yi mata ba, saboda shegen son jiki ne da ita.
Bayan watsewar ƴan gidansu, ta ƙuduri aniyar ƙuntatawa dr. Ta hanyar nuna halin ko in kula ga yarinyar, gashi mutum ne mai mugun son yara, baya son ya ga ƙaramin yaro cikin damuwa.
Yarinyar shegen kuka ne da ita, ba ta taɓa ɗa mai kukanta ba, idan tana kukan sai ta yi banza da ita. Yayi ta maganar ta kula da ita amma ta share shi.
Ranar da aka yanka hakika kuwa, ummi ce ta zage ƙwanji, tsaf ta gyara hanjin nan, dan kuwa rahama ƙin fitowa tayi kan naman, ga rana na dukan kayan kitchen.
Abdul ne ma ya kama mata wasu abubuwan, ta kunna murhu ta ɗora sai ka ce babbar mace.
Sai azahar yayenta suka zo da ƙanwar babanta, suka tarar da ummi a akan aikin, suka din ga yi wa rahama da farida faɗa, wai dan me za su bar ummi ta yi aikin naman, sai ta sace ta cinye tukuna.
Abdul ne ya fusata ya ce "Yaya ummi ba ɓarauniya ba ce ba, ba ta taɓa ɗaukar abun da ba nata ba"
"Rufewa mutane baki kan in mareka, mara kunya fitsararren banza"
Ummi da jikinta yayi sanyi ta ƙyale musu aikinsu.
Suka gama aikin nama suka kwashe wanda za su kwashe, suka bar saura suka tafi, dr. Ya dawo ya tarar da farida da yaranta suna ta cin naman, ya leƙa ɗakin ummi tana zaune tana ta tilawar Alqur'ani ga gida ya buɗe da ƙamshi, ya shiga ɗakin farida ya ciko leda da nama, ya kai ya bata.
A gaban yara ta rufe shi da masifa, a kan ko dai ummin nan kishiyarta ce ba ta sani ba.