Kenza eBookz

Gurbin ido huguma complete - Chapter 37

Gurbin ido huguma complete - Chapter 37

Gurbin ido huguma complete Chapter 37: Gurbin ido huguma complete Chapter 37. "A'ah,amma ita tayi maka auren" ya fada yana dariyar tsokana,sai akwai…

4,481 words

"A'ah,amma ita tayi maka auren" ya fada yana dariyar tsokana,sai akwai ja'afar din ya saki murmushi ba tare daya shirya ba yaja gajeran tsaki sannan a fili yace

"Rabbish rahli sadry,wa yassir ly amry" sai ya dauka correction fluid ya bude ya soma gyara inda yake da kuskure yana gyarawa,jabir na zaune suna tattaunawa akan kasuwancinsu.

Haka kawai ya samu kansa da yawo saman titi bayan an tashi daga office,jabir da ya dauko ya rakashi aka masa gyaran fuska ya dubeshi

"Ka yiwa Allah ka kaini gida,na gaji da wannan ragaitar,kada fa'eema ta dauka wani gun na wuce tayi fushi dani" harara ya waigo ya watsa masa,sai ya qarawa motar wuta

"Ni da kuka hada baki da anni kuka maida tawa makarantar kwana wato na mutu kenan?" Dariya sosai ya sake

"Wa ya isa ya daukar maka mata ya kaita can?,kai kakai kanka" shuru ya kasa na wasu mintuna sannan ya sauke ajiyar zuciya

"Abu daya zai hanani daukota yanzun,wannan aikin da nakeyi a kanta,amma da zarar ya kammala na daukota daga makarantar to ta fito kenan,ba ruwana da wata anni" dariya ya kuma yi,sai kuma ya katse yana cewa

"Niko kamar naji kace unaisa bata nan?,ina ta tafi?" Ajiyar zuciya ya sauke hade da wata zazzafar iska daga bakinsa,ba boye boye tsakaninsu da jabir,a nutse ya gaya masa komai.

Shuru jabir din yayi abun yana kadashi,magana ta Allah bazaiso ja'afar dinsa ya hada jini da unaisa ko ya riqeta amatsayin matar aure ba,shi kansa tun randa ya fara ganinta ya gane fuskarta,yayi shuru ne baice komai ba saboda baisan me Allah ya shirya ba,sannan kuma ma babu kyau mutumin da yayi tuba na gaskiya ka tona asirinsa,ashe da sauran rina a kaba.

Shawara ya bashi ta hankali,wadda ta kusan zuwa daya da abinda ja'afar din ya yanke,saidai shi yace ya sanar da abbi abinda ake ciki

"Ka qyaleta,idan baka iya kama barawo ba sai barawo ya kamaka,da kanta zata fadi me tayi da inda taje,idan tana taqamar gata sai gatan ya qwaceta" har suka isa gidan jabir din suna tattauna batun.

Babu yadda baiyi dashi ya shigo ciki suci abinci ba amma yace aah,ya kunna motarsa ya qara gaba,dama yasan mawuyacine ya shigo din.

Samun kansa yayi da kasa komawa gidan,saboda yasan idan ya koma din ma bawai zama zai iyayi ba,gaba daya both gidajen guda biyu babu wanda yake masa dadi,yaja tsaki yafi a qirga a saman titi,kafin ya yanke ya tafi gidansu kawai ko zai rage tsahon dare a can.

Ganin lokacin sallar magrib ya kusa sai ya sanyashi zama saman motar abinsa ba tare daga shiga cikin gidan ba bayan ya faka motar a parking lot na gidan,ya fidda wayarsa ya soma dannawa,kusan babu wanda yasan ya shigo idan banda ma'aikatan gidan.

Bai rufa minti ashirin ba aka sake hon,mai gadin ya tashi ya sake budewa,sau daya ya daga kai ya kalli motar,sai ya maida kansa yaci gaba da danna wayarsa,motar hisham ce,ta gangaro gefansa tayi parking.

Sosai abbi dake zaune gefan hisham din yadan kafe ja'afar da ido wanda.baima san waye da waye a cikin motar ba

"Miskili kafi mahaukaci ban haushi" abbaya fada yana murmushi yana duban fuskar ja'afar din,kallonsa hisham yayi shima yana taya abbi murmushin,ya karanci kamar akwai damuwa akan fuskarsa,amma ba wanda zai iya buda baki ya gayawa,yasan bazai wuce case dinsa da anni ba,ko kuma unaisa da yau minister ya kirashi ya gaya masa cewa ya turo ta gida ba tare da sunsan meye ya faru ba,bude murfin motar abbi yayi yana cewa hisham ya biyo shi da jakarsa.

Yana ganin abbi din ya ajjiye wayarsa ya duro daga bayan motar ya tako inda yake cikin girmamawa yana masa sannu da zuwa

"Yauwa ja'afar,ya gida ya iyali?"

"Alhmdlh abbi" ya fada yana shafa kansa

"To masha Allah,bari na shiga ciki na fito sai mu wuce masallaci tare ko?"

"Okay abbi" ya amsa masa,zuwa sannan hisham ya qaraso,ya miqa masa hannu sukayi musabaha yana gaida yayan nashi,sannan suka rankaya ciki suka barshi a wajen.

Babu jimawa abbi ya fito da alwalarsa,tuni shima yayi tasa a bayan gidan suka wuce masallacin.

Bayan an idar a hanyar dawowarsu abbin yake tambayarsa

"Me yarinyar nan unaisa tayi maka manya?,abun kuma har yayi girman da zaka turata gida?" Abbin ya fada a tausashe,duk da tsauri da zafinsa amma yana sauqin kai da kuma saurin fahimtar al'amura

"Abbi,tafi kowa sanin abinda tayi,ita ya kamata ta gaya musu da bakinta" kai ya girgixa

"Yanzun ai ni nake tanbayarka bawai su ba,me tayi maka,ka gayamin ko mene ne,sai asan yadda zq'a gyara abun" kai ya girgiza

"Abbi.....banajin zai gyaru"

"Meye wanda bazai gyaru ba?" A nutse ya gaya masa dukka wani abu daya taba sani a baya akan unaisan,da kuma abinda ya farun yanzu da binciken da yayi da hujjojin da ya samu.

Sosai abbin ya kadu,don bai taba kawowa yarinyar haka ba,duk yadda suke takatsantsan wajen samawa 'ya'yansu maza da mata abokan rayuwa na gari,amma duk da hakan bai nunawa ja'afar din ba sai yace

"Ka barni da kaina zan sake bincike"

"To abbi" ya fada hankalinsa a kwance,tunda dai ya sani,koda abbin din zaiyi binciken zai binciko kwatankwacin abinda shi ya samu ne koma wanda ya fishi.

Zuciyarsa ce ta dinga raya masa ya yiwa abbi zancan maimunatu,sai kuma yaga bazai iya ba,don haka ya share batun,yasan dai akwai lokacin daya dibama koma meye anni ta shirya.

Sassan amma suka wuce shida abbin din gaba daya,saboda yace yunwa yakeji,yau da wuri zaici abincin darensa,baya wasa da girkin amman,saboda yadda ta qware sosai wajen sarrafa abinci,tarin masu aiki ko sarauta ko arziqin da take dashi baisa ta sako abincin mijinta ba hannun yara ko masu aiki,har yau har kwanan gobe ita keyi,saidai a tayata.

Amma na shirya musu abinci suna fira sama sama,bayan ta gama itama sai ta samu kanta da zama a cikinsu,abinda ba kasafai takeyinsa ba,duk da ita bacin abincin take ba,tana ta dai serving dinsu ne,daga baya saiga hisham ya shigo shima yayi joining dinsu, khadim ma sai gashi,da yake sau tari sai ya baro abincin ammi ya taho wajen amma ci,duk da itama ammin gwana ce,amma shi dan dakin amma ne.

Bai waiwayi sassan anni ba sai da ya dawo daga sallar isha'i ya kusa wucewa gida,tasan ya shigo gidan sarai,kuma batayi mamakin rashin shigowarsa ba,sanda ya shiga tana zaune a falo tana shan damammiyar fura data sha sugar,don annin ba daga nan ba wajen shan zaqi,kanta ta daga ta dubeshi sannan ta tabe baki ta maida kanta ga abinda takeyi,ya samu hannun kujera ya zauna yana gaidata,a yatsine ta amsa masa,yadan zubawa tv ido sannan ya miqe

"Wannan sugar din da kike yawan sha fa yana yawa,shekarunki sun ja" dama jiransa take,saboda haushin qin shigo matan da baiyi ba,saboda ta saba anan yake sauka ko yaushe bayan ya gama gaisawa da kowa

"Kai arcannnn.......kayi ta kanka malami,mu jikinmu ba irin naku bane, sugar abin banza ba abinda zaiyi mana,haka zamu mutu ras da lafiyarmu in sha Allah,damu da mazanmu ba irinku bane,wanda sai mace ta shekare a gidansu su kasa yi mata ciki sabodq tsabar raggwanta" dole ya dora idanunsa akan fuskar anni,tirqashi😂, abun yazo harda gori?,ya tabbatar dashi take,shi takema gorin baima maimunatu ciki ba,don yasan itace tata,da ita ta damu.

Murmushin gefan baki ya saki yana cusa hannuwansa a aljihun wandonsa,shima bari yayi mata ta 'yan zamani

"Me kike ci na baka na zuba anni?,ba tsallaken shekara daya bane?,to itama za'a ciketa,ki rubuta ki ajjiye biyu xa'a baki ko uku,nex year mu sake maimaitawa" daga haka ya juya yana ficewa daga falon,sai ta bishi da kallo,tana jin sanyi qasan ranta tare da cewa

"Ameen ya hayyu ya qayyumu,'yan ameen su amsa ya rahman" can qasan ranta,amma a fili sai tace

"Ahhh waima,zamu gani".

Yana mota yana tuna matter dinsu da anni,sai kawai ya samu kansa da sakin murmushi,tare da imagining diyoyi daga wajen maimunatu,wanne irin kyau zasuyi?.

Duk guje gujensa yau dinma sai da yasha baqar wahala kafin ya samu bacci ya daukeshi [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 76

A hankali ta rufe bangon littafin dake gabanta gami da sauke ajiyar zuciya,zuciyarta na wani irin karyewa da kuma samun rauni,a hankali ta zubawa wajen da afra suke zaune suna hira kallo,tun dazun suka ce mata ta bar karatun tazo tayi joining dinsu amma taqi,saboda bata da wani karsashi ko farincikin hirar,tunda ta dawo sati biyu cikin na uku zuciyarta a quntace take,ba wani walwala ko farinciki.

Wayarta ta zaro ta sake kallon fuskar wayar,cikin sarewa da gajiyawa ta dora wayar saman table din data aje littafin nata sannan ta zame ta kwantar da fuskarta saman table din,daga dawowarta zuwa yau batasan sau nawa ta duba fuskar wayarta ba,haka kawai taji tana tsimayin kira daga gareshi,saidai ko sau daya bai kirata din ba,tana ta sanya rai taji ance tazo gashi,duk da tasan ba bari ake azo ganin naka ba idan bada wani babban uzuri ko dalili ba,amma tata zuciyar nata shauqin jin hakan,saidai shuru,lumshe idanunta tayi tana jin yadda zuciyarta ke tabuwa,ba zata taba kiransa ko sau daya ba,sabida tayi alqawarin jan ajinta da mutuncinta,zata kuma cika burin anni in sha Allah

"Maimoon,lafiya?,me ya sameki?" Taji muryar afra saman kanta,sai ta bude idanunta da kyau a kan fuskar afran

"Me kike gani?"

"Kuka.....hawaye fa kike?" Bata yarda da zancan afra ba sai data sanya hannu ta shafi fuskar tata sannan taji danshinsu,abinda ya sake sanya zuciyarta karyewa,kawai sai ta saki kukanta sosai tana kifa kanta a table din.

Da sauri afrah taja kujera dab da ita ta zauna tana fadin

"Innalillahi,wai menene yake damunki maimoon?,meye matsalar?" Bata bata amsa ba,sai kawai tasa hannu ta zare wayarta dake gefe,tasan me zatayi mata.

Contact ta shiga ta fara laluben sunayen soyayya data sama wata contact,saidai babu ko daya a ciki data gani,haka ta haqura,ta sanya ainihin sunansa saiga number din ta fito,kallon maimunatu da batasan ma tanayi ba tayi taja qaramin tsaki,wai itakam yaushe zata bude zuciyarta ta yarda soyayya takeyi?,ta kuma gane ita ke wahalar da ita?,kawai saita canza sunan dake kan number zuwa honey bee,sannan kanta tsaye ta danna masa kira.

Dai dai lokacin yana kwance a wajen hutawa daya ware cikin office dinsa,tunda yazo yake zaune a wajen,ya gaza hassala komai,baisan me yake damunsa ba,gaba daya tunda ta tafi ta tafi da walwalarsa,hannunsa daya bisa fuskarsa,sai yaji shigowar kira wayarsa.

Har tayi ringing dinta ta katse bai dauka ba,ta sake shigowa ta kuma katsewa,ya shareta yana ci gaba da kwanciyarsa,har sai da yaji qishirwa,sannan ya miqe zaune ya jawo wayar yana son duba lokaci,don da wuri zai fita daga company din yau,saboda ya lura bazai iya aikata wani abun kirki ba.

Ganin miscall da number ta yasa ya tashi ya zauna sosai,bai zaci wayarsu na amfani ba a school,daga sama kuna tex ne

_ka kira pls yaa ja'afar,qawar maimoon ce_

Bai gama karantawa ba ya fita a saqon ya kira number din,yana jin yadda zuciyarsa ta tafi gaba daya ta kuma afu gason jin muryarta.

Da sauri afra ta duba kiran sannan ta dan matsa gefe kadan daga inda maimunatu ke zaune ta daga

"What's happening?" Ya tambaya kai tsaye,jin ba muryar maimunatun bace

"Kuka dai takeyi,na tambayeta taqi magana"

"Bata wayar" ya fada cikin jin wani tashin hankali yana shigarsa,meye ya sameta?,itace tambayar daya fara yiwa kansa.

"Yaa ja'afar ne" ta rada mata a hankali,kafin ta gama fuskantarta har ta nana mata wayar a kunne

"Angel" ya furta cikin wani irin taushi,da zuzzurfar muryarsa data aike mata da wasu saqonni lungu da saqo na jikinta karo daya,wani nauyi taji zuciyarta tayi,hawayenta kuma ya dauke cak,ta zuqi numfashi sosai tanason fesarwa amma kamar ya riqe

"Hello.....angel,my moon" ya sake fada very softly,wannan karon fidda numfashin tayi gaba daya,wanda ya zame mata kamar ajiyar zuciya mai sauti,batasan sanda tasa hannu ta dafe wayar sosai a kunnenta ba,har yanzu idanuwanta suna rufe tana sauraren saukar numfashin sa daga cikin wayar,da alama shima ta taba zuciyarsa sosai

"Say something mana angel,bazan iya jurewa ba,meye ya faru?"

"Zazzabi" ta fada muryarta a mugun narke,kuka mara sauti me dauke da hawaye yana kubce mata

"Ya salam......jirani gani nan zuwa" ya fada yana katse wayar gaba daya.

A gaggauce ya maida takalminsa ya kira PA yayi cigiyar key din motarsa,ya karba ya fice ba tare daya tsaya sauraren kowa ko kuma meeting dake gabansa awa daya mai zuwa ba.

Kasa motsawa tayi daga wajen,sai kunnuwanta suka shiga maimaito mata abinda yace

"Ta jirashi gashinan?,da gaske zuwan zaiyi??" Zuciyarta dai ta cika da wasi wasi,amma duk da haka sai tayi likimo taci gaba da kwanciya a wajen,har zuwa sanda ta tsinci muryar afra na kiranta irin kiran gaggawa,idanuwa kawai ta bude tana jiran isowarta

"Ana kiranki office din principal,yaa ja'afar ne yazo" batasan ta miqe da hanzari ba sai data ji kanta ya saara,ta dafe kanta da hannunta sannan ta dubi afra

"Muje ki rakani please" hannunta ta riqe tana murmushi,tanason tsokanarta amma kuma yanayinta yana nuna seriousness dinta kan condition din duk da take ciki,don haka shuru tayi tana taka mata zuwa office din.

A nutse tayi sallama a office din,idanuwanta na kallon qasa,don ta tabbatar indai idanunta a dage suke kuma yana cikin office din,tofa lallai idanunsa suna kanta ne,ita kuma a yanzun batajin zata iya dauke idanunsa akanta,bata jin zata iya jurema wannan kallon nasa,qamshinsa kawai ya isa ya bata tabbacin yana cikin office din,taci gaba da takawa a hankali,sai zuciyarta ta gaza jurema rashin kallon fuskarsa,ta yanke shawarar ko satar kallonsa ne tayi.

Ta kuwa aikata hakan,saidai kuma ya kamata,don caraf idanuwansu suka hadu waje daya,yana binta da wani irin mayen kallon da shi kadai yasan fassararsa,gaba daya yaga kamar an sake canza masa ita,ta sake kyau ta sake fresh,saidai tadan faada kadan

"Zaki bishi zakuje ku dawo" principal din ya fada kansa tsaye,tunda yasan waye ja'afar din a wajenta

"Okay sir" ta fada kanta a qasa,sannan ta miqe ta soma takawa a hankali tana ficewa a office din da zummar zuwa dakinsu ta gani idan akwai abinda zata dauko.

A hankali taji an riqo hannunta ta baya a tausashe tana hanyar komawa hostel,da sauri ta waiwayo,tadan razana saboda hanyace da babu masu wucewa sosai a kanta,sannan kuma batasan ana biye da ita ba.

Idanuwansu suka sarqe waje guda,kowanne ya jefi dan uwansa da wani abu mai matuqar tasiri a ruhi da gangar jiki,suka shiga jin kamar zasu narke a wajen saboda abinda ke zagaya zugata da gangar jikinsu,sukaci gaba kuma da kallon junansu kamar an manne idanuwan nasu cikin na juna ne,bata ankara ba ba zato taji ya fusgeta zuwa cikin jikinsa da wani irin zafi,har takalmin qafarta yana zamewa daga qafartata.

Sosai ya riqeta a jikinsa saidai kuma cikin taushi,baiyi wata wata ba ya kama fuskarta da kyau ya riqe gam,ya fara sauke mata kisses,tare da lashe labbanta da yayi matuqar missing dinsu kamar hauka.

Gaba daya ya kunce mata noti,jikinta ya dauki rawa,tanata qoqarin tureshi amma yafi qarfinta nesa ba kusa ba,sai da dabara tazo mata,ta kama labbansa ta ciza da dan qarfi,sannan ya saketa ya d'an ja da baya yana fadin

"Wash Allah na amma na" a wahalce kamar wanda aka yiwa duka aka galabaitar dashi.

Da rinannu idanuwansa yake kallonta,yayi da ita kuma dariya taso kubce mata jin kiran sunan amma da yayi kamar wani qaramin yaro,amma saita danne,ya rigata magantuwa

"Wannan fa mugunta ce,so kike ki.kasheni ko?,tunda kika shigo kinqi kallona,sannan kuma kin fito kin barni ni daya irin baki damu dani ba ko?,kuma yanzun ina welcoming naki saiki cijemin labba?" Ya fada yana taba leban nasa da zara zaran yatsunsa guda biyu.

Bakinta tadan rufe tana fidda fararen idanuwanta waje,wanda hakan ya qara fidda girmansu

"Bafa haka bane,ban wani cijeka sosai ba,nan din hanya ce,wani yana iya zuwa wucewa" sauke yatsun nasa yayi yana ci gaba da jifanta da mayataccen kallonsa,sai ya fara takowa yana fadi a hankali

"I don't care ni ko waye zai ganmu,ni ke kadai nake gani idanuwana da zuciyata gaba daya,kuma zakisan kin cijeni,you will pay" ya qarasa maganar yana riskarta gami da surarta gaba daya cikin hannuwansa.

Bugun zuciyarta ya qaru,tsoro ya cikata,kada a ganta fa mutuncinta ya zube,tunda ba kowa bane yasan alaqarsu ba,shi bayajin kunya ne

"Don Allah......don Allah,ja saukeni,akwai abinda zan dauko a daki"

"Bana buqatar komai,ke kadai nake buqata"

"To zan iya qarasa mota da kaina"

"Banaso shima,jikinki akwai dan dumi amma ba mai yawa ba" runtse idanunta kawai tayi sosai,ta buda suit dinsa ta saman ta cusa kanta a ciki tana jin tsoro da fargabar wanda zai iya ganinsu a haka,cikin taimakon Allah har suka kai bakin motar basu gamu da kowa ba,dama yammace,kuma hanyar bata jama'a bace.

"Sauka to madam karki hadiyeni,irin wannan riqon haka?" Ya fada yana duban fuskarta murmushi na qwacewa miskilar fuskarsa,wani zillo.tayi ta sauka jin fassarar da yayi mata,gefe guda kuma zuciyarta ta cika da mamakin dama.yana raha da tsokana irin haka?.

Da kansa ya bude mata motar ta shiga,ya tattara mata hijab dinta daya fito zuwa ciki ya rufe mata,sannan ya zagaya seat dinsa yana jin zuciyarsa wasai,duk wani nauyi da tayi ya nemeshi ya rasa cikin qanqanin lokaci,yayin da itama ta langabar da kanta a kafada tana kallonsa sanda yake zagayowa ta gaban motar zuwa seat dinsa

"Ya Allah,yashe ta fara sonsa har haka ne?" Saita lumshe idanunta itama sirritaccen murmushi yana kubce mata. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 78

Wata shirt ta zaqulo,tana da dan fadi daban,dama irinta take nema,sai ta zura,tayi amfani da turarensa ta feshi jikinta,sannan ta dauki hair drayer dinsa ta fara busar da gashinta da ya dan jiqe,ta gama fa shafeshi da mansa mai qamshi,sannan ta dauki band ya fara kiciniyar daurawa.

Duk tsaiwarsa a dakin sai lokacin ya qaraso,sai daya iso dab da bayanta sannan yayi sallama,ta fito da idanunta tana kallon fuskarsa data sauya,daga fuskar da babu rahamar fa'a zuwa fuskar data saba da murmushi ciki yan mintuna qalilan,ya soma takowa zuwa inda take tsayen.

"wa yace ki sakamin riga?" Ya fada cikin sigar tsokana,amma kuma yana dan bata rai,narai narai tayi da idanu tana langabe kai

"Banga kayan da zan saka ba" kai ya jinjina yana isowa dab da ita,ya sanya hannuwansa duka biyu ya nade rigar sama ya riqe qugunta yana kallon fuskarta,tafin hannuwansa saman lallausar fatar jikinta yana kallon tsakiyar idanuwanta

"Gaskiya bazan iya baki aro ba,nima ita zan saka" yayi maganar yana tafiya da hannayensa zuwa sama,inda yake ta tsole masa ido tare da jan hankalinsa,narai narai ta sakeyi da ido,a narke tace

"Please mana,aro kawai?" Kai ya girgiza

"Bazan iya ba"

"Don Allah"

"Ok,but let me feel your....." Sai maganar bakinsa ta.katse, numfashin sa ya fusga kadan,saboda tuni yakai.hannuwansa inda ya nufa,kafin tace komai ya tsugunna ta qasan rigar ya cusa kansa.

Fara qoqarin zamewa tayi amma inaa,ya saka dukka hannuwansa biyu ya riqeta sosai ta bayanta,cikin qanqanin lokaci ya fara birkita mata kwanya,saqonnin da yake aikema qwaqwalwartata sun girmama,ta fara tangal tangal zata fadi,sai ya zare kansa daga ciki yana dubanta da idanuwansa da suka sauya launi

"Please nima,ki sanmin dan kadan,i promise you wannan karon no more any pain.....i promise.....i promise angel" ya fada a dan rude saboda yadda hankalinsa yayi gaba.

Bata jin dadi idan taganshi a gabanta cikin kwantar da kai yana roqarta akan hakkinsa,a hankali ta gyada masa kai tana lumshe idanu,caraf taji ya sureta yana cewa

"Thank you angel moon, thank you" ya azata a tausashe saman gadon ya maye gurbin duvet yana sanyata tsakiyar qirjinsa gami da sake lullubeta da wata tattausar soyayya mai dimautarwa da kuma gigita hankali.

Kaman yadda yayi mata alqawarin kuwa babu wani sauran radadi data fuskanta,saima tarin kunya da ya barta da ita, saboda yayi ta koya mata abubuwa yana sanyata tana responding masa saqonninsa,abinda ya basu wani irin dare mai matuqar qayatarwa,daren daya sake.narkar da kowannensu,ya kuma sukurkutar masa da tunani,ya sake dasa musu so da qaunar juna mai tsanani.

Ko bayan komai ya kammala cikin jikinsa ya matseta tsam,idanunsa a rufe yake cewa

"Let's make this lovely journey last for a lifetime,do not ever let me go,am yours as long as you want me to" wani irin abu taji yana sulalewa yana kwaranya a kwanyarta,ta gyada masa kai a hankali ta lumshe idanu tana jinta a wata duniya ta daban,dama haka soyayya take?,sai ta tuna da wani korean drama data gani,kamar haka a lokacin ta dinga imagining kanta,amma sai zuciyarta ke gaya mata it can't,ashe zai yiwu,harma fiye da yadda take hasashe.

°°°°°°°°°°shi da ita dukkaninsu a shirye suke tsaf,ita cikin shirin komawa makaranta,shi kuma cikin shirin office,tsaye take shima haka,tana rungume tsakiyar qirjinsa suna musayar numfashin juna da kuma scents na turarukansu,kowannensu ji yake kamar bazai iya tafiya yabar dayan ba,cikin wata karyayyiyar murya yace

"Can we go?" Ta gyada masa kanta a hankali zuciyarta na karyewa kamar kuka zai subuce mata

"Okay angel.....but,inason naji kalma daya a bakinki,me yasa kikemin rowarta,baki taba gayamin ba" sai data daga kai ta kalleshi sannan ta tambayeshi

"I want you to say i love you ja'afar" murmushi tayi tana cusa kanta sosai cikin qirjinsa,kunya....kunya takeji wallahi,tun jiya ya gama sakwarkwatar da ita gaba daya

"Uhnnnn.... please,say it" ajiyar zuciya ta sauke,tana jin yadda zuciyarta keta azalzalarta kan ta fada din,cikin wata irin murya dake dauke da amo na daban ta fadi

"Ina sonka,ina qaunarka.....i love you"

"Da gaske daga zuciyarki ne?" Saita jinjina masa kai cike da qwarin gwiwa

"Ina nufin dukka abinda na fadi din,da gaske nake,daga zuciyata ne" zallar farinciki ya kamashi,sai kawai ya hadeta cikin jikinsa,ta sauke ajiyar zuciya tana jin dadin kasancewarta a qirjinsa,akwai wata nutsuwa mai tarin yawa tattare da gurin,har batasan tayi subutar bakin furtawa ba

"Hugging someone taller than you is the best feeling ever,bcoz you fell protected" wani murmushi mai dadi ne ya subuce masa,ya dagota yana duban fuskarta dake a kulle

"Really?" Kai tsaye ta gyada masa kai

"Zanci gaba da rungumarki har gaban abada,kuma.koda baki a jikina cikin qirjina kina zuciyata,and i will give you protection everywhere you go bakin rai bakin fama". Da qyar suka yakice juna ya dauketa sai makaranta.

Ko cikin mota sai data kusa missing first period sannan ya barta,ta wuce dakunansu ta saka uniform ta koma aji,shi kuma yaje yayi confirming maidota da yayi yayi singing.

Tun a aji suka dameta da iskanci su afra,saita sharesu saidai tana ta smiling,saboda ita kanta tasan jiyan tabar mata abubuwa masu yawa da bazata.mance dasu ba,su afra kuwa haka ta haqura da tsiyar da suketa mata har sukayi haquri sukayi shuru.

Tofa captain ja'afar da maimunatu sun fasa dadin abun,kwana daya rak yaji ya kasa sukuni,da qyar ya raka zuwa qarshen sati ran Friday ya sake zuwa ya nema alfarma ya daukota,tazo tayi masa weekend,idan yaso Sunday da yamma ko Monday da sassafe ya maidota.

Wani irin weekend mai bada kala sukayi, weekend din da tunda yazo duniya baijin akwai wanda ya fishi dadi a wajensa,ran litinin kuwa basu samu fita daga gidan ba sai azahar,da qyar ya taushi kansa,yana da tabbacin ya kusa gazawa,haqurinsa ya kusa qarewa,don haka ya sama kansa more effort ya gama aikin da xai sanya ya fake dashi ya raba maimunatu da makarantar gaba daya ta silarsa.

K'arfe shida da mintuna ya shiga gidansu kamar yadda yawancin lokuta yake zuwa a yanzun,amma sai ya wuce sassan ammansa,ya sameta a falonta a zaune,ita daya saboda yaran basu dawo a islamiyya ba,duk girmanki a gidan dr marwan baki wuce zuwa islamiyya ba,har su salma 'yan university da ake shirin aurarwa,kasancewarsa sanannen mai ilimin addini,yakance neman ilimi baya qarewa dan adam sai idan mutuwa yayi,akwai makaranta nan saman unguwarsu me special classes irin nasu.

Duqawa yayi nan gabanta ya gaidata,sannan ya zame ya zauna sosai yana jan fruit din dake gabanta hade da qaramar wuqa tana gyarawa,da alama zatayi fruit salad ne, murmushi ta bishi dashi,har yau baya ganin ya girma ko ya taka wani matsayin da zai hanashi kama mata aiki idan yazo ya taras tana yi.

"Manya,me yake faruwa tsakaninka da unaisa ne?" Ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke,duk duniya baya iya boyema mahaifiyarsa komai,don haka ya labarta mata komai a nutse.

Sosai hankalinta ya tashi,amma kuma bata nuna masa ba

"Haquri ake da sha'aninmu,tunda ai bata taba aikata hakan ba,sai ka bata uzuri" kai kawai ya gyadawa ammansa,amma bayajin zai taba iya riqe unaisa,bayason suci gaba da zama yana zaluntarta Allah ya kamashi kan hakan.

Bai tashi a kai ba sai da suka gama aikin duka tare sannan ya daura alwala ya fice sallar magariba.

Daya dawo wajen anni ya wuce,itama tana falo baba tabawa na gefanta suna kallon musabaqar duniya da ake haskowa a wata channel,wata 'yar nigeria ce ke karatun a yanzun,suna ta tattaunawa akai,saidai kowanne hannunsa riqe da carbi da alama basu jima da gama sallah ba. Baba tabawa ce ta miqe tana marabtarsa

"Barka da zuwa" ya amsa mata cikin girmamawa yana zama,sannan suka gaisa

"Ina uwar dakina?,tayi mana nisa"

"Suna makaranta"

"Uhmmm.... makaranta ko gantali daga wannan kwararo zuwa wancan?" Anni ta fada tana tabe baki,daga kai yayi ya kalleta,sai kawai murmushi ya subuce masa,shi qarfin halin anni dariya yake basa,batasan a yau idan yaso.maimunatu ta gama zuwa makaranta ba?,ya fita iya kwaso rigima sosai,amma tana da wani babban matsayi a rayuwarsa,sannan she deserved respect daga wajen kowannensu,don ta taka rawar gani a rayuwar duk wani ahali nata

"A daiyi haquri a sassauta"

"Yoni ai bazan dauki wannan iskantun ba,kowa ta kansa zaiyi ya shiga hankalinsa,bazan bari a haifamin jika tsakanin qarya da gaskiya ba"

"Kin samawa kanki sauqi" ya fada hankalinsa kwance yana relaxing cikin kujerun hadi da lumshe idanu,dariya taso qwacewa baba tabawa saita fice,yayin da annin ta watsa masa daquwa

"Kayi ta kanka ja'afaru ka kiyayeni fa?"

"Na kiyeyeki" ya fada ba tare daya bude idanunsa ba,don shi yanzunma weekend dinsu na baya yake tunowa yana sa masa nishadi,tare da shirya musu next weekend yadda zai wakana.

Kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai abbi ya shigo,cikin girmamawa ya miqe yana masa sannu da zuwa,bai zauna ba sai da abbin ya samu waje ya zauna nan kusa da tsohuwarshi

"Dama ina nemanka,naji dadi dana ganka" sai yayi bismillah yana zama

"Zauna" ya bashi umarni,ya aikata hakan yana tattara hankalinsa akan abbi din.

Maganganu ne duka kan unaisa,da yadda tace batasan wani abu daya faru ba,qarshe ma dai saita buge da fadin irin zaman da sukayi,shuru ne ya biyo baya,anni tana ta jeranta abubuwan cikin ranta,ita gaba daya yarinyar bata yi mata ba,sannan data sake kawo mata qara ta kuma kalli tsantsar idanunta tace mata ayi masa fada bata taba kwanan turaka ba saita qarasa sare mata a rai,babu kunya ko qanqani cikin lamarinta,sannan ita kanta ta sanya cikin jikokinta sun mata bincike,sakamakon ba mai dadi bane, saidai dan yau baka bashi qofa haka kai tsaye.

Shima abbi din kusan hakan take,amma bayaso lokaci guda ya bashi go ahead na aikata wani abu,saboda gudun halin dan yau,don haka yace dashi

"Ka samu lokaci kaje ku fahimci juna ka dawo da ita dakinta"

"Zan samu lokaci" yace da abbin kawai,yanayin fuskarsu kawai ya nuna suma akwai abinda suke dannewa. [11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram: 77

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull