Farrah complete Novel - Chapter 6
Farrah complete Novel Chapter 6: Farrah complete Novel Chapter 6. Wani irin faduwa gaban Zayn yake ganin gardawan maza su uku sunyo kanshi yanaso yatashi…
4,260 words
Wani irin faduwa gaban Zayn yake ganin gardawan maza su uku sunyo kanshi yanaso yatashi yagudu amman babu dama, duwaiwai yashiga ja yana komawa baya suna binshi yace “don’t touch me, don’t f**king touch me, I am telling y……” bai karasa maganan ba daya daga cikinsu yamai kafa abaki sai jini kafin ya ankara saukan dukan maza kawai yakeji ta ko’ina babu ko digon tausayi sumai ta kafa sumai da hannu, tun yana iya ihu har bakinshi yau liss ya mutu yana kwance awajen kaman wanda yamutu bakinshi ya kumbura sosai yana fitarda jini hakama fuskanshi duk ya kumbura sabida da kafansu dake Dante da jungle booth sukamai duka.
“Oga angama” Lamido yafadi suna komawa baya, Oga ya katse wayan dayake yi sanan yataho ahankali yazauna akan kujeran yana kallon Zayn din dake kwance akasa yace “Lamido adagomin shi ya zauna” dasauri sukai kanshi dagashi sukai suka zaunar dashi saida yay kara sabida azaba sanan suka koma bayan Oga suka tsaya. Kallon fuskan Zayn din Ogan yayi yace “welldone boys” sanan yakalli Zayn yace “you look Cute Dadys boy” HAHAHA yakara dariya sanan yace “dagamu sai kai adajin nan babu mai kwatan ka, kariga kabaro Abuja kabaro yankin garinku ma kwata kwata inda zan fada maka inda kake dasaikasha mamaki so kada ma kayi tunanin zaka kubuta daga hannunmu” yay dan shiru sanan yace “mutane uku suka bamu Wanan kwangilan na kidnapping naka, biyu daga cikinsu naso mu halakaka har lahira kamutu kawai babu labarinka, mutum daya kuma nasonka da ranka amman sai an gama karbe komi na mahaifinka sanan za’a maidaka, so the whole case akanka is interesting, kidnapping aikina ne tun inada saurayi amman bantaba kamo babban nama iri ka ba, kasan irin kudin dana samu nakuma ke samu akanka kuwa? Yanzu muka fara wasan” Hahaha yasake dariya sanan ahankali yace “kubashi abinci” hanyar jakansu Lamido yayi sanan yadauko wani bushashen buredi na irin na naira hamsin da pure water guda daya yataho gaban Zayn sanan ya Yar akasa kaman yabama kare, ture abincin Zayn yayi azuciye yace “I am not eating” dariya dukansu sukahau yi harda tafi, tsinkewa zuciyanshi yayi da kyar ya iya bude baki yace “konawa mutanen dasuka saku ku kamoni zasu baku zan baku x10 inhar kun sakeni” duk kallonshi suka tsaya yi kaman wayanda suka gamsu da maganan shi sanan sukahau dariya, kafin Ogan yace “ku karyamin hannunshi daya” wani kalan zaro idanu Zayn yayi tsabagen shock yama kasa magana, ganin sun taho kanshi gadan gadan yasa yafara ihu. “Somebody help me, help me, mutanen nan sun saceni, mutanen nan sun saceni” hannunshi suka fuzga suka warware kullin sanan suka kama left hand din Zayn yanajin yana gani wanda ke kama da doki ya ballamai hannu bass tsabagen azaba sumewa ma yayi, Ogan yace “finally gwara yayi bacci yadameni”. Wanan kenan……
Tana zaune acikin dakin nan nata ita kadai dayake da duhu ko fitila babu tana zaune ta idar da sallan isha’i taji muryan Rakiya ta kwalamata kira cikeda bala’i. “Farrah” tashi tsaye tayi da sauri jikinta harya fara rawa hannunta dasauri takai ta taba goran pepper spray da Shafa tamata dake makale gefen zaninta tana numfashi da sauri da sauri. “Wai bakiji ina kiranki ba Shegiya Yar Jaka nazo dakin nan naki na tumakai kashekine kawai bazan yiba” Rakiya tafadi ranta abace, ahankali tasa hannu tabude kofan taramo tafito daidai lokacin itama Inna dake sallan isha’i lokacin da Rakiya tashigo gidan tafito tana kwace hijabin tana daurawa kan igiyan tsakar gidan tace “meya faru Rakiya”? Cikin fushi Rakiya takalli Farrah daya fito tana rabewa abango daga nesa dasu, Rakiya tace “yau kin hadu da Modibbo kobaki hadu dashi ba”? Da bala’in sauri Farrah ta girgiza mata kai tana hadawa da yatsu alamun a’a basu haduba, cikin fushi Rakiya tadubi Inna tace “Inna kinga dai yarinyar nan da Baba yasaka mana agida bata gabana bana shiga harkanta, wlh Inna takiyayan mini Moddibo na, ko ganinshi tayi tama chanza hanya dan banso ko hanya yahadasu, Inna yau ina kawomiki karanta na karshe wlh wlh na rantse da zatin Allah ko magana aka kara zuwa akacemin anga ta tsaya tanayi dashi koko kima hada hanya dashi komenama yarinyan nan ita taja, komenamata ita taja, Modibbo nawa ne nikadai ne matarshi a kap karkaran nan, idan kunne yaji……” Inna tace “gangan jiki ya tsira” Rakiya tajuya tawuce dakinsu itakuma Inna takalli Farrah da kanta ke kasa tanaji kaman ta kasheta tace “in ciyar dake sanan in ciyar da Baffan ki da kudina sanan kice zaki kwacema y’ata Modibbo Farrah wlh wlh zan iya halakaki har lahira ki kiyayeni” tana maganan tajuya fuuuu tai ciki ganin Malam yaleko daga dakin ahankali itakuma tajuya takoma dakinta tasamu gefe daya ta kwanta sai bacci Allah yasota takoshi.
Da asuban fari ta bude ido tana fitowa ta zaga bayangida sanan tadauro alwala, tadawo dakin ita harta saba rayuwa acikin duhu salla tayi na asuba sanan tazauna tana addu’a, mahaifiyarta kafin tarasu takoya musu karatu sosai dan haka ta iya ta iya salla daidai gwargwado sanan bata wasa da addu’a. Gari nafara haske tafito ita kadai da sanyin safiyan nan nan tadauki tsintsiya ta share gidan tass, sanan tai wanke wanke, saida tagama sanan tabama tumakan gidansu da shanaye abinci daidai lokacin Inna tafito daga daki fitowa tayi daga wajen tumakan ta tsugunna har katsa alamun gaisuwa ko amsata Inna batayiba tawuce bandaki itakuma tadauki tulu dan fita debo ruwa rafi tanada kuzari da zafin nama nan da nan tashiga cike ko’ina, tana cikin tafiya zata koma rafin zuwan karshe kenan zatayi ko’ina yacika agaban rafin taga Modibbo tsaye rikeda wani paranti mai kyau da buredi kekai da kofi babba dayacika da shayi sai cinyan kaza agefe soyayye dakuma soyayyan kwai, kallo daya tamai tawani irin juya, dasauri yabiyota yace “Farrah Farrah tsaya” tana shirin kwasa dagudu yasha gabanta yana kallonta yana murmushi yabi kayan jikinta da kallo sunyi daka daka dan tabe baki yayi yakalli fuskanta dahar wani sheki yake dudda ko wanka ma batayi ba ga uban gashi a goshinta da giranta baki sudik har wani kyalli suke yace “bakiji ina kiranki bane zaki gudu, Kari nakawo miki nasan ba’a baki abinci awanan gidan bani tulun nan kigani” yakai hannunshi zai sauke tulun daga kanta dasauri takoma baya tace “iiiiii” cikin yanayi na kurmanci alamun yabar shi, jiyayi ranshi yabaci daurewa yayi yamika mata tray din yace “to gashi kici” dauke kai tayi takalli gefe dasauri dan bamataso taga abincin ranta yabiya, sosai yaji ranshi yabaci cikin fushi yace “wlh idan baki amsaba zansa akulleki amiki bulala dariya wawiya kawai sabida kinga ina sonk……” “Farrah” wani irin bari jikinta yayi jin muryan Rakiya daga ita har shi Modibbo juyawa sukayi suka kalli Rakiya, kana ganinta zakaga tsantsan bacin rai da kishi a idanunta dan takai minti daya tsaye a wurin amman ta daure dasauri takaraso wajen Farrah tai baya dasauri danta dauka dukanta zatayi Rakiya tasa hannu ta amshi tray dake hannun Modibbo tace “Allah sarki Hamma haka kake sona kabama Farrah takawomin gida, gidan su Atine fa zani nace bari nabiyo tanan, nagode Hamma Modibbo” tai maganan tana amsa tana juyawa dantama Farrah mugun kallo amman harta bace daga gudun, juyawa Modibbo yayi fuuu yawuce batare dayace ma Rakiya uppan ba, saida yabace mata sanan tai kwafa tawuce gida.
Awani irin zuciye Rakiya tashiga gidansu tana ihu. “Farrah, Farrah” Inna datagani na rege shinkafa atsakar gida tace “Inna ina Farrah”? Baki Inna ta tabe tace “kinfasan tunda tagama gyara gida ta debo ruwa sai kwasan awakai da shanaye ta wuce daji kiwo ko Rakiya baki sani bane? Me Wanan ahannunki” ko kallon Inna batayiba tajuya tawuce tashige dakinsu.💫 FARRAH 💫
✍🏻M SHAKUR
Littafin nan is 500 pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank Saiki turomin evidence of payment ta WhatsApp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting.
EPISODE 9️⃣ Tunda aka haifeshi yataso yafara wayau baitaba shiga wani yanayi na azaba dazaisa harya furta sunan mahaifinshi ba sai yau, yanada gatan dakome yakeso basaiya fadi ba za’amai, kafin yay tari anmai providing, baitaba shiga wani yanayi dazai kira mahaifinshi ba dan mahaifinshi has always being there for him kafinma ya nemeshi, yau shine dayaji azaban karya kashin hannu da idanunkashi biyu kuma yana cikin hayyacinshi bawai anmai anesthesia bane kowani abu ba baisan lokacin da bakinshi yafurta. “Paaa….paaa!” Da bala’in karfi hawaye na tsantsan azaba na zubomai, dariya gardawan sukahau yi babu ko alamun imani a tattare dasu sukace “sannu yaron Papa, ko Papaya kakira yau ba Papa ba bazaijika ba” sukai maganan suna haska fuskanshi da tocula dan duhu yasomayi amman tuni yasume sai hawaye dasuke kan fuskanshi nan fresh ganin haka yasa suka koma wajen Boss dinsu dake waya, juyowa yayi ya katse wayan dayake Lamido yace “Oga wai yaya ake ciki ne”? Dan ajiyan zuciya yasauke yace “sunce nabasu awa ashirin da hudu, yisu yisu su ukun sun kasa tantance abinda sukeso na akashe yaron ne koko abarshi da ranshi ne, kuma uban yaron da shine kadai zai iya bada order kudi idan muka kira ya gigice yana asibiti anyi kidnapping rayuwarshi wanan katon banzan dakuke gani, nidai nabasu 24hrs din, inhar basuyi making decision ba suka bani order kiran uban yaron ba dan Billyan dari nakeso yabamu toni kashe yaron zanyi asalin aikina najirana chan, bazan wuce gobe agarin nan ba saina kammala aikin nan, kuma bayan na kashe shi ko sunaso ko basaso saisun biyani kudin aikina da resources dina da akai amfani dashi inba hakaba suma sun sanni shi kidnapper baida amana dan tonamusu asiri zanyi ku yageta kawai” Lamido yace “bakada case Oga kome kace ayi hakan zamuyi bamaja dakai” yay maganan da muryan nan nashi irin na yan wiwi dinnan, murmushi Ogan yayi yanajin dadin aikin Lamido, dan sosa kai dayaga Lamido nayi yasa yace “ya akayi dawata maganan ne” dan yake Lamidon yayi yace “ahhh Oga dama nazo nadan zaga dajin nanne naga kaman akwai rugan fulani kusa sonake naje nasamo mana taba sanan idan akwai bani (yammata) nadan girgije nasa chaji kagane ai Oga eh yane” dariya Ogan yayi yana zare safan fuskanshi yace “dakai da Lamba kuje, Sagir yazauna gadin wanchan yaron kada kubata lokaci” angama Oga yay maganan yana cire tashi safar fuskan shima Lamba da Sagir duk suka cire sanan suka wuce shikuma Sagir yatafi gadin Zayn dake baccin wahala anan kasa kan ciyaye.
Wuraren 6 nasafiya wani kalan sanyi dakuma zugi na innanaha da hannunshi keyi yafarkan dashi daga wahalallen baccin dayakeyi bude idanunshi tass yayi yanabin dajin dasuke da kallo gasu Lamido duk suna kwance akan bargon dasuka shimfida akasa suna shakan bacci abinsu shikuma kwance a kan ciyayi, wani kalan fuzar da iska yayi abakinshi yana kokarin yunkurawa yatashi zaune amman yakasa sabida hannunshi dayake akarye kaman ya kurma ihu yakeji hannun ya kumbura, ahankali yabi buredi da pure water da aka bashi jiya daya zubar yakeyi akasa da kallo, yunwa yakeji bana wasa ba rabonshi da abinci tun na safen jiya da Mami tabashi baida wani cin abinci dama sabida su taba da sauransun dayake sha suna cikamai ciki amman inhar bai shaba sanan baici abinci ba yunwan dayake zuwa yaji yana zama extreme, dudda kalan yunwan dayakeji baikai kalan kishin ruwan dayakeji ba, lips dinshi sun bushe, bakinshi ya kape sabida tsan tsan kishi dayakeji ga azaban ciwo, tunda yake shi baima taba ganin pure water ba sai jiyan dasuka bashi, ganin abin yayi kaman fitsari amman yanda yakejin kishin nan yanzu he’s willing yasha maybe yamasha zaiji sassauci a zugin da hannunshi kemai, yunkurawa yayi da hannunshi dakeda lafiya amman ina abin yagagara sabida hannun a daure suke tare koyaya yay motsi damai lafiyan saiyaji amara lafiyan, wani kalan kara na azaba yasaki yahakura da tashin yana kallon sama yana tunani cikin tsananin tsoro da azaba da fargaba dakomi ma yace “am I going to die”? Yay maganan ahankali muryanshi a tsinke shi baitaba sanin akwai kalan wahala da azaba haka aduniyan nan ba saiyau, hawaye ne suka zubo daga gefen idanunshi na tsananin wahala ahankali yace “Dad, Mami I am scared” yay dan shiru sanan kaman karamin yaro yace “I am afraid of this place, I am afraid of this people, Papaaa” har cikin ranshi yakejin tsoron komi na wurin, shi baitaba fada ba, he just lived a wired life, baidama friends at all, rayuwanshi kawai yayi shaye shaye, yaci abinda yakeso, yasha abinda yakeso and have sex, ko matayen dayake sex dasu bawai yana magana dasu bane no, kawai yayi abinda yakeso yabasu kudi su wuce, ko kina sonshi kin sama kanki wahala ne dan baimasan yaya ake soyayya ba, baisan anything kan life ba, his entire life revolve around, shaye shaye, cin mata, kallon ball, ga zuwa club, babu any aboki namiji ko Aboki ya mace in his life, he is Zayn, and he is alone kaman yanda Baban shi ya haifeshi alone haka ma life bashing yake alone. Baisan inane wajen nan ba, baitaba zuwa wani gari a Nigeria ba banda Abuja wanda nan iyayenshi suke sai lagos, lagos ma airport kadai baitaba fita daga airport ba, baisan inane nan ba, baisan wani daji ne nan ba, baisan tayaya aka kawoshi nan ba, tayaya su Papa zasu rescuing nashi, ahankali yace “am I gonna die today”? Yakara tambayan sararin samaniya dayake kallo wanda rana ke shirin fitowa, hawaye ne suka zubomai ahankali cikin wata kalan raunanniyan murya irin muryan wanda yay loosing hope completely dinan yay giving up yace “Ya Allah save me please” (niko M shakur nace yau kasan da Allah Zayn). Tafiyan abu dayaji akan hannunshi yasa dasauri yajanye idanunshi daga sararin samaniya yakalli hannu, wani bakin babban gizogizo yagani irin na dajin nan wani kalan zabura yayi yatashi yakwala ihu. “Ahhhhhhhhhh Spider, Spiderrrrrrrrrrr somebody help meeee” yanda yake ihu with all his power saika tausayamai kaman zai zare, farkawa kidnappers din sukayi jin kalan ihun da Zayn keyi duk atsorace suka zazzauna, ganin yanda yake ihu yana juye juye yakasa kabar da gizogizon shima gizogizon ya rude dan ihun Zayn ya rudashi yana neman hanyan guduwa, wani kalan tsaki Oga yaja. “Mtssswwwww what kind of a spoilt boy is this” sanan yakalli Lamido yace “please tashi kaciremai abinchan daga jiki koyabar kunnuwanmu suhuta dan dodon kunnena na gab da mutuwa” azuciye Lamido yatashi zuciyarshi tai bakin kirin sabida yanda Zayn yatadasu daga bacci yana zuwa gabanshi hannu daya yasa yacire gizo gizo yaa jefar sanan akufule ya dumama Zayn wani annamimin naushi akan idonshi yace “dan shegiyan yaro kawai malalaci gizogizo yakema ihu haka saikace mace” tashi Oga yayi dasauri ganin nushin dayama idanun Zayn dayasa Zayn yakife fuskanshi kan kafafunshi dasauri yace “haba Lamido kakosan iyayen yaron nan zasu tambayi proof of life zaka tsiyayemai idanune” cikin fushi Lamido yajuyo yadawo Ya kwanta yace “shiyaja ai uban wayace yatadamu kashe shi girgizon zaiyi, saisa na tsani yaran masu kudin nan wlh, bana ragamusu idan mukai kidnapping nasu, Allah ya soshi namiji ne da wlh ya cinyemai gutsu” kallon Lamidon yayi dahar yamaida idanunshi Ya Lumshe sanan yakalli Zayn da fuskanshi ke kife kan kafafunshi yay shiru kaman anyi ruwan sama an dauke sanan yakoma shima ya kwanta ranshi abace da abinda Lamidon yayi. Zayn ji yayi idanunshi na dama da Lamido ya nusa yama daina aiki, jiyayi kaman irin an fasa kwai abu kawai tsiyayowa yake daga cikin idanun hakan yasa yay shiru yama kasa kuka yakasa ihu yakasa komai sai dan karen azaban dayakeji gashi bazai iyakai hannunshi yataba idanunba saisa kawai yadaura fuskanshi akan kafafunshi yay shiru yariga ya sadakar mutuwa zaiyi. ****
Saida ta chanza kaya agurguje kafin ta kwaso tumakon su fito tana addu’a Allah yasa kada Rakiya ta rutsata agidan, kayan fulanin ta tasaka dan rigan fulanin da suka koma kaman brown tsabagen sakawa koda yaushe yay mata chachas ajiki sai zanin dabai gama kaimata har kasa ba ta daurashi tsaf sai fararen kafafun dake sanye da silipas dinta da duk yagama sudewa shima Shafa tabata, kanta ta daureshi tsaf da adiko (dan kwali) na wani kodaddiyar atampa, goshinta sanye da wani oldi (sarka) ja na beads dayan fulani kesawa a goshi, kunnenta na sanye da dankunni na beads suma ja, sanan tadaura babban hulan hat 👒 na zuwa kiwo dinan akanta tadaure igiyan a gemunta sabida rana, hannunta rikeda sandar kiwo, tai wani irin bala’in kyau dudda babu wani something meaningful kokuma mai kyau ajikinta amman ka kalleta baraka iya cire idanunka akanta ba saika gama karemata kallo tsaf sabida she looks simply beautiful abinda yake karasa Modibbo ke bala’in sonta kenan.
Ahankali take tafiya sabida yunwan datakeji tun safe ko ruwa ba’a bata tasha ba, amman bata wani damuba dan yawanci dama idan tafita kiwo saitayi nisada karkaran su zata tsaya ta tatsi nonon shanu tasha abinta tai nak sanan tasakesu tashige cikin wani kogo Awani dutse daya zaman mata kaman gidanta tai bacci ta abinta.
Sosai tai nisa dan sunbar karkaransu gabaki dayama suna dajin Allah awakan sai cin ganyayyaki suke suna jin dadinsu, gawani babban dutse (rock) awurin tsakiyan dajin hawa dutsen tayi sanan tashiga cikin wani lungu daga waje bazakace lungun nada fadi aciki, daga waje barama kagane lungu baneba dan yay kama da dan fashewan dutse, sai kashiga daga ciki, fadi ne dashi dayay girman daki gawani kalan sanyi ni’ima aciki, wani kofi ne mai kyau awanke awajen, tsugunnawa tayi tadauka tana murmushi sanan ta ijiye sandarta tajuya tafice, cikin tumakan ta shiga sanan ta tsugunna gaban wata saniya ta tara kofin tana tatsan nono tana murmushi, saida tagama tatsan iya nonon datakeso sannan ta mike tsaye rikeda cup din a hannu yana kallon fresh nonon dake cikin kofin, wani kalan murmushi tasaki daya bala’in karama fuskanta kyau sanan tawuce wajen dutsen tahau batare daya shiga kogon ba tazauna awaje, ijiye kofin tayi agefenta sanan taja hulan kanta ta saukarda shi abayan wuyanta sanan tasa hannu tadauki kofin takai bakinta tafara shan nonon, tanasha tana kallon yanda shanaye da tumakan ke shanawa abinsu sunacin abincin su suma, kaman daga sama taji wani kalan ihu daya bala’in firgitata saida cup din hannunta ya kibude yafadi tundaga nan sama inda take har zuwa chan kasa nonon ciki yabare akasa kofin ya fashe, bin ko’ina tashigayi da kallo bataga kowaba, duka rugarsu ita kadaine kezuwa kiwo wajen nan dan nan bangaren dajin babu kowa anrigada anfita daga karkaransu daman gudunma su Modibbo kada yasan inda take zuwa kiwo yasa batayi a rugarsu saita kawo tumakan sun fita daga gari, cikin ikon Allah kuma Allah yabata har daki awajen Wanan dan kogon nata idan tazo dazaran tagama shan nono shiga take ta narki bacci abinta bayan ta tashi takara debo nono tasha sanan da yamma sutafi gida. Babu wani kwana ko lungu da sako dabata sani ba cikin wanan dajin gabaki dayanshi, bata sabajin mutane adajin ba hakan ta firgita sosai to waye adajin nan dahar yake ihu? Kodai koma waye ke ihun maciji ne ya sareshi kokuma wani abune yafaru? Taje taduba ne? Wani kalan ajiyan zuciya tasauke tasan ba Modibbo bane dan baisan wajen nan ba, hannunta tasaka ahankali tabaya tajawo hulanta tamaida kanta tasake kulle igiyan da kyau yakama fuskanta chas, sanan ta tashi tashiga kogon sandarta tadauko tafito wanan karan bata tsaya sauka normal sauka ba wani kalan tsalle tayi tadiro tundaga kan dutsen har kasa chak, murmushi tadanyi dan ta tuna Shafa ne, Shafa tahanata tsalle tsalle da dirke dirke tacemata babu kyau mace nayi.
Ahankali tafara tafiya zuwa direction din dataji ihun wanda taji yataho daga yankin gabas din dajin, gently take tafiya babu ko alamun tsoro akan fuskanta sosai tai tafiya mai nisa bataga wanda yay ihun ba hakan yasa tace to Kodai kunneta ne kokuma kukan tsuntsune, dan tabe baki tayi ganin tayi nisa sosai da inda take tajuya tafara tafiya kaman daga sama taji magana. “Nifa nagaji Lamba tun jiya banci abinci mai kyau ba, munje rugar fulanin chan ko shaguna basu dashi, gashi Oga yahanamu mu shiga cikin city mu kashe yaron nan muhuta” jin sahun tafiya yasa dawani irin sauri Farrah takalli bishiyan dake kusada ita na mangwaro dayakeda ganye acike, hawa bishiyan tayi da bala’in sauri kada aganta abunku da yar karama bacewa tayi asaman bishiyan tai lamo tana rungume da sandarta kirjinta na bugawa dum! Dum! Dum!
Dazaran taji ana maganan kashe mutum ko kisan kai gabanta ke fara faduwa dan tanada trauma da kisankai, daidai gaban bishiyan Lamido da Lamba suka tsaya duk suna sanye da bakaken kaya hannun Lamba da bindiga yana gogewa da handkerchief yace “nima Lamido nagaji, jibi yanda bindigata tai kura ace tun shekaran jiya batasha jini ba saikace ba Lamba ba, ni wlh dama tsiyayemai duka idanun biyu kayi ba dayaba kachal, bantaba kidnapping mara dadi ba kaman wanan” dariya dukansu sukayi Lamido yace “dadin zaizo saiyafi na duka kidnapping din daka tabayi dadi aduniya” sukai wani irin dariya, Lamido yace “ni kawai so nake na nakasa yaron gabaki daya hakanan kawai na tsaneshi” dariya Lamba yayi yace “kodan kaganshi yaron kyakkywa dashi, nasan tunda kake baka taba ganin yaro namiji mai kyau kaman shi ba” hararanshi Lamido yayi yace “tsiyayemai idanu da karyashin danayi basu isheni ba, farkamai ciki nakeso nayi wlh da ask zomuje kaga” yawani ja hannun Lamba suka wuce bin hanyar dasukayi Farrah tayi da kallo gabanta nafaduwa din dim din, yanzu mutanen nan wani sukai kidnapping zasu kasheshi, yanzu yaya zatayi? Taje tafada ma kai gari? Jikinta har bari yake tana tunani taje gidan mai gari kafin ma abarta taganshi saita bata awanni akama bari ta ganshi Tayaya zatai musu bayani, yanda suke da bindigan nan kuma tasan yan garinsu da tsoro bazasu taba zuwa ba, to taje takira Shafa? Takara tambayan kanta, yanzu taje Shafa batanan ta tafi yawon ta, ihun azaban Zayn taji dayasa tawani kalan dirko daga kan bishiyan ko’ina na jikinta na rawa, takalli gabanta takalli baya tagudu ne koko taje tagani, kasa daurewa tayi tai hanyar dasu Lamba sukabi da rarrafe daga nesa ta hangosu su hudu tagani yan fashin sai wani saurayi da kallo daya tamai taji kirjinta yabuga sabida yanda fuskanshi ya kumbura suntum idanunshi daya duk jini yabata idanun arufe sai dayan yake iya budewa kadan, an daddaureshi, kallo daya tama hannunshi tagane akarye sabida yanda yake lilo.
Ahankali Zayn yana kallon pure water shi natun jiya yace “ru……ru…wa” dariya dukansu hudun sukayi Lamido yace “Oga yaji wuya wai zaisha ruwan” dariya duk sukayi Oga yace “bashi ruwan” daukan ruwan Lamido yayi sanan yataho gaban Zayn din yakai ruwan bakinshi yabude yadauko kan Zayn daya bude baki yana zazzago da harshe baida burin daya wuce yaji ruwan nan abakinshi, pure water Lamido yakai kaman zai samai abaki Zayn yataho da sauri Lamido yawani buga ledan pure water ruwan tafashe kan Zayn yace “kamutu da kishi” hawaye Farrah taji yazo mata a idanu sosai dawani irin sauri tajuya tana rarrafe saida tai nisa da wajen sanan ta mike tsaye ta kwasa da gudu cikin one minute takai wajen tumakan ta, wani kalan bari jikinta yashigayi tana shaking tana tafiya tana zagaye tarasa mema zatayi kaman daga sama takai hannunta gefen zaninta goran turaren yajin da Shafa tamata taji, cirowa tayi tai wani kalan murmushi dudda gabanta na faduwa, rikewa tayi a hannunta gam sanan tashiga hada shanayen da tumakan zuwa direction din gaban, sanan cikin wani kalan sauri da karfi tashiga dukansu hakan yasa suka wani haukace suka kwasa da gudu ji kake dim dim din kaman saukan aradu yanda suke gudu haka itama yake gudu gasu da yawa saida sukakai ta saitin hanyar dasu Lamba suke ita tai kwana danta bullo ta baya sukuma su bullo ta gaba.
Kaman daga sama duk suna tsaye suka shigajin alamun gudu kasa na amsawa, dasauri Oga yace “kunji abinda nakeji miye ke sauti kaman gudun mutane, haka? Jeku dub……” kafin yakarasa maganan wasu bijiman sanaye da raguwa da bazasu iya gane iya adaddinsu ba sun shigo wajen da gudu uwa ana korasu, wata saniya taci karo da Lamido ta watsar dashi, gabaki daya sakasu a tsakiya shanayen sukayi sun cika wajen tas sukuma duk sun firgita abunku da criminals kowa na ciro bindigarshi yana setawa.
Ganin haka yasa Farrah tafito daga inda take leke dan ita tazagayo tabaya ne tazo gaban Zayn da shanu ya kare da gudunta, baima lurada ita ba ko kadan sabida wahalan dayake ciki hannun mutum kawai yaji an daura akan kafadarshi daga tabayanshi dayaji wani kalan sanyi ya shigeshi saikace hannun kankara dasauri yadago kanshi da idonshi kwara daya dayake iya kallon mutane dashi daya kankance Ya daurashi kan Farrah, cute little farin index finger dinta Farrah tadaura kan pink lips dinta alamun yay shiru, bama ta tsaya kallonshi ba tasa hannunta da bala’in sauri tashiga warware mai kullin da akayi a hannunshi Zayn nawani irin kallonta da ido daya tazare igiyan hannun ta yar, sanan tashiga kwance na kafan nashi da bala’in sauri kafin kidnappers din su juyo suganta, tundaga kan hulan kiwon dake kanta yake kallo irin na kauyen nan da akeyi da itace daya daure igiyan akasan gemunta yake kallo, zuwa gefen fuskanta da gashi ke kwance akai kaman na yar jaririya har zuwa kumatunta zuwa red dogon bead Earings dinta dake lilo a kunnenta zuwa fararen hannuwanta datake kwancemai igiyan dasu, kodan yana tsakiyan azaba ne and she appeared from nowhere but ahankali cikin muryan dashi kadai zai iya jinta yace “is she an angel?” Wani kalan fincikota akayi. “Ke Yar Fulani? Dama Kece kika cika mana wajen nan da tumakai”? Oga daya damki Farrah yafadi hankali tashe ranshi abace.
To jama’a is FARRAH going to be okay??💫 FARRAH 💫
✍🏻M SHAKUR