Kenza eBookz

Garkuwa complete novel - Chapter 11

Garkuwa complete novel - Chapter 11

Garkuwa complete novel Chapter 11: Garkuwa complete novel Chapter 11. Ɗaya daga cikin mutun huɗu dake gaban motarne, yasa hannu ya rufe ƙofar, sannn ɗaya…

4,442 words

Ɗaya daga cikin mutun huɗu dake gaban motarne, yasa hannu ya rufe ƙofar, sannn ɗaya kuma ya kira waya, cikin yaren Ɓachamanci yace. "Mun sace mutun biyar, uku yaran gidan Malam Liman ne, biyu daga ciki yaran gidan Ahaji Horo ne". Ɗan jim yayi alamun karɓar umarni. Tsawon daƙiƙu biyar sannan ya ƙatse kiran kana ya juyo ya kalli, sauran tare da cewa. "Yace ku, ku tafi dasu a cikin motar, ku wuce dasu,inda kuka shirya, mu kuma yace mu ɗan tsaya nan, yanzu zaiyiwa shanun Rugar Malam Liman kiranye da dogon fito. To in shanun suka nufi inda yake ba mamaki wasu su biyo shanun daga cikin makiyayan, to yace idan sun biyosu mu kashesu!". Kusan a tare suka sara mishi tare da busa sigarin dake hannunsu. Nan mutanen cikin motar sukaja, suka tafi.

Su kuma saura mutun huɗun, komawa mafakarsu sukayi.

Can cikin tsunƙurun dajin kuwa. Ba'ana ne zaune cikin taron matasan ƙabilar ɓachama da a ƙalla sun kai goma, cikin kausasa murya da bada umarni yace. "Zanyi fito ɗaya zuwa uku, cikin daƙiƙu 10 shanayen Malam Liman da Alhaji Haro da wasu. Zasu baiyana, a nan. Suna zuwa ku jasu ku fuskanci gabas, ta ƙasar Jihar Gombe zaku ratsa, kana ku nufi ƙasar chadi daga can." Shiru ya ɗanyi tare da zuba musu idanu, wani irin azzalumi murmushi yayi cikin barbarci ya kalli biyu dake kusa dashi wanda ƴan ƙanwar Bukar ne su barebari ne, cikin izaya yace. "Kada ku kauda ido akan ko wacce gonar makiyayin da zaku wuce ta gabanshi, ku shiga gonakin manoma, kuyi kiwo a ciki. Idan manoman suna cikin gonakin in sun muku mgna ku kashesu, sannan ku gudu da dabbobin yankin wurin". Cikin barbarci ɗaya daga cikin su yace. "Ba'ana, tsayuwa kiwon bazai ja mana tsaikoba, har cekiyar ya riskemu ba tare da munyi nisa ba". Murmushi yayi mai cike da fajirci sumar kanshi ya shafa tare da cewa. "Ba'akana Ku kiwaci duk gonakin manoma, hakanne zai jawo faɗa tsakanin MAKIYAYA da manoman, daga haka saiku gudu, kaga mun jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, domin su mutanen duniya sun ɗauka duk wanda suka gani da dabobbi yana kiwo, BAFULATANI NE, sam mutane sun kasa ganewa cewa ba sai Fulani kaɗai ke kiwoba, kaga mun tada faɗa mun kwashi dabobbinsu, mun kashesu mun gudu, kuma in sunje kai korafinsu ga hukuma a kamasu ko a korasu ko azagesu, ace suke haddasa faɗa tsakaninsu da manoma, sun zama ƴan ta'adda a idon duniya. Mun kwashe dukiyoyinsu". Dariya sukayi baki ɗayansu, kana suka sara mishi, juyawa yayi, ya fuskanci gabas kana ya durƙusa, ya zuba guiwowinsa duka biyu a ƙasa, yatsarsa manuniya ta hannun hagu ya kafa a ƙasa, kana yatsarsa ta hannun dama kuma, ya toshe kunnenshi na dama, da ƙarfi ya rufe idanunshi kana, ya tsuke bakinsa ya rinƙa zuro iskar wata zazzafar fito mai bala'in sauti. Su kuwa sauran duk rufe ido sukayi dan jin fiton sukeyi tamkar zai fasa musu dodon kunne.

Shi kuwa Ya Lado yana cikin kiwonshi kawai yaga gaba ɗaya, shanun sun juya sun fuskanci gabas, kana sun ɗaɗɗaga kunnuwansu sama, daga baya kuwa sunata karkaɗa binɗinsu. Cikin mamaki yake ratso tsakiyarsu. Dan in makiyayi yaga dabbobi suna haka yasan akwai abun da suka gani, ko mutun ko iska, ko maciji ko dai wani abu na daban to sukanyi wannan alamar dan sanar da makiyayinsu. So ganin hakane yasa Lado ya ƙara kutso kai cikinsu.

Su kuwa dabbobin gaba ɗaya fiton da Ba'ana yake hurawane ya cika musu kunne, ai fa a take suka nausa a guje suka fuskanci gabas, da wani irin masifeffen gudu. Shanu da dawakai na gaba tumaki da awaki na baya hatta belbelun dake cikinsu, suna kiwo binsu sukayi. Cikin ƙarfi Ya Lado yayi wani irin ihun wanda dashi suke kiran dabbobinsu, amman ina basu juyoba.

Da gudu ya fara binsu kana yana ihun neman taimako a wurin sauran makiyayan su.

Amman da yake gudun dabba dana mutun ba ɗaya ba, Sun mishi nisa mai tarin yawa, hakanan shi kuma yayiwa sauran makiyayan dake biyoshi a guje su kawomishi agaji ya musu nisa. A haka suka rinƙa gudu, waɗannan mutun huɗun dake laɓene suka fito suka, tareshi ba zato ba tsammani kawai yaji an burma mishi wuƙa juyowan da zaiyi kuma yaji an kuma burma mishi wuƙaƙe a tako ina na jikinsa. A nan take ya faɗi babu rai.

Su kuwa nan sukabi shanun da gudu.

Koda sauran makiyayan suka iso inda gawar Ya Lado take. Hankalinsu yayi masifar tashi. Tabbas sun san babu masuyi musu wannan aikin sai ɓachama. Ko hanƙo kurar dabbobin basayi. Hankalinsu yayi mummunan tashi ganin gawar Lado, ga kuma tashin hankali da firgici rashin ganin su Gaini da Giɗi da Seyo Manunu da Sale. Junaidu ne yayi sauri ya kira mahaifinsu Ahaji Horo a waya ya sanar mishi halin da ake ciki.

Wannan mummunan labari yayi matukar firgita al'ummar Rugar Bani hankalin kowa ya tashi.

Hankali Bappa kuwa in yayi dubu to ya tashi, kuka cur-cur yakeyi da idanunshi.

Junainah kam kuka da ihu harda burbuwa takeyi tana cewa. "Wayyo Ya Lado, Bappa ku nemo min Ya Gaini na da ya Seyo". Sai ta kuma faɗa jikin Ummey daketa kuka tamkar ranta zai fita, cikin kukan take cewa. "Ummey kicewa Bappa suje su nemo min Ya Giɗi na, kada su bari a kasheshi kamar yadda aka kashe Ya Hashimu da Ya Isa, da kuma Yaya Lado". Babu mai iya bata amsa a cikin wannan gida. Duk da tarin maƙota da suka cika gidan. suna zagaye da Inna wacce, take sume tunda taji yaranta Rai uku babusu babu dalilinsu su ko gawarsu ba'a ganiba ga kuma mutuwar Lado wanda shine yasata, sumewa. Faɗin tashin hankali da mutanen Rugar Kikan ke ciki bazai taɓa misaltuwa ba. Saidai ƙunane wanda duk mai imani zai iya ƙiyastashi a ranshi.

A cikin garin kuwa tuni Arɗo Yabani yasa anyi shela anyi taron gaggawa, kowa ya shirya za'a shiga daji neman su Gaini, ko Allah zaisa a samosu.

Haka matasa kusufa-kusufa suka rinƙa kusa kai cikin daji suna ratsa tsaununka da kozozzabai.

Bappa kuwa da Arɗo Yabani da Ahaji Haro, da Ahaji Umaru ne da sauran dattawan rugarsu dana kewaye, gawar Lado suka ɗauko suka dawo gida da ita da sauran shanayensu gaba ɗaya matasa kuma suka bazama nemansu Gaini.

Su kuwa sauran matasa majiya karfi daji suka rinƙa ratsawa. Amman babu koda kurar dabbobin nan, bare alamun su Gaini illa iyaka dai takalmansu da suka tsinto.

A Rugar Bani kuwa, hankali na matukar tashe, Bappa ya tasa gawar Lado a gaba wacce sunyi mata wonka sun kimtsata cikin sutura kamar yadda shariya ta tanadar. Kuka mai tsananin cin raine ya kwabcewa Bappa, yana ruggume da gawar. Inna ma da yanzu ta farfaɗo da kukan ta farfaɗo, kuka takeyi tamkar ranta zai bar gangan jikinta. Hakama sauran matan maƙota. Hiden da Binto ma kuka sukeyi sosai a gidajensu sabida ɓacewar samarin su.

Dattawan ne sukayi ta bawa Bappa haƙuri da tausan zuciyarshi. Ganin dare yayine yasa akace dole a bar gawar tayi kwanan keso.

Su Sule, Iro, Ado, Junaidu, Madu, Ari, Sani, Ibi, ja'eh, Ori, Binbi, dama sauran samari majiya karfi kuma kab sun cikin daji.

Haka suka kwana a can. Suna tafiya suna nema, kafin gari ya waye, wasu sun isa har jihar taraba, wasu Gombe, wasu har bauchi, wasu har cikin iware da mutun biyu na taraba, Wasu sun nausa da nisa, sabida in dai tafiyace bata taɓa bawa bafulatani tsoroba domin anyi ittifaƙin duk ƙabilun duniya babu ƙabilar da takai ƙabilar fulani saurin tafiya da jumurin doguwar tafiyar ƙafaba, bayan laraban da.

Washe gari Litinin. ɗin, sauran dattawan garin suka sallaci Ya Lado, kana suka zauna amsar gaisuwa. Suna kuma jin labarin inda yaransuke. Ganin sunata wahalar tafiya ba lbrine yasa. Bappa yace su dowo. Domin wanna abu addu'ace mgninshi. Sannan kuma wannan karon bazasu saurari masarautar Numan ba , gangami zasuyi su kai kukansu, ga masarautar Joɗa, wanda a cikinta ne GARKUWAN FULANIN ƙasar Nigeria gaba ɗaya yake. Da fari Arɗo Yabani bai gamsu da hakanba saida Bappa yayi mishi bayanin. Dolefa suna da buƙatar hukama mai tsarki ta shiga tsakaninsu da ƙabilun Ɓachamawa nan, kana dole mgnar ta isa ga babbar masarautarsu, wacce za'a miƙa mgnar ga Ƙungiyar *TABITAL POOLAKU, DA KUMA ƘUNGIYAR.* *MIYETTI ALLAHA* Wannan dalilin ne yasa Ardo Yabani ya umarci gaba ɗaya matasan da suka bazama neman su Gaini su juyo su dawo gida. Haka kuwa akayi kafin yamma sai gasu duk sun daddawo domin. Wasu da yawa motoci suka shigo.

Bayan sallan ishane suka zauna zaman mitin domin sun gama shirya komai gobe dai kai tsaye masarautar Joɗa zasu wuce.

Bayan sun gama tattauna yadda abun yake suka tsaida zance kan cewa dattawansune zasuje. Daga nan Duk suka tashi taron kowa ya koma gidanshi da tarin al'hini a zuƙatansu.

A can cikin birnin Ɓadamaya kuwa cikin makarantar su Aysha.

Zaune take bisa salla hannunta riƙe da carbi tana ja. Kana hannunta ɗaya kuma rike da wayarta, wacce taketa kiran yayunta kab baya shiga tun jiya da yamma. Cikin kula Rafi'a ta kalleta a hankali tace. "Aysha ba komaifa, kinsan garin naku kunada matsalar Network, wasu lokutan kuma kinsan basu da cajine". Kanta ta jingina da jikin gini, murya can ƙasa tace. "Gaba ɗaya fa, woyoyinsu basa, shiga, na maƙotanmu kuma ko sun shiga basa ɗagawa, Rafi'a hankalina ya tashi." Da sauri Rafi'a tace. "No kada ki damu tunda kikaga basa ɗagawa alamun kenan woyoyinsu na wurin cajine ko?". Idonta ta lumshe tare da cewa. "Zuciyata na yawan sinkewa Rafi'a, fargaba nakeji". Cikin sanyi Rafi'a tace. "Yauwa to ki kira Ba'ana mana". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Eh hakane fa". Ta karishe mgnar tana dannawa wayarshi kira. Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga, Da sauri tace mishi. "Ina wuni ya Ba'ana". Ba'ana dake zaune tsakiyar ƙabilun Ɓachamawa suna mitin yadda zasu farma garin Rugar Bani da yaƙin sunƙuru gobe, murmushi yayi cikin sonta yace. "Lfy lau Mata, ya karatu?". Alhamdulillah tace tare da cewa. "Ya Ba'ana ya garinmu ya lbrin gidanmu duk suna lfy?". Murmushi yayi tare da cewa. "Duk suna lfy garinmu duk anata kewarki ɗazuma na wuce ya Ladonkin a kwance yanata shan baccinsa babu ruwanshi da damuwar duniya". sam bata kawo komai a rantaba kan mgnarshi ta ƙarshe, saima sanyi da ta ɗanji daya bata tabbacin, suna lfy, sabida iya tsawon zamanta da Ba'ana bai taɓa yi mata ƙaryaba, koda zaiyiwa duk mutanen duniya ƙarya to ita baya mata ƙarya, kuma duk zafin gskyar mugun abunda yakeyi zai gaya mata. Abu biyu ya ɓoye mata a rayuwarshi sata da kisan da yakeyi, sai dai yana gaya mata in dai a kantane zai iya kashe kowa ma. So cikin sanyi tace. "To yasu Ya Gaini kuma". Murmushin mugunta yayi tare da cewa. "Shima na wuceshi wurin Binto sunata hirarsu har tanata raira masa waƙoƙin soyayya". Murmushi ta ɗanyi tare da cewa. "To ka gaida min su bari in ɗanyi wonka". Murmushi yayi tare da cewa. "To Mata kiyi wonkanki anjima zan kiraki muyi hira". To tace mishi kana ta katse kira, tare da cewa Rafi'a. "Alhamdulillah duk lfyarsu lau ashe". Itama Rafi'a murmushi tayi kana sukaci gaba da hirarsu sai dai still fa tsoro da fargaba da bugawar da zuciyar Aysha keyi bai bariba, ganin hakane yasa Rafi'a, kallonta kasancewar Rafi'a ƙwararriyar mai koyar da girgirkene, a zahiri cikin makarantar tasu, da kuma social media. Cikin kula da son samawa aminiyar tata nitsuwa tace. "Yauwa GARKUWA, zomu shiga kitchin, muyi ɗan alalan kwai, naga kin kawo mana koyaye da yawa." Murmushi Aysha tayi wace, akefi kiranta da ƙarshen sunanta. hannun ta miƙa Rafi'a, cikin sanyi tace. "Help me my friend, jikina yayi sanyi da yawa, ji nake kamar bazan iya tashiba". haka nan itama Rafi'a jikinta ya fara sanyi, sai dai sanin in ta baiyana kasalarta tashin hankali Aysha zaifi tsananta ne yasa ta dake, cikin sauri ta kamo hannunta ta jata-ta miƙa kana suka shiga kitchin ɗin. Nan suka fara aikin sunayi tana ɗan janta da hira. a haka dai har suka gama, kana, ta shiga wonka.

Shi kuwa Ba'ana maida woyarshi yayi cikin al'jihunsa, kana ya kalli Sarkin mayaƙan ƙabilar ɓachama da yake ce mishi. "Shege Ba'ana wato, yana bacci cikin kabarinsa babu ruwansa da damuwar duniya". Dariyar mugunta sukayi dukansu, wanda yake gefenshi ne ya kece da wata dariyar tare da cewa. "Wai ita kuma Binto kukan natane waƙen SOYAYYA ko?". Kanshi ya gyaɗa musu cikin muguwar fuskarshi. Wannan matashin ɗaya fara sokawa Ya Lado wuƙane lokacin da suka kasheshi. yace. "Ita kuma da yake sokuwace har ta yarda k...".

Wani irin tashi sukayi gaba ɗayansu sabida wani irin shaƙa da naushi da Ba'ana ya kai mishi, wanda a take ya fara kakarin mutuwa. cikin zafin rai ya hankaɗa tarin mutanen dake son cotan yaron daya shaƙe ɗin amman ina sun kasa, wata zabgegiyar wuƙa ya lumtsumamishi a ciki wanda yasa sauran duk suka watse tura gawarshi yayi gaban su cikin ɗaga murya yace. "Ina kashe wanda ya yabi Shatuma yace yana son Shatuma bare wanda ya zageta, duk wanda baya son ransa ya aibata min Shatu a gabana ya gani". Cit kake jinsu sabida masifar tsoronshi sukeji. Dan ya fisu taƙadiranci dan Ba'ana mugun babarbarene mai baƙar zuciya.

Haka dai aka tashi wannan taron da yake dama sun gama tattauna yadda zasuyi farmakin.

Washe gari ranar wata Tuesday 21 November 2017 itace ranar da har abada al'ummar Rugar Bani bazasu mance da itaba a tarihin rayuwarsu, itace ranar da duk motsin da numfarfashi Shatu zatayi sai ta tunashi ranace data girgiza, zukatan al'ummar musulmai, ranace da tasa duk wani bafulatani makiyayi jin ƙuna da tafasar zuciya. Ranace da tada hankalin al'ummar ƙasarmu nan dama maƙotanmu.

Tunda safiyar ranar, dattawan garin suka gama shirinsu cikin shigarsu ta al'farma, Malam Liman (Bappa) Arɗo bani Jauronsu, Ahaji Horo da Ahaji Umaru, kana Malam Yero, da kuma Alhaji Sa'idu. su rai takwas dai suka shirya cikin kamala da mutunci. Junaidu ne yake cikin Shikan ya samo musu mota kirar siyana wacce suka ɗauki shatarta, domin zai kaisu har cikin fadar masarautar Joɗa kuma zai jirasu. Su dawo tare.

Nan suka shiga Mota gaba ɗayansu, suka tafi.

Kai tsaye har bakin masarautar suka tsaya dan an hanasu shiga, sai da ɗaya daga cikin hadiman dake tsaron ƙofar, yaga duk manyan daddatawa ne yasa yaje ya samesu bayan sun gaisane sukayi mishi bayanin abinda ke tafe dasu. Jin abin babbane yasa yaje yayiwa sarkin ƙofa bayanin. Nan shima yaje suka gaisa suka ƙara jaddada mishi, zancen abinda ke tafe dasu, sannan sukayi musu izini suka shigo cikin asalin farfajiyar mashigar masarautar. Kan kujerun dake jere a wurin suka nuna musu su zauna. Bayan sun zaunane sarkin kofa yaje, wurin sarkin fada ya sanar mishi, to nan sarkin fada ke cewa. "To ai babu abinda zamu iya musu, tunda shi GARKUWAN FULANI, baya ƙasar waye zai saurari kukansu, suje sai ya dawo su sake zuwa". Cikin rauni sarkin ƙofa yace. "Ranka ya daɗe sarkin fada, da dai an nema musu izinin ganin mai martaba, domin bazaiji daɗi ba in yaji sunzo kuma an medasu". Cikin isa da izaya sarkin fada yace. "A kul sarkin ƙofa ka tsaya iya matsayinka, kaje kace suyi maza su bar nan domin GARKUWANSU baya nan". Cikin sanyi da mutuwar jiki sarkin ƙofa ya juya ya fita, koda yaje ya sanar musu, abinda sarkin fada ya faɗa hankalinsu yayi masifar tashi. Cikin tashin hankali Arɗo Yabani yace. "Shikenan danmu fulanine makiyaya mazauna daji, sai ya zama matsalarmu ba abar dubawa bace, wa al'ummar birane, duk inda muka kai kukanmu sai a koramu". Cikin sanyi sarkin ƙofa yace. "Kuyi haƙuri ba korarku akayiba, in sha Allah za'abi kadunku, wlh shi kanshi mai martaba in zaiji abinda sarkin fada yayi to zai barranta dashi, kuma haka nan shima GARKUWAN FULANI in da zaiji abinda sarkin fada yayi wallahi zai haɗu da fushinsa mai tsauri, domin shi zuciyar Sheykh zuciyace mai cike da imani da tausayi". Cikin rauni Alhaji Haron yace. "Ana binmu ana kashemu, ana sace yaranmu ana kora dabbobinmu. Munje Police station an koramu, da mukaƙi tafiya suka watsa mata tiyagas, muje masarautar Numan akaci mana zarafi, sannan yanzu mun gudo gareku da yaƙinin zakubi kadunmu sannan kuma zaku koramu, so kuke mu ɗauki makami domin ramuwa ne?". Da sauri suka juyo gaba ɗayansu jin muryar Jamil da yanzu ya iso wurin da hadimanshi, cikin sanyi yace. "A a Baba kada ku ɗauki makami domin ramuwa zuwanku nan shine babban abinda ya dace". Cikin jin daɗi suke kallonsa, murmushi sarkin ƙofa da sauran hadiman sukayi dan sun san yanzu dai sarkin fada bai isa ya hanasu ganin Maimartaba. Domin yanzu bai fito fada bama tukun so zasu ganshi a kebantaccen wuri na musamman. Cikin kulawa da sakin fuska Jamil yace. "Baba ku biyoni". Cikin jin daɗi sukace mishi to, kana suka bishi a baya. Ta gaban shashin Sarkin fada suka shiga, kai tsaye har cikin fada ya shiga dasu, shida kanshi yasa hadimai suka kawo musu ruwa. Sannan a nitse yace. "Baba ku zauna a nan zanje in sanarwa mai martaba, duk sanda ya fito daku zai fara, tattaunawa In da masu buƙatan zagawa gacan wancan kusurwar in kumbi cikinta zata sadaku da bayi". Cikin jin daɗi sukace. "Mun gode yaro Allah yayi maka al'barka". Amin Amin yace kana ya sallamesu ya fita. su kuma sukaci gaba da zaman jiran fitowan sarki.

A can kasa mai tsarki kuma, Sheykh ne zaune a gaban Sitti, kana Haroon da Jannart na gefenshi Sheykh Aliyu Abdulkareem, kuma da Sheykh Jabeer Aliyu da wasu manyan malamai na zuriyar tasu duk suna zaune a cikin falon. Jazrah kuma na gabanshi da wani tray mai masifar kyau da tsada. Madara da zuma take zuba mishi a cikin wasu ƴan kananun kofuna masu masifar kyau da ɗaukan hankali.

Wannan ya kasance al'adarsuce ta baiyana nuna yarda da soyayya ko akasinshi, indan ana son a haɗa yara aure, to za'a tattauna tsakanin manya, bayan sun gama dai-dai-ta magana tsakaninsu kamar yadda yanzu su Mai alfarma Jalaluddin da Sarki Nuruddeen, da kuma su Sheykh Jabeer Aliyu da babban babansu Sheykh Aliyu Abdulkareem da kuma Sitti suka gama haɗa zancen auren Jazrah da Sheykh Jabeer, to yanzu ta zuba mishi madara da zuma a gaban kowa, ta ajiye mishi, idan ya ɗauki kofin madara to yana nufin yana sonta ya kuma amince da ita da aurenta. In kuma ya ɗauki kofin zuma, to yana nufin ya tsaneta baya kuma sonta bazai kuma auretaba bare ya zauna da ita. Za'ayi komai a gaban manya ne, don suga zahiri kuma a tsarin ko ɗan uwanka zai iya yi maka zaɓin da kuma in dai am zaɓa maka sai ka aura.

Shiru sukayi baki ɗayansu falon, kowa da tunanin da yakeyi.

Sheykh Jabeer dake zaune a tsakiyarsu cikin shiga ta al'farma sai sheƙi al'kyabbar sa keyi, ga tattausan hirami a kanshi, ido ya lumshe daya gane manufarsu. "Domin shi basu gaya mishi cewa, zasuyi wannan abun bane daya sani wallahi da yasan duk yadda zaiyi ya gudu, ya tafi harami, har sai sun gaji sun watse. A hankali ya kalli Sitti dake kallonshi cikin rauni da alamun. "Dan Allah kada kace, a a yar ɗan uwanane, kada ka bamu kunya nida kakanninka maza yar uwarkace kasan tarbiyarta". Kauda idonshi yayi daga kallon Sitti, wani irin kallo yayiwa Haroon daketa yi mishi, murmushin muguntan yau dai an titseka baka da hanyar tsira. Cikin ranshi yake mgnar zuciya. "Ta yaya zan amince ince zan aureta? Dame zan zauna da ita?". Sai kuma ya ɗan fidda nannauyan numfashi. "To idan ban amince da aurentaba me zamcewa, waɗanannan bayin Allah'n da sukayi min dukkan gatan duniya, na zauna a gidansu tsawon shekaru masu yawa nayi karatuna har na gama, sukemin komai na rayuwa, suna nuna min soyayyar da mahaifinama baya nuna min, da wanne idon zan kallesu inna ɗauki zuma alamar na tsani yarsu?". A hankali ya buɗe idonsa, jin muryar. Sheykh Aliyu Abdulkareem kakan Mamanshi kenan, baban kakarshi Sitti dottijon daya yake sonshi tamkar ranshi yana cewa. "Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa, kayi zaɓin da ranka keso, bamu da nufin yi maka dole, sai dai ina da burin aurar maka jikata Jazrah ɗiyar mai sunanka. Ina so da fatan ganin nasabarka ta cika, cikar nasabarka kuwa, shene aure." Wani irin sassanyan numfashi ya shaƙa a hankali, wasu irin zafafan tunanuka ne ke zirya a zuciyarshi". Cikin harshen hausar katsinawa, Haroon yayi mgna can ƙasa yadda ko Sitti bazata jisuba. "Sheykh kafa, shanyamu, nifa zan ɗaukar maka Madara". Ido ya lumshe tare da ɗan jingina da jikin kujerar da yake zaune, wanda yake kusa da Sheykh Abdulkareem. Sitti ce ta ɗan kalli Haroon tare da mishi alamun ya taɓo Sheykh. cikin harshen larabci Haroon ya kalli kakar tasu, tare da cewa. "Sitti ai nasan zaɓinsa, bari ki gani in nuna miki". Ya ƙarishe mgnar yana kai hannunshi kan kofunan. da sauri Sheykh Jabeer ya buɗe kekkyawar ƙwayar idanunshi da wasu ke kiransu da zaiba, wato kamar idon mage, idon ya ɗan zaro ganin Haroon yasa hannunshi kan kofin M...!

😂😂😂😂😂

Masu cewa na kulle musu kai kada ku damu zan kuce kawunanne, lokaci ne😂🙏🏻🤝🏻

By *GARKUWAR FULANI*

📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘

*GARKUWA*

PAGE 12

NA *AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘

Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku ta wannan number 09097853276. KO kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz domin samun shiga Special Group, wanda cikin kwanaki ƙalilan za'a gama littafin da izinin ubangiji. Ga asusun kamar haka 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, 1k ne SPG sai ki turo min shaidar biyan ki ta wannan number 09097853276.

Gareku iyayen ƴan mata da za'a aurar, akwai sittin amare mai kyau na gyaran jiki, bisa farashi mai sauƙin, akwai na manyan robobi akwai na ƙananan robobi, akwai haɗin masu jego, da na maida tsohuwa yarinya, sayan na gari meda kuɗi gida, in kayan gyaran kikeso ki fara min text message ta inbox ta wannan number 09097853276 sai ki gaya min kaya kikeso, kana sai ki kirani to nan zan ɗaga kirankin sai muyi mgn zaki turo kuɗi ta ACCOUNT number ni kuma zan tura miki kaya ta mota, duk garin da kike a Nigeria ina aikawa, in dai ba lungu yayi sosaiba. Kana mutanenmu mazauna ƙasashen ƙetare kamarsu Saudia, India, Gabon, Ghana, Niger, Cameroon, da dai sauransu in kinada dalili kayana na zuwa can cikin salama. Ina saida kaɗan-kaɗan ina kuma bada sari.

A dai-dai kan kofin madarar ya sa hannunsa, alamum zai mishi zaɓi kenan, murmushi yayi dan ya samu damar, da zai tserewa tsarinsu. Cikin ihima da sanin makaman kariyar kai daga jin kunya ko yin abinda zai ɓata ran wani, ƙafarshi ta dama dake kusa da hannun Haroon yasa cikin hikima ya bugi hannun Haroon da ke gab da ɗaukar kofin. ture hannun yayi da babbar yatsarsa, wanda, hakan yasa hannun Haroon ya bugi kofunan da ɗan karfi, sai gashi duk sun tuntsure a tsakiyar tiren madarar da zumar kab suka malale cikin tray ɗin. A tare suka zubawa tray idanu gaba ɗayansu. Sitti kuwa wani irin kallo tabi Madarar dashi. Shi kuwa Sheykh Jabeer, cikin iya taku da kamalarsa murya a mutunce ya kalli Haroon daya kafeshi da idon tuhuma, cikin harshen larabci da kamala yace. "Harooon meyasa baka da nitsuwa?". Cikin tarin mamaki Haroon ya gwalo ido tare da cewa. "Haaahh". sai kuma ya kalli Sitti da ta kwaɓe fuska tamkar zata kurma ihun takaici. Shi kuwa Sheykh Jazrah ya zubawa ido, ganin yadda ta zuba mishi kekkyawan idanunta, wanda suke sheƙin hawayen dake nuni da zazzafan son da takeyi mishi. Kauda kwayar idanunshi yayi, da sauri. Jannart kuwa hannun Sitti ta kamo ganin zata jawo tray. A hankali Sheykh Khalillullah wanda yake ƙanin Sitti ya gyara zama cikin sakin fuska da murmushi ya kalli jikan nasu, nitse yace. "Laaba'as". Dib-dib haka ƙirjin Sheykh Jabeer Habeebullah ya fara bada sauti, fahimtar kakanun nashi zasu ɗaura zabin kan, fahimtar lafazin Haroon. Shi kuwa Haroon, wani irin murmushi jin daɗi yayi. Shi kuwa dottijon nan, ido ya zubawa ƴaƴanshi da jikokin ƴaƴan nashi, da wasu jikokinshi. Kallonsu yake yana nazartansu.

A hankali wayar Sheykh Jabeer ta fara bada wani sauti mai masifar sanyi da daɗin sauraro, sautin gwauraye yake da kukan sassanyan tsuntsaye. da sauri ya zaro wayar a al'jihun tattausan al'kyabbar tasa. Ganin sunan Maimartaba Nuruddeen ne, ya sashi sakin wata sassanyan ajiyan, cikin ladab ya kalli Sitti, kana a hankali ya kalli Sheykh Abdulkareem, cikin sanyi da nitsuwa yace. "Mai martaba Nuruddee ke kirana, bisa alamu da babbar mgna domin baya kirana haka banza". Murmushi dottijon yayi, domin ya fahimci hanyar fecewa, Sheykh yake nema, hakan yasa ya mishi izinin tafiya. Cikin sauri Sitti ta yunƙuro da niyar yin mgna, sai kuma tayi shiru, sabida nuni da tayi shirun da mahaifinta yayi mata. Shi kuwa Sheykh Jabeer, a hankali ya yunƙara, ya miƙe ya nufi hanyar fita bayan yayi musu, su huta gajiya.

Kai tsaye Side ɗinsu ya wuce. Yana shiga kai tsaye bedroom ya wuce, gyara al'kyabbar jikinshi yayi kana, ya zauna bisa wata tattausar doguwar kujera.

A nan ƙasar kuma, cikin faɗar masarautar maiartaba Sarki Nuruddeen.

Bayan Jamil ya fita, wurin da yayiwa su Bappa Masauki, kai tsaye, sashin kakanin nashi ya nufa. Bayan an mishi isone, ya shiga, ya gaisa da kakan nashi kana ya ƙara da cewa. "Mai martaba, akwai baƙi ma buƙatar kulawarka, suna tsumayinka". Murmushi mai cike da kamala farin dottijon bafulatanin yayi, cikin ratsin sarauta yace. "Yau ka zama, sarkin fada kenan, kaine mai yiwa baƙi iso ko?, ko dai matane baƙin dan nasan ta nan kafi ƙarfi". Ya ƙarishe mgnar da yanayin tuhuma.

Kanshi ya ɗan shafa, kana a hankali ya girgiza kansa tare da cewa. "A,a mazane dattawan Fulanin dajine,". Ido ya ɗan zuba mishi kana yace. "Kaje kace a kula dasu, gani nan zuwa yanzu". Kanshi ya ɗan rusunar tare da cewa. "Nasa an basu dukkan kulawar da zasu, buƙata, zuwa yanzu sunfi buƙatar ganinka fiye da komai". Kai ya ɗan jinjina alamar to. Yunƙurawa yayi tare da cewa. "A fito lfy".

"Allah yasa".

"Amin Amin". Yace kana ya fita.

Shi kuwa Sarkin ya fara shirin, fitowa fada.

A can sashin Sheykh Jalal ne, zaune da Ya Jafar, Aunty Juwairiyya na gefenshi. karatu yakeyi kamar koda yaushe, tun jiya yaƙi barin sashin Sheykh, koda aka kira Sheykh Jabeer video call, ya ganshi sai yayi ta kuka. Wannan abun shiya ƙara tada hankali Sheykh Jabeer.

Yana yawan, bin Jalal, wanda mutane ke zaton ko dan tsananin kamannin da Jalaluddin keyi da Sheykh Jabeer ɗinne yasa, yake ganin kamar shine, to sai dai sam Jalal baya iya mu'amalantar Babban yayan nasu, kamar yadda Sheykh keyi har yake sama mishi nitsuwa, sai dai shima yana iya yinshi.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull