Kenza eBookz

Idan kaya ya gaji book 3 - Chapter 14

Idan kaya ya gaji book 3 - Chapter 14

Idan kaya ya gaji book 3 Chapter 14: Idan kaya ya gaji book 3 Chapter 14. SABUWA:. Har ƙofar gida motar Dr Kamilu ta kawo mu duk da saurin da yake yi hakan…

3,760 words

SABUWA:. Har ƙofar gida motar Dr Kamilu ta kawo mu duk da saurin da yake yi hakan bai hana bayan dasu Adama suka sauka ya tsaya ya rarrasheni ba. "Ƙanwata kiyi haƙuri nasan dai hankalinki ya kwanta amman fa ba duka ba sabida rayuwar yaranki zaki duba. Amman zan baki shawarar ki nutsu sosai ki kama kan ki, sannan kada kice wai ba zaki yi Aure ba da zaran miji ya fito miki kuma anyi bincike an tabbatar da nagartarshi kiyi aurenki kije ki huta hakan shine mutuncinki. Sannan ki sani ba duka maza bane suka taru suka zama ɗaya ba. Wani in kika aureshi sabida tsabar dadi ji zakiyi tamkar ba a wannan duniyar ta mutane kike ba. Kar ki mance gobe kina da ganin likitarki kar kice ba zaki je ba. Sannan ki dage da shan magungunanki da sun ɗakko ƙarewa ki sanar dani. Kuma duk abinda kike bukata kada kiji nauyi ki bugo ki faɗa mun. Ga kayan abinci a both na kuma kawowa ki nemi yara su shigar miki dashi." Godiya nayi mishi sosai sai washe baki nake yi wai yau nice nayi firi babu igiyar kowa a kaina ni Sabuwa. Sakkowa yayi ya sauke mun kayan abincin mu kai sallama ya ja motarshi ya tafi. Sadiya ce ta shigo layin a mota, tsayawa nayi har dai ta gama sallamar baƙonta kafin ta taya ni muka kwashe kayan abincin muka adana a ɗakinsu Adama wanda anan nima zan zauna, muka koma cikin gida da sallama a bakina. Rakiya sai zage _zage take yi ta inda ta shiga ba tanan take fita ba. Ina shigowa tace. "Ga filin tsakar gidannan Lolo ba dai zawarci ke baki sha'awa ba? To gaki ga zawarci wallahi kun ɗaura ai. Duk waɗannan riɗa riɗan banzan da suka cika gidannan ko wacce mafaka take nema ko wanda yafi mazajensu na baya talaucine yazo aurensu za suyi ko babu komai ai Aure yana da daraja." Gaza ne ya leƙo daga ɗakinshi labule a hannunshi yace. "Rakiya yafa isa haka Lolo ba lafiya bace da'ita. Shi kuma Babangida Allah ne ya so shi shi yasa ma alƙali ya raba auren. Rakiya baki san me muka shirya mishi bane wallahi shi yasa. Kuma babu wanda ya isa yasa Lolo ta koma mishi ta fito kenan. Zawarci ai ba mutuwa bane. Da yawan yaran gidannan sau nawa eh su ka yi aure eh suka fito kuma me ya cinyesu. Wani auren dashi bama gara babu ba. Ko ni nan da nasan ma haka aure yake da me zai aikeni in wani faɗa. Ni naga abokaina sai rubibi suke yi ashe babu daɗi auren" Adama tace. "Nima dai shi na gani. Gaza ya batun ɗebo kayan nata anjima zamu je tunda Baba Malam yace taje ta ɗebe kayanta shi ya siya kuma aure ya bata?" "A_a da yamma akwai inda zani an bani wani aiki. Mu barma gobe ba sai in tattaro eh yarana muje a ɗebo mata kayan ba? Duk wanda yayi mana warki in sa yara su farɗe shi eh wallahi Allah Rakiya naga eh kina haratata ne ai" A haka suka barshi. Ni dai ɗakin Rakiya na shiga na kwanta. A ɗakin na tarar da Uzairu Zuchiyata da Salaha. Salaha yaushe kika zo garin?" Na faɗa muryata da sanyi duk da zuchiyata fal farin ciki. "Ban jima da shigowa ba Lolo ashe dai auren ya mutu to barkan ki na taya ki murna. Nima yaji nayo ke ni auren wallahi ya isheni haka. Zagi da cin mutuncin ya isheni. Su Adama ne suka shigo duk aka bararraje gidanmu gidan daɗi duk da ko wacce da matsalarta ba'a zama ayi jigum sai dai ayi ta hira ana musu ana nishaɗi. Jin tashin muryoyinmu ne yasa Gaza shima ya shigo aka ci gaba da hira dashi. "Adama kunji labarin Aisha tayi ɓari ko? Tana asibiti bata ma wai gane wanda yake kanta. Ɗaxunnan ƙanwar mijin ta kira waya" "Wayyo cikinne ya zube? Zaki je ne Rakiya ki zauna da'ita ko ni gobe sai in shirya in tafi?" Rakiya tace. "Gara ke kije ɗin dai gaskiya ni kam bazan iya wata doguwar tafiya ba. Kafinma ta rufe baki sai ga kiran waya ya kuma shigowa wayar Rakiya Aishan ce wai suna hanya ita da mijin zai kawota gida tayi jinya anan. "To ai shikenan tunda saida kuka kamo hanya zaki sanar. Da zamanki kikayi a ɗakin ki ai yafi dama yanzu muke maganar Adama gobe zata tawo" Tsaki Rakiya tayi ta kashe wayarta ta shiga mita. "Kai wato a gidannan dai dole mutum ya dage ya zama mai kuɗi ko dan ya huce takaici wallahi. Kai da naka amman sai ya ba da kai jibi Rakiya yadda eh kike tsaki fa dan kawai Aisha zata zo jinya, eh ba gara tazo ba" Cewar Gaza kenan. Ni dai sai ido kawai nake binsu dashi har wani murmushi nake yi wanda sai dai kawai naji yazo mun sabida a cikin farin ciki nake duk da yarana suna tsaye a raina. Abu ɗaya nake tunawa inji hankali na ya kwanta na watsar da batun yaranma. Yafi mun alkhairi in fuskanci abu na gaba. Khalid ne naji ya faɗo mun a raina. Amman sai take zuchiyata ta gargaɗeni da faɗin. "Kada ki sake ki koma ƴar gidan jiya. Ƙila matsalar da zaki samu tare da Khalid ta danne ta gidan Babangida. Auren Khalid tamkar an rabu da bukar ne aka haifi Habu. Ajjiyar zuchiya na sauke na gamsu da zuchiyata ɗari bisa ɗari tuni nayi fatali da tunanin Khalid. Yanzu burina shine sake gina sabuwar rayuwa ina fatan ta kasance mai inganci. Da yamma lis sai ga Aisha sun iso ita da mijinta da ɗiyarta muna can ɗakinmu ana tattaunawa akan batun inda in an ɗebo kayana za'a roƙa a ajjiye Aisha ta shigo duk ta rame ta lalace ta saje ta zama ƴar ƙauye sai dai idanunta har gobe yananan a buɗe tar kallo guda zaka yi mata ka gane hakan. "Kun iso kenan. Ina shi mijin naki ko yana gidansu Rakiya ne?" Cewar Adama dake zaune tana ma Laraba kitso. A wahale tace. "Yaje ya siyo magungunan da aka rubuta mun a asibiti ne. Wallahi tunda na fito daga wannan ƙauyan na fito kenan tunda ashe shima yafi son in zauna anan tare dashi dangin mahaifinshi ne suka zigashi. Ni kuma nace wallahi bazan koma ba" Tashi zaune nayi nace mata. Shi to me yace dake ina kuma yarinyar taki kika barota?" "Cewa dai yayi na ɗan zauna a gida ko na wata shida ne ya gani tukunna zai san yadda zai shawo kansu su haƙura mu zauna anan. Sai ya kwaso mun kayana mu kama haya a nan yarinyar tana wajenshi, tare amman zasu koma tunda ni jinya nazo yi." To hakan yafi zaman ƙauye tsakani da Allah su ya kama. Amman Rakiya ta san komai?" Idanu ta zare tace. "Ina fa a hakanma sai zagina take yi wai na tawo. Nifa nakai sati a asibiti cikin yakai kwana goma da ɓarewa kuma maganar gaskiya zubarwa nayi kawai sabida zaman garin bai yi mun ba. Shi kanshi ya fice mun akaina bazan sake jiki inta sumɓulo ƴaƴaba wallahi kazo duk ka tsofe." Bakina na taɓe kawai. Adama kuma bazawarinta dakaci ne ya iso dama da shirinta tsab mayafi kawai ta saka ta fice. Labbai kuma ta dubeni. "Lolo ku haɗo kuɗin cefane ayo sai a ɗora sanwa. Kema Aisha ki kawo. Ɗari biyar na miƙa Aisha ta bada ɗari uku anfa soma kenan. Da daddare mu huɗu akan katifa ɗaya kuma bawai shida da shida (6 by 6) ba ƙaramar katifa ta gadon bono fa. Wallahi baccinma kasawa sam nayi saida na dawo ƙasa na kwanta a leda shine na ɗan samu sassauci, zafi da sauro suka gallabeni naita juyi ina tsaki. Labbai kuwa kusan raba dare tayi tana waya tana kashe murya. Adama ma tayi nata ta gamane ta kwanta. A ranar na sake tabbatar da tsayin dare. Washegari muka tashi da sabon lamari faɗa tsakanin Maigogul da Rakiya wallahi har waje. A guje muka fita muka samu Rakiya ta cukume Maigogul ta shakeshi fa sosai har idanunshi sun yi ja. An cika layin maƙil kullum a cikin abun kunya mu dai muke a gidanmu. Da ƙyar Gaza ya raba faɗan ya ja hannun Rakiya ya jefata zaure. Wuƙa ya zaro a ƙugunshi yana ta ɗebo ashariya yana ɗumawa jama'ar da suka fito gulma. Daya karta wuƙar a ƙasa kuzo kuga gudu. Ni wallahi dan takaici da baƙin ciki ma ko magana na kasa yi su Adama suka biye ma Gaza akaita duma zagi na borin kunya. Maigogul ya shiga gida suka ɗaura rikici daga inda ya taya. "Tur wallahi da wannan gidan. Ni wallahi ba dan Madamcy ta matsa sai mun zauna a gida ba wallahi ɗa ba zaku sake ganina ba ma har abada nima fa ji nayi kamar in shaƙe Maigogul ɗin dan baƙin ciki. Ya wanna zubar da mutunci a layi haka. Dan Allah ya ba za'a dinga kore muku samari nagari ba? Ku fa duba eh duk fa masu zuwa neman naku duk ƴan balaja'u irinkune suke zuwa har ita Lolon mijinta ɗan kunamane fa." Adama tace. "Gaza bar wannan sokiburutsun dan ALLAH ya batun ɗebo kayan Lolo nace?" Wukarshi ya mayar ƙugunshi. "Ku jirani zan tawo da ƴan iska cikin bus tare da motar kaya. Zan kiraki ku fito titi mu haɗu mu wuce. Eh duk wanda yayi mun wani wata wata bazai ji daɗi ba wallahi in na dama sai an shanye." Ya wuce fuu zuwa ƙasan layi. Mu kuma muka shige cikin gida. Ashe_ashe wai Rakiya kama Maigogul tayi yana gulmarta a ɗakin Hauwa shine fa akayi ta dambarwa daga ƙarshe faɗa ya koma kan Hauwa da shi dai muka karya mu kam. Ana haka Gaza yayo kiran Adama akan su fito su wuce ɗebo kaya. Adama da Labbai, da Sadiya, harda Aisha mara lafiya aka fice. Labbai har da soke wuƙa itama Maigogul yace. "Gara in bi yarannan kada suje suyi ɓatacciya nasan ba'a haɗa hanyar arziki da Gaza" Aikuwa rigarshi ya bige ya fita da sauri na bishi na tsayar dashi. Maigogul yanzu dakai za'aje ɗebo kayan? Nikam dan ALLAH " Daga haka hawaye ya soma zubo mun. Taya in banda gida irin namu ace a saki Ƴarka kuma a matsayinka na mahaifi ace dakai za'a tafi kwaso kayanta. Wannan abun kunyar har ina" Tsaki yaja daya dubeni yaga bil haƙƙi kuka nake yi wiwi yace. "Aikin banza da wofi ai baki yi kuka ba Lolo badai zaman wannan gidan kika zaɓa ba?" Ya nuna gidan da bakinshi tare da ɗorawa da cewa. Abinda nake guje miki fa suna da yawa. Yanzu dubi da bala'in kayi nayi muka tashi a gidannan dashi muka karya fa. Lolo wa yasan sanda zaki kuma wani auren. Zamu je a ɗebo kayan naga inda ma zaki ajjiye kayan naki a gidan uban naki da kike gadarar a sake ki ki dawo" Ana ga yaƙi Maigogul yana ga ƙura. Bai ko sake bi ta kaina ba yabi bayan su Adama suka gangara, ni kuma jikina a mace mus na shiga gidan. A ɗaki na samu Uzairu zuchiyata da Rakiya. "Zo lolo Felisha ta ganki" Ya kirawoni na matso kusa dashi. Wata baturiya na gani a kwance sai murmushi take yi. Tana ganina ta faɗaɗa murmushinta tana ɗaga mun hannunta. Nima murmushin dole na ƙaƙaro nayi mata na ɗaga mata hannu. Turancin nawa bazai wuce gaisuwa ba sai yes da no su biyo baya a haka dai muka gama gaisawa. Shi ko Uzairu zuchiyata yaji turanci da figi da yagi sabida aji daɗin yin ƙarya har yanzu yana karanta ƙamus tare da wasu littattafan koyon turanci irinsu tech your self ( koyi da kan ka). Kaina na girgiza kawai na zauna kusa da Rakiya ina sauke numfashi. Uzairu zuchiyata sai zuba turanci bil haƙƙi yake yi. "Nace wai in aka ɗebo kayan naki ina za'a jibge miki su Lolo. Ga kaya masu tsada kada a jibgesu a tsakar gidannan su lalace. Gu Gaza da Sama su biyo dare su sace miki. Shine nace ko gidansu Bala zan shiga in roƙi alfarma ko zasu ara mana ɗaki a ajjiye kayan kafin Allah ya ɓullo miki da wani sha ƙundum ɗin?" Uzairu zuchiyata da ya gama bidiyo da baturiyarshi sai yace. "Kema kinsan ba zasu wani karɓi ajjiyar gidannan ba. Ko sanda Auren Labbai na biyu ya mutu ba anje an roƙi za'a ajjiye kayan ba suka ƙi fur ba. Amman lokacin da auren Halimar gidan Malam Habu tsohon mijin Labbai daya mutu su suka ajjiye musu kayan har tayi wani auren. Ni Rakiya wallahi baturiyarnan in fa na aureta kinsan Allah ɗaukeki zanyi daga wannan gidan in sake miki gida. Ranar girkinki Dad ya dinga zuwa yana dubaki, ban kuma yadda ya koma ba ke kaɗai zaki zauna ehe" Dariya muka yi ta yi dukkanmu na dubeshi nace. Amma a mafarki ko? Wacce baturiyar ce zata aureka Uzairu zuchiyata? Yaro bari kada kyanka ya ruɗeka. Kuma ina laifin a madadin ka ɗauke Rakiya ka kyara musu gidan? Maigogul yau kuma shine Dad ɗin. To nima in ka ɗauke Rakiya sai nima in gyara ma maigogul gidanshi in mishi aure ba shikenan ba tunda Ummin Mama ta kafe tana ciki. Wallahi Allah har mamaki take bani. Shima maigogul ɗin murmushi yayi da Labbai ta kawo mishi taɗin." Daƙuwa Rakiya tayi mun. Miƙewa tsaye yayi ya shiga jujjuyawa yana wata mayaudariyar dariya gashi a tsaye a kanta. "Tabb na rantse da Allah ba duk turawaba wannan kyau nawa. Motsa jikima zan soma tace ƙirjina tana ɗanso yafi haka faɗi kinga banci ta zama ba wallahi lolo ke bafa wasa bil haƙƙi Auruwa zanyi a turai tsab" Rakiya ta kwaɗo mishi takalmi duk muka kwashe da dariya. "Ɗan baɗo ji abinda yake yi sak ubanshi. Ina tuno sanda Maigogul yake kamarshi. Ai har Uzairu zuchiyata ya mutu bai isa ya kamo ƙafar gayen Maigogul ba. Tunda a yanzun ma shiga yake jerin gwanon manyan masu kuɗi in dai a sutura ne ya saje harma ya fisu kwarjini. Ai lokacin da yake zuwa zance wajena wallahi da yamma ƴan matan layin sa'annina da wanda suka girme mun firfitowa suke yi ko wacce ta zauna a ƙofar gidansu. In maigogul ya tunkaro layinmu zo kuga kallo a lokacin farinshi har kashe idanu yake yi halin rayuwane kawai ya mayar dashi haka. Amman maigogul yana halin a so shi" Tafi Uzairu zuchiyata yayi yace. "Yau dai ɗaya bayan an ci dambe Rakiya ta yabi Dad. Uhm ai Maigogul na baza capacity. Jiya naje gidan cin abinci ni da wata yarinyata muna fitowa Maigogul ya paka wata ƙatuwar baƙar jeep ya fito. Wallahi tsabar yadda yayi kyau ni da kaina nakai mishi yarinyar suka gaisa. Yanata murmushi ga haƙoran makanshi sai ƙyalli suke yi. Rakiya kinga yadda ya sake ɗaga mun aji kuwa ita kanta fa sai da tace wow gaskiya Dad ɗinka ya iya wanka kamar ka. Gaskiya in bikina da Felisha ya taso zai ɗaga mana aji a wajen turawa" Dariya muke ta yi tamkar bani da damuwar komai nice har da birgima a ƙasa Uzairu zuchiyata ɗan iska ne lamba ɗaya wallahi. Gidanmu gidan daɗi a kullum ina adda'ar Allah ya kawo wani sanadi da zai zama tsani wajen shiryar da ƴan gidanmu ko wanne ya hau kan gwadabe tartibi.

SU ADAMA:. Gaza mota biyu yayi ɗaya bus da zaratan ƴan iska su biyar ko wanne da sandarshi ga karnuka sunfi biyar a motar baƙaƙe masu dogon harshe. Sai ofun bodi ta ɗiban kaya babba. "Wai Maigogul wai dakai eh zamu je ne wai ya haka. Kai mai zai kaika wani ɗebo kaya ehhh? Kana zubar mana da mutunci meye haka wai. "Babu shakka waɗannan ƴan iskan daka ciko mota dasu wato Gaza kai baka gudun abun magana ko?' Gaza yace. "Kamar yadda kaima baka gudu ba ai in hakane kaina gado ehh wallahi" Matsa ma su Adama yayi duk suka shige mota harda Maigogul. Nan yaran Gaza suka shiga Gogoriyon gaishe da Maigogul. Shi kuwa sai fara'a yake yi musu. Ga matasa har matasa amman tamkar ba ɗiyan musulmai ba tamkar ɗiyan arna. Ga gashi an tara, ko wanne ba'a rasashi da tabon sara sabo ko tsoho. Ga kwallin rashin mutunci duk sunbi idanunsu zizara. Ana tafe suna busa hayaƙi suna ihu A haka har suka isa layin duk wanda ya gansu saiya kauce wani irin tuƙin jahilci suke yi tamkar zasu bige yaran mutane. Dattawan anguwa da matasan unguwa kowa yayi cirko_cirko yana baza idanu yaga ina motar zata tsaya, sai ga mota a ƙofar gidan yawa ta ci burki.

Babangida:. Jikinshi a mace, zuchiyarshi cike da raɗaɗi ga zafin maganganun su Sa'a da yadda suke nuna ƙiyayyarsu a fili ga Mardiyya. Tabbas akwai ranar da dole ya zaunar da Mardiyya ya faɗa mata gaskiya inma ba haka ba ƙila ta tsinci maganar a bagatatan ko a bakin Sauban ko a Bakin Sa'a da kanta. Tura ƙofar ɗakin Ƴar Shuwa yayi abun mamaki tana zaune a falo taci uwar kwalliya harda lalle da sabon kitso taje aka yarfa mata tamkar sabuwar Amarya. Dama ga ɗan gyare_gyare da suka ɗanyi na zuwan sabuwar Amarya. Tsakaninta da Ramatu ko wacce gasa take wajen ganin ɗakinta ya fito fes kafin dai Amarya tazo suga da wacce tazo. Sababbin manyan kuloli ya gani jere a daining mai kujera biyu. Baisan ta sai daining ba ai kuwa yayo kyau. Kuma wannan daining ba ƙaramin ɗagama Ramatu hankali yayi ba gani take shikenan Ƴar Shuwa ta cinyeta. Ga wasu sababbin plates da jug sabo shaƙe da zoɓo mai ɗari. "Sannu da zuwa Jannaty sai yanzu ka shigo?" Bai gama mamakin abinda ya gani ba ta kuma saka shi a wani mamakin ta hanyar riƙo hannunshi ta zaunar dashi ta cire mishi hularshi da agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunshi mai ɗauke da kwantacciyar gargasa. "Yaran ban gansu a falo ba a ɗaki kika shinfiɗesu ne?" Yayi tambayar ne kawai amman baisan ma abinda yace ba har saida ta bashi amsa ya gane me yace. "Suna store na mayar musu dashi ɗakinsu duk na fitar da tarkacen saina ɗan sai musu ƙaramin katifa na yar musu. Idanu kawai ya lumshe tare da jingina a jikin kujera kunnenshi babu abinda yake tariyo mishi face muryar Sabuwa. "Wanka zaka soma yi ko abinci zaka ci?" Yajiyo muryar Ƴar Shuwa. A hankali ya buɗe idanunshi ya ƙura mata idanu cikin tuhumar da saida ta tsargu a karan kankin kanta. "Uhm kina farin cikin Sabuwa ta fita fit a cikin rayuwata ko Aisha? To baki sani ba rabuwata da Sabuwa tamkar an kashe macijibe ba tare da an sare mishi kaiba. Nasan duk wannan kwalliyar, da sababbin kula da wata sabuwar tarairaya duk sabida kinji labarin da kike mafarkin jine tunma baki zama mallakina ba. Lokacin kina ƴar kwalta kina yawon bina hotel_hotel muna aikata ɓarna." Sai yayi wani murmushi wanda shi kaɗai ya barma kanshi sanin fassararshi. Miƙewa yayi ya shige banɗaki. "Baka yi ƙaryaba Babangida burina shine Sabuwa tayi rayuwar wulaƙanci, ƙaskanci kuma ta hau layi. Duk da ko sanda take gidan naka sharar gidanka ta fita kima da daraja. Sabuwa naci nasarar rabaki da yaranki da Babangida. Saura nasara ta gaba ɓalɓanta yaranki da kuma damejin ƙwaƙwalwar Mardiyya da sannu zata san cewar wannan gidan bana ubanta bane, ƙannenta ba nata bane, uban da take taƙamar itace babba a wajenshi ba nata bane." Ƙaran wayar Babangida daya ajjiye a kujerane ya katse ma Ƴar Shuwa saƙarta da mugun zare wanda take ta saƙawa a zuchiyarta. Ganin sunan Sumy yasa ranta ya ƙara yin matuƙar zafi. Agogo ta kalla ta girgiza kai. "Lallai wannan yarinyar sai na saisaita mata hankalinta. Sha ɗaya da rabi na dare zata kira magidanci sabida iskanci bayan jibi za'a ɗaura auren ma" Tana cikin surutanta Babangida ya shigo falon ɗaure da tawul a ƙugunshi. Shagala kawai tayo wajen kallonshi Allah ya jarabceta da wata iriyar soyayyar Babangida tun a haɗuwar farko da suka yi. Amman shima sai ya nufo wajen sabuwa kamar dai yadda Khalid yayi mata. Kuma fa duk abinda shi babangidam zaiyi mata soyayyarshi rufe mata idanu take yi wannan itace ƙaddararta ta yadda. Domin daga lokacin da Babangida ya talauce ta gane Babangida ne ƙaddararta. Gashi shi yana da wasu matan bayan ita, dama karuwan da bata sansu ba na waje masu juya ƙwaƙwalen mazajen wasu abar matan gida da cizon yatsa. Ko tayi yinƙurin son barin gidan sai taji inta bar Babangida kamar rayuwarta tazo ƙarshe ne. Har ya ƙaraso inda take bata sani ba ta yi zurfi a tunani. Gira ya ɗaga mata. "Bani wayata nasan Amaryace tayi kira." "Amarya ko karuwarka ba. Ƴar iska ya za'ayi ta kiraka a irin wannan daren in ba ka nuna mata mu matan gidan bamu da wata daraja ba tama isa?" Wayarshi ya fisge ya wuce daining ya zauna yana daddannawa. Daidai Ƴar Shuwa ta karaso zata zuba mishi abinci ita kuma Sunmy ta dauki wayar. "Hello Amaryar Babangida har yanzu baki yi bacci ba ko dai ɗokin gobe zanzo ne ya hanaki bacci?" Wannan maganar a iyakar fatan bakinshi kawai ta tsaya ita kanta Sumy tayi mamakin furucinshi ballantana yar Shuwa da take tsaye tana ji tamkar ta danneshi ta karɓe wayar ta dankarata da ƙasa. Sai dai shi yaƙi ai ɗan zamba ne. Tananan tana jiran shigowar Sumy tayi alƙawarin saita raina kanta kuma bata isa ta wuceta a zuchiyar Babangida ba. Murmushin takaici kawai tayi ta zuba mishi abincin ta ja kujera ta zauna tana fuskantarshi sonshi na cin ƙasan zuchiyarta kamar son Babangida zai halakata haka take ji. Gashi talaucinshi ya gama isarta Mamansu ma sai lokaci take bata na kaso auren, in ta yinƙura sai taji ina ba zata iya ba. Mrs Bukhari

Tabb ko yaya zata kasance dasu Gaza masu zuwa ɗebo kaya oho [8/22, 11:42 AM] BADA'AT IBRAHIM: https://chat.whatsapp.com/EEK9H2V5iSOFXz0Xud5Eox?mode=ac_t Yar uwa ta, kin dade kina neman in da zaki samu nighties da lounge wears masu musulmin kyau, saukin farashi da kuma kyan gani? 😍 To ki daina nema! A thrift bae closet, mun bude exclusive group inda za a dinga kawo thrift nighties, lounge wears da sauran su masu kyau, kamar Sabbi kuma farashinsu abin mamaki ne, very affordable 🤩.

A nan ne za ki kasance cikin na farko da za su ga sababbin kaya kafin su kare. Idan kina son kada ki rasa mafi kyawun kaya kafin a sayar da su gaba ɗaya, to shiga cikin group ɗin yanzu kafin ya cika 👇 https://chat.whatsapp.com/EEK9H2V5iSOFXz0Xud5Eox?mode=ac_t

IDAN KAYA YA GAJI.. GAMMO MA YA GAJI LITTAFI NA UKU SHAFI NA GOMA SHA BIYAR

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull