Ganin ido complete - Chapter 74
Ganin ido complete Chapter 74: Ganin ido complete Chapter 74. "Uhmm! To na gode. Kai ma ka yi kyau sosai..."
3,375 words
"Uhmm! To na gode. Kai ma ka yi kyau sosai..."
"Yanda kika ce kenan."
Bowl ɗin na miƙo ina faɗin.
"Na baka ka ciyar da su.."
Zaro ido ya yi sannan ya yi dariya ya ce.
"What! No...kada na shaƙa musu a hanci."
Dariya na yi ina jinjina kaina na ce.
"Hardai Aryaan, wallahy idan ba ka yi da gaske ba, sai ka shaƙa masa a hanci saboda gadauniya da rashin zama wuri ɗaya."
Matsowa ya yi a kusa damu ya taimaka mini ina basu yana ta dariya ganin yanda muke ta drama, Idan na yi da wannan kafin in waigo wannan ya kama wani abun na daban, a haka dai har muka gama sannan na gyara musu muka wuce ɗaki domin yi shigar da su bacci.
Dariya na yi tuna abinda na faɗawa Suwara ɗazu na ce mata maganin bacci zan ba su domin kada su shiga rayuwata da ni da mijina a yau. Da haka na yi ta addu'a a raina ina roƙon Allah yasa idan suka yi baccin nan kada su farka a yanzu sai na gama bai wa mijina farin ciki da na ƙudurta da shirya masa a wannan daren.
Shi dai yana tsaye tun ɗazu yana kallona ganin yanda nake ta lallaɓa su suna shan Nono har na samu Allah ya taimakeni suka yi baccin.
Bayan na gama tofesu da addu'a na taso ne na ji ya rungumeni a hankali ya ce.
"Thank you for everything Bibi...you are the best mother ever. Allah ya baki lada akan duk wata hidimarki akan su da kuma ni..."
Murmushi na yi tare da saƙalo hannuna cikin wuyansa ina kallon idonsa na ce.
"And thank you for being the best Husband and Super Daddy. Allah ya ci gaba da kare min kai a duk inda ka shiga a faɗin duniyar nan. Allah ya ci gaba da baka halal ɗinka komai ƙanƙantarta ya kuma kare daga sharrin haram komai yawanta..."
"Amin.."
Saukar da hannuna na yi na saƙala a cikin nasa ina masa wani kallon na ce.
"Can we?"
"Anything special?"
Lips ɗina na kai a hankali na goga a nasa sannan na janye tare da kashe masa ido na ce.
"We are gonna burn in fire today..."
Cikin wani irin yanayi ya jinjina kansa yana mai riƙo kwankwasona ya ce.
"And Dayaa is ready to burn in fire..."
"Let's go..."
Tun a wurin wanka ya tabbatar da kalamaina domin na bashi mamakin da sai dinga kallona yana jin na koma masa wata Bibin ta daban a yau. Bayan mun fito muka shirya inda a gabansa na ɗauko wata fitinanniyar Nighty wacce tun ɗazu na gama jiƙeta da sihirtaccen ƙamshin da na shirya masa. Bayan na saka na zare ribom ɗin kaina na zubo gashina kamar yanda na san yana burgesa.
Kallona yake yana mai jin duk wata gaɓar da ke jikin sa tana amsar saƙona yanda ya kamata.
Rigar da ke jikina da ita da rashin ta duk ɗaya, maimakon shi da ya saba fara kawo mini far miki, ni ce nan yau na nemi na zautar da shi da wata kalar zazzafar soyayyata wacce ya ji ta a yau har can cikin ƙololuwar birnin ransa.
Zallar madarar ƙauna muka zuba mai matuƙar daɗi da sanyaya zuciya. Bayan mun kambala mun yi wanka ne na je na ƙara duba su Arhaam wanda duk tsawon lokacin nan suna nan suna bacci abin su sannan na juya na koma a hankali na kwanta a jikinsa tare da ɗora kaina a ƙirjinsa.
Ji na yi ya rungumeni tare da kissing lips ɗina a hankali ya ce.
"Thank you for the Love we made today...kin bar ni wani tarihin da har abada ba zai goge mini ba kamar yanda farkon tarayyarmu ta kasance a tunanina...you promise us to burn...and we burn Happily...thank you."
Shiru na yi tare da ƙara narke masa ba tare da na ce komai ba. Sai dai kalamansa sun yi tasiri a zuciyata sosai, da wannan farin cikin na yi ta murmushi a raina har na yi bacci.
Shi kuwa, gabaɗaya baccin neman sa ya yi ya rasa a wannan daren tsabar yanda ya ji duniyar ta yi masa daɗi. Bayan ya tabbatar ta yi baccin da gaske, nan ya lallaɓa ya zame ta gefe tare da lulluɓa mata Duvet ya saka pillow ya tare da kada ta ji ta ita kaɗai.
Sai da ya jima yana kallon fuskar twins ɗinsa yana ta zubo da hawayen farin ciki sannan ya tashi daga ƙarshe ya je ya yi alwala ya zo ya duƙufa yana ta nafila yana godiya ga Allah da kuma neman albarka da fatan cika da kyau da imani.
Yana nan zaune yana karatun Qur'an ya ji motsawarsu. Koda ya duba agogo ƙarfe huɗu saura ne na dare.
A hankali yaje ya tasheta taje wurin ta ji da su wanda sai da ya dawo masallaci yaje ya tarar ina ɓingire a nan na ci gaba da baccina tare da su.
Murmushi ya yi sannan ya tashe ni a hankali yace.
"Kin yi sallah ne?"
"A'a! An yi ne?"
"Ƙarfe shida da rabi fa..."
Dirowa na yi a raina ina faɗin ai yanzu salla ta daman sai wuraren ƙarfe shida zuwa bakwai nake yinta, duk yanda Ammie ke tashina sai na yi da gaske sannan nake iya miƙewar tsabar yanda bacci ke dagula lissafina.
Bayan na yi sallahr na kambala na kira Bibi domin ta yi musu wanka ta shirya su, sannan na wuce kitchen na duba mai girki, wacce ɗaya daga cikin chefs ɗin Ziza ne na Eatery ɗinta. Ɗayar kuma ita ce mai share-share.
Wanka na yi na shirya cikin wasu English wears na riga da skirt da hula sannan na je na gyara mana table muka je muka karya.
Haka muka yi ta mu huɗu muna ta rayuwarmu inda a nan muke ta ƙara sanin wasu abubuwan dangane da juna tsawon kwanaki uku.
Ina ɗaki da Arhaam a bayana ina duba wasu ayyukan Daddynsu Arhaam da ya nuna mini yace an kawo musu talla na duba na gani kafin ya mini bayanin yanda abun yake sai ga kiran Ammie ya shigo.
Hankali a tashe ba ta ko bari muka gaisa ba ta ce.
"Beenafah Jafaru ya ɓata, tun ranar da ya iso ya ajiye jakarsa ba'a ƙara sanin ina yake ba. Wayarsa kuma a kashe."
Kai tsaye na ce.
"Ni da Mijina ne muka kulle shi a police station...ni tun a ranar ma na so a kashe shi amma Daddynsu Aryaan ya hana...."
Cikin wani irin tashin hankali ta ce.
"Mi kika ce Beenafah? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Miye ya yi muku haka da zafi..."
"Ammie Jafaru bai da mutunci....kuma a can zai ƙare rayuwarsa har ya mutu."
"Dan Allah Beenafah ki yi haƙuri ki rufamin asiri,...kinga...ina shi Hammodin yake??"
Daga haka na ji ta kashe wayar wanda daga nan ban san mi ya faru ba, sai gashi ya shigo saɓe da Aryaan a kafaɗarsa ya kalleni ya ce.
"Ki shirya mu tafi police station ɗin. Ba dole sai na je ba, amma zan tafi domin wani dalili."
Sauke shi na yi na shirya cikin wani Lace da mayafinshi sannan na sauya musu kaya, sai da na gama duk shiririta ta sannan muka fito a tare muka shiga mota. Na yi mamakin ganin Convoy ɗinsa domin in dai a cikin gari ne daga ni sai shi muke fita a mota. Sai dai idan garin ne zamu bari zamu fita a irin wannan yanayin.
Koda muka isa mun tarar da su Ammie har sun Iso da su Maman Fakiha da Baba.
Tuni duk mutanen da ke wurin suka ɗauki saiti sai ya yi musu umarni da a fito da shi.
Ganin yanayinsa kaɗai sai da ya sanya su Ammie fashewa da kuka mai tsanani. Domin baka ma gane fuskarsa muddin ba ka yi masa kyakkyawan sani ba.
"Jafaru! Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Wai miye yake faruwa ne??"
Cewar Ammie tana mai kallona da ni da Daddynsu Arhaam.
"Kowane irin laifi ya aikata muku ai bai cancanci wannan hukuncin ba. Shi fa tamkar ɗan uwa yake a wurinku..."
Wani kallon ya yi masa sannan ya ce.
"Wannan dalilin ne yasa har kika iya ganinsa a nan Hajiya. Ba don hakan ba da yanzu wani zancen ake na daban....Kai! Ka buɗe baki ka faɗa musu laifin da ka yi, komai da ka aikata bana so ka rage musu, idan ba haka ba, zan saka ka a motana na tafi da kai wata duniyar da har abada ba za ka taɓa mantawa dani ba."
A somaye ya buɗe bakin sa tsabar yanda ya sha baƙar wahala ya ce.
" Zan faɗa! wallahy zan faɗa dan Allah ka yi haƙuri na tuba."
Yawuna na tofa masa ina mai yi masa kallon tsana na ce.
" Ashe kai ɗin marar kunyar ƙarya ne matsoraci. Ba ka ce a shirye kake domin akan son da kake mini ba koda za ka mutu ba? Miyasa kake magiya kana bada haƙuri a yanxu?"
Hannu Mama ta ɗora a ƙirji tana mai doka wata irin taslima sannan ta ce.
"Yanzu ashe duk tsawon lokacin nan ba ka ji maganata ba Jafaru? Duk yanda na tsawatar maka akan wannan shashancin baka saurare ni ba ashe?..."
Kallon Police ɗin ta yi ranta a ɓace tace.
"Yallaɓai! Ni ce nan mahaifiyarsa, wannan kuma mahaifin sa. Ku ɗauke shi ku mayar da shi cikin Cell ku yanke masa duk hukuncin da ya dace da rayuwarsa mun baku dama.."
Jinjina kai Baba ya yi ya ce.
"Wallahy ni ma nan na baku dama! Marar mutunci wanda bai san harkar girma ba..."
Rai babu daɗi Ammie ta ce.
"Kayya! Dan Allah ku saurara Haba..."
Kuka Jafarun ya fashe da shi sannan ya ce.
"Dan Allah ku yi hakuri, wallahy daga yau har abada ba zan ƙara kallon ma inda take ba..."
"Sai fa ka buɗe bakinka ka yi musu bayanin irin cin zarafi da toxarcin da ka bi ta da shi. Bana so wani ya riƙe ni a rai ya yanke min hukunci da cewa saboda ina da kuɗi ina iko na ci zarafin ka. Na fi ƙarfinka ta kowace fuska, waɗanda suka fika komai sun buga dani sun bar ni ballantana kai wanda ko a silifas ɗina ban kawo ka ba. "
" Ai zan faɗa musu. Wallahy zan faɗa..."
Daga nan ya zayyane musu duk irin yanda ya yi ta bibiyata da irin nasarar da ya samu ta haɗamu husuma da kuma bibiyata da ya riƙa yi a waya, har zuwa wurin bokan sa bai rage komai ba.
Kuka sosai Mama take tana faɗin.
" Allah ya isa tsakaninmu da kai Jafaru! Allah ya wadaran rayuwarka. Abin da kake yi kenan ashe bayan duk nasiha da jan kunnen da na yi maka. Mi kake da shi mi kuka kake taƙama da shi da har ka sanya kanka a cikin wannan masifar ka nemi rabata da gidan auren ta? Ashiru ma da ya fi ka sanin zafin ta ya turo neman aurenta Allah ne bai yi ba, sannan yana da sana'arsa yana da madogararsa, ya haƙura da ita ya yi mata fatan alheri ballantana kai...maimakon ka ɗauki maganar iyayenka ka haƙura ka je ka yi karatu ko don gobenka, shi ne kaje ka lalata karatun ka cinye kuɗin registeration har sau biyu, kana ɗaukar kuɗin kana kai wa wani ƙaton boka ƙaton mushriki saboda shafewar basira. Allah ya isa ban yafe maka ba duniya da lahira, ka je tunda ban isa da kai ba shi ke nan. Zumuncinmu kuma tunda ba kai ne ka haɗa ba, wallahy ba ka isa ka raba mana shi ba."
Daga haka ta miƙe daga kan bench ɗinda take zaune ta yi tafiyarta. Duk kiran da Ammie ke mata bata tsaya ta waiwaye ta ba.
Itama Ammien jiki a sanyaye ta kalle shi ta ce.
" Jafaru ba ka kyauta ba. 'ƴar tawa ka ke ta bibiya ashe kana bin ta da sharri? Yanxu kai ba ka ji kunya ba? Da ace Fakiha ce ko Farisa wani ya dinga mata haka ya za ka ji a ranka?"
Ajiyar zuciya Ya Mohaa ya sauke sannan ya ce.
"Ku zama shaida...dukkanku ku zama shaida..idan har ya sake bin koda inuwar inda matata ta taɓa, to lallai ba zan tsaya tunani na biyu ba a kansa."
Daga haka ya ja hannuna muka fice wanda a lokacin har an fara kiran sallar Magrib. Gidan Hajiyarsa muka wuce inda sai da muka shiga bakin Main door ya ce na yi musu sallama domin gobe zamu tafi, kuma asuba zamu yi.
Ina jin haka na ce masa Allah ya kaimu rai da lafiya. A raina kuma nace ni dai Jafaru ka ja mini salalan tsiya, bukin Fakiha da Ya Ashiru da nake buri da saka ran a ɗan jira na yau ka gwanɓale mini shi.
Ina shiga muka gaisa ya fita masallaci ni kuma na tsaya nan inda Hajiya wacce ta cika da farin ciki ganin Abeer da Mima suna yi wa su Aryaan wasa. Wurin Munira na zagaya muka gaisa, nan ta shaidamin cewa na aurar da Haulatu tana Mafara aka kaita. Allah sanya alheri na yi mata sannan na fito shaf-shaf na shiga sashensu Aunty Ziza ita da Suwara.
Zaune na tarar da su da paper da Biro a hannun Suwara.
"Miye kuke yi?"
Dariya suka yi sannan Aunty Ziza ta ce.
"Girke-girke ne nake koya mata Theoretically, kafin mu fara practical.."
Jinjina kai na yi ina murmushi na ce.
"Mun yi mubaya a domin kujerar ki ce,kuma mun bar miki kayan ki. Allah ya ƙara basira da zaƙin hannu. Gaskiya na yi farin cikin ganin yanda kuka haɗe kanku haka. Allah ya ƙara muku zaman lafiya ya ƙara buɗe Ya Emraan hanyoyin arziki..."
Hannuna Aunty Ziza ta riƙe tana wani irin murmushi ta ce.
"Ina mai ƙara baki haƙuri Beenafah. Muma ɗin nan muna alfahari da samun ki kuma muna gode miki, domin shigowarki rayuwarmu ce wasu abubuwan da yawa suka sauya. Alhamdulillah da irin samun mijina a lokacin da yake Naval officer, a yanxu ma Alhamdulillah zan ce domin samun sa da darajarsa sun ƙara yin sama, ta dalilin ki da yarjewar ubangiji ga shi zamu ƙara yin gaba muma zamu koma UAE da zama,... "
Cikin wani irin farin ciki na ce.
" Dan Allah da gaske kike? Yaushe?"
Dariya Suwara ta fashe da ita ta ce.
" Ni fa daɗina dake azarɓaɓi Aunty Beenafah."
"Wallahy kin ji na rantse miki bani da wannan labarin.."
Aunty Ziza na dariya ta ce.
"Sai Suwara ta haihu tukun.."
"Wayyo Allah daɗi. Allah ya nuna mana ya sauketa lafiya. Mu gobe zamu tafi in sha Allahu, sai kunxo. Don dai kam, nasan abun da zai dawo damu ƙasar nan ba kusa ba."
"Allah ya kai lafiya. Idan kin je muna gaishe da Mijinmu..."
Dariya na yi sannan na ce.
"To a nawa?"
"Ko nawa kike ce."
Cewar Suwara tana dariya.
Waje na nufa ina faɗin.
"To ba za a faɗa ɗin ba. Ku da yanzu haka ma baku fi minti biyar da gama magana da shi ba, shi ne za ku wani aike ni da saƙon renin hankali. In ƙulle gaisawa ta fatar baki daga nan har Dubai saboda ga Beenafahr iyayi."
Dariya suka bini da ita har muka shige sashen Hajiya sannan muka sallar Isha muka fito har mota suka rakamu.
Bayan mun fito gidan Ammie muka wuce itama na yi mata sallama. Ta ji mamaki da ta ji zancen tafiyarmu wai gobe-gobe. Amma kuma tuna irin abin da Ya Jafaru ya yi sai ta ga cancantar hakan, duk da cewa an kai ƙarshe da shi kuma yayi alƙawarin ha zai ƙara ba. Sannan aka sake shi Baba ya riƙa shi shi da Ya Hamza suka kai shi asibiti.
Kallon yanda Bahrain yake ta wasa da su Aryaan na yi ina murmushi na ce.
"Za su yi kewar ka Uncle Bahrain..."
Hawaye na gani a idonsa sai kuma ya yi murmushi ya ce.
"Tun ranar da kuka tafi gidanku na ke kewar su ai."
Dariya Ammie ta ce.
"Ai a ranar kasa bacci ya yi, sai ga shi ya dawo ɗakina ya kwanta wai kewar yaransa ta hana shi bacci."
Dariya na yi na ce.
"Allah sarki uncle Bahrain! To ko dai na bar maka su?"
"A'a, ki dai bari idan lokacin cire su a Nono ya yi ni zan je da kaina na dawo da su."
Fira muka ɗan taɓa sannan daga ƙarshe Ya Mohaa ya shigo suka gaisa da Ammie, haƙuri ta ƙara ba shi sannan muka fito zamu tafi.
Kallon sa na yi na ce.
"Dan Allah ina neman alfarmar 5M"
Jinjina kansa ya yi ya ce.
"Cash kike so ko transfer?"
Kallon sa na yi da mamaki na ce.
"Ba za ka fara tambayata mi zan yi da zunzurutun kuɗi har haka ba?"
"Har abada ba zan tambaya ba, ai daman tun da muke baki taɓa tambayata kuɗi ba. Yau ɗin ta kasance mini rana ta musamman. Duk abinda kuma za ki yi da su,na san mai muhimmanci ne..."
"To na gode, Allah ya saka da alheri ya ƙara arziki."
Ya Hamza na ce ya bini ya karɓa kuɗin sannan na koma ciki na cewa Ammie.
"Ammie zan ba ki kuɗi dan Allah ki ba wa Ya Ashiru hannunki da nasa."
Jinjina kanta ta yi tace.
"In sha Allahu kuwa. An gode, Allah ya amfana."
"Amin Ammiena, sai da safe."
Bayan mun fito sai da muka biya ta gidan Daddy ya yi wa Mummy gaisuwa sannan muka biya gidan Aunty Labiba sannan bayan mun koma gida Ya Hamza ya zo tare da Bahrain suka karɓi kuɗin suka wuce.
Washegari tun asuba kuwa muka fita har da Biba a wannan karon. Kaduna muka yada zango inda muka kwana ɗaya gidan Aunty Nadeeyah kamar yanda na roƙi alfarma sannan shi kuma ya je ya duba aikinsa sannan muka wuce Abuja muka wuce.
*******
Su Ammie kuwa, sai da ta tsaya aka yi bukin Fakiha da Yaya Ashiru wanda ya ji matuƙar farin ciki na zuwa bukin sa da ta yi sannan ga kyautar kuɗi har 10M daga gareni wanda ni ma kaina ban san 10m ɗin ba ne, ni dai kuɗi na tambaya kuma na ɗauka su aka bani ashe ashe an ninka mini.
Ya yi matuƙar farin ciki da shi iyayensa da en uwansa ba kaɗan ba. Sai godiya yake yana faɗin dan Allah ta isar da saƙon godiyar sa zuwa gare ni.
Bayan an kammala bukin da kwana biyu suka juya suka koma gida tare da su Ya Hamza har da Aunty Hussaina wacce ta dinga kuka akan cewa ta tafi da ita kamar yanda ta saba a da.
Cikin dangi aka binciko yara guda biyu aka kawo wa Mummy Zaliha, sannan kuma aka kai Kayan auren Ya Hafiz wanda za'a yi nan da wata uku.
Wanda idan an yi auren ne yace zai kai ta gidansa domin matarsa ta ci gaba da kulawa da ita.
Nan ne Ammie ta bashi shawara akan cewa ya sake komawa makaranta tun da wancan da ya yi ya riga ya zama wasted. Amma idan ya jona in sha Allah ba jimawa zai ga ya kambala.
*******
Muna komawa da sati ɗaya ya koma aikinsa wanda ya dawo fita sau uku a sati, Monday, Wednesday da kuma Friday.
Rayuwa muka sake shimfiɗawa sabuwa mai cike da zallar farin ciki muna renon yaranmu.
Muna nan tsawon wata uku wanda a lokacin ne su Aryaan suke watan su na bakwai a duniya. Ina kitchen tare da Madam Amima tana haɗa breakfast ya kira ni a waya.
Ina shiga na gansu yana kwance su Aryaan na ta hawansa suna tsalle-tsallensu na ce.
"Miye wani gani ga gaka amma sai ka kirani a waya?"
Murmushi ya yi mini sannan ya ce.
"Because. Tomorrow, is going to be special. Very, very special."
Cikin farin ciki na ce.
"Wow! Tun ban ji ko miye ba na ji cewar something special ɗin ya yi deeping in to mah heart..."
Kinkimar Aryaan na yi na kashi wurin Biba da sauri sannan na dawo na tallabi Arhaam shi ma na kai shi tare da buge mata warning na ce kada ta kira a waya da sunan suna kuka. Dariya ta yi sannan ta ce shikenan to.
Ɗakin na dawo na kulle ƙofar na jinjina a jiki ina masa wani kallon ina murmushi.