Kenza eBookz

Kamar da wasa complete novel - Chapter 2

Kamar da wasa complete novel - Chapter 2

Kamar da wasa complete novel Chapter 2: Kamar da wasa complete novel Chapter 2. Khulsum ciki tawuce ta zauna kan kujerar roba dake kusa da keken nazifi…

3,274 words

Khulsum ciki tawuce ta zauna kan kujerar roba dake kusa da keken nazifi yayinda ita kuma bilkisu tazauna daga bakin kofa kusa da keken fahad wanda kansa yake asunkuye yana hada wata skirt ta atamfa, kamshin da yajine tun lokacin da ta zauna ya janyo hankalinsa har ya daga ido ya kalleta domin wannan shine karo nafarko da ya taba jin wani turare wanda ya sanyawa zuciyasa wani al'amari, ganinta yayi tana latsa wayarta yar karama kirar baby Nokia, ahaka yake dinkin sannan kuma yana aikin kallonta wanda kusan ita bata ma san yanayiba jimm kadan wayar tata tayi kara nan tatashi tafita yabita da kallo,shigarta ita tafi komai jan ra'ayinsa agameda ita domin gaba daya jikinta a lullube yake babu abinda zaka iya gani sai tafin hannunta da fuskarta dan ko kafarta asakaye take, bata wani jimaba ta dawo ta zauna tana sauraron su khulsum wadanda ke maganar dunkunan da suka kawo,

"Kawata ya za ayi? Daga nan gida zamu wuce ne ko zamu koma office?" Khulsum tafada tana kokarin ciro kayan da suka kawo daga cikin leda,

Saida ta dan ja numfashi sannan ta kalli khulsum din,

"Gaskiya muyi tafiyarmu gida..., yanzu haka da kikaga nafita director programs ne ya kirani wai naje nayi program dina shine nace masa bana nan kawai amaimaita na baya"

Tunda tafara magana ya dakata daga dinkin da yakeyi yana kallonta kasa kasa, muryarta ce ke kai kawo acikin kunnuwansa tabbas ko shakka babu itace macen da yajima yana burin gani, itace wacce muryarta ke sanyaya cikin kunnuwansa dan tsananin sanyinta sannan take sashi nishadi cikin kowanne irin yanayi ya tsinci kansa.

"Yanzu waye zaiyi mana wannan dinkin na amaren acikinku?" Khulsum ta bukata,

"Gaskiya sai dai ko prince domin kamar yafi iya dinkasu" Nazifi yabata amsa,

"Ina shi prince din?" Khulsum tasake tambaya,

"Gashi can " yanuna fahad da hannunsa, daga bilkisu har khulsum juyawa sukayi gareshi suna kallonsa hakan yasashi dauke manyan idanuwanshi daga kallon da yake yi mata kamar wani tsohon maye,

"Dan Allah zamu samu dinki?" Bilkisu ta tambayeshi tana kallonshi, lumshe idanuwanshi yayi sannan yabude cikeda kasala,

"Kala nawane?"

"Ko iya na amaren ne ma kala biyu sai kayi mana"

Girgiza kanshi yayi yana juya skirt din hannunshi,

"Zanyi harda nakin ma"

"Nikuma fa?" Inji khulsum,

"A'a ke banda naki"

"Ai kuwa baka isaba wallahi, mu kawo dinkin tare ita kayi mata ni ka ki yimin?"

Murmushi yayi batare da yadaga kansa ya kalli kowaba,

"Kawo kayan nagani" yace da Bilkisu, mikewa tayi bayan ta dora wayarta akan kekenshi taje ta dauko ledar kayan ta soma fito masa dasu tana yi masa bayani, shagala yayi da sauraron muryarta harta gama, tasowa khulsum itama tayi tazo ta ajiye masa nata bai ki ba duk ya hada ya karba yana tambayar measurements dinsu, khulsum Bilkisu tafara gwadawa da tape din da yabasu sannan itama khulsum tafara gwadata sai dai tun kafin khulsum ta fada masa yake rubutawa wuri dayane aka samu sabani Boob's dinta ya rubuta 34 khulsum tace masa 38,jinjina kansa yayi ahankali ya furta,

"Manyan mata"

Saida komai ya kammala sannan Bilkisu ta tambayeshi kudin dinki, na amaren cewa yayi subada 10k sai na khulsum 6k sai na mamaa ita kuma 4k,handbag dinta ta dauka tana kokarin ciro kudin,

"Nikuma nawa fa?"

"Ke sai bayan nagama dinkawa"

"To shikenan ga wannan din"

Kudin ya karba yana ciro wayarshi daga aljihu sakamakon karar da yaji tanayi ganin husnah ce ke kiranshi yasashi saka wayar a silent ya ajiyeta gefe, sallama su khulsum sukayi masa suka fita nan yayi tagumi yabisu da kallo su nazifi binshi da kallo kawai sukeyi domin su dai asanin da suka yimasa baya karbar dinki kai tsaye haka musamman irin wannan na gaggawa. Yajima ahaka kafin ya hakura yasoma tattara kayan yana sakawa cikin leda kamar amafarki yaga wayarta kan kekensa bayan ya dauke atamfar dake wurin, jujjuya wayar ahannunshi yayi kafin ya bude yasaka number dinshi ya kira, goge number tashi yayi bayan yakira wayarshi ya ajiye wayar agefenshi. Bilkisu kam saida sukayi nisa da kasuwa sannan ta farga cewar ta manto wayarta ashagon dinki cikeda takaici ta sanarwa da mai keke napep din yajuya suka koma. Koda sukaje gaban plaza din ita kadai ce tafita domin zuwa karbo wayar tabar khulsum acikin keke napep din,

Tunda ya hangota tana tahowa ya kafeta da idanuwansa domin dama gaba daya hankalinsa awurin yake, cike da nutsuwa take takawa sannu sannu wadda kallo daya zaka yi mata ka fahimci cewar hayaniya bata rabeta ba sannan ba magananniya bace domin yanayinta kadai ya isa ya gamsar dakai hakan.

Yana nan zaune tayi sallama tashigo, shine ya amsa mata sallamar domin su nazifi basu ma kula da shigowarta ba dalilin hankalinsu yana can ga kallon kwallon da sukeyi a yar karamar television dinsu dake can saman wata kanta,

"Sorry kamar nabar wayata a nan ko?" Tafada tana dube dube,

"Ehh gashi, nayi niyyar inbiku inkai miki ma but har kun rigada kun tafi"

Hannu ta mika ta karba tana fadin,

"Babu komai nagode"

Hannun nata yabi da kallo wanda yatsunta sukasha dark maroon din lalle wanda yayi mutukar kawata hannun,

"Karki damu, Allah yakiyaye hanya"

"Amin, nagode"

Daga haka tajuya tafice daga cikin shagon, kamar dazu yanzunma binta yayi da kallo kamar zai cinyeta har yadaina hangota sai lokacin hankalinsa yakoma jikinsa domin gaba daya lokacin da tana nan baya tareda shi. Murmushi yayi yajingina da jikin bango yana bin number dinta da kallo wacce ta kasance special number, sumar kanshi yashafa yana murmushi,

"Wato komai nata special ne kenan kamar yadda itama take special...."

Haka yaci gaba da zama yana kallon number dinta har husna tashigo ta iskeshi ahaka, zama tayi akujerar dake gaban kekenshi,

"Ya fahad murmushin me kakeyi?"

Duk da yana son ya daure mata fuska kamar yadda yasaba yau yagaza yin hakan yasan hakan baya rasa nasaba da farin cikin da yake ciki, lumshe idanuwansa yayi yana sake tuno fuskarta mai dauke da beautiful points wadanda ke kara mata kyau,

"Ya fahad ina dinkin nawa?"

"Na saidashi"

Murmushi tayi dadi yana ratsata, yau wacce rana fahad ya sakar mata fuska harda tsokanarta,

"Idan kasiyar ai nasan zaka siya min wanine shiyasa"

Tallafe kumatunshi yayi da tafin hannunshi na hagu yana kallonsa, hannu takai zata warci wayarshi yayi saurin kaucewa yana harararta,

"Wai bana hanaki tabani ba?? Meyasa bakya jin magana ne?"

Marairaicewa tayi tana kallonshi,

"Am very sorry my heart beat"

Baice komai ba yasoma laluben kayanta acikin tulin himilin kayan dake gefenshi, aranshi yana tunanin halayyar husna ta son tabashi shiyasa baya sakar mata fuska sosai saboda indai zatazo wurinshi to sai tayi yunkurin taba masa hannu ko wani abu mai kamada haka, ciro mata kayanta yayi ya ajiye mata agabanta sannan yatashi ya hado mata kan kwanukanta wadanda take kawo masa abinci duk da bawai ci yakeba dan su nazifine ke cinyewa, saida tagama janshi da magana da wasa sannan ta kwashi kayanta ta tafi, tashi yayi yafita salla ana idarwa yadawo yazo yasoma yanka kayansu Bilkisu.

***

Agajiye lilis takoma gida kamar koda yaushe yauma gidan acike yake da makota da kawayensu meenah amare domin anata shirye shirye,kanta yau har wani ciwo yakeyi sakamakon uban yawon da suka sha a kasuwa itada khulsum ga yunwa da take ji,

Sama sama take amsa kowa ta bude dakinta ta shiga itada hudah wacce ke makale da ita, tana zama Hindu tashigo rikeda lemon roba mai sanyi da ruwa,

"Yawwa yar albarka kamar kuwa kin san kishi nake ji sosai, gaskiya yau mun kwashi rana"

"Sannu anty mai gado, ai duk wanda yaganki yasan kin wahala"

"Kedai bari Hindu" tafada tana balle murfin robar lemun"

"Inkawo miki abincin?"

"Kawo min Dan sai nafara ci sannan zanyi salla" tabata amsa tana kokarin bawa hudah lemon abaki, fita Hindu tayi ita kuma taci gaba da karbar lemon tana bawa hudah.

Shinkafa da wake da ganye Hindu ta kawo mata da manja da yaji nan ta sauko taci sannan tashiga ta watsa ruwa tafito tayi salla, nan inda tayi sallar suka baje itada hudah suka hau bacci.

***

Fahad bai bar shago ba sai bayan sallar magrib domin saida yagama yanka kayansu Bilkisu kaf sannan yanufi gida duk da irin tarin yunwa da gajiyar dake baibaye dashi, lokacin da yaje gida bai shiga cikiba dakinsu yafara shiga yayi wanka sannan yashiga cikin gidan, dukkansu suna falon mamu suna kallon wasan kwaikwayo na aku mai labari wanda ake gabatarwa agidan television din ART, daga bakin kofa yatsaya yagaidasu sannan yawuce dakin ayiyah duk da yanajiyo tsokanar da mamuh keyi masa bai kula ba domin yunwa yakeji dan rabonshi da abinci tun safe.

Abincin dare yazuba yaci wato tuwon biskin masara miyar taushe yana ci yana santi har yagama yafito bai koma inda su ayiyah sukeba yafice ya nufi dakinsa, farar jallabiya yasaka yafita sallar isha'i domin daf ake da ashiga. Koda aka idar yadawo kwanciya yayi da niyyar runtsawa amma sam yakasa yin baccin sai juyi da yafara yi, fuskarta kawai yake gani wacce ke dauke da murmushi tana yimasa magana,bashida zabi illa na yabi shawarar zuciyarsa ko zai samu sassauci.

*_Ummi A'isha_*👌🏻 [11/28, 08:14] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO*_ _(Home of expert & perfect writers)_

*KAMAR DA WASA...!*💖

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*2*

***Har suka kusa zuwa gida magana daya suketa yi shine maganar zuwan kakarsu iyallo,

"Mai gado Allah kina bani dariya yau dinnan" khulsum tafada tana tuntsurewa da dariya,

Harararta Bilkisu tayi daidai lokacin da suka isa kofar gidansu bilkisun yayinda gidansu khulsum ke can wata unguwa daban gaba da ta su Bilkisu,

"Banida lokacinki sai anjima saura kuma gobe karki fito da wuri"

Daga haka tafice daga keke napep din tabar khulsum na yimata dariya, ji tayi kamar kada ta shiga gidan sakamakon ganin motar ya mudan da tayi, sam ita ta tsani takura da naci amma babu yadda ta iya dole tashiga tana tafiya sadaf sadaf, atsakar gida ta hangoshi zaune kan farar kujerar roba yadora daya kan daya yayinda ammah ke cikin kitchen suna yar hira dashi,

"Sannu da aiki ammah..."

Daga haka tanemi wucewa dakinta, maganar amma ce ta dakatar da ita,

"Ke mai gado, bakiga yayanki bane zaki wuce baku ko gaisa ba?"

Juyowa tayi tadawo da baya, fuskarta babu fara'a,

"Yaya mudan ina wuni? Anzo lafiya? Yasu iyallo?"

Ta hada gaisuwar gaba daya lokaci guda, murmushi yayi ya amsa mata yana yi mata wani kallo mai cikeda sha'awa,

"Lafiya lau mai gadon zinare, ya aikinku?"

Tana tafiya take amsa masa da "lafiya"

"Manyan yan jarida kenan, ku da anganku anga labarai"

Bata amsa masa ba ta soma cuku cukun zaro key din dakinta daga cikin handbag dinta adaidai lokacin taji sallamar Hindu da minah har da mamaa wacce ke rikeda hannun yarta hudah yar kimanin shekara daya da rabi, yarinyar na hango Bilkisu ta kwace daga hannun mamaa tatafi da gudu wurin Bilkisu, dakatawa tayi daga bude kofar da takeyi ta dauketa fuskarta dauke da fara'a,

"Hudah na oyoyo daga ina haka?"

Kafin hudah tayi gwarancinta su mamaa suka karaso,

"Adda maigado yau baki taso da wuriba" inji mama,

"Wallahi fa mamaa aikinne sai ahankali, daga ina kuke?"

"Bakin kasuwa mukaje suka kai nadin gwaggwaro"

Murmushi tayi tawuce dakinta tana cewa,

"Amaren kamshi kenan"

Akan gadonta ta ajiye hudah ta kunna mata cartoon awayarta ta bata sannan ta zage ta fada wanka, tana wankanne meenah ta shigo sadaf sadaf ta dora mata wata farar takarda akan sallayarta tafice.

Bayan tafito doguwar riga kawai ta saka marar nauyi ta dauki hijabinta domin tanata jiyo kiraye kirayen salla daga masallatai daban daban, hudah kuwa tana zaune tana kallon cartoon dinta sai dariya takeyi,

Kan sallaya tahau har zata fara sallar idonta yakai kan farar takardar da meenah ta ajiye dauka tayi ta warware ta tafara karantawa,

_Adda labour yaya mama ce tace wai baza abamu komai bane na hadin amare? Wai kibada kudi zata siyo mana kaza ta dafa mana_

Murmushi tayi ta yaga takardar ta watsa ta cikin dustbin, dama kusan duk lokacin da zasu tambayeta abu indai na kunya ne sai dai su rubuta mata sai su ajiye mata wurin da zata gani ko su tura mata text, ko pad zasu tambayeta sai dai su rubuta mata shiyasa kafin lokacin ma yayi take siyo musu ko tabasu kudin su siya domin tana mutukar kaunar kannen nata saboda suma suna sonta sannan suna bata girmanta tsakaninsu babu reni hatta mamaa da tayi aure harda baby bata yimata reni bare rashin kunya, sallar magrib tayi bayan ta idar ta kara da nafila, tana kokarin shafa addu'a mamaa ta shigo,

"Yarinyar momy kallo takeyi awayar momy?"

Mamaan tafada lokacin da take zama agefen gadon Bilkisu,

"Ai kin jita shiru, nawane zai isheku dafa kazar?"

"Adda labour yafi dubu biyu zuwa uku?"

"To shikenan zan baki kafin ki tafi, shekaran jiya fa har naturawa wannan matar da tayi miki hadin kayayyakin nan lokacin bikinki kudi suma tayi musu kuma nasan itama harda kazar zata dafo musu"

"To shikenan ai iya natan ya isa tunda yama fi kyau nifa na bikina har na haifi hudah yana jikina..."

Harararta Bilkisu tayi,

"Ban son fitsara"

"Yi hakuri Adda maigado subutar baki ce" daga haka ta shige bathroom domin yin alwala.

Daukar hudah tayi ta fita domin yunwa take ji, atsakar gida ta iskesu saman katuwar tabarma wata na sallah wata kuma ta idar rashin ganin ya mudan yasata zargar kila ko yatafi, zaunar da hudah tayi tashiga kitchen, faten doya da wake shi akayi da rana yanzu kuma da daddare tuwon shinkafa ne miyar zogale, tuwon ta zuba ta dauko tadawo wurin hudah ta soma bata itama tana ci da haka har amma tafito ta samesu. Zama tayi kusa da ita tana tsokanar hudah,

"Acici kinzo zaki cinye min abinci nida mijina, to maza kiyi kibar min gidana...." Ta karashe maganar tana jan kunnenta daya, rike kunnen da taja hudah tayi tana guduwa jikin bilkisu, janyeta tayi tana kallon amma,

"Zo baby na rabu da amma kinji, maza ci tuwo idan baki koshi bama inkaro miki"

"Badai tuwo na ba tunda ba ita ta tuka minba"

Kowa na wurin saida yayi dariya saboda jin abinda tace, mamaa ma fitowar tayi tana dariya nan tasamu gefen tabarma ta zauna,

"Yawwa mai gado wai nikam meyasa kikeda taurin kaine? Meyasa duk ranar da dan uwanki mudassir yazo bakya sakar masa fuska ku gaisa? Iya gaisawar ce fa kadai daga ita shikenan babu wani abu, dan Allah ki gyara"

"To ammah insha Allah" daga haka taci gaba da cin tuwonta tana sauraren zantukan da su mamaa keyi wanda baya rasa nasaba da shirye shiryen bikin su Hindu lokaci lokaci ta kan dan saka baki harta kammala cin tuwon tatashi taje tana wanke musu hannu itada hudah daga nan dakinta tawuce tabaje akan gado bayan ta dauko yar madaidaiciyar laptop dinta, tana ji yara suna go slow din shigowa dan kiran hindu da meenah wanda ko ba afada ba tasan angwayen ne masu kiran. Aikinta taji gaba dayi na rubuta takardar neman hutu har na tsawon sati biyu wato (casual leave) saboda bikin su meenah domin tana bukatar isasshen lokaci so take idan biki yarage saura kwana uku saita nema kamar dai yadda tayi abikin mamaa. Har misalin karfe 9 saura idonta na kan laptop din tana wani aikin daban, shigowar mamaa ce ta katseta ta tashi zaune tana gyara hudah wacce ke makale ajikinta tana bacci,

"Adda maigado faruk yazo zamuje mu tafi, ko inbar miki hudah ta kwana?"

"Ke wai ban hanaki fadar sunan mijinki kai tsaye ba, tunda ga yarku ai gara kirinka sakayawa da abban hudah wallahi idan kuma baki gyaraba wata rana sai kinji sunan nan abakin yarki"

"Wallahi Adda bana fada agida anan ne dai nake fadar sunanshi"

"Nidai na fada miki ai, dauketa kutafi da ita kinga gobe zan fita aiki kuma idan nafita bazata yarda da kowaba sai kuka zata ishi mutane dashi da dai weekend ne sai kibarta"

Daukar hudah mamaa tayi suka fita bayan bilkisu tasaka hijabinta, atsakar gida suka samu ammah da Faruk mijin mamaa suna gaisawa. Yana ganin bilkisu ya soma dariya yana cewa,

"Barka da fitowa babbar yaya, anwuni lafiya"

"Lafiya lau faruk ya mutanen gida, ya aiki"

"Lafiya lau anty mai gado"

Dunguma sukayi gaba dayansu suka fita banda amma,suna fita tun daga compound din gidan kamshin turaren su hindu ya budadesu suda angwayensu kowacce suna tsaye agefe itada angonta suna hira,

Dukkaninsu saida suka matso suka gaisa da bilkisu kafin takoma gida, tana shiga daki ta iske miss called din hamood zama tayi gefen gadonta tana kokarin bin kiran yasake kiranta nan ta daga bayan ta lumshe idonta tana saurarensa, kamar koda yaushe sun shafe lokuta masu yawa suna hira har saida bacci yaci karfinta sannan sukayi sallama.

Washe gari da sassafe ta shirya tafita domin tana da zuwa dauko rahoto kamar yadda tasaba, ko khulsum bata nemaba ta kwashi kayan aikinta itada driver suka tafi,bayan ta dawo daga daukar rahoton taje tayi voicing saida ta kammala komai sannan tasoma neman kawar tata, news room taje acan ta iske khulsum tana fassara labaran da za agabatar da misalin karfe daya nan tazauna tajirata harta gama daga nan sukaje suka dauki permission suka nufi babbar kasuwa.

Ko acikin keke napep bilkisu sunata waya itada hamood har saida suka shiga kasuwar sannan sukayi sallama tafito daga napep din tana yiwa khulsum kallon ta ina yadace mufara? Shagon sayar da kayan kitchen suka fara zuwa domin tanada sauran siyayya da yawa wadanda bata karasa ba, sun bata lokaci sosai awurin domin yau so take tagama da wannan bangaren awuce wurin. Sai da suka kammala siyan duk wani abu wanda ke rubuce jikin list din da tayi awata takarda sannan ta biya kudin suka shiga can tsakiyar kasuwar domin dubo kayan da amare zasu saka na fitar biki da wanda ita kanta zata saka itada kawarta khulsum.

***

Kamar koda yaushe yauma yatashi cikeda zumudin sake jin muryarta domin ayaune take gabatar da shirinta mai farin jini wanda yake sanyaya zukatan masoya da duk wani mai sauraron shirin,

Yana daga kwance saman dingimemiyar katifarsa ya dauki agogon hannunshi silver colour kirar kamfanin LX,karfe 11 saura yan mintuna, cikinsa yashafa sannan ya mike yana gyara gajeren wandon dake jikinsa, farar t shirt dinsa mai dogon hannu yaja ya mike yafita yanufi cikin gida yana mai saka rigar, baiyi mamakin jin gidan shiruba domin yasan su maryam sun tafi makaranta haka shima baba yafita kasuwa, sai dai ko motsin ayiyah da mamuh baiji ba, dakin ayiyah yadaga labule ya shiga, ga kayan karin kumallonsa nan ajiye agefe dan haka ya zauna ya lankwashe kafafu yajawo kwanikan, dan karamin food flask ne dauke da gurasa wacce tasha kuli kuli yaji sosai da man gyada hadida tumatur da albasa da koren tattasai sai zuba kamshi take sannan ga koko nan a dan madaidaicin kwanon sha na silver sai kosai shima awani kwanon na daban, bisimillah yayi ya soma karyawa yana tsice danyar albasar dake cikin gurasar domin shi baya cin danyar albasa da danyar tafarnuwa, yana daf da kammalawa yajiyo maganar mamuh wadda tafito daga bandaki tana rikeda bokiti da kwandon wanka,

"Wannan ja'irin yasamu yafito ne? Bacci sai kace mai baccin mutuwa"

Murmushi yayi yashafa kansa,

"Ina kwana mamuh, ina ayiyan ne?"

Saida ta amsa gaisuwarshi sannan tabashi amsa da,

"Taje nan makota gidan mai dan wake jajjabin yaronta murtala wanda aka sacewa babur shekaran jiya"

Mikewa yayi yana cewa,

"Allah yarufa asiri"

Daga haka daki yakoma yashiga wanka bayan yafito ya shirya cikin kananan kaya brown din riga da blue din wando, saida yagyara sumar kanshi sannan yafita yanata zabga kamshin turaren Amirul oud, cikin gida yafara shiga yayi musu sallama sannan yawuce shago.

***

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull