Kenza eBookz

Farhatul qalbi complete - Chapter 2

Farhatul qalbi complete - Chapter 2

Farhatul qalbi complete Chapter 2: Farhatul qalbi complete Chapter 2. "Baki gama ba kenan. To kici gaba idan kin gama se ki tashi ki koma inda kika fito."

4,358 words

"Baki gama ba kenan. To kici gaba idan kin gama se ki tashi ki koma inda kika fito."

"Kiyi hakuri Marka. Ni kawai so nake ki janye zancen ki..."

"Aure babu fashi..."

"Nalado ka sa baki dan Allah. " Najaatu ta dubi nalado dake gefe yana katsar ruwan dake kasan tukunya na taliya.

"Me zance Naja..?" Ya amsa ta hadi da lashe bayan hannun sa.

"Yanzu ba zaka tausashi zuciyar marka ba ta janye zancen nan? Haba dan Allah."

Malam Nalado yayi shiru bai ce komai ba.

"Aure babu fashi. Yace dama inde zuciyar sa ta aminta da ita. To fa ko kayan daki yace shi zai yi. Ita kadai za a wanke akai. Saboda Allah meya fi wannan karamci? Na'Ateeku kyakkyawa da shi , Sambalele jazur da shi . Kina ganin matansa kowacce da kayanta maya maya. Sunyi 'bundun da su.. wallahi ance ba yunwa agidan sa. Duk sallah sai ya dinkawa matan sa turame maya maya. "

Waheedah dake labe tana sauraron komai. Kasa jurewa tayi. Dan kukan da take rikewa ne ya kufce mata ya shigaa sharara a idanunta. Cikin rawar jiki da baki ta fita tsakar gidan. Ta sukwane agaban Marka tana faman rokonta.

"Dan Allah Marka kiyi hakuri. Ki barni na cigaba da karatu na. So nake na zama ma’aikaciyar lapia Marka. So nake na bawa harkar lapia gudunmawa Marka. Dan Allah kar ki mun aure ki bari na cika burina. " Ta karasa hade da riko kafafun Marka. Hawaye sai dalala yake daga idanunta.

"Matsa kafin na hamb'are ki. Me sunan Malam kana jin maganganun da tsageriyar yarinyar nan take faada....?”

"Laàa. Ke yanzu Waheedah Markan kike gayawa haka?Uhm tab. Lalle. Kokari." Cewar Inna Sa'adatu matar Nalado ta biyu, Mahaifiyar su Zainab da su ke uba d’aya da su waheedah…..

#FARHATAL QALB #FARIN CIKIN ZUCIYA #ZAFAFABIYAR2022

❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰[11/23, 9:00 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ 💞 _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_LAST FREE PAGE: 5_ _(SHAFIN KARSHE NA KYAUTA!)_

××××××

"Haba Sa'adatu, Wannan ba girman ki ba ne wallahi." Najan Isubu , Ta fadawa Inna Sa'adatu haka.

"Yo ai gaskia ta fada.. Me sunan Malam kana jinta ko kayi kunnen uwar watsi?"

"Kiyi hakuri Marka... Ke waheeda baa ta hakuri." Malam NaLado ya tsawatar wa Waheedah.

Ita dai Umma Hadiza bata ce komai ba. Tayi zugum a gefe kanta a kasa.

"Ummaaa kafaata, Umma kafata. Kafata ummah ..Wayyo, wayyo " Najibu ya shigaa maimaitawa yana mai dartse hakoran sa

Marka taja tsaki, Umma hadiza ta miqe da sauri ta koma cikin daki wajen su Najib.

"Haba wannan wahala har ina? Ga wannan ga wannan. Gaskia da sake " Marka ta fada tana mai hararo dakin su Najibu

"Kai Marka ki dena cewa haka. "

"Kinga Naja ki fita idanu na. Ni dama tun da na kyalla ido na hango shigowar ki, Nasan tabbas wani katsalandan dinne ya kawo ki.."

"Kiyi hakuri Marka. Da yardar Allah komai ya kusa wucewa. Lokaci ne, Idan Allah ya nuna mana wucewar da sai kiga tamkar ba'ayi wannan tashin tashinar ba." Naja ta karasa fada idanuwanta akan Marka dake faman cin magani.

Can ta sake sakin wani dogon tsaki tana karkada kafafu. Cikin kufulewa tace,

"Kin isheni da zubar lallami Najaatu. Har kina wani lankwashe kai kina jin haushin Sa'adatu. Yo ai gaskia Sa'adatu ta fadi. Yaran Sa'adatu babu abunda zamu ce da su agidan nan sai san barka da fatan samun nasarar Allah akan dukkanin lamuran su. Zainab da suke kusan sa'anni daya da wahidin ne sau uku mai nemanta ya kawo mana kayan abinci ga su nan idan karya nayi."

"Zancen ki haka yake Marka. Domin wainar yar tsalan jiya ma zainab ce ta sayo." Cewar Sa'adatu hade da kecewa da dariya.

"Wannan duk ba abun damuwa bane Marka.."

"Babbar damuwa kuwa Naja. Natsani safiya tayi dare ya maye idanuna su sake dora ganin su akan Hadiza da ahalinta. "

"Kash. Assha Marka. Ki bar cewa haka. Babu fa bawan da ya tsara rayuwar sa haka fyace wadda Allah ya rubuta. Kuma menene yan uwantakan da zumuncin idan har dan uwanka baya kyautata maka?"

"Ke Naja. Duk abubuwan da zaki fada ba tasiri zai yi a zuciyata ba don in gaya miki..."

"Kibar cewa haka Marka..."

"Dole na fada. Kinga wuya. Nan inda abu ya tokare mun yaki tafiya. ? Ba komai bane fyace bakin cikin da Hadiza da yaranta suke samun. Nagaji idan da gaban gajiya nayi..."

"Ya SubhanAllah! Ki dubi girman Allah Marka ki dena cewa haka, Dukkanin yaran nan fa jikokine. Haka kuma Allah yaso acikin jikokin naki zaa samu biyu marasa lapia "

"Marasa lapia? Nakasassu zaki ce. Masu tattare da kunci da 'dacin rayuwa."

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun! Marka!! Marka!! Ki dena cewa haka. Malam ka saka baki. Wannan ba dede bane."

"Ba ze saka ba Najaatu. Idan kin gaji da ji ki tattara ki fice mana daga gidah ."

"Kiyi hakuri Marka. Kawai dai gani nayi wannan maganganun dik basu taso ba."

"Dole ne ayita. Shi ya saka nace wallahi kwayar hatsi nawa hadiza dasu Najib ba zasu sake ci ba. Su dan kinibibi sunyi shabe shabe ga nakasassu da baza su fita su nemo ba. Ita kuma uwar tasu ta daure musu gaba ba zata tursasu ba. Kullum dan tsagwarar munafurci suna daka suna sakin numfarfashi. Ita kuma ta faake kullum tana gefen su ba zata fito cikin mata tayi shiqa ba ta samu kudin batarwa. Ragowar me lapiar kuma ta tsiri boko ba kakkautawa. Ba zeyiwu ba wallahi. Su tunda maza ne suje can su karata ita kuma tinda macece dole ne a aurar da ita. Baqin jini ya mata katutu maza basa zuwa. An samu kuma Na'Ateeku yace yaji ya gani zai aure akan wane dalili zamu fasa? Bayan idan ta aure shi kakarmu ta yanke sa'a . Ita kanta Hadizan sai tafu jin nutsuwa da kwanciyar hankali... Wahala zata ragu. "Marka ta karasa fada tana gyade kai.

Najan isubu ta numfasa kafin tace,

"Kowane bawa da yadda Allah ya kadarta masa rayuwar sa, Wala dadi wala akasin haka. Rayuwar hadiza da yaranta haka Allah ya rubuta mata tata jarabawar. Sai dai fatan Allah yaba su ikon cinyewa yasa jinkirin alkhairi ne Aamin . Zancen nauyin dake kanta da yardar Allah yazo karshe. Domin na samo mata aikin wankau da yan kaude kaude a layin manyan can na shurah. Saboda haka zata sauke nauyin wasu abubuwan . Haka zalika itama Waheedan akwai abunda zaa sama mata ta dingayi bayan su Najeebu sun ji saukin jikin su. Don haka Marka ki ajiye zancen Na'Ateeku agefe yanzu."

"Na ajiye na zuba mata idanu ina kallonta? Ba dan mashinshini a kusa sai zuryar boko? To bokon yaci uwatas."

"Kiyi hakuri. Insha Allah kwanannan samari zasu fara zuryaa a kofar gidan nan. Komai lokaci ne. Mijin ta na nan kusa da yardar Allah. Wanda zai share hawayen ahalin gidan nan kai dama na kusa da ku baki daya. Insha Allahu. Kice Aamin Marka.."

Umma hadiza dake daki hawaye suka shigaa zirara a idanunta. Tabbas Najan Isubu aminiyar kwarai ce data san dattako take kuma yi musu madaukakiyar kauna marar misaltuwa.

"Marka, Sa'adatu, Malam baku ce Amin ba."

"Aamin Najaatu." Malam Nalado ya fada yana sosa keyar sa.

"Uhum.... Inji me ciwon baki."Cewar Sa'adatu hadi da yin kwafa ta juyar da kanta gefe.

"Aamin inda gaske ne hakan zai kasance ba karairaki bane da wucewar zance."

"Insha Allah Marka... Na'Ateeku abunda yasa ki kaga na kauda zancen maganar sa akan irin lalurar su Najibu ce. Ta sikila da ake cewa amosanin jini."

Marka taja dogon tsaki tana kauda kai gefe.

"Ke wallahi Najaatu kin iya samun waje kiyi ta sakin ta."

"Allah ba karya nake ba Marka."

"Wohoho ni lauya zan ce ne banaso wallahi. Na'Ateeku ban taba gani ya kwanta ciwo ba. Zaki jajiba masa."

"Marka abunda nake nufi shine. Shima ai yanada iyali dake dauke da irin ciwon su Kamal. Ba wai ina nufin shine mai ciwon ba. Amman yana dauke da wasu sinadarai na ciwon wanda idan ba'ai gwaji ba kafin aure shine zakiga anata hayayyafan yara masu dauke da ciwon. Yanzu kai ya waye Marka... Sai anyi gwaji kafin ayi aure saboda gudun 'barakar ciwuka. Hakan yasa na ce miki ki bar zancen Na'Ateeku da Waheedah. Domin kulla auren su kan iya haifar da illoli da yawa astagfirullah. Ba tsumi babu dabara. Maganin kar ayi kada a so ma "

"Keda Naja kinada kale kalen balai wallahi. Allah shi kyauta "

"Wannan shine tushen gaskia Marka. Ba Na'Ateeku ba. Ko wani ne daban yazo neman auren Waheedah ko zainab dole ne kafin ayi auren suje suyi gwaji. Wannan shine babbar shawara da ma'aikatan lapia suka kafa. Don gudun bacewar rana. Azo ana danasanin auren."

Marka ta tabe baki hade da jan karamin tsaki.

"Gidan aikin da zataje ina fatan nima inada nawa kason acikin albashin nata.?"

"Duk ba zai gagara ba Marka. Kuma insha Allahu tare daku duk zamuje taron nan ayi mana gwajin."

"Uhm.." cewar Marka.

"Bari na tafi. Allah ya kiyaye gaba."

"Toh Najaatu. Agyada gidah."

"Gidah yaji."

"Ke kuma tashi kafin na hamb'are ki. "

Takarasa tana mai wurgawa Waheedah harara. Gaba daya maganganun Najaatu sai shawagi sike mata akai. Ta kaikaice kai ta hango ledar taliyar kakkaryawa da tumatirin gwangwani. Na'Ateeku ya sake fado mata arai. CikiN zafin nama ta mike ta shige kuryar daki .

Waheedah ta mike jikinta a sanyaye ta shigaa dakin su Kamal. Umma hadiza kuma ta tafi ta yowa Najaatu rakiya. A soro Najaatu ta sake kwantar da hankalin umma hadiza. Da karfafa mata gwiwar ta zage damtse ta fara aikin nan da karfin ta. Ko zata kwatowa kanta da yaranta yanci a idanun su Marka .........

Tab!!! Lamarin ga ya ta’azaara… Jama’a wannan karon zafafa da zafin su suka taso. Ga fa gidan Malam na lado nan mai dauke da iyali da kuma gyatumar sa Marka. Ya rayuwar waheedah Zata kasance acikin wannan littafi. Shin su wanene wai The Adams family?? Na tabo muku bangaren zayn Adams Nasser kuwa? Hmmm inji me ciwon baki… Lalle labarin nan yana tafe da wani salo na daban mai taka rawar gani a wannan zamanin namu… Gefe d’aya dauke labarin yake tafiya da zazzafar kauna marar algus…. FARHATAL QALB!!! Lalle FARIN CIKIN ZUCIYAH…..yanki ne dake take rawar gani a zukatan bil adam. Musanman zuciyoyi biyu da ke begen kaunar juna…. A stunning love story😘don’t afford to miss this chance💯👍🏾 Ku shigo a dama da ku dan ganin yadda tafiyar Zata kasance…. Zafafa biyar. Yan biyar masu baiwa. Hikima, Fasaha da tsarkakkun alqaluma 💯📍

Yadda zaku biya👇🏾👇🏾

❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/23, 9:00 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ 💞 _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG: 6_

××××. ××××. ××××.

Tunda asubahi su Umma Hadiza basu koma bacci ba. Kamar ko da yaushe. Ita da Waheedah suka fita zuwa tuqa tuqa suka shigaa zuba ruwa a manyan jarkokin da Najeebu ke garuwa idan rashin lapiar ta lapa musu . Bayan sunyi wanka .

Yan takardun Waheeda data gama amfani dasu ummah hadiza ta dauka ta shiga kunna su a murhu daya bayan daya da ruwan bunu acikin samira. Nan da nan kuwa ya tafasa.

Ta zuba ragowar sukarin daya rage ta zuzzuba musu a kofuna. Can Umma hadiza ta miqe ta fice. Ba jimawa ta dawo da kullin leda hannunta. Biredi ne da kosai mai zafi.

Ta kakkarya ta miqa musu. Kamal ya dafe cikin sa yana bin biredin da kallo.

"Umma ba dai bashi kika sake karbowa ba.."

"Bashi kuma..? A'ah."

"To ai umma ina kike da kudin fisabilillahi. Dan Allah ki dena karbo bashi ummah. "

"Dan Allah banason mita. Ku cinye kafin kosan yayi sanyi."

Ita dai Waheedah na daga gefe tana karyawa. Hawaye na zurara daga idanunta. Tana karasawa ta miqe tana hamdalah.

"Mungode ummah. Allah ya saka miki da mafificin alkhairin sa. Amin Yaa rabbi. "

"Aamin Waheedah. Maza ki karasa shirya wa ki tafi. "

"Tohm Ummah."

Waheedah ta fito daga dakin su Kamal ta shiga dakin da yake kallon sa wanda yake a matsayin nata ita da Umman su .

Bude yar baccon kayanta tayi ta zaro robar ruwan alumun da yaji lemon tsami ta goggoga a hammatar ta. Tana jin dadin hakan. Domin suna tsantsame gumin hammata su kuma kauda tashin da hammata keyi tunda ba halin siyan turaren hammata na deodorant. .

Ta diga turaren ruwan da Kamal ya bata a hannunta. Ta shafe jikinta dashi. Hade da zizara kwalli . Ta daura dankwalinta na shedar prefect ta zura hijabinta. Hadi da goya jakarta ta fice daga dakin zuwa na su Kamal.

Dake gidan irin na da dinnan na masu karamin karfi ne. Babban gidah mai dauke da dakuna 6. Uku na kallon gabas uku na kallon yamma. Sai bandaki da dakin girki.

"Wane dan gaba da wulakancinne ya take mun takalmi saboda kaskanci da karshen wulakanci ?" Cewar Inna Sa'adatu da ke bin takalmin wari daya da kallo. Yar jikakkiyar kasa ce a gefen takalmin kadan.

Waheedah zatayi magana kenan. Umma hadiza ta fito daga dakin su Kamal. Da sauri saboda rashin son tashin hankali ta dauki takalmin ta saka wani guntun kyalle ta goge.

"Kiyi hakuri."

"Yo idan ban hakura ba zan dake ki ne?"

"Ki deyi hakuri."

"Ah ni fa banason haka. Wallahi yanzu sai ince sai an biyani sabon takalmi na." Ta shigaa duba gefe da gefen takalmin nata silifas.

"Toh ya kikeso ayi?"

"Ya da haka Hadiza.? Kina wani zazzaro idanuwa sai kace wata uwar mata. Aikin akwai. Gaskia kada mace ta sake biyemun ta kan takalma . Dan wabillahil lazi anyi na farko anyi na karshe. Idan aka sake maimaici mace zata ga abunda zan mata."

"Toh Allah ya rufa asiri ya tsare gaba."

Mtsssssssssssssssssss!! Taja tsaki hadi da shigewa dakin ta.

Umma hadiza ta juya ta kalleta kawai ta girgiza kai.

"Ungo wuce ki tafi." Ta mikawa Waheedah nera 20.

" Umma ki basshi."

"Banason jan magana."

Ta tsugunna har kasa ta karba tayi mata godia. Ta zura safarta hade da gyara zaman takalmanta .

Zainab 'yar wajen Inna Sa'adatu sai danna soyayyen kwai take da biredi a baka tana hadawa da shayi dayaji madara.

"Ke wahee ki tsaya ni mana." Zainab ta fada da sauri tana goge bakinta da bayan hannun ta.

"Dan ubanki tunda bataso kuna tafiya tare makarantar dole ne?"

"Kai Inna ba tafiya nayi ba na barta." Cewar Waheedah kanta a kasa.

"Dalla rufemun baki munasurar banza. Ke kuma can daya sokuwa tamkar kare ya cinye zuciyar ki. Sai ki bita ai ku tafi."

Ita dai zainab batace komai ba ta saka safarta tanata sauri.

"Zainabu. ! Zainabu."

"Na'am marka"

"Ungo kudin tara. "

"Tohm"

Waheedah na tsaye zainab taje dakin marka ta karbo nera hamsin kudin cin abinci a makaranta.

"Sai kin dawo. Allah ya miki albarka."

"Amin Marka."

Hawaye suka cicciko idanun Waheedah saboda tsananin kiyayya da kakarsu take nuna musu.

Haka suka jera suka tafi makarantar bayan Waheedah ta leka tayiwa marka sallama. Wadda ta debeta ta watsar tamkar taga kashi.

×××××

Su waheeda na tafiya ba jimawa najan Isubu tazo gidan da wata mata wadda tayi hanyar aikin.

Umma hadiza ta sauya kayanta zuwa wasu riga da zani da hijabin ta da ya sha karin guga.

Sai data tabbatar ta tanadar wa su Kamal komai.

"Toh zan tafi wajen aiki... Kunce da sauki ko?"

"Allah da sauki Ummah... Ni zan dan watsa ruwa ma na fita insha Allah."

"Toh Masha Allahu. Kai ma Najib ka danyi ko zaka ji karfin jikin na ka "

"Insha Allah Umma."

"Yauwa sai na dawo. ".

Ficewa sukayi zuwa hadaddiyar unguwar dake kusa da su wadda ake kira da NEW GRA SHURAH. Unguwa ce ta masu hannu da shuni. Wanda ke da jijjigaggun gate da manya manyan gidaje luntsuma luntsuma hadi da manyan motoci masu nishi.

No: 194: THE ADAMS FAMILY!! shine sunan da ke rubuce da manyan baki awani kawataccen allon karfe.

"Nanne gidan fa Hadiza ." Cewar Najan Isubu dake tabo Umma hadiza.

"Nan. Tsarki ya tabbata ga Allah. Cancadi."

"Hmm carkwadidi kai. Kede kallo na gaba ma."

Tunda suka tura kofar da ke masu gadin sun san da zuwan su. Umma hadiza tsayawa tayi kawai tanabin sarautar Allah da idanu. Gidane daya amsa sunan gidah. Gidah ne wanda alkalami yayi kadan wajen bayyana irin kawatar da yayi. Gidah ne dayaji komai na rayuwa da abubuwan morewa.

"Kinga motoci ko harda titi acikin gidah ko hadiza. "

"Uhm bari kawai Naja."

"Kinga wadannan abubuwan kamar kwayayen fitila?"

"Eh fa gasunan birjik."

"To na'urar bidiyon hadahadar cikin gidan suke nunawa dana waje. Komai . Yanzu haka ma suna kallon mu."

Umma hadiza ta riqe baki kawai tana kambama lamarin.

Ciki suka shigaa. Wani hadadden parlor daya gaji da haduwa. Ba jimawa wata mata fara tamkar balarabiya ta shigo ciki fuskarta kumshe da fara'a ...

*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*

*ZAFAFA BIYAR BACTH A*

1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)*

2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)*

3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*

1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)*

_Duk biyar 1500_

*______________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_ *(Mamu gee)*

5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_*

_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*

*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/23, 9:00 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ 💞 _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:7_

××××. ××××. ××××.

Gaishe ta suka shigaa yi dukkanin su ukun. . Ita din kuma ta dinga amsa su da fara'a da tsantsar farin cikin zuwan su .

"Hajia ga... Wadda zata kama muku aikin." Ta karasa tana nuna mata Umma Hadiza.

"Ah masha Allah! Ya sunan ki baiwar Allah?"

"Sunana Hadiza."

"Khadija.. Mai babban suna. Toh ni sunana Hameedah Muhannad. Ni mata ce ta biyu ga mijin mu professor Adams Nasser. Ma'aikaciyar lapia ce ni ina aiki da asibitoci da dama a garin nan domin bangaren aiki na ya shafi surgery. Inada yara hudu. Zayn da Nadra, Nassem sai auta Muhammad muna ce da shi Moha... Muna fatan zaki ji dadin aiki tare damu. Allah ya saka alkhairi a tsakanin mu Amin.. "

Umma Hadiza tayi murmushi tana fadin,

"Aamin ..." A hankali kafin ta shigaa cewa,

"A kusa da ku bayan unguwar ku muke. Inada yara 3. Kamal da Waheedah sai Najeebu. Da fari na haifi biyu basu yi rai ba. Nima mu 2 ne awajen me gidan mu . ...Mun koma gode da yadda kika karbe mu hannu biyu. Allah ya bani ikon yi muku dede ya kauda fitina a tsakani Amin."

"Allahumma Aamin" suka hada baki wajen amsawa.

Dr. Hameedah tace,

"Daman zuwan ku nake jira .. Fara aikinnan sai zuwa wani satin nanda kamar kwanaki 10 dai da yardar Allah. Yara sun kammala karatu acan waje. Da bazamu jeba sai da me gidan ya dawo yake sheda mana cewa an samu visa kuma zamu tashi ta Abuja insha Allah. Amman ba zamu dade ba, Sati daya zamuyi. So kafin mu dawo Kano haka dai nasan mayi kwanaki biyu a Abuja don acan ma munada gidah. "

"Allah sarki... Babu komai hajia. Allah ya bada saa kan abunda aka karanta. Allah kuma ya dawo da ku lapia "

"Aamin Yaa rabbi."

"Bari mu tafi Hajia. Idan kun dawo ma yi waya."

"Ku tsaya ina zuwa Indo. " Mikewa tayi ta haura sama. Ba dadewa ta dawo da ledoji bakake manya manyan guda 3 ta shige cikin kitchen ta zuzzuba abunda zata zuba ta fito.

"Gashi Indo wannan ledar kowa dai dai. Sai wannan kudin takalma kuke cewa ko?"

Najan Isubu ta shigaa daria ahankali.

"Laa kuyi dariyar ku. Wai a haka ma fa nayi kokari. Tunda ba yare na bane. Amman de kusan nafi iya hausa akan yare na ma. Amman da da muke Spain hausa ta wallahi tafiya ta dinga yi. Saboda yaren da akeyi acan "

"Kinma yi kokari hajia. Yadda kike hausa wallahi ba wanda zai ce ba yaren ki bane, Sai idan an kalli hasken fatar ki da yanayin ki an san kin sirka da larabawa. " Cewar Indo ta fada karshen gaskiyar ta.

Ita dai Dr. Hameedah dariya kawai tayi. Ta sake zaro wasu kudin ta bawa Indo tare da doriyar,

"Wannan kuma ki basu Hadiza da yama sunan ta.?"

"Naja'atu."

"Kwarai Najan ishaq ko?"

"Eh Najan Isubu. "

"Allah sarki. To godia nake. Indo da Najan Isubu. Da Hadiza Allah yabar zumunci. Laa na mance shaf bari na kawo muku ruwa."

"Aamin Aamin. Ai da kin barshi hajia "

"A'a ba za'ai haka ba..." Miqewa ta sake yi ta bude freezer ta dakko ruwan roba guda 3 da lemuka guda 3. Ta ajiye agaban su. Dan Allah ku tafi dasu. Kamar dai yadda na gaya miki Indo. Insha Allahu munyi magana da mai gidan kan kudin da zaa dinga bawa Hadiza idan ta fara aiki. Ya fadi yadda zai bayar ni kuma na kara dubu goma akai. Hadiza iya abunda zaki dinga yi dukda nasan Indo ta gaya miki yan kananan kayayyakin mu ne haka wanda ba zeyiwu mu saka a injin wanki ba. Bare kuma mu bayar can kamfani su wanke mana. Don ana kai mana wanki da guga. Don suke zuwa da kansu su karba. Ana kuma yi mana a gidah a injin wanki. So abubuwan da zaki dinga wankewa idan ya taso sune su dusters haka na goge goge , Da undies din auta Moha shekarar sa 5. Sai socks ina nufi safa da kuma wanke su mopping stick. Shikenan fannin wanki. Sai yan goge goge na parlorn baban su da kaude kaude na gyaran kitchen. Don munada masu aiki da ke kwana da kuma wanda suke zuwa su tafi. Dubu 30 yayi a wata? Sannan na tsayar miki kwanon abinci safe, Rana, idan kin kai dare ma nanma zaki tafarwa da yara shi. Ina nufin bayan wanda kikaci anan zaki dinga tafiya da wani gidah ko ki aiko a karba miki. Kinji Hadiza. Hakan ya miki?"

Umma Hadiza ta kasa magana saboda tsabar farin ciki. Duk sai ta dubibi ce. Ta kuma kasa boye farin cikin ta. Nan da nan ta dubi gabas ta zuba sujjadar godia ga Allah. Hawaye daya na bin daya.

"Kuka kuma? Haba Hadiza?? Menene na kuka? Idan beyi ba ki fadi nawa kikeso."

Ina Umma hadiza ta kara man kukanta. Yayinda Najan Isubu ta rungumeta tana lallashi , Kafin ta ce,

"Kukan farin ciki ne take hajia. Hakika hadiza abar tausayi ce. Tabbas Kedin haske ce acikin rayuwar hadiza. Lalle farin ciki marar misaltuwa zai fara wanzuwa a fuskar hadiza da ahalinta. Hajia mungode. Mungode Allah ya saka miki da mafificin alkhairin sa. "

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull