Kenza eBookz

Ina tare da ita novel - Chapter 4

Ina tare da ita novel - Chapter 4

Ina tare da ita novel Chapter 4: Ina tare da ita novel Chapter 4. ******* Yau Yakama sat day week end kowa na gd a babban parlourn gdn suke kowa da kowa…

4,322 words

******* Yau Yakama sat day week end kowa na gd a babban parlourn gdn suke kowa da kowa sbd abbune yatarasu zaayi family meeting ,yyinda abbu ke zaune kusada Abba abdullah sai mm zulai da Ummi suma suna Jere yaran gdn tun dg yah Suleiman zuwa Fatima suna zaune kan carpet.. "bayan anbude taro da addua " abbu yyi gyaran murya yace to masha ALLAH naso ace Ibrahim na nan zaayi taron nan amma bbu damuwa tunda sunkusa dawowa Nigeria, kuma zansa nardashi komai game da taron." Amatsayina na uba ga kaf din yaran gidan nan ,na yanke hukuncin Yusuf nabashi auren zubaida ,yaseer nabashi Habiba ,Usman nabashi Fatima ,Habib nabashi Rukayya ,sadeeq d Muhammad da basa kasar duk da yarane to suma zan zab'a musu acikin yaran dangi,sannan Usman d Habib sai nan da shekara k'ila ma da wani abu sannan ayi auren lokacin sun ida karatunsu nadai fadane ko bayan raina acikamin Burina....mm zulai bata bari ya idaba cikin gadara tace gsky wannan hukuncin be munba to shi Suleiman wa zaya aura kenan?"

To gsky shiyaka mata ya auri zubaida inkuwa b hakaba to gsky yaranmu bazasuyi biyyayaba....Abba abdullahi yace kwarai kuwa gskiyarki....duk mutanen parlourn sunyi mamakin mm zulai ciki harda yaranta akan zak'ewarta yyinda yah Suleiman yaji kamar yatashi yyita jibgarta ....shikuwa yah Osman murna fal aransa dan dama wlh fatimace azuciyarsa kawaidai bai fad'a kuma bai nunaba...shikuwa yah Yusuf kuwa fuskar nan tasa amurtuke dan yyi alkawarin muddin itace matarsa sai ya saita ta yakoya mata hankali...muryar abbu sukaji yana cewa gsky kunyi daidai kaida ita matar taka to bari kuji Suleiman Ibrahim yabashi iftihal tun washe garin sunanta yarubuta takarda kobayan ransa iftihal bata mini sai Suleiman saidai ko in cikinsu wani ya mutu dan haka ni yanxun bazanmasa aureba abarsa yaji d damuwar rashinta dan yimasa aure yanxun wani kara masa damuwane dan insha ALLAH inaji ajikinsa duk runtsi iftihal sai tadawo ,koda nan gaba in yabukaci aure sai amasa intadawo sai ya aureta....afusace mm zulai ta ce hmmmm ta tsuniya kenan kukunada tabbacin zata dawo ne da zaace haka kawaidai dan anga ubanta nada kudi shiyasa zaa ce shizai aureta ......yaseer yyi zunbur yace nidai gsky Fatima nikeso...wata tsawa yah Suleiman yyi masa idanunsa duk sun rine yanakokarin nufar yaseer Ummi ta rikesa tadawo dashi kusa da ita...

"Afusace abbu yace abdullahi! abdullahi!! abdullahi!!!"

Wlhy! Wlhy!! Wlhy!!!

Kai na rantse maka ko?"muddin dg kai har yayanka bakubi abinda naceba to zakubar gdn nan zan karbe duk wani abu nawa Dana mallakamaka..

Kabani mamaki Ashe kai soko ne mijin tace ,har mace ta isa tasaka kamun rashin kunya itama tamun agabanka d yaranmu lallai har kabi bayanta hmmm ita bata isa nayi musayar kalamai da Ita ba sai dai inaso kusani dg kai har ita duk Wanda yace gonar wani bazatayi kyauba to wlh tasace bazatayi kyauba....

Kuficemun dg nan kuduka na sallameku INA sauraron abinda ka zab'a ko kabar gdn kokamun biyayya, yana fadin hakan fuuuuu yafice afusace yinda Ummi itama tabiyosu tana rike d hannun yah Suleiman dan gudun kada yyi ta'asa tasansa d zafin zuciya. "

Abba kuwa shiru yyi dan maganganun Abbu sun shigesa ,yyinda mm zulai sai cika take tana batsewa tana surutai had'e da kokarin yiwa Abba mgn tsaki yyi had'e da ficewa nan duka yaran suka fara fita .

Yah Yusuf ne dke kokarin fita yakalli zubaida yabanko mata harara had'e d kallon tsana yace keeeeee!"

Atsorace tace ma'am "yace kisameni apart dinmu"

Bejira amsartaba ya fice yyinda afili tace oh ni zubaida ta wa tasameni ,gsky zanyi wa mama mgn kada ta bari ayi auren nan wlh k'ila kasheni zaiyi sbd tsana..

Nan kowa d kowa aka watse dg taron."

***** ***** ***** Wata kyakkyawar yarinyace yar kimanin shekara 14ce rike d tulu ahannunta wani saurayi dan kimanin 20years na gefenta suna tafiya ,kyakkyawa ne bafulatani abbas ke nan Wanda yake karatu a birni duk week end yake zuwa k'auye ,Wanda inba bakasaniba bazakace dan kauye neba..

Kurama yarinyar ido nayi ganin irin kyawunta ,Ashe wai iftihal ce(nah nah)duguwa d ita amma bacanba dukda gsky tafi d kyau Wanda yasanta ada to bazai ganeta sbd kyawun data kara uwa uba kuma ilimin addini dn boko dan yanxun ss2 take kuma yah Abbas nakoya mata lasson dan haka take kiransa kuma suna soyayya dashi dUkda tanajin kunyarsa,dan mutanen kauyen casuke ai saidai ta auri Abbas sbd suna ganin shi Dan bokone batason marar ilimi kuma suna ganin tanada girman kai dan bata kula kowane namiji dasuke tururuwar cewa suna sonta..

Tafiyarsu suke suna fira akan karatu saidai Abbas yalura bbu walwala afuskarta .

"Ahankali yace my sweet heart meke damunki pls ?"

Cikin damuwa tace wlh inna ce bbu lfy tun farkon satin nan har xuwa yanxun gashi tayi kumburi duk jikinta komai sai antaimaka mata takeyi dan ma baba atine yanxun tana gdn tunda mijinta yarasu..

Cikin al'ajabi yace oh subhanallahi "

ALLAH yabata lfy ,kiyi hkri kita mata addua kinji?"nima zan tayaki adede nan suka iso k'ofar gidan mlm..

Sai kokari yake sunada ido d ita amma taki,ahankali yace hmmm zanciremiki wannan kunyar taki ....kafin tayi mgn mlm yafito ,cikin jin kunya yah Abbas yaduka yagaidashi ,ya amsa cike d kulawa fuska asake...

Mlm yakalli nah nah yace ...

Share..

📚📚mmn fareesa ce✍🏻✍🏻[3/19, 6:08 AM] Itz B Y ebrerheem:AWESOME WRITER'S ASSO..🏮

(palace of excitation and pleasant writer's)

INA TARE DA ITA ! 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾 (bansan ita bace) 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾

Story &written by mmn fareesa

🅿25&26

NOT EDITED

Mlm yakalli nah nah yace y'ar albarka kindawo?" Tace eh Abba nadawo"murmushi yyi yace to sannunku kunji...cikin jin kunya Abbas yace yauwa mlm yakoma cikin gdn." Sallama sukayi ta shige ciki da tulunta dkeda ruwa,bayan tayi sallama tasamu inna d baba atine zaune kan tabarma sai mlm kan kujera y'ar tsugunne ,Jidda nagefensa yarinya y'ar 10 Years. bayan ta juye ruwan tadawo tanama innarta sannu da jiki..inna ta amsa had'e da saka mata albarka." Mlm yace gsky zuwa jibi zamu tafi birni akwai wani mutum Dana karantar dashi to Dr ne munyi waya dazun agunyin waya yace mun muje abuja ayimata aiki...bb atine tace ikon ALLAH hakanma yyi gsky ALLAH yasa adace! Mlm yace ameen" Nah nah tace oh Abba yanxun jibin zaku tafi kenan?" Yace eh wlh kinga ki kwantar da hankalinki kinji?" bamu wuce sati3 ko wata 1 mudawo "kuzauna dkeda k'anwarki d atine kinji y'ar albarka? Nan tace to tana jin tausayin mahaifiyar tata"..

******* Yah Suleiman ne kwance kan bed din sa rigingine pic d'in angel insa na a hannunsa".

" ahankali yace pls my angel kidawo gareni mu rayu dke wlh namiki alkawarin kulada ke tamkar raina...yafad'a hawaye masu zafi na zuba afuskarsa.

Dan tunda aka gama meeting yashigo bed room din zuciyarsa acinkushe ,wani gefen kuma so,had'e d kaunar daddy Ibrahim yaji wato Ashe tun tana jinjirarta yabashi ita.

Share hawayen sa yyi yashiga lissafin shekarun iftihal yaga harta haura 14years tuni yashiga yin gumi sbd yadda gabansa yafadi fatansa ALLAH yasa ifteenshi bata mantashiba.

"ga wani mugun kishinta daya taso masa " dan yasan yanxun ta isa wani yace yana sonta oh ALLAH dai yatsare masa ita...

Addua yyita yi dg nan bacci yyi gaba dashi.""""

Zubaida kuwa tunda yah Yusuf yace taje jikinta keta kirma ,tasan muddin inbata jeba kashinta yabushe.

,,,atsorace ta nufi part d'in su ,dakinsa ta nufa ta murd'a k'ofar had'e da yin sallama har sau3 ana3 ne ya amsa...jiki na rawa ta shige ,zaune tasamesa kan bed g lop top agabansa yana latsa....doguwar tsuka yyi had'e da cewa ke wawiyar inace ?"zakimun tsaye bisa kai"hmmm koda yake k'ila dan kinji abbu yace yabanike sadaka shiyasa ko?"to wlh yarinya zaki gane bakida wayo indai nine ."

Oya kije inner wear's dina da jallabiyoyina na jike atoilet ki wankemunsu Ta's,zaki wuce ko kuwa?"

Yafada cikin tsawa ,jikinta na bari sum sum ta wuce ,tafara aikinta ,azuciyarta tana zaginsa da ganin muguntarshi ,amma dole ta janyewa auren yah Yusuf inba hakaba kuwa tana tare da wahala..

Yana nan kan bed ta fito "ahankali tace yaya!tsaki yyi yace inajinki ,nagama ne dama ,yace ok kije kiwanke toilet din. dan murguda baki tayi ganin baya kallonta tace to pls zanje gun kamun friend dita..wani mugun kallo yamata had'e da cewa ke xonan!

Hakuri tafara bashi,tsakiyyi yaisa gunta yad'auketa d mari gigitacce ...tasaki k'ara had'e da dafe kuncinta...cikin jin haushin ta yace kamun gidankui!bazakiba sakara kawai duk ranar da naganki gdn nan bbu hijab hmmm wlh kinsan saura ,maza kixo kimun kamun kunne .

Kuka tasaka tana bashi hkuri, kallonta kawai yyi beyi mgn ba jikinta na rawa tazo ta yi ,bece tabariba said a yaga takusa suma tukum yace tatafi.

Aranar d ciwon kai zubaida ta kwana mm zulai kuwa ta tsinewa yah Yusuf yafi akirga ,kuma tasha alwashin bazata bari ayi aurenba kota halin k'aka..

Bayan kwana,2 ***** ***** ***** Ayaune mlm d inna kuluwa suka bar kauye sbd zuwa asibiti anemata lafiyarta.

Nah nah ce da Jidda zaune suna cin abinci, bb atine na gefensu " ahankali tace dan ALLAH nah nah inkun k'are cin abincin kije kidebomana ruwa asola"nah nah tace to baba ai mungama bari na wanke hannu.

Nan ta tashi taje ta wanke hannunta ta d'au tulunta ta nufi gun solar.

Tana a hanya taga Dije k'awarta itama can zasu,maganar jamaa d tafiya sukaji abayansu ,Dije ta waiga yatsine fuska tayi tace hmmm wlh mai garine d jama'arsa mu basu hanya su wuce kafin su ida isowa d alama ta nan gun zasubi dan nasan gd zashi...itadai nahnah batace komai ba ,suka tsaya gefen wata bishiya yyinda mai gari mamuda d jamarsa suka tafo dan wucewa...saidai me kamar ance nah nah tad'ago kawai sukayi ido 4d mai gari yyata kuri d ido yanata kallo kamar zai cinyeta..

Tuni Dije ta lura ,suna wucewa Dije tace oh kinga wannan tsohon najadun yana ta kallonki to ALLAH dai yasa kada yace sonki yake dan xai iya wlh tunda haka yake bbu abinda ya iya sai auren yara jikokinsa bbu jimawa inyaga wata yasaki wata ya aura..

Zaro ido nah nah tayi tace oh to nidai wlh kwalelensa ALLAH yakiyaye tsoho dashi ina yarinya na auresa...adedenan suka iso gun dibar ruwan,nan kowace ta diba ta nufi gd...

Mai gari kuwa suna wucewa yasaka sallau babban yaronsa ya binciko masa wacece wannan yarinyar..

Haka kuwa akayi yazo yasanar dashi ai y'ar mlm.Haruna ce kuma baya gari ,amma ai habu yayansa na nan,mai gari yace akira masa baffa babu.

Aiko sallau yaje har gdn baffa habu yace yazo Mai gari na kiransa,cikin fad'uwar gaba yace ALLAH yasa banyi laifiba?"

Sallau yace ah ah alkhairi ne muje dai.

Bayan sunje mai gari sai nan nan yake d baffa habu ,nan suka gaisa.

kai duke mai gari yace dama dalilin kiranka.....

Share..

📚📚mmn fareesa ce✍🏻✍🏻[3/19, 6:08 AM] Itz B Y ebrerheem:AWESOME WRITER'S ASSO..🏮

(palace of excitation and pleasant writer's)

INA TARE DA ITA ! 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾 (bansan ita bace) 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾

Story & written by mmn fareesa

Banida bakin godiya ga masoya wannan novel naga comments bbu adadi agrps daban daban d PC kuyi hkuri darashin reply mutane sunmin yawa ngd sosae mmn fareesa natare daku duk wuya..🤝

wannan page din nakine kawata ta kaina my safeenah kiyi yadda kikeso dashi kinfi kowa son INA TARE DA ITA!😍😍

🅿27&28

NOT EDITED

Kai duk'e mai gari yace dama dalilin ki ranka shine naga y'ar k'aninka tamun to ance baya gari kuma ba yanxun dawowarsaba." Ajiyar zuciya baffa habu yyi yace hakane ranka shi Dade....mai gari yace nikuma gsky inason na aureta asatin nan yaya za ai?"baffa yace eh to ko kabari ubanta yadawo tukum" Mai gari yace gsky nafiso ayi yanxun kuma duk abinda kakeso nabiya yanxun zanbiyya shi .....d sauri baffa yace to to to aibbu komai kabada komai aina isa da ita ko ubantama balle ita " fuska awashe mai gari yace to madallah,nan yafito da damin kudi yabashi yace nasada kine da Neman aure.. Sannan yafito da wasu yace gashi wannan nakane bbu damuwa zanma kara maka wasu burina ta amince d aurena.....cikin zakuwa had'e da had'ama baffa yace bbu komai dolenta ma ta amince tunda batada wani uba ayanxun bacin ni ,yafada had'e da saka kudin cikin aljihu yace rana eta yau zaa d'aura muku aure d ita,cikin jin dad'i mai gari yace to shikenan jibi zanxo tadi gunta sai natambayeta me take so?"sai inbata kud'i ko?"azuciyar baffa yace nikuma na karbe dan bazan bar banzaba wlh dan wad'an nan kudin cima raina zanyi kuma nima nakara auren dasu..afili yace to shikenan sai jibin amma gdna zaka sameta kuma kazo d marece " Mai gari yace to bbu damuwa ,nan sukayi sallama yayinda baffa yakudurta gobe zaije yasanar da atine kota yarda ko karta yarda,kuma yatafo d nah nah takoma gdnsa da zama har ayi auren..""

********

Ummi ce zaune da su Fatima Auta da Habiba suna break a dining area, Fatima ta ce nidai gsky Ummi in yah Usman baya sonafa? "Murmushi Ummi tayi tace hmmm yaro kenan ai duk cikinku bbu Wanda naji dad'in hadnsu kamar keda Usman dkuma iftihal da yayanku, ALLAH dai yabayyanata... Ameen sukace baki d'aya, amma wlh banso hada Habiba d yaseer ba sbd halinsa ,amma kuyita addua nima zantayaku dan had'a zuria d zulai bawani abun jindadi bne..amma har gobe ina godiya ga daddynku d mommy sun nunawa zuria ta so d k'auna shiyasa naji dadi da zaku auri jininsa...Habiba takatse mata mgn da cewa nidai gsky Ummi banason yah yaseer acanjamun d...sallamar yah Suleiman ce ta katse mata mgn ,shigowa yyi fuska bbu walwala da kakinsa ajikinsa na sojoji yyi masifar yin kyau,dukawa yyi yagaishe d mahaifiyarsa yayinda kannensa suke gaidashi ya amsa atakaice". Ummi yakalla yace dama yanxun zantafi can wani k'auye gaba da kauyen KALGO anturamune dg office sbd bbu tsaro agurin, yan fashi natare fatake...zanyi kwana2 insha ALLAH ,bayan gurin yyi yadda akeso zan komo gd...murmushi Ummi tayi tace to babana ALLAH yatsare yabada sa'ar abinda akaje yi,yace ameen fuska asake alamar yaji dad'in addu ar ta.. Nan kannansa sukayi ta masa fatan isa lfy nan yafice dg parlourn yanufi parking space yashige motarsa yabar gdn..

Bbu jimawa da fitarsa abbu yashigo yasamu Ummi itada yara dan yau week end ,tashi sukayi suka basu guri ..

"Abbu yazauna gefen Ummi " ahankali yace hmmm ai abdullahi yazo jiya d dare yabani hkri kuma yace ya amince d umarnina!"Ummi tace to alhmdllh "abbu yace na hakura saidai matarsa nagama yimata wata kyautatawa tunda batada mutunci d tarbiyya ...Ummi tace ah ah alh kayi hkuri dan ALLAH" tsaki yyi yace hmm ALLAH yahad'a abdullahi d shu'umar mace wlh yaran nan banhadasu d junansuba saida naga sun dace kowa saida nayi tunani sannan nahadasa da wacce nike tunanin kobajuma zasu fahimci juna...kinga kamar Yusuf na lura da zubaida natsoronsa gashi itama bataji,uwarta ta batata...nasan dole yasaitata.Ummi tace hakane wlh alhj "yace to kinga ma yaseer bayaji ,Habiba tanada hakuri duk yaran gidan nan batada fushi nasan shima da yardar ALLAH zata saitashi...

Ummi tace to muyita cigaba da addua dai kawai" abbu yace insha ALLAH..

******* Washe gari d marece baffa ne tafe gdn mlm Haruna ,bayan yyi sallama yasami atine na tace kullin koko,cikin faraa suka gaisa yazauna,bbu boye boye yazaiyyane mata yadda sukayi d mai gari d kuma zsitafi da ita gdnsa yau dan gobe mai gari zaixo tadi agunta...yafad'a had'e da mikowa atine dubu2 wai natane...

Atine datacika d mamakin baffa dakin son gskyarsa tace hmmm yaya kenan ka rike kudinka samaka amfani...saidai inaso kabani banyardaba ka aurawa mai gari nah nah bacin ubanta bayanan,Wanda ko yana nan inada tabbacin wlh bazaibawa mai gari y'ar saba ...kaiko ninan dakake gani ko?"

To wlh bazanso mai gari ya aureniba balle ita yarinya d'anya sharaf d ita inyaci moriyar ganga ya yada kwafranta to wlh das......wani wawan mari baffa yayiwa atine cikin zafin rai yace ungu nan yana mata dakkuwa yace to wlh ba ki isaba nabiki ta lalama zakimun rashin kunya ko?"

Ayanxun kuma agabanki zantafi d ita kiyi abunda kika ga dama amma inkin'isa...

Atine dke rik'e da kunci tace bbu abinda zanyi dan bani da iko saidai inaso kasani akwai ALLAH yanaji yana gani....baffa be saurareta ya yaye labulan dakin yakalli nah nah dke ta kuka jin za'a rabata d yah Abbas d'inta, cikin tsawa yace zaki tashi muje ko kuwa? "

Bbu musu ta ta shi tasaka hijab tabisa ,suka fito ,takalli atine dketa kukan tausayinta ,tace baba atine sai wata rana !tafada tana hawaye yayinda baffa ko ajikinsa..yyi gaba nah nah tabisa suka fice dg gdn yyi da atine keta kuka Jidda natayata..

Haka kuwa akayi baffa yakaita gdn ta zauna atakure gaba d'aya taji duniyar ta fitar mata arai "taci alwashin gobe saita ma mai gari abinda baya tunani..

Washe gari bayan sallar la'asar mai garine tsaye asoron gdn baffa habu ,yaci wata uwar malun malun sai zufa yake bakinnan duk goro,yayinda yaransa ke k'ofar gd..yanajiran xuwan nahnah dan yasaka akirata, azuciyarsa cayake ALLAH yasa tasoniiii" sallamar ta yaji tuni ya watse hakoronsa yellow yana dariya Shiga masoyinta ....shiru tayi batayi mgn ba kanta aduke yayinda yyi mata kuri d ido yana kallon baiwar kyawunta yana hadiye yawu...afusace ta d'ago had'e da bankomasa harara tace mlm zantafi inbakada abun cewa"

Murmushi yyi yace nazomiki daso da kauna...tsaki taja tace ALLAH yakiyaye dg yau zakayi nadamar cewa kanason wata yarinya ak'auyen nan kafinyyi mgn tafasa ihu iya karfinta tana cewa wayyo ALLAH jamaa kukamun dauki...tayiwuf ta matsakusa dashi hade da kece hijab d'inta dg gaba....baki bude mai gari ke kallonta kafin yyi mgn mutane sun cika zauren yayinda nah nah keta kuka harda hawaye...kasancewar ansanta kamilace tuni jama'a suka yarda aka hau ihu da tir da halin mai gari,ita kuma ta shige cikin gd yanajin dadi sumsumasunyi mamakin mai gari..

Shikuwa,mamakin ,kunya,nadama ,hade d danasani yyi yisu bbu addi yadauki alwashi sai yacima baffa babu mutunci yanxun ba anjimaba tunda yasan yarinyar batada mutunci ya yarda zaibashi ita..

Cikin jin kunyar mutane yanufi gd yasa aka kira masa baffa babu akasuwa..

Bayan yazo yyi masa zafin kare had'e da cewa yakamasa kudinsa dayabasa tunda yarinyar batada mutunci harta iya masa sharri d girmansa d komai agari..

Afusace baffa yanufi gd yasamu delu na isa wutar sanwar tuwo g muciya a hannunta,cikin bacin rai yace ina y'ar iskar yarinyar nan take?"

Delu ta tab'e baki tace hmm tana daki wai mai gari ne zai mata fyade sai kururuwa take ta Tara masa jamaa,ni wlh ban yardaba..baffa yace Karya take wlh yakirani yatozartani gaban jamaa harda cemun tsohon banza ,dan haka itama zataji ajikinta nan yakwala mata kira!

Delu tace ai Maimuna tayarda(kishiyarta)sai wani sannu take mata ,tski yyi yace ina maimunan?"tace ai batadade d tafiya kauyeba kasan can zatakwana gun sunan "yace itama zata dawo ta karbi hukuncinta....adedenan nah nah ta fito ,afusace baffa yafisgi muciyar hannun dela yabuga mata aka iya k'arfinsa yasake atake ta fadi gurin bata numfashi kamar matacciya dan ba suma bace yyinda kanta yafashe yana jini..

Zaginta yacigaba da yi ,saidai me?" Yarud'e ganin bata motsi,shida delu suka duba ,baki bude delu tace oh mlm Kodai mutuwa tayi?"arikice yace ina tunanin hakan....arude tace meye abinyi ?"

Waigawa yyi yace jeki rufe gdn tunda bbu kowa bbu musu taje ta rufe tadawo tasamesa yakaita dakinsa yarufe da buhu sai zare ido yake yace delu kirufamun asiri dan ALLAH tace lahhh bbu komai wlh bbu Wanda zaiji .

Gobe cikin dare kasata abaro ka kaita karshen gari can bakin titi ,maana kafitar d ita dg garin nan ..

Da safe sai auren dole...muce ta gudu sbd zaamata auren dole,,,cikin murna yace yauwa ngd sosae matata ALLAH yabarmu tare...tace ameen..

Haka kuwa akayi d asubar fari yaje yakaita ya yasar da ita ya nufo gd bebari aka gansaba...

da safe gurin 10am yah Suleiman ne tafe zaya gd sai gudu yake sbd bayaso azahar tayi masa ,saidai tundg nesa yaga kamar mace kwance gefen titi...har ya wuce kuma yadawo dan yaga ba irin macutan nan neba da ake hada baki dasu acuci mutumda su..

Parking yyi yafito....

Share..

📚📚mmn fareesa ce✍🏻✍🏻[3/19, 6:08 AM] Itz B Y ebrerheem:AWESOME WRITER'S ASSO..🏮

(palace of excitation and pleasant writer's)

INA TARE DA ITA ! 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾 (bansan ita bace) 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾

Story &written by mmn fareesa

Dedicate to all my fans😍

🅿29&30

NOT EDITED

parking yyi yafito"ahankali yanufeta "saidai me?" Yana kallonta yaji wani mummunan fad'uwar gaba Wanda baisan dalilinsa. Matsawa yyi gab da inda take kwance fuskarta na kallon Gabas"yakalleta yaga bbu alamar numfashi atare d ita kuma yasan ba mutuwa tayi ba dan da tafara warii" Yatsina fuska yyi ganin bbu kowa mutane nata wucewa amota har yajuya ...wata zuciyar tace hmmm kataimaki me bukatar taimako !afili yace bansantaba!tunawa yyi da my angel dinsa ,shin in itace awannan halin ba'a taimaka mata aibazaiji dadiba..da azama had'e da karfin gwuiwa yabude gdn baya yatattare hannun rigarsa yazo ya sungumeta yasakata yakoma gdn gaba yaja motar."azuciyarsa yana tambayar kansa me yafaru d yarinyar nan?"ya'akayi taji rauni haka?"dg gani yarinyace gsky...wata zuciyar tace kakaita hospital kawai... Hakafa yah Suleiman yyita sharar gudu cikin awa 2d Rabi suka iso Kd basu tsaya ko inaba sai hospital, bayan yyi parking yafito yashiga ciki bbu jimawa suka fito d nurse akayi emergency d iftihal yyinda yah Suleiman yawuce masjeed,bayan yadawo yyi zaman awa2amma shiru bbu Dr d'in da yafito Ji yyi yagaji da jira tashi yyi yaje yyi sallar la'asar yadawo shiru...can saiga wata nurse zata wuce sai kallon kurullah takewa cpt Suleiman ,shikuwa yana ganin hakan yatamke fuska....cikin iyayi tace sannu ko!banza yyi d ita "ahankali tace kayi hkuri naga tunda aka shiga d patient d'in ka basu fi....wani mugun kallo yyi mata ." Atake taji yamata kwarjini ...adede lokacin kuma Dr jabeer yafito duk yyi gumi d wasu doctors yakalli cpt Suleiman yace kasameni a office. " Cpt Suleiman ya juya had'e da tashi cikin nutsuwa ya nufi office din Dr din yyinda nurses dinketa jin inama ace wannan gwarzon nmjin nasune..lolx

Bayan ya zauna Dr yacire glass din dke fuskarsa yace gsky akwai matsala babba da yarinyar nan!cpt yace wacce matsala kenan?" Dr yace Kaine yayanta ko mijinta?" Yatsina fuska yyi had'e da yin kicin kicin d rai yace meyasa kamun wannan tambayar ne?"Dr yace hmmm sbd dole sai su zasu sani ne...shiru yyi can yace ok ni yayantane yatsinci kansa da fadar hakan ...saidai kuma yaji haushin fadin hakan dayyi,Dr yace to gsky yarinyar nan dukane aka mata ba nawasaba akai! Wanda sanadin hakan tayi loosing memory d'in ta...inna lillahi wa inna ilaihir raju un kawai cpt Suleiman ke maimaitawa ...cikin damuwa yace meye mafita Dr?" Dr yace to agsky da wuya kuma bbu wuya"?yace kamarya?"Dr yace eh to indai yanxun ko wani lokaci kadan nan gaba taga Wanda tasani ko tashak'u dashi to zata dawo normal ta warke ...inkuma bbu Wanda tasani harta gansa to gsky sai tajima ta warke !amma zamu azata kan magani ina fatan kafahimta?" Cpt yace eh to yanxun ciwon dke kanta fa?Dr yace munyimata dinki kuma insha ALLAH nanda 2days zai warke indai yasamu kula dukda naga fatarta mai kyauce zata yi saurin warkewa indai ana kula d ita sbd ciwon yanason kula dan yanxun itafa tamkar jinjira take sai abinda a ka nuna mata zatayi...cikin wani yanayi cpt yatashi tsaye yace bara naje gun cashier nabiya kud'i na wuce gd kafin ta farka,Dr yace ok ,,,,

Bayan yagama biyan makudan kudin da aka rubuta masa yawuce gd.

A parlour yasami ummy tana shirya diner dan lokacin 5ta gota...zama yyi yana gaida ita ,amsawa tayi had'e da cewa oh babana shiru sai yanxun tun karfe2:pm niketa dubar hanyarka amma shiru sai yanxun lfy dai ko?"

"Yace lfy lau wlh watace na taimaka....nan yasanar da ita komai game da ita harda loosing memory d'in datayi...cikin tausayi Ummi tace wayyo ALLAH amma natausaya mata komaiye dalilin hakan?" ALLAH masani"

Cpt yace eh anjima zan koma kihada abinci saina kai mata ko?"Ummi tace to amma dan ALLAH babana ka bits ahankali tunda ance kamar jinjira take nasanka d zafin zuciya "ALLAH shixai baka ladar tunda danshi kayi ,amma saika daure d'a duk nakowane in ALLAH yasa ta warke sai a sadata da iyayenta ko?"

Ta shi yyi yace to Ummi zankiyaye yafice dg parlour part d'in su yawuce yaje yyi wanka had'e da yin arwallah .

Bayan yafito yashirya cikin suit farare sai kamshi yake zabgawa yyi masifar kyau ,masjeed ya wuce bedawoba saida akayi isha'i Gun Ummi yanufa yasamu ta had'a masa komai a basket,abbu na gefenta yana dinner, nan yagaida abbu,anan yake jajanta masa dan Ummi ta fada masa kuma yamasa nasiha akan yabi y'ar mutane ahankali banda hantara..

Fuska bbu walwala yadauki basket din yafice ....axuciyarsa yanajin haushin yarinyar sai wani cewa ake yabita ahankali shifa gsky bbu dole ...wata zuciyar tace kada kazobe ladarka !kayine dan ALLAH..

Ahaka ya iso asibitin straight office in Dr yanufa yasameshi zai fita, nan suka gaisa Dr yace oh shiru shiru baka dawoba sai yanxun amma acikin wannan lokacin zata farko insha ALLAH "cpt yace to ALLAH yasa.

Dr yace dama gd zani room8 ne room dinta na cire mata drip magunguna nanan bayan taci abinci tasha ,amma katabbatar kamata brush ,kuma tea ne zata fara shaaaa.sbd hanjin ya warware"

Cpt yadan yatsina fuska yace ok amma ni gsky bbu brush aguna Dr yace akwai a toilet sabo ma "yace ok yana niyar tafiya... Dr yace amma kai zaka kwana d ita ko ?" Cikin kosawa d maganarsa yace ah ah menene?"yace to ai gsky kasamu wacce zata kwana d ita da matsala abar patient ta kwana ita d'aya..

Wani haushi cpt Suleiman yaji wai shizai kwana gunta kenan?"

Cikin jin haushi yabar office in saidaifa Dr yafara zargin anya wannan hadadden sojan y'ar uwarsace..

Cpt na fita yanufi room 8saidai besan dalilin dayasa gabansa faduwaba kawaidai yatura k'ofar yashiga.

Maida k'ofar yyi yarufe bayan yashiga...

Share...

📚📚mmn fareesa ce✍🏻✍🏻

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮

(palace of excitation and pleasant writer's)

INA TARE DA ITA! 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾 (bansan ita bace) 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾

Story &written by mmn fareesa

🅿31&32

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull