Hayateem book 1 And 2 complete by mamuhgee - Chapter 18
Hayateem book 1 And 2 complete by mamuhgee Chapter 18: Hayateem book 1 And 2 complete by mamuhgee Chapter 18. 42 *_MAMAN YUSUF LIKITAR MATA_* 07069711327…
4,480 words
42 *_MAMAN YUSUF LIKITAR MATA_* 07069711327 GYARA SHINE MACE *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327
*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻
-Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata -Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi, -Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji, -Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki, -Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ba, -Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki, -Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso,
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻
Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi
Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi
Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra
Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers 07069711327 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata.
************ Tenya da idanuwanta sukai jajir hannuwanta na rawa ahankali dago jajayen Idon tayi ta saukesu Akan fuskar Ayanah dake rintse da ido kanta cikin kafafunta tana Wani irin kuka mai tada tsikar jiki sbd rasuwan Nurat data dawo mata sabuwa da rashin Abaas harma da rabuwa da Zuhrah da irin rayuwar da sukai ta qangin bauta a hannun wainda bazata taba mantawa ba kusrawa.
Ita kanta sakinah data bada labarin kuka takeyi sosai komai ya dawo musu ‘danye da harma suke Jin sun yadda mutuwar suke so su huta kawai,
Tenya duk yanda taso riqe kanta saida zuciyarta ta kasa tayiwa Nurat kukan daya sakata Miqewa tana juya musu baya tana yinsa sosai sbd yanda komai da akai mata ya ringa ratsa kunnuwansu tin farko har gamawa da yanda Abaas ya koma macen da duk wannan tsawon lokacin bai taba bude Baki ba ya bayyanarda azaba ko baqin cikinsa ba yan uwansa su kaji muryansa ba har suka rabu rabuwarda shikenan har abada.
Tsit dakin yayi dukkaninsu sunyi kukan da har karfinsu ya qare musamman Ayanah da daman karfinta ya tafi gurin naquda da haihu.
Sakinah ma karfinta ya qare babu me kuzari a cikinsu hukuncin tenya kawai sakinah ke jira Banda Ayanah da kamar ma bata hayyacinta dan kuwa zuru tayi bata iya ko dagowa da babynta a jikinta da kila rabuwa zatai dashi take ji kaman yanda ta rabu da kowa nata.
Tenya Ayanah ta zubawa ido zuciyarta gabaki daya ta karye akanta, Acan baya tana tsaye a kanta da duk lamarinta ne sbd cikar burinta na wargaza duk abinda HAILE zata so a rayuwa amma ayanzu Jin tsananin kauna da tausayi tareda sonta takeyi yana ratsa jini da zuciyarta a tsaftace babu sirki babu wani Buri,
Shi NUAB tinda ya fado duniya a hannunta ya fado take kaunarsa mara sirkin komai ta shigeta da zata iya komai akansa amma ayanzu dataji waye mahaifiyarsa sabuwar kaunarsu ce mai karfi da zata iya bada ranta akansu ta shigeta dan haka take daukanwa kanta alaqawarin tsayawa a kansu da lafiya da rayuwarta har inda tata rayuwar zata qare,
Cuta da hadari kowane iri ne indai zata gansa ko jisa zata basu kariya kota halin yaya dan haka a yanzu da gaske qiyyyar HAILE take ji a jininta da batajin zata iya barin kowace burinta Akan Ayanah ya cika dan shi LEUL jinin BOYEM ne kuma magajin kujeran BOYEM duk Wanda yayi gangancin tabasa tamkar miqa rayuwarka ne kayi ga zakunan da zasu ci namanka da ranka a gangan,tinda Yazo a jinin sultan YASAR ai yagama samun kariya duk duniyar da zaa bawa kowane irin me rai dayake BOYEM bazai iya cutatar dashi ba dan haka mahaifiyarsa ce a hadari da buqatan me tsaya mata a kowane irin yanayin da zata samu kanta.
Cikin yanayin daya saka su dukansu biyun dagowa suka kalleta ta kafe idanuwanta Akan Ayanah da sauti me cire tsoron hadarin da zasu iya shiga su dukan tace
‘Kinada alfarmar fiddo Zuhrah daga kurkuku amma bakida damar ‘yanta ta sbd hakan zai iya zamowa hadari fiddota da yantata, Kinada matsayin wishmah dazai Baki cikakkiyar daman da zaa cika miki Buri uku na rayuwarki, A ranar da zaayi bikin sunan NUAB a ranar zaa yi taron Baki cikakken matsayinki na wishmah a kuma ranar ne zaa Baki damar fadar Buri uku da kike dasu Wanda Kina fadar su Sai an cika miki su,
Bazan fada miki abinda zaki fada ba sbd bansan burin da kike dashi ba a rai amma dai zan fada miki Abu daya idan har kinason zuhrah ta rayu rayuwa me kyau wadda ko bakwa tare zata samu rayuwar nutsuwa da kwanciyan hankali Wanda hakan shine burinki to kada ko fiddata daga kurkuku kuma ki yantata a lokaci daya dan kuwa kika yin hakan Zaki iya rasata gabaki daya dan sedai ki tashi Washe gari ki ga gawarta kwance a gabanki,
Na miki alkawarin Zuhrah zata samu rayuwa me kyau da gata tareda kwanciyan hankali amma idan zaku iya sadaukar rabuwa da rayuwa batareda juna ba har abada…..
Wasu hawaye ne masu dumin gaske suka gangaro daga idanuwan Ayanah tana kasa dauke kallanta daga tenya cikeda Wani irin yanayin dayake sassara rayuwarta zuwa matakin qarshe na qunci da radadin zuciyar datake mutuwa daga Sauran walwalan rayuwa.
Itama sakinah rintse idanuwanta tayi ahankali jikinta na sakewa wani dumi na zagaye jikinta da sarawar Kai.
Tenya tasan ba abune me sauki ba ko kadan hakan kuma qunci ne sabo da zai dasu a zuciyar Ayanah na har abada amma hakan shi kadai ne mafita dan kuwa matiqar zasu yadda ita tayi alkawarin da dubararta zata kawo sauyi da aminci a rayuwar Zuhrah duk da har abada su biyun zasu rasa rayuwarsu kenan ta walwala ko farin ciki dan kuwa zasu tabbata ne a quncin rashin juna suna ji suna gani.
Girgiza Kai Ayanah ta fara yi ahankali da karfi tana fizga kafin sakinah ta riqeta jikinta da karfi tana rungumeta tana Gyada Kai tana hawaye tana cewa
‘Indai Zuhrah zata fito zatayi rayuwa me aminci zaki iya Ayanah,Zaki iya Ayanah….’
‘Bazan iya ba,bazan iyaba shine abinda take fada da karfi tana qwacewa amma dole sakinah ta saka karfi ta riqeta harta gaji dan kanta tayi Laushi.’
Ganin tayi Laushi ya saka sakinah da tenya da kanta suka kamata zuwa toilet inda hadaddun ruwan Zafin wanka ke jiranta suna fidda hayaqi da dan qamshin wani maganin al’ada na wankan haihuwa.
Su biyun ne sukai mata gashin wanka me nutsuwa dukansu jikinsu a sanyaye kaman yanda ita kuma ta koma tamkar batada sauran hankali ko kuzari a jikinta.
Sun dauki lokaci sosai kafin suka fito sakinah ce ta tsaya tayata shiryawa tamkar yanda aka Saba gashinta ta goge mata ta busar dashi ta Kamasa sako sako sbd karya dameta ta dauko mata Kaya tana miqa mata tana sakawa kamar wadda bata gani.
Abinci da lafiyayyar dafaffiyar madarar datasha hadin Kayan qamshin da zafi sosai aka kawo mata tenya da sakinah ne suka tirsasata taci aka kwantar da ita take bacci me nauyi ya dauketa sbd akwai maganin bacci a cikin madarar.
NUAB ma sabon wanka da shiri tenya tayi masa da kanta sbd bata yadda da kowaba Akan Ayanaah da shi yanzu,
Wuni Ayanah tayi tana bacci sai yamma lis ya farka aka sake hada mata ruwan Zafin da aka kuma gasata da kyau ta shirya ta zauna a daki ita kadai sakinah ta saka mata NUAB a hannunta San shayar dashi,
A lokacin data masa shayarwar farko Jin tayi wani abu ya ratsata Wanda ya sakata kafesa da idanunwata da suka qanqance sbd kukan baqin cikin rayuwarta da baya qarewa,
Addua ta bude bakinta a sanyaye ta fara jero masa tana fatar rayuwarsa ta haskaka hasken da zai haskaka rayuwar duk wainda basada gata ko yanci a rayuwar nan.
Dan qanqamesa tayi ahankali da hannuwanta tanajin tamkar ruhinta yana zame wa yabar jikinta na rabuwa da zatai da Zuhrah wannan Karan da gaske kenan har abada sbd hakan shine kadai zai bawa kowannensu rayuwar da ba ita suka so ba,
Indai Zuhrah zata rayu ta samu kwanciyan hankali nutsuwa da walwala tabbas zata zabi rayuwa da gurbin da babu me cikesa idan ba Zuhrah din ba har abada,zata zabi rayuwa babu digon farin ciki bare walwala har abada indai Akan samun rayuwar Zuhrah ne dan haka a yanzu NUAB ne kadai jininta dayake rage mata a rayuwanta da batada komai sai qunci a cikinta, NUAB shine gata,rayuwa,ruhi,zuciya da hasken idaniyar daya rage mata Wanda kuma zata ci gaba da rayuwa sbd shi.
Da wannan tinanin da quncin ta kwana da ‘danta a jikinta datake Jin tsananin sonsa fiyeda rubabbiyar rayuwarta.
Washe gari haka akaita hidima a masarautar ta farin ciki da murnar jarumai biyu da aka samu,
A bangaren Haile kuwa kwance take rigis hawan jini da ciwon zuciya yana mata karfi dole aka aika mata kwararrin likitocin da zasu tsayu a lafiyarta,
Tenya kuwa sosai ta sake kafewa Akan kiyaye komai na bangaren ayanah sbd abubuwan daya fara gani.
******* babban bangare daya dayake komai iri daya dana HAILE da MARAKI a kuka bangaren da suke aka bude Anai masa wani irin gyaran daya saka ko MARAKI da bata damuwa shiga damuwa da fargaban matsayin da wishmah take dashi gurin Masarauta gabaki daya,
Duniya guda aka zuba a bangaren da a cikin kwana shida aka gama zuba masa dukkanin wani luxuries Ayanah da babynta suka tare harma da bayinta da tenya wadda aka dawo da bangarenta anan itama bisa ga umarnin sultan daya saka ciwon hawan jinin HAILE yin sama dan babu matarsa da jakadiyarta ta taba zama kusa da ita.
Ranar da kwanaki bakwai suka cika a ranar akai gagarumin nadin sunan daya girgiza BOYEM da wajen BOYEM gabaki dayanta dan kuwa duk wani babban mai sarauta da mulki na kasashe daban daban suna qasar BOYEM dan radin sunan magaji da dan uwansa tareda babbar hidimar qaddamar da wishmah ta uku a tarihin BOYEM. #MAMUH
HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070
Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali_*HAYATEEM*_ Mamuhgee
43 Gagarumin radin sunan NUAB ALMAZZ YASAR BOYEM aka fara yi kafin na ASIM YASAR ALMAZZ BOYEM aka ringa barin dukiyar data ringa jijjigar bayin fadar sultan sbd daukan kyaututuka zuwa bangaren iyayensu mata wato bangaren Ayanah dana HAILE dukda yawan kyautikan bangaren uwar magaji ta ringa sauka sbd yanda aka ringa barar masa da dukiya.
Da dare ne bikin wishmah dan haka anfi kwana uku Ana shirye shirye da decoration na fadar inda zaa qaddamar mata da matsayinta Wanda kowa saiya sheda kuma ya bata matsayinta datake dashi na macen farko data karbi matsayin Bayan shekaru masu yawa gata kuma uwa ga ‘da na farko daya haske zuciya da idaniyar mahaifinsa da zuwansa duniya.
Masu kwalliyar wishmah da kanta kusan su biyar ne sbd ado ke na musamman da Ayau zai nuna Itace mace ta farko da kyanta zai dake na queen HAILE hakama macen data motsa zuciyar mai girma sultan dan haka wasu irin sarkokin zinari masu daukan ido da kyau ne aka fara shigowa dasu a tray Layi Layi kowa da abinda ya dauko a cikin bayin da suka fara shigowa suna jeruwa,
Tenya ce ta shiga qarshensu dan itace a tafe dasu,
Fara daukan sarkokin akai aka saka mata Akan wata irin lafiyayyar kwalliyan da akai mata ta maroon doguwar rigar datake jikinta data bi jikinta ta lafe daidai shape dinta mai tsari kaman bata haihuba,
Wasu irin stones dake daddabe a jikin rigar masu daukan ido suka dan sitirta shape dinta daya fito sosai a jikin rigar suka sake qarawa kyanta da adonta kyau,
Gyalan rigar Maron shima akai rolling akanta Ana rufe gashinta mai tsayi daya qarawa kwalliyanta kyau kafin aka saka sarkoki da chains na zinari akaiwa rolling din nasa adon gaske me Kyau kafin aka saka babban transparent mayafin Kayan still mai tsayi sosai haryana ja da qasa aka Dora Akanta aka rufe rabin fuskarta da babu Wanda ya isa ya gani shima akai masa nasa adon da chains na zinari take ta fito tamkar macen da aka saka golden biro aka zana dan kuwa komai nata daukan hankali d jan hankali yakeyi.
Tenya Jin tayi duniyarta ta sake haskaka da farin ciki suka fito da ita a daidai lokacinda zaa fara tana dauke da NUAB a hannunta.
A bisa dolen al’adah sai matansa sun fito sune zasu tarbesa su rakota a tare har inda yake dan haka koda akai sanarwar isowanta kofar fadar tareda bayinta da securities din dake tsare da NUAB da jakadiyarta take HAILE ta Hadiye wani kakkarfan busashen yawun daya saka hannunta rawa tana yagar fatar Dayan hannun nata da karfi yana yagewa,
Cikin sauri da basarwa Aslam dake kusa da ita ta Dora hannunta Akan hannun mahaifiyar tata tareda dan kallanta a natse tana girgiza mata Kai kada kowa ya gani.
MARAKI ma dagowa tayi zuciyarta na daukan Wani irin nauyin zazzafan kishi mai tsananin ciwo da dumama jini ta zubawa AYANAH GHAZ idanuwanta tana kallan Wani irin fitinannen sirrin kyau daya saka kusan koina tsit sbd duk da tana rufe amma gyalan yayi shara shara din da babu abinda basa gani na halittar da Allah ya qera a gurin,
Akan sultan MARAKI da HAILE suka sauke kallansu a lokaci daya zuciyoyinsu na shiga wani nannauyan kishin da babu wadda batajin kaman ta Hadiye zuciya a lokacin ta mace.
Wani irin kallo ya dago fararen idanuwansa masu kyau da girgiza dan Adam ya saukewa AYANAH GHAZ daga lokacinda ta sako kafa a cikin fadar batareda ya kyafta ba dan kuwa duniya biyu ne aka hade masa guri guda a gabansa ita da NUAB datake rungume dashi suna tinkaro sa.
Yan jarida da televisionsa da duk wani dan media suna gefe daya da aka ware musu sbd tsari da Kyan fadar daga can suke daukan hotinan da flashers kawai ake gani tana haskowa babu kakkautawa.
Haile da maraki ne suka iso gefenta kowacensu da adonta mai kyau da tsari tareda daukan ido itama suka fara tako wa tareda da ita dukansu idanuwansu Akan sultan ta cikin nasu rufar Ayanah kuwa kanta a qasa shi kuwa nasa idanuwan Akan ‘dansa dake hannun Ayanah kawai yake kalla taqaita kallansa daga gareta hana kishinsu Kai illa ga zukatansu.
Isowan AYANAH GHAZ gabansa suka zauna inda aka tanada dan zamanta da nasu take aka fara gabatar da kosher din Wanda yake tamkar daurin aurensu ne zaayi.
Dukiyar kosher datake tamkar sadaki aka gabatar daga jinin BOYEM na manyan cousins din sultan dake qasashe daban daban suna rayuwar mulki da daula tareda hutawa a qasashen turai daban daban dayake dik jinin BOYEM indai suna raye ko a ina kake Ka Halarta dan haka masarautar take shaqe da masu duniya a hannunsu.
Irin dukiyar da aka bayar ya saka masarautar jijjiga take aka karba dukiya aka bawa jakadiyarta sbd itace gatanta wadda kadai take da ita aka fara adduar kosher din tsawon lokaci kafin aka rufe da Amin Wanda Amonsa sbd yawa ya ringa amsawa har wajen Masarauta.
YUNAR KAREEM ALMAZZ BOYEM Shine babban dan wan mahaifin YASAR Wanda yake Zaune a qasar Kuwait da matarsa daya da Yaya uku sai yaya hudu daga imebētinsa daya dan haka shine ya isar da cika Burikan wishmah guda uku Wanda Kai tsaye budar bakinta idanuwanta a kafe kan NUAB dayake kan kafafunta muryanta na tsananta sanyi da karfin Hali tace Abu na farko datake so shine a yanta bayi dari a cikin bayin dake kurkukun masarautar, Sai Abu na biyu shine tanason a ‘yanta mata baiwarta daya tak sakinah, Na ukun shiru tayi zuciyarta na yin Wani irin rauni da sanyi ta dago idanuwanta da sukai ja ta saukesu Akan sultan tace tanason ko tana raye ko baya raye idan NUAB ya girma kada a tirsasata hawa mulkin Masarautar BOYEM matiqar baida raayi idan ba shine yayi raayi ya hau dan raayin Saba.
Tsit kowa yayi koina ya dauki Wani irin shiru mamaki na kashe kowa musamman sultan da HAILE da Wani irin sanyi a Karan farko ya dan ratsa zuciyarta ta kafe Ayanah din da ido tana mata kallan mahaukaciyar data rasa tinaninta dan kuwa batada labarin cewa tinda ta fada wannan burin saiya cika koda zata mutu Akan sauya hakan, Tayaya zata ce idan danta baida raayi kada a basa mulki? Ta kuwa san menene samun mulkin Masarautar BOYEM?
Sultan kuwa kafeta yayi da idanuwansa Wani irin daci mai karfi yana Sosa zuciyarsa dan kuwa tamkar Kai tsaye ta kallesa ta yaga burinsa daya kullata koda zai mutu ne ta yaga a gaban idonsa,
A matsayin datake dashi harta isa samun wannan tinanin? Menene nufinta na fara lalata burinsa Akan dansa tin yanzu? Tabbas tayiwa burinsa na shekara da shekaru tabon da har abada bazai goge ba musamman idan abinda ta fada din ya tabbata.
Manyan fada dik da shock din da suka shiga take aka sanar babu burinta da baama gama cika wa dan haka take aka bada umarnin a saki bayi dari biyu ma da suke kurkukun,
Sakinah ma take aka yantata tareda kyauta me tarin yawan data saka Ayanaah din rufe idanuwanta ahankali hawaye masu dumi na gangaro mata sbd samarwa sakinah yancin da sukam bazasu samu ba har abada.
Har tsakar dare sosai Ana hidimar sai kusan gap da asuba aka gama kowa ya watse zuwa masaukinsa.
Washe gari da sassafe aka saki bayin da akace a saki, Koda aka fara fitowa dasu tenya na bakin kurkukun dan cika sabon aikin daya hau kanta na hadawa mai girma YUNAR BOYEM sabuwar imebeti a matsayin tukuicin dukiyar kosher daya bayar ta wishmah daga mai girma sultan YASAR,
Tin farko tasan daman zaa bada tukuicin imebeti ga duk Wanda ya bada dukiyar kosher din wishmah a matsayin tukuici Shiyasa ta fadawa Ayanaah sadaukar da zatai na rabuwa da Zuhrah har abada sbd ita zata bayar dan hakanne zaisa itama ta samu rayuwar da har zata haifa nata yayan amma sun yafe juna kenan har abada sbd daga ranar da aka gane jininsu daya duka su biyun zasu rayuwarsu matiqar ba yayansu sunyi girman da zasu sassauta musu hukuncin hakan ba kuma a yanzu Ayanah ta yadda da hakan matiqar zasu rayu Zuhrah ta Gina tata rayuwar harma zuriar kanta,
Hakanne ya saka tenya take tsaye a lokacinda aka fito da Zuhrah wadda ta fita kamanninta gabaki daya Kai tsaye gurin duba lafiyarta tasaka aka wuce mata da ita dan shiri da gyaran gaggawa zaa fara yi mata na tsawon wata daya cif kafin a Kai masa ita ya wuce da ita qasar kuwait. #MAMUH
HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070
Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali_*HAYATEEM*_ Mamuhgee
44 A daidai lokacinda Zuhrah ta sako kafarta wajen kurkukun fata shafe Sheka daya da watanni a ciki a daidai wannan lokacin Ayanah ghaz datake tsaye zuciyarta na Wani irin harbawa da Wani irin zallan kewar datake ratsa ruhi da zuciyarta kafafunta na dan rawa tanaji a jikinta Zuhrah na cikin halinda itama take tsananin son ganint su shaqar da rahamar ganinsu.
Sakinah dake tsaye gefen Ayanah din itama zuciyarta cike take da yanayi na sanyi da mutuwar jiki tareda tsananin so da kaunar ganin Zuhrah wadda shikenan wannan Karan sun rasa juna kenan da gaske har abada.
Tenya ma dake tsaye wajen kofar kurkukun zubawa Zuhrah idanuwanta tayi babu kyaftawa tana Jin tsananin tausayin Ayanah da zata iya rasa ranta idan taga Zuhrah a halinda take ciki daidai wannan lokacin.
Barin sukai da zuhran wadda bata iya Miqewa qyam tsaye sbd yunwa da wahala hakama fatarta tayi duhu gabaki daya ga gashinta duk ya zama abin tsoro da qyama,
Suna barin gurin tenya ta aika baiwa ta isarwa da wishmah sakon Zuhrah ta fito kurkukun da babu komawa insha Allah har karshen rayuwarta.
Sakon yana isowa wishmah Lumshe idanuwanta tayi ahankali tareda silalewa qasa tana bin bango ta zube qasa tana bude idanuwanta Akan sakinah data riqeta tanason magana ta kasa sai kawai ta sake rufe idanunwata tana dora hannunta daya Akan kirjinta dake mata radadin azabar da har abada bazai dena ba sai ranar da ranta yabar jikinta dan kuwa baqin ciki ne da quncin da baida magani.
Sakinah da samun yancinta bai saka taji zata iya barin Ayanaah ba har abada itama sanyaye jikinta yake hakama ta shirya zama baiwar Ayanah har qarshenta ko da yanci ko babu yanci zata bauta mata ta kuma bauta ma ‘danta har girmansa.
******acan tenya kuwa Kai tsaye bangaren gyara ta isa da Zuhrah ta fara bada umarni aka wanke Zuhrah tas aka ringa cire datti harma da wasu qananun qwari a jikinta tsawon kusan wuni guda, Taso a yanke gashinta amma sbd imebeti zaa turata tana buqatan dogon gashin dan haka sai aka barshi shima ya ringa Shan wanki kan wanki,
Ana gamawa gyaran kafafunta da hannuwanta akai na farce tukuna aka kirawo likitoci suka duba lafiyarta,
Magani dasu multivitamins aka bata sai kuma tenya data bada umarnin aka hado mata mai na gargaji dayake goge tabo a qanqanin lokaci dan goge tabon raunikan data yiwa kanta duk da sun warke sun fara bace wa da disashewa saura dakan Wanda shine kila bazai fita ba sai sun hada masa da magani.
Har dare sosai tenya bata huta ba tana kan lamarin Zuhrah da babu wani lokacin batawa matiqar tanason jefata a matsayin imebēti tana buqatar tsayuwan gaske a gurin gyaranta.
Ayanah kuwa a nata bangaren tinda Zuhrah ta fito sai taji jikinta yayi sanyi ta sake raunana da komai,
Ta bawa sakinah dukiya me yawa Akan ta tafi ta samu yanci tayi rayuwarta amma sakinah Sam bazata iya barinta ta kafe zata zauna da ita har karshen rayuwa,
Batada Sauran walwalan daya rage mata kokuma shaawar rayuwa dan haka bata takura sakinah dinba dan kuwa daman ita kadai ce a yanzu ta rage mata a asalin rayuwarta hakama tana buqatan Wanda zai tsaya mata ya tayata bawa danta kariya duk da ta zabar masa yancin zabar abinda yakeso da kansa ba tirsasawa tin yanzu Akan mulkin datake tsoron kada a illata mata shi akai, Hakaman tayi hakan ne dan basa kariya daga masifu da hadarin da zai fara fuskanta ta ko ina tin yana jinjirinsa so yanzu zaa bar mata shi yayi rayuwa a cikin aminci tinda an riga an cika mata wannan alkawarin sai kuma idan ya girma idan yanada raayi hakan zai zama barazana ga Maqiyansa da masu so.
A bangaren sultan YASAR kuwa Ayanah ghaz tayi masa babbar sukar data rage mata matsayi a zuciyarta dan kuwa duk irin soyayyar da jinin BOYEM zaiwa mace baya taba sauya abinda yake yawo a jininsa dan ako Yaushe harkar mulkinsu da iko tareda abinda suke Buri yana gaban kowace irin soyayya da kauna,
Duka shekarun daya Debo na tsananin burin samun ‘da namiji sbd hakan ne, Sbd tabbatarda magaji Akan karagarsa bama batareda ko yanada raayi ba ko bayada raayi amma a Karan farko na tarihin masarautar ta zabawa ‘danta kaddararsa tin yana zanin haihuwansa,
Yanada wani magajin Bayan NUAB da zai iya gadon karagar amma abinda tayi masa ya sakasa Jin ko zata rasa ranta sai ‘dansa da yayi raayi ya mulki BOYEM koda hakan na nufin fizge ta daga matsayinta sedai amma zuciyarsa na kasa barin sa ga aikata hakan dan kuwa kaman yanda jinin BOYEM da bazai taba barin burinsa ba yake a jininsa haka soyayyarta take a jininsa dan haka idan bazai iya cireta a zuciya da jininsa ba to zai iya cireta daga dukkanin qudurinta da bazai taba cika ba.
Haile a yanzu ne ta samu damar sassautawa zuciyarta ta fara Neman lafiyarta da gaske dan kuwa a yanzu ta samu tabbacin tanada dama me karfi ta qwatowa ASIM matsayinsa da aka bawa ‘dan mistress, Bazata taba hutawa ba ko samun bugawan zuciya daidai har abada idan ba ganin ASIM BOYEM tayi ba Akan kujeran mulkin BOYEM,
Batada Buri ko kudirin daya wuce saka ASIM a zuciyar sultan YASAR fiyeda dan mistress dinsa, Zata tabbatar ta dawo da matsayi da ikonta a hannunta na juya rayuwar kowace macen datake imebētinsa, Zata ninka tsoronta da zafinta akansu ta yanda bazasu taba iya kallan Ayanah da ‘danta da darajar data wuce mistress ce da dan mistress dan kuwa a yanzu ne zata tada asalin rashin imaninta Akan abinda takeson ‘yayanta su mallaka, Ko rai nawa zata kashe batada shakka zata kashesu tamkar dabbobi sbd saita tabbatarda Ayanah ko kallan inda take babu me yi bare bata girman matsayin datake dashi.