Kenza eBookz

Kamar da wasa complete novel - Chapter 1

Kamar da wasa complete novel - Chapter 1

Kamar da wasa complete novel Chapter 1: Kamar da wasa complete novel Chapter 1. [11/28, 08:14] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO.*_

3,363 words

[11/28, 08:14] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO.*_

*KAMAR DA WASA....!* 💖

_*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI._

*1*

"Masu sauraro kamar kullum anan shirin namu zai dasa aya ayau kun dai ji mun tattauna akan wata babbar matsala wato ta yadda zakaga saurayi da budurwa sun kwashe shekaru suna gudanar da soyayya amma abin haushi arabu batare da anyi aureba shin laifin waye? Mazan ko matan? kafin inyi sallama daku ina mai janyo hankalin masoya da arike amana, gaskiya da kuma kulawa sannan aguji karya da yaudara domin hakan ba abune mai kyau ba sannan daya daga cikinsu yana raunata soyayya kuma ya illatata, anan zanyi sallama daku sai Allah yakaimu sati nagaba inda zaku jini acikin wani sabon shirin naku mai farin jini wato *Sakon na masoya ne...* kamar kullum nice taku mai gabatar da shirin wato *BILKISU LUKMAN ALIYU* Nabarku lafiya...."

Ahankali yake zare earpiece din dake kunnenshi sakamakon jin wakar _Sulken so...._ ta maye gurbin zazzakar muryarta, cikeda takaici ya kifa kansa asaman keken dinkin da yake zaune akai yana dinka wata kyakkyawar doguwar riga ta mata, tunani yake aransa yanzufa shikenan bazai sake jin muryarta ba sai wani satin indai ba shirye shiryenta na baya wadanda yayi recording zaiji ba domin hatta wannan wanda ta gabatar ayau ma yayi recording dinshi yana nan ajiye cikin wayarshi. Babu zato babu tsammani yaji wani abu saman sumarshi mai kamada almakashi, hannu yasa domin yakamo abin amma yaji anjanye ahankali yabude lumsassun idanuwanshi yatashi zaune, kamar yadda yayi zato husna yagani tsaye sai faman yi masa murmushi take, maimakon ya mayar mata da martanin murmushin da take yimasa sai ya daure fuska kamar ta kawo masa sakon mutuwa.

Bata damuba tabawa kanta masauki da wata kujerar roba wadda ke ajiye agaban keken dinkinshi, bata damu da yanda sauran abokan aikinshi wadanda ke zaune akan kekunansu suna gudanar da ayyukansu yanda zasu dauketa ba domin idan da sabo tasaba, zama tayi ta tallafe kumatunta da hannuwanta tana kallonshi kamar yadda yayi sai dai shi sam ba ita yake kallo ba domin yafada duniyar tunani.

"Prince..., Prince....ina dinkin yarinyar nan?"

Sai lokacin yadawo hayyacinsa sakamakon maganar tj abokin aikinsa da ta daki dodon kunnuwansa, gefenshi ya duba ya ciro wasu kaya acikin leda ya mika masa,

"Wai meke damunka fahad?"

Kallonta yayi adage sannan cikin rashin kulawa yace,

"Mekika gani fa?"

"To ai naganka ne kamar wani marar lafiya" tayi maganar cikin kalar tausayi,

"Lafiya ta lau..." Yabata amsa yana kokarin mikewa tsaye, wata leda ta mika masa tana langwabe kai,

"Please my prince ga uniform dina ka dinka min kaji"

Batare da ya kalleta ba ya karba ya jefa cikin wani kwali dake girke gefen kekensa,wani food flask dan madaidaici mai kyau ta sake mika masa,

"Ga abinci na kawo maka"

Karba yayi ya dora saman keken dinkinsa sannan ahankali kamar wanda tayiwa dole ya furta,

"Thank u"

Jingina tayi tana kallonshi shi kuma yana kallon wayarshi, babu abinda kake ji sai karar keken dinki wanda sauran abokan aikinshi keta faman aiki. Scissors din da ke ajiye kan kekenshi ta dauka ahankali ta kai kan tararriyar sumarshi,

"Inyi maka aski?"

Sake daure fuskarshi yayi yakai hannu ya doke almakashin,

"Kibari bana so, nafada miki bana son wasan banza"

Murmushi tayi tana sunkuyar da kanta,

"To kayi hakuri"

Baice mata komai ba yatashi da niyyar fita nan itama ta mike tana kallonshi ganin haka yasa shi yafasa fitar yawuce can wani lungu kusa da wata drawer ya kwanta, duk da tana son su fita tare amma haka tayi hakuri tawuce tatafi ba don taso ba.

Yajima kwance awurin yana jin sauran yan shagon sunata gulmarsa shida husna amma bai tanka ba har saida lokacin sallar la'asar yayi sannan yatashi,alwala yayi ya shiga masallaci duk da yana son ganin salim abokinshi amma sai yashare yashiga salla wanda acan din yahadu da salim din.

Yana fitowa daga salla keke napep yatare yanufi gida, atsakar gida ya iske mahaifiyarshi tana wanki koda yakarasa kusa da ita kamar yadda yazata kananan kayanshi take wanke masa.

"Ayiyah wankinne dai?"

Murmushi tayi tajuyo ta kalleshi,

"To ai ba komai nakeyi ba shiyasa nace gara inwanwanke maka sauran kayan ma na hadasu zuwa gobe zan bayar akai awanko maka"

"Godiya nake Ayiyah tah, Allah dai yabar min ke"

"Amin autana, maza kaje ga abincinka can a falo na tanadar maka"

Yunkurawa yayi ya mike daga tsugunnen da yake hakan yayi daidai da fitowar mamu,

"D'an nema kadawo ashe?"

"Hajiya mamu wallahi nadawo, kina daga ciki kenan?"

"Andai ji kunya, gandamemen saurayi dakai amma baka iya wanki ba"

Kafin yayi magana ayiyah tayi caraf ta cafke zancen ta hanyar bawa mamuh amsa,

"Tunda yana da masu yimasa ai ko ya iya bashida amfani"

Wata shewa mamu ta saka tana karasowa inda suke,

"To nidai naga yanda za ayi duk ranar da akayi masa aure"

"Yakuwa za ayi? Matarsa ce zata rinka yimasa"

"Idan ta iya ko?"

"Sai ta koya" inji ayiyah, jan yar karamar kujerar tsugunno mamu tayi ta zauna kusa da ayiyan, shi dai bazai iya cigaba da kallon wannan dramar tasu ba shiyasa yawuce dakin ayiyah fuskarshi shimfide da murmushi domin idan da sabo yasaba ganinsu ahaka kusan tun tasowarsa ahaka yake ganinsu bai taba jinsu suna fada ba kai idan baka saniba baka taba cewa kishiyoyine dan ko yanzun ma da suka gama wannan rahar hira ya jiyosu suna yi kuma da alama wankin mamuh take taya ayiyah. Zama yayi saman daddumar dake shimfide cikin falon yasoma bude kwanukan dake jere reras awurin wanda yasan shi aka tanadarwa domin kullum haka ayiyah keyi masa kamar wani mai gida, funkaso da miyar taushe yagani sai shinkafa da wake da manja da salad sannan ga zubo nan mai sanyi da kankara aciki cikin wani madaidaicin jug, hannun riga ya nade yasoma zuba shinkafa da waken domin kusan abubuwan nan na soye soye irinsu waina, sinasir, funkaso duk ba damunshi sukayi ba dan haka yazage yaci shinkafa da wakensa yayi dam yasha sanyayyen zobonshi daga haka ya mike ya fito,su ayiyah har sun kammala wankin sun fada wani aikin kuma sunayi suna hira shiyasa ma ko ganin fitowarshi basuyi ba, dakinsu ya nufa wanda yake cikin soron dake hanyar kofar gida yabude yashiga daga shi sai yayanshi Abba adakin amma yanzu abban baya nan yana can jami'ar Maiduguri wato unimaid yana karantar computer science dan haka sai shi kadai adakin yanzu, kayan jikinshi yarage yabar gajeren wando kadai bayan ya Kara kofar dakin, kan dundumemiyar katifar dake malale adakin yahau ya kwanta bai kai ga rufe idanuwansa ba yajiyo alamun karar shigar sako cikin wayarshi, akasalance ya mika hannu yadauko wayarshi kirar Galaxy S10,BILKISU shine password din kan wayar tashi nan yabude yasoma duba text din duk da baiyi saving number dinba yagane husna ce domin har ya haddace number dinta saboda yanda take damunsa arana sai ta kirashi akalla sau biyar ko fiyeda haka banda text massages kai idan takira ma taji shiru abune mai sauki yaganta ashagonsu ta biyo sawunshi yarasa gane kan wannan yarinyar gashi ta tsani ta ganshi da wata mace suna ko maganane alhalin kuma shi aikinsa na matane tunda dinkin mata shine sana'arshi. Sakon yabude yasoma karantawa kamar haka... _"Ya fahad yakake, ina fata lafiya kake, abincin yayi dadi?"_ murmushi yayi ya ajiye wayar bayan yasata a silent domin shi sai yanzu ma yatuna da wani abincin da ta kawo masa dazu saboda can yabaroshi ashago bararrajewa yayi saman katifarshi domin yin bacci duk da yasan ayiyah ta hanashi wannan dabi'ar ta baccin yamma amma babu yanda zaiyi ne sakamakon yagaji dayawa gashi ya jima bai samu isasshen bacci ba kullum yana kan keke yana dinki.

***

Murmushi tasaki ahankali wanda yayi sanadiyyar bayyanar fararen hakoranta sannan ya bayyanar da kyawawan beautiful point dinta wadanda ke kara kawata kyakkyawar fuskar da Allah yayi mata. Wayar dake makale a kunnenta take jujjuyawa cikeda annashuwa,

"Yes half soul, yanzu dai kabari sai nakoma gidan kawai sai naturo maka...."

Dan Jim tayi tana sauraron abinda yake fada bata kai ga bashi amsaba tamike daga kujerar datake zaune wacce ke rukunin kyawawan kujerun dake zagane cikin zungureren office din wanda ke dauke da kayan alatun more rayuwa banda na'urar sanyaya daki wacce ta cika dakin da sanyi wanda bazai cutar da jikin dan adam ba, jakarta ta dauka wadda take ajiye bisa dogon teburin da ke tsakanin rukunun jerarrun kujerun masu fuskantar juna, hakan yayi daidai da shigowar khulsum kawarta,

"Noorul kalb ga khulsum ta shigo zamu tafi ni ina ganin kawai kabari sai naje gida din kawai sai muyi waya ko?" Batare da khulsum tajiyo amsar da yabata ba taga tayi murmushi sannan ta amsa da,

"Zataji half soul, me too"

Daga haka ta katse wayar tana kallon khulsum,

"Wai har kin kammala voicing din?"

"Tun yaushe, ina can inata jiranki amma najiki shiru ashe kina nan kina soyewa"

Murmushi tayi ta saba jakar hannunta suka doshi kofa domin fita daga office din,

"Nima fa yanzun nan nagama fassara labaran kasuwancin nan kin san yanada wahala shine kuma hamood yakirani,namanta ma yace yana gaisheki"

"Ina amsawa, am yawwa kafin namanta wai ke mekike shirya mana ne abikin nan?"

Juyawa tayi ta kalli khulsum sannan ta harareta,

"Me zan shirya muku kuwa, ko nice amaryar da zakiyi min wannan tambayar? Ban son wulakanci"

Murmushi khulsum tayi ta dafa kafadarta,

"Bakece amarya ba amma ai kece babbar yaya kuma uwar biki kinga kuwa yazama dole kiyi wani abu"

Lumshe idanuwanta tayi sannan ta budesu bayan yanayin fuskarta ya sauya cikin sakannin da basu gaza biyu zuwa ukuba,

"Ni yanzu duk ba wannan ba wallahi abunda ke damuna guda dayane zuwan Grandma dinmu iyallo, yanzu tana zuwa zatabi ta uzzurawa mutum ta daga masa hankali, tun lokacin bikin mamaa take damuna gashi yanzu bikin Hindu da meenah yazo, ni wallahi ji nake kamar inbar gidan sai angama bikin nadawo"

Murmushi khulsum tayi bayan taja ta tsaya kamar yadda taga tayi,

"Labour kema fa da laifinki gaskiya, why not bazaki baiwa hamood dinki damar yafito kuyi aureba tunda kuna son juna? Haba dan Allah, shekara da shekaru kuna abu daya sai kace wasu wannan..., ai yakamata yanzu ace yabaro kasar Chinan nan yadawo kunyi aure inyaso sai ku koma tare idan bai gaji da zaman canba"

Saida ta sake bata fuska sannan ta kalli khulsum,

"Zanyi miki rashin mutunci idan kika kara kirana da labour dinnan, nafada miki bana so"

"Atoh kiyi min mana wayasa lokacin da kina secondary school din da aka baki labour prefect din kika karba? Ai da sai kice bakya so abaiwa wata"

Dariya tayi ta dauke kanta daga kallon khulsum,

"Kin san me kawata? Hamood shima burinsa yanzu kawai yaga yadawo Nigeria munyi aure, kuma nanda 3 months fa zai dawo, sai dai shi yafi son yayi komai na aurensa dakanshi, baya son uncle dinsa yayi masa acewarsa lokaci yayi da yakamata uncle barewa yahuta tunda tun yana dan 7 years yake yimasa wahala sannan dukkan karatunshi da wanda yayi a Nigeria da wanda yayi a outside duk shine yake sponsoring shiyasa yace sai yadawo yasamu aiki tayadda zai iya yiwa kanshi aure sannan zai kai maganar gaban uncle dinshi"

Dan karamin tsaki khulsum taja,

"To kuma sai me dan yafadawa uncle dinshi yanzu? Minister nefa, ai yanada kudin da zaiyiwa samari goma irinsa aure"

"Hakane khulsum amma kigane wani abu guda daya, abunfa da kunya kuma da nauyi ace tun kana dan karami mutum ke dawainiya dakai sannan ka girma nanma kace komai shi zaiyi maka alhalin bashi ya haifeka ba kawai zumunci ne"

"Ehh to hakane kuma da wannan dan wannan, to Allah dai yadawo dashi lafiya musha biki"

"Amin, yanzu dai tunda magrib takusa ni ina ganin mubari zuwa gobe sai mu shiga central market mu siyo kayan da zamu saka abikin dan gaskiya basaka ankon nan nasu zamuyi ba tunda nasune suda friends dinsu"

"To shikenan babu damuwa Allah yakaimu, Allah kuma yasa mutashi da wuri daga aikin nan"

"Amin,Kuma wallahi commitment dina yawa gareshi goben nan dan har dinki nake son kaiwa ga sauran siyayyar yaran nan da ban karasa ba ta kayan kitchen dinsu"

"Babu komai dai kawai Allah yanuna mana goben komai mai saukine"

"Amin ya Allah"

Daidai lokacin suka tare wani mai keke napep suka shiga domin tafiya gida.

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:14] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

*KAMAR DA WASA...!*💖

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*4*

***Kasa nutsuwa yayi sakamakon dukan luguden da zuciyarsa keyi tamkar zata faso kirjinsa tafito waje dan tsananin zafin sonta, ahankali cikin sanyin jiki yatashi ya dauko wayarshi wacce ke ajiye tana charge saboda akwai wutar nepa agari,

Komawa yayi ya kwanta ya lalubo contact dinta, _soul mate_ shine sunan da yasaka mata nan yakurawa number tata ido kamar wanda ke son haddaceta har zuwa tsawon wani lokaci, yanke shawarar tura mata da sakon karta kwana zuciyarsa tayi nan ya rubuta mata ya tura mata cikeda shaukin kaunarta har saida yaga sakon ya tafi sannan yaji ya dan samu nutsuwa, ajiye wayar yayi akusa dashi kamar wadda ake jira nan tasoma tsuwwa amma bai kulaba domin jikinsa yabashi husnah ce wadda ba komai zata fada masaba illah ta kara masa damuwa dan haka yashare yaci gaba da tunanin abar kaunarsa.

***

Jikinta sanye da yar guntuwar karamar riga kalar ruwan madara wacce take marar nauyi da kauri tana tattara wani report da zata gabatar acikin laptop dinta taji shigowar sako, duk da bata dubaba saida tayi murmushi domin tasan bazai wuce hamood dintaba wanda ko mintuna biyar kwarara basuyi da gama wayaba, saida ta shanye sanyayyen lemon dake gabanta sannan ta janyo wayar bayan ta rufe laptop din. Kwanciya tayi tabude sakon, abin mamaki yabata saboda ganin wata number wadda bata hamood ba, cikin mamaki ta soma karantawa kamar haka, _Salam yake kyakkyawa,hakika kinyiwa zuciyata wani tarko mai wuyar Ketarewa, ganinki sau daya tal yana barazanar kawar da tunanina daga gangar jikina, wallahi ban taba ganin wata halitta wacce tayi daidai da ra'ayina kamarki ba, kece mace tafarko da nafara so tun kafin nayi ido biyu da ita, dan Allah karki ki k'i amsar soyayyata domin idan baki amintaba zan iya rasa rayuwata akan sonki, wallahi ina mutukar sonki, ina sonki bilkisu._

Dora wayar tayi akan kirjinta gabanta yana faduwa sannu sannu, aranta tana tunanin to shikuma wannan waye shi? A ina yataba ganinta da har yaji yana sonta? Bata da amsa dan haka tayi watsi da tunanin batare da tabarshi yayi tasiri acikin zuciyarta ba. Addu'ar bacci tayi ta shafa tayi kwanciyarta bayan takashe wayarta, amma me koda gari yawaye tana kunna wayarta sakonshi ne yafara shigowa cikin wayarta inda yake yimata barka da safiya da wasu kalaman soyayya masu sanyaya zuciyar masoya, dan guntun tsaki taja ta ajiye wayar gefe ta kwanta batare da tabi takan mai turo sakon ba.

Aranar ko aiki bataje ba domin sunata soye soye da dafe dafe kasancewar ranar za akawo lefen meenah, itace akan komai gashi gidan ba laifi yayi albarka domin yan uwa na kusa da makota duk anshigo domin karbar kayan, sai misalin karfe uku na yamma aka kawo kayan nan aka shiga tarbar baki da abubuwan da aka tanadar musu basu bar gidanba sai bayan da sukayi sallar la'asar sannan suka tafi nan kuma makota aketa shigowa ganin kaya wadanda suka kasance akwatuna hudu manya sai dan karamin kit na biyar kalar ruwan kasa ita kuma Hindu sai nanda kwana biyu za akawo nata. Ita dai bilkisu yau tunda tatashi kanta adaure yake domin maiyi mata sakon nan ba dainawa yayi ba sau hudu kenan yau yana turo mata sakonni masu dauke da kalaman so da kauna tun tana sharewa har ta zauna tana son sanin waye.

***

Fahad yau tunda yafita shago baiyi aikin kowaba sai nasu bilkisu nata yawuni yana hadawa domin dinki na musamman yayi mata wanda babu irinshi ashagon kuma koda yagama hadawa bai barshi ashagon ba bare har aratayeshi a hangar wurin da suke rataye kayan da suka dinka, shi kansa ya yaba da dinkin da yayi mata shiyasa yake jin zuciyarshi wasai, Abu daya kawai yanzu yake bukata shine yaji muryarta amma yasan hakan ba mai yuyuwa bane. Wata numbershi wadda bai cika amfani da itaba yasa numberta yakirata amma harta tsinke ba adaga ba sai da yasake kira sannan yaji ta dauka cikin sanyayyiyar muryarta wadda kamar tana bacci, sallama tayi amma sai yasamu kansa da kasa amsa mata domin wani irin faduwa gabanshi yasoma yi wanda bai san daliliba,

Sau uku tana fadin "hello.... Hello....., hello"

Jin bai amsaba takatse wayarta, wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke sai lokacin yaji yasamu kwarin gwiwar yin abinda yake gabansa, tashi yayi ya tattara inasa inasa ya nufi gida lokacin misalin karfe biyar da wurin mintuna ishirin, yana zuwa gida kayan ball dinsa yasaka yafita batare da yashiga koda cikin gidanba acan yasamu ya ragewa kansa damuwa domin sai karfe 6 da wani abu yadawo. Wanka yayi yasha turare kamar wanda zaije zance yafita masallaci can yayi zamansa shida saleem har saida sukayi sallar isha'i sannan suka fito, wani sabon zaman suka sake dasawa akan dakalin simintin dake kofar gidansu saleem wanda wurin yake fuskar mutane ga hasken farin wata wanda ya hadu da hasken lantarkin dake kafe atsakiyar layin wanda ya ratsa ta cikin unguwar tun daga farkon layi har zuwa babban titi can gefe daya kuma yarane dankam masu soya awara nayi wasu kuma gyada suke saidawa da dafaffen kwai da sauransu.

Daga kansa sama yayi yana kallon taurari wadanda suka karawa sararin samaniya ado da kawa, cikin sanyin murya yafurta,

"Abokina am in love....."

Juyawa saleem yayi ya kalleshi yana murmushi sannan ga alamun mamaki nan bayyane akan fuskarshi,

"Yaushe? Kuma wacece?"

Lumshe idanuwa fahad yayi yana jin wata sabuwar soyayyarta tana shigarshi,

"Wata classic beb ce, kuma wallahi najima dauke da sonta"

"Kodai husnah ce?"

Harararsa fahad yayi kasancewar akwai yalwataccen haske yasanya saleem ganin hararar hakan yasashi yin murmushi sannan yadafa kafadarshi,

"Bani labarinta abokinah..."

Saida yayi murmushin da shi kadai yasan dalilin yinsa sannan yafara fada masa,

"Nafara sonta ne tun ban gantaba, tun ranar da nafara jin muryarta a radio tana gabatar da wani shiri naji tashiga raina, kullum da ita nake kwana nake tashi, cikin ikon Allah sai gata jiya a shagonmu ta kawo min dinkunanta..... Amma bana jin zata soni" Yakare maganar yana cizar lips dinsa cikeda damuwa,

"Saboda me kake ganin bazata soka ba? Kanada wani mummunan haline wanda ban saniba?" Saleem yafada yana fuskantarshi,

"Sam bahaka bane, saleem ta girmeni fa, jikina yana bani bazata yi accepting dinaba saboda zatace nayi mata yaro dayawa may be ma zata ji kunyar nunani awurin friends dinta da relatives dinta"

Dariya saleem yayi yana dafashi,

"To kai da waye ya aikeka son wacce ba sa'arka ba?"

"Saleem kenan, shi so ba ruwansa da cancanta,shekaru ko duba matsayi, kawai yakan shigane aduk sa'ilin da yaso koda kuwa ba ashiryawa hakanba, saleem wallahi dagaske ina sonta, ni girmemin din da tayi ba damuwa bace zan iya rayuwa da ita mutukar zata yarda ta aureni"

Shiru saleem yayi yana kallonsa, ganin yanda yanayin idonshi ya sauya zuwa ja yasashi gasgata aminin nashi,

"Abokina ka kwantar da hankalinka, ina kyautata zaton koma wacece zata soka itama domin baka da makusa kuma bakada wani hali ko dabi'a wadda bata kirkiba, kana da zuciyar neman na kanka sannan kana da kyakkyawar mu'amula da kowa, kayi addu'a abokina insha Allah zaka dace"

Kalaman saleem sune suka sanyayar mishi da zuciya sannan yasashi jin nutsuwa ta saukar masa, cigaba da kwantar masa da hankali saleem yayi har saida yaji acikin ransa zai samu bilkisu, cikeda farin ciki suka rabu da saleem yana tsokanarsa,

"To kai ka isa aurenne?"

Girarshi guda daya ya dage masa yana kallonsa cikeda mamaki,

"Nine ban isa aureba? Kabari abani matar a lokacin zaka fahimci na isa ko ban isaba"

Daga haka yamike yakama hanyar gida yana jin saleem har lokacin yana tsokanarsa amma bai tsayaba.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:14] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO* _(Home of expert & perfect writers)_

*KAMAR DA WASA....!* 💖

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*3*

***Nazifi ne ya amsa musu sallamar yayinda sauran kowannensu yana duke yana aikinshi,

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull