Kenza eBookz

Farhatul qalbi complete - Chapter 3

Farhatul qalbi complete - Chapter 3

Farhatul qalbi complete Chapter 3: Farhatul qalbi complete Chapter 3. "Ai Hajia wanda ya rab'i wani na ki ma yana cin albarkacin ki bare wanda ya samu…

4,478 words

"Ai Hajia wanda ya rab'i wani na ki ma yana cin albarkacin ki bare wanda ya samu kansa a tattare da ke. Dole ta zubar da hawaye hajia. Hawayen farin ciki ne, Hawayen yaye baqin ciki ne. Hawayen samun kanta cikin sabuwar rayuwa take. Hawaye ne mai tattare da labarai da ba zasu fada ba. Tabbas hawaye ne take zubar wa da kololuwar madaukakin farin ciki marar algus. Hajia angode. Angode . Allah ya saka miki da mafificin alkhairin sa. Allah kuma ya raya miki zuri'ah ya albarkance su. Allah kuma ya kara yaye miki dukkanin kuncin da ke cikin rayuwar ki ya lullube ki da lullubar rahamar sa. Da karamcin sa. Da buwayar sa. Da zatin sa. Domin Allah buwayi ne kuma gagara misali. Hajia na ari bakin hadiza nace Allah ya saki da ahalin ki da dik wani masoyi naki a aljannatul frdwas. Allah kuma ya kara wadata ki da wadatar sa Allahumma Amiin "

"Aamin Indo.. Amin "

Umma Hadiza ta sharce hawayenta da kasan rigar ta. Cikin rawar murya da tsagwaran farin cikin data samu kanta aciki tace,

"Hajia banda bakin godia agare ki . Kalmomi sunyi kadan wajen bayyana godia ta agareki.wallah baki ba zai iya fasalta yadda nake ji ba arai na da zuciyata dama gangar jiki na baki daya. Hajia ubangiji Allah ya cigaba da suturta ki. Allah ya wadata ki da ga wadattun bayin sa. Allah ya kara miki karama da karaamci. Ubangiji Allah ya biyaki da aljanna. Allah ya raya zuri'ah. Allah ya biya bukatu na alkhairi. Allah ya kara daukaka . Allah kuma yaja kwana da imanin sa. Allah ya jikan mahaifa idan sun rasu . Yasa aljanna ce makoma agare su. Idan suna raye Allah ya kara musu nisan kwana ya wadata su da lapia . Allah ya faranta miki ya kara arziki mai albarka. Ubangiji Allah ya rubanya miki fiye da yadda kike temako. Allah ya biya ki Hajia. Allah ya biya ki. Allah ya b..."

"Aamin, Ya isa hakanan Hadiza. Dan Allah kubar godiar nan. Wadannan addu'oi haka." Dr. Hameedah na magana tana matse hawayen dake zubo mata.

"Nagode. Nagode. Wannan addu'oi haka? Jazakum Allah khairan "

Nan suka cigaba da godia. Har dai ta samu ta dakatar dasu. Suka danyi hira. Kafin daga bisani suyi mata sallama su tafi. Kowanne da ledar sa baka ciki da kayan miya da kaji guda biyu. Da taliya guda 5. Da kuma dubu 5 kyauta kowannen su.

"Wannan mata gaskia insha Allahu yar aljannah ce. Wannan abun arziki haka?" Cewar najan Isubu.

Haka dai suka tsaya suna ta mayda zance. Umma hadiza nata jera musu magiya kan su bar kudin ta dau kayan. Saboda hanyar arzikin da suka mata. Sai da Indo tayi jan Ido kafin hadiza ta riqe kudin. Ta kuma sake musu godia kwarai matuka .

Akan hanyar su ta komawa unguwar su. Indo ke basu labarin gidan na,

×THE ADAMS FAMILY...×××

"GIDAH ne da ya amsa s ..........[11/23, 9:00 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ 💞 _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:8_

××××. ××××. ××××.

Da yaa amsa sunan gidah, Gidane na yan boko da tsantsar aqidar musulunci. Babu batun kyamata ko tsangwama irin na wasu masu hannu da shuni. Suna da temako da kuma kyautatawa marasa karfi. Farfesa Adams Nasser shine mai gidan na su. Matan sa biyu kamar yadda ta gaya mana. Kishiyar tata ita aikin alkalanci take. Kuma itace matar sa ta fari. Tanada yara biyar: Basher, Saani,. Abubakher ,. Sai mata guda biyu da Jannat da Yasmin . Ita kuma Hajia Hameedah wadda mukaje wajenta tanada yara hudu: Zayn shine na fari, Sai Nadra da Nassem sai autan ta Muhammad. Suna ce da shi Moha ai kunji ma ta fada. Suna da gida a Abuja su kanje can suyi hutu su kan kuma futa zuwa wata kasar. Dama can a baya a kasar wajen suke daga baya suka dawo nan din. Kusan dukkanin iyalin nasu ma suna ketare. ...." Cewar Indo dake labarta musu komai.

"Ah lalle Masha Allah! Tabbas sun san darajar mutane. Dan mungani da idanun mu. Gaskia batada matsala matar nan. Gata ba bahaushiya ba kuma ." Najan isubu ta fada tana jinjina kai.

"Gaskia babu kam. Allah ya kara daukaka, Aamin " Inji Umma Hadiza

"Aamin dai. Toh kunga dai yadda unguwar tasu take ma, Su ba shigaa harkar makota suke ba ma. Bare akai musu gulma da munafurci. Shekara ta nawa da su. Wallahi 'daga murya wannan basu taba mun ba. Daga ita har abokiyar zaman ta ta. Kuma mijin nasu ma wallahi bakuga kirki ba. Allah ni dai haduwa ta da su. Bazan iya kasafce muku alkhairin dana samu a tattare da su ba. Shi mijin na su dan Sudan ne shi da matar tasa ta farko. Ita kuma Hajia yar masar ce me suke ce mata a turance. Wannan. Kinji sunan. Ya yake ma? Yauwa ijif (Egypt) To shi..."

"Ki ce du larabawa ne?" Najan Isubu ta katse Indo.

"Ina kai ku. Ai bangama ba."

"Ai yo ho... Yi hakuri. Cigaba ."

"Yauwa shi mai gidan na su. Mahaifiya ta sa bahaushiya ce. Mahaifin sa kuma balarabe. Hajian tacemun usuli. Mahaifin nasa ne aka turo shi ofishin jakadanci da ke nan reshen najeriya. To anan Allah ya yi auren sa da mahaifiyar ta sa. Su kaita hayayyafa. Har shima dan na su ya auro yar Sudan. Wai sun hada jini ma da matar tasa ta farko. Sai kuma Hajia da ya kara a ta biyu yar ijif (Egypt)..."

"Masha Allahu! Kai arziki yayi. Ubangiji Allah ya wadata mu da shi Aamin."

"Aamin Yaa Rabbi. Kuma gwanin ban sha'awa ma sai kunje auren dangin su."

"Haba dai? Ganima kala kala ko?" Cewar najan Isubu tana hasaso yanayin a zuciar ta

"Habawa haduwar ma ta karshe. Dangin su gwanin ban sha'awa wallahi. Kuma auren da suke yi auren junan su suke. Ma'ana auren zumunci."

"Yo ai dole. Yadda suke da tushe me kyau ga su labarawa ai dama ba zasu iya auro wani tsatson ba "

"Gaskia Masha Allahu. Auren gidah suke yi. Harta bukukuwan du irin na larabawa dinnan suke yi. Harda su shayi ake rarrabawa. Ke fa da mun jima a gun Hajia shayi zakuga tazo ta babbamu. Shayin me wani irin gard'i da dad'i. Wani irin kamshi na larabawa yakeyi. Kai arziki yayi "

"Habawa. Bari Indo, Ai bakiga yadda idanuwana ke hasaso dukkanin abubuwan da kike fada ba. Allah ubangiji yasa arzikin ki ne yazo Hadiza "

"Aamin Najaatu. Tare da ku baki daya. Nagode muku. Allah ya saka da alkhairi Amin."

"Tabbas inde kika rike gaskia da amana zaki ji dadin zama da Hajia wallahi. Dan kinganni nan yadda kukasan yar dangin su wallahi haka suka dauke ni. Kowa ya sanni. Lamarin sai godiar mai sama. Ai shi yasa da Naja ta gayamun halayen ki nace to Alhamdulillah komai yazo a dai dai."

"Nagode Indo. Ubangiji Allah ya saka da alkhairi. Allah ya biya muku dukkanin bukatun ku aamin Aamin."

"Aamin Hadiza . Amin"

Cigaba da hira sukayi suna tafiya, Indo da ke gidan ta abayan unguwar su take ta gangaren makabarta. Hanya daban tabi bayan sunyi sallama. Hadiza ta sake mata godia har Indon ta bace daga ganin su.

"Naja nagode. Nagode Allah ubangiji ya buda muku kofofin alkhairin sa. Nagode kwarai. Wallahi na rasa yadda zan muku godiar ma."

"Kayya Hadiza. Da girman Allah ki dena godiar nan haka. Wallahi ta isa. Ko ba ta kanmu ba wallahi idan Allah yayi kinada rabo da su dole zaki je gidan. Haka Allah ya rubuta ya kuma tsara. Dan haka ki bar godiar nan haka."

"Toh ungo wannan kara akan naki." Umma hadiza ta shigaa kiciniyar kunce ledar ta."

"Mts! Wallahi Hadiza idan kikai wani abun yadda kikasan a hau ki da duka wallahi. Meye hakan fisabilillahi da girman ki? "

"Naja kar muyi haka da ke." Cewar Umma hadiza cikin karshen gaskiyar ta.

"Sai kiyi tayi kuma." Tayi gaba abunta. Umma hadiza ta bita da sauri .

"Naji na dena tsaya dan Allah."

"Yauwa yanzu kika yi magana. Muje ki sayi mai da su magi ki dafe muku kazar nan Hadiza. Kuci da biredi ko ki dafe muku taliya ku na ci kuna yagar naman."

"Insha Allahu Naja."

"Sannan inason jan kunnen ki dama. Don nasan ke zuciyar ki daya zaki saki baki ki gaya musu komai "

"Insha Allahu Naja. Ina sauraron ki"

"Yauwa. Karki soma fada musu yadda kukayi da Hajia. Kya iya ce musu dai tafiya zasuyi sai sun dawo zaki fara aikin."

"Tam insha Allahu. "

"Yauwa. Sai kuma karki soma gaya musu adadin kudin aikin da za'a dinga biyan ki. Daga ke sai su kamal kawai. "

"Insha Allahu haka za'ai."

"Yauwa. Kin fini sani dai sarai halin surukar ki da kishiyar ki . Muddin suka ji zancen kudin aikin ki kema kinsan abunda zai biyo baya . Bayan kin zamar musu saniyar tatse. Dan kuwa kema kinsan ke zasu barwa dawainiyar komai nasu... Dan haka ki shiru da bakin ki. Dan abunda kika samu idan kinyi niyya kya iya ba su. Shine zancen da zan ja ki da shi dama."

"Insha Allahu haka za'ai......"

Suka jera suka nufi wajen mai sayarda mai da kayan abinci. Dake najan Isubu mijinta na da dan rufin asiri. Da zai tafi ya saya musu komai sai dan abunda ba a rasa ba. Don haka magi kawai ta saya da curry. Umma Hadiza kuma ta sai su man kulli da magi da curry da sauran spices.

Suka yiwa juna sallama. Umma hadiza ta shigaa gidah. Yayinda Najan Isubu tayi hanyar gidan ta....

*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*

*ZAFAFA BIYAR BACTH A*

1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)*

2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)*

3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*

1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)*

_Duk biyar 1500_

*______________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_ *(Mamu gee)*

5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_*

_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*

*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/23, 9:01 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ 💞 _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:10_

××××××.

××Bayan anyi addu'oin bude taro da addua. An kuma karanto jadawalin da za'ayi acikin taron. Mai girma mai babban taro bayan an bashi dama. Nan ya fara bayani cikin kwarewa da kuma yi bisa tsarin dakkan dakka wato daki daki,

"The term “sickler” is often used by medical practitioners to refer to children and adults with a diagnosis of sickle cell disease (SCD) .Noun. sickler (plural sicklers) One who uses a sickle; a sickleman (medicine, informal) A person who has sickle-cell disease.) A hausan ce muna cewa:. Ma’anar cutar sikila,

"Cutar sickler tana nufin mutum yana dauke da sinadaran haemoglobin guda biyu marasa kyau (ba lafiyayyu ba) a jikinsa. Ma’ana dai ya gaji gurbatattun sinadaren haemoglobin daga wurin mahaifiya da mahaifi

"Yadda ake samun cutar sikila: Ana samun cutar sickler ne daga wurin iyaye (uwa da uba). Uba shi kadai ba zai iya haifar da/’ƴa mai sickler ba, haka ma uwa ita kadai ba za ta iya haifar da/’ƴa mai sickler ba. Dole sai da gudunmawar kowanne daga cikinsu (uwa da uba). Kowane mutum yana da sinadaren haemoglobin a jikinsa nau’i biyu. Zan yi magana a kan haemoglobin A da kuma haemoglobin S kawai saboda su ne suka fi yawa. kowane mutum yana da daya daga cikin wadannan Haemoglobin ɗin:

(1) Haemoglobin AA (HbAA)

(2) Haemoglobin AS (HbAS)

(3) Haemoglobin SS (AbSS)

"Wanda HbAA yana da lafiyayyun haemoglobin guda biyu. Mai HbAS yana da lafiyayyen Haemoglobin guda daya da kuma wanda ba lafiyayye ba (ba mai kyan ba) guda daya, Mai HbSS yana da haemoglobin guda biyu marasa kyau. Mai HbAA lafiya kalau yake. Ma’ana ba shi da ciwon sickler. Mai HbAS shima lafiya kalau yake, ba shi da ciwon sickler, amma zai iya haifar da/’ƴa mai sickler idan ya auri mai HbAS. Don haka, HbAS shi ake kira da ‚carrier‛

"Mai HbSS, shi ne yake da ciwon sickler: lokacin da za a halicci mutum a cikin mahaifiyarsa, uwa tana ba da gudunmawar haemoglobin guda daya, sannan uba ma yana bada gudunmawar haemoglobin guda daya. Idan uba ya bada gudunmawar haemoglobin maras kyau (HbS) sannan uwa ma ta bada gudunmawar haemoglobin maras kyau (HbS), to tabbas dan da za’a haifa, zai kasance sickler ne (HbSS). Kuna ganewa ko?"

"Eh..." Suka hada baki wajen amsa shi.

Ya sake gyara tsayuwar sa kafin ya cigaba da cewa,

" Ga dai yadda za ta kasance idan aka yi aure.

Iyaye (Uwa da Uba)

Yanayin ‘Ya’Ya

AA da AA AA a kowane Lokaci AA da AS AA, ko Kuma AS AS da AS AA ko AS ko SS AS da SS AS ko kuma SS SS da SS SS a kowane lokaci AA da SS AS a kowane lokaci Don haka, idan ana so a kauce wa cutar sikila, to kada a yi aure tsakanin.

‘AS’ da ‘AS’,

‘AS’ da ‘SS’,

‘SS’ da ‘SS’.

" Kun fahimce ni ko?"

"Mun fahimta dakta."

"Toh akwai Alamomin cutar sikila: Suna bayyana ne tun yaro yana karami a mafi yawancin lokaci. Alamomin sun hada da: kumburin ƴan yatsu, Ciwon kashi mai tsanani, Dashewar jiki (karancin jini) Kankantar jiki da sauransu

"Sai kuma wasu daga cikin illolin ciwon Domin shi ciwon sickler yana haifar da illoli daban–daban, kamar: Yawan rashin lafiya akai–akai kamar ciwon kashi, ƙirji, ciki da sauransu Shanyewar barin jiki (stroke) Ciwon koda Rashin zuwa makaranta ko kuma yawan tangardar karatu Yawan karancin jini Shaye–shaye Saurin mutuwa (mutuwa lokacin kuruciya da sauransu). Ba wai ana nufin su mutu kafin lokacin su ba. A'ah ba haka nake nufi ba. Ina nufin wahalar da suke sha su kuma zo su rasu wasunsu da karancin shekaru. Sannan akwai bangaren

"Maganin ciwon sikila: Babban maganin ciwon sickler shi ne kada a yi aure idan akwai yiwuwar a haifi da mai sikila. Kuma ana iya gane haka ta hanyar yin gwajin genotype. Amma idan ciwon ya samu, to hanya daya ce wadda ake iya maganin wannan cuta., Kuna saurara ko?"

"Eh... To Marka kinji dai ko?" Cewar najan Isubu. Ta juya kofar kunnen Marka tana gaya mata.

"Ina ji ai."

"Yauwa ai na gayan ki."

"Uhm...." Marka ta juyar da kanta gefe kawai tana harare harare.

"Yauwa hanyar ita ce, dashen baargo, A turance muna kiran sa da: (Bone marrow transplant), shi wannan dashen bargo yana tare da irin tasa matsalolin kuma ba kowane lokaci ake yin nasarar warkewa ba. Sannan kuma yana da tsada matuka da gaske... Dan cikin kaso dari bebi kashi daya ne ke yi ba. Kuma acikin kashi dayan. Rabi da kwata ba sa rayuwa. Ragowar ne nasara wani lokacin. Domin shi sauki ko akasin sa ai daga Allah ne.... Ina fatan kuna tare da ni?"

"Muna sauraron ka Dakta."

"Yauwa to: Ana ba wa masu sickler wasu magunguna domin samun saukin rashin lafiya akai-akai. Shi yasa ake so masu sickler su dinga zuwa wajen likita lokaci zuwa lokaci, koda babu abin da suke ji na rashin lafiya... Domin dik cutar da ake kokarin takatsantsan da ita ana bin ka'idoji da tsare tsare da dokokin da likita ya gindaya to babu shakka wani kaso daga cikin cutar zai ragu. Musanman idan ana hadawa da addu'oi ana kuma fawwalawa Allah lamurra.. Sannan inason sanar da ku wasu daga cikin: Abubuwan da suke tayar da rashin lafiya ga masu ciwon sikila sune':

"Zafi mai tsanani Zazzabi (ko na malaria ko kuma wani abu daban, Motsa jiki mai yawa Bacin rai. Da sauransu, Don haka yana da kyau a kaucewa wadannnan abubuwan. Sai daga karshe, Ciwon sickler yana saka rashin lafiya akai–akai, yana hana jin dadin rayuwa, sannan kuma yana sanadiyar mutuwar mutum yana karami. Ana iya kaucewa ciwon idan aka bi shawarwarin likitoci ta hanyar yin gwajin genotype... Na hada ku da girman Allah kada ku aurar da 'yayayen ku haka sakaka ba tare da anyi gwaje gwaje ba. Mu likitoci mumu ka san wahalar da suke sha.

"Wadannan mutane masu lalurar sikila ababen tausayawa ne ga duk wanda yake tare da su. Dan Allah a rage yawan yaduwar wannan ciwon ta hanyar yin gwaji. Idan an gwada komai kalau to shikenan sai ayi auren . Idan kuma an samu akasin haka to fasawar auren itace mafi alkhairi. Saboda idan an haifi yaran ma su zasu yita shan wahala. Iyaye yan sannu ne. Sai dai suyi wahala da jikin su day kuma dukiyar su. A zamanin baya kai bai waye ba. Haka iyayen mu sukayi auren su suka hayayyafe mu. Amman Alhamdulillah yanzu kai ya waye. Cutar nata yaduwa. Allah ya temaka zamani ya zo da abubuwan gwaji da zaa debi jinin ka agano kanada cuta kaza ko babu. ?

"Abunda ya saka kenan. Kungiyar mu ta ma'aikatan lapia da ke wakiltar reshen karamar hukumar shurah. Muka tsaya tsayin daka wajen ganin munyi da gumin mu da aljihun mu wajen yaki da wannan cuta. Kuma Alhamdulillah mun samu nasarar Allah aciki komai ya tabbata kamar yadda muka tsara. Zamu debi lokaci wajen yiwa dukkanin al'ummar unguwar nan gwaji dan tsare rayuka daga fadawa halakar wannan cuta mai sanmatsi. Muna kuma fatan zaku bamu hadin kai muyi wannan tafiya tare. ?"

"In shaa Allahu!"

"Toh Masha Allah . Duka Duka anan zamu dakata. Zakuma mubi gida gidah mu dau kidayar yawan su. Ta hakane sauran ma'aikatan mu zasu rarrabu su kuma yi wa kowanne gidah gwaje gwaje da kuma abubuwan da suka dace. Mungode kwarai da ara mana lokutan ku da kuka yiyyi. Munyi farin ciki, Mun kuma ji dadi. Allah kuma ya hadamu a ladan duka. Amin.! Malam a yi mana adduar rufe taro. "

Malamin ya hau kan dan tudun ya shigaa janyo addu'oin rufe taro. Aka karasa. Jami'an suka shigaa bin gidah gidah suna daukar sunayen su da kuma adadin yawan su. A ranar aka fara dibar jinin wasu daga ciki. Sati biyu zasuyi su kammala komai.

Kuma babu lefi mutanen unguwar shurah sun bada hadin kai. Anyi komai lapia an karashe babu wata tarzoma ko husuma. Illa dai Marka data kwarara rantsuwa ta dire hade da jan aradu kan babu wanda ya isa ya tsikara mata basulla (allura) ya debe mata jini. Bata amince ba baza kuma tayi din ba. Anyi magiyar anyi nacin tace wallahi ba zata yi ba. Haka aka kyaleta kuwa. Don babu wanda ya isa ya saka Marka abu. Bare kuma a hane ta ......

*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*

*ZAFAFA BIYAR BACTH A*

1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)*

2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)*

3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*

1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)*

_Duk biyar 1500_

*______________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_*

1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)*

2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)*

3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)*

4... _INAYAH_ *(Mamu gee)*

5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)*

_Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_

*YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:*

_ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR*

_BANK NAME:_ *ZENITH BANK*

_ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_*

_SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_

*_07040727902_*

_IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_

*_09134848107_*

*_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/23, 9:01 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ 💞 _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:9_

××××××.

*Da* sallama Umma Hadiza ta shigaa cikin gidan . Bakinta na furta adduar shigaa gidah a hankali. Da Sa'adatu ta fara cin karo a zaure. Tabi ledar hannunta da kallo har tana lankwasar da kanta .

"Unguwa zaki? A dawo lapia."

"Kiji ki da wata tambayar banza. Dama idan zan fita ina sanar miki ne? Sabon salon kinibibi. To aniyar ki ta bi ki idan ma da wata kullalliyar kika dawo."

"Ya SubhanAllah! Haba Sa'adatu "

"Atoh ai gaskia ne. "

"To Allah ya baki hakuri."

"Matsalar ki ce."

Umma hadiza bata sake cewa komai ba. Tayi hanyar dakin Marka kai tsaye tana sallama a hankali. Shiru ba amsawa . Ta dan zura kanta kofar dakin Markan. Bata nan sai yar rediyon ta da keyi ita kadai. Nan da nan kuwa Umma Hadiza ta saka hannu ta kashe gudun kar battery din yayi sanyi.

Sannan ta fito daga ciki tayi dakin su Kamal. Sai Najib shi kadai yana fiffita da mahuci. Tayi sallama ya amsa yana dan gyara kwanciyar sa.

"Sannu da zuwa Umma..."

"Kai zan wa sannu Najib. Ina yayan na ku?"

"Bai jima da yin wanka ba ya fita. Yace na ce miki ya dan ji dadi jikin sa ya tafi kasuwa "

"Masha Allahu! Allah ya kara muku lapia . Amin"

"Amin Ummah. Nima daman jiran dawowar ku nake . Ko ke ko Waheedah "

"Ai ga ni na dawo. Wani abun ne Najib?"

"Ah babu komai wallahi. Nima so nake na fita na dan zauna ko a bakin titi ne."

"Alhamdulillah! Jiki ya yi sauki. Allah ubangiji ya kara muku lapia mai dorewa. Allah ya takaita wahala, Aamin Yaa rabbi."

"Aamin Aamin Umma. Bari na dan watsa ruwan ni ma."

"Toh Najibu. Akwai ruwa ai. Na kwallan yafi dumi."

"Tohm Umma."

Fuskarta cike da farin cikin jin dadin ganin ciwon nasu ya dan lapa. Gashi har daya ya futa ma daya kuma zai fita yanzu. Bayan dogon zangon da suka dauka suna fama da jinya. Dama haka cutar sickler/ amosanin jini yake. Ya lapa ya tashi. Sai fatan samun lapia ga dukkanin masu fama da ciwon. Allah kuma yasa hakan ya zamto musu samun rahamar Allah , Aamin. (Our warriors !! Allah ya baku lapia mai dorewa. Da dukkanin marasa lapia na gidah dana asibiti.) Aamin.

"Ummah ya naga kinata murmushi ne? Allah yasa murmushin alkhairi ne." Cewar Najib daya gama wanka ya zura kayan sa.

Umma hadiza ta sake murmusawa kafin tace,

"Murmushin farin ciki ne Najib. Babban murmushin da nake yanzu bai wuce na ganin warwarewar jikin ku yayi ba wallahi. Har a raina baka ji dadin da nake ji yana ratsa ni ba."

"Allah sarki Ummah.. Allah ya kara mana lapia ya yaye mana dukkanin matsalolin mu. Ya azurta mu muma muyi miki iyakar kokarin mu. Dan har mu koma ga Allah ba zamu iya biyan ki abunda kike mana ba Ummah. Allah ya kara miki lapia da nisan kwana..."

"Da imanin Allah."

"Ai kuwa dai da imanin Allah. Allahumma Aamin Umma."

"Sai abu na biyu. Idan kun dawo baki daya an jima na gaya muku. Amma kafin sannan dubi abun arzikin da ke gabana. Gidan da Najaatu ta sama mun aiki ne suka babba mu. "

"Masha Allah. Allah ya saka musu da mafificin alkhairin sa . Gaskia mutanen arziki ne. Yanzu du wannan abubuwan haka ? Masha Allah ."

"Wallahi kuwa Najib. Amin Aamin. Sun san abun arziki. Mutanen kirki ne."

"Toh umma me zan tayaki da shi kafin na fita?"

"Ba abunda zaka tayani dashi Najib. Kayi ficewar ka. Yanzun nan zan hada komai "

"Toh shikenan Umma. Sai mun dawo."

"Sai kun dawo Najib. Allah yayi albarka ."

Nan da nan Umma Hadiza ta shigaa harhada kayan girkin da zatayi. Ta dake kayan kamshinta waje daya saboda qarnin kajin. Ta wanke su tas bayan ta yayyanka su tsoka da yawa.

Ta hada wuta ta fara tafashen kazar da kayan kamshi. Dayan murhun kuma ta dora ruwan taliya. Tanata aikinta ita daya agidan du ba kowa. Har Allah yasa ta kammala komai ta soye naman ta zuba komai a muhallin sa tukun sannan ta kai cikin daki bayan ta kakkasafce na kowa a faranti. Taliyar da miyaar ma nanma ta zuzzuba ta ajiye.

An kira sallah kenan. Bayan tayo alwala ta tada sallar ta idar. Tana zaune tana addu'oi. Waheedah ta dawo daga makaranta ita da Zainab . Can sai ga shigowar Marka. Ba jimawa tamkar hadin baki sai ga Sa'adatu itama ta dawo. Sai malam NaLado daya dawo a karshe.

"Kamshin meye wannan haka?" Cewar malam NaLado hadi da fara dauke murafan kwanuka. Yana sake bude kofofin hancin sa.

"Marka kamshin me nake ji haka.?"

"Kai wanene ya kashe mun yar radio di ta iyye?" Cewar Marka. Ta fito daga cikin dakinta tana huci tamkar zakanya.

Sai da Umma hadiza ta shafa adduar da ta daga hannuwa sama tukun sannan ta mike ta nannade sallayar ta ajiye ta a bakin gefen katifa.

"Ni ce marka. Naga tana tayi ita kadai kada batirin yayi sanyi."

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull