Kamar da wasa complete novel - Chapter 3
Kamar da wasa complete novel Chapter 3: Kamar da wasa complete novel Chapter 3. Sosai bilkisu takashe kudi wurin siyawa amare kayan da zasu saka banda nata…
3,235 words
Sosai bilkisu takashe kudi wurin siyawa amare kayan da zasu saka banda nata da na mama da ta siya material mai kyau light blue da manyan atamfofi guda biyu sannan ga ankon da zasuyi ita da khulsum na wani golden din leshi, tunanin wurinda yadace su kai dinki suka farayi domin bata son takai kayan gida batare da andinka ba, khulsum ce tace ta taba ganin shagon wasu teloli daga waje can a albarka plaza nan suka ciccibi kayan suka fita,babu wani nisa sosai amma agajiye suke jinsu lis, suna shiga plaza din suka wuce sama ahawa na uku suka ga shagon wanda ke dauke da zanen dinkunan mata kala kala ajiki anruba _Golden scissors and fashion design_ a mutukar gajiye suka kutsa kai ciki bakin khulsum yana dauke da sallama.
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:15] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO.*_ _(Home of expert & perfect writers)_
*KAMAR DA WASA.....!*💖
***Hannayensa gaba daya ya aza cikin aljihun wandon bakin jeans din dake jikinsa, jar rigace ajikinsa mai rubutu kamar haka, _All the best_,yana tafe yana kallon dukkan jama'ar da kowa hada hadarsa yakeyi, wayarshi ya zaro daga cikin aljihun wandonshi domin duba ko waye ke kiransa sunan Nazifi yagani abokin aikinshi domin shagonsu daya, yana dagawa yaji yace,
"Prince ga wasu sun kawo dinki wai nanda next week suke so"
"Gaskiya bazasu samuba dunkuna sunyi min yawa"
"Hakane but amma naga ka karbi na wasu jiya ai"
"Ehh hakane amma ai kadai fi kowa sanin yawan dinkunan dake zaman jirana ko"
"Babu damuwa bari nakira hamza naji"
Katse wayar fahad yayi aransa yana cewa "yadai fi domin ita wadda kaga jiyan na karbi nata daban take bazan iya bari wani yayi mata ba shiyasa"
Ahaka yakarasa gida direct cikin gidan yawuce domin cin tuwo baba yahango kofar dakin mamuh yana magana dasu maryam wanda baya iya jiyo mai yake fada,durkusawa yayi kasa yagaida shi sannan yawuce dakin ayiyah yana dallawa Mariya harara saboda laifin da tayi masa da sassafe tun kafin tatafi makaranta, zaune ya iske ayiyah tana damawa baba fura acikin kwanon sha na silver da ludai ga sukari agefe cikin wani kofi madaidaici, zama yayi gefenta yana fadin,
"Ayiyah kamar kuwa kin san yunwa nake ji"
"To ai ga tuwon tsari nan miyar kubewa da mamanku tayi sai ka saka kaci idan kaci sai kasha fura"
"Ai kibar tuwon nan kawai ayiyah iya furar kadai zansha"
Kafin tayi magana baba yayi sallama yashigo, matsawa fahad yayi yabashi wuri ya zauna kan lallausar dardumar dake shimfide awurin,
"Muhammadu wai yaushe dan uwanka zai bullo ne?"
Murmushi fahad yayi domin yagane Abba yayansa baba yake nufi, gyara zamansa yayi yana daukar cup din furar da ayiyah ta zuba masa,
"Dazu munyi video call dashi baba yace insha Allah cikin karshen satin nan zaizo gida"
"To Allah yakawo shi lafiya muna zuba ido, ai saika yanke masa wadancan barun naka ko ko kaji ayi masa sauka"
Murmushi yayi bayan yazare cup din dake bakinsa ya hadiye furar da ya kurba.
"A'a baba,zan dai siyo masa akasuwa sai ayiya ta dafe masa su amma wadancan na kiwone bana ci ba"
Ayiyah tana mikawa baba furar da ta dama masa ta daga kai ta kalli fahad,
"Ni ban taba ganin irin wannan kiwon ba sai awurinka ayita kiwata abubuwa amma baza aciba..."
"A'a ai kedai babu ruwanki, barni dashi" Inji baba,
Murmushi fahad yayi yakarasa shanye furar da yake sha,
"Baba ayi min hakuri dai har sai sun kara yawa"
"Ni ai bance komaiba muhammadu, Allah yasa albarka"
"Amin babanmu"
Daga haka yatashi yafita,sai da ya leka dakin mamuh ya rarrankwashi mariya sannan yafito yana kunkunin idan tasake zuwa sassafe ta buga masa kofa yana bacci sai ya lakada mata duka. Dakinsa yawace ya rage kayan jikinsa sannan ya kwanta yana nazarin rayuwa, ganin tunanin nasa yana neman yin zurfi yasashi katseshi ta hanyar daukar wayarsa ya fada yanar gizo yana duba labaran abubuwan dake faruwa aduniya.
Har karfe goma saura yana haka zuwa can yatuna da bai turawa rabin ransa good night massage ba dan haka yayi hanzarin tura mata yana lumshe idanu kamar tana kallonshi.
***
Abangaren bilkisu ganin takasa gano wanda yake turo mata da massages dinnan sai tunaninta yabata cewar ya mudan ne cousin dinta wanda sam jininta bai hadu da nasa ba, wani tsaki taja bayan tagama karanta massage din da yashigo yanzu wanda take sa ran nashine, duk ji tayi kunci ya rufeta har saida takira hamood sukayi hira sannan taji damuwa da bacin ran dake tattare da ita sun kau.
Washe gari bayan tataso daga aiki kamar ta biya ta shagon su fahad sai dai tafasa saboda tasan su ammah na can gida suna jiranta saboda gobe za akawo lefen Hindu shiyasa suketa shirye shirye domin bata son lokaci yakure ba ashirya komai ba kuma tasan baza ayi komaiba agidan har sai anjira zuwanta.
***
Shi kuwa fahad yau tunda yafito shago suke tare da husna duk da ba wai yana son zaman nata bane domin kallo daya zaka yimasa ka fahimci haka sakamakon fuskarsa dake hade babu alamun fara'a ita kuwa husna duk inda yayi sai binsa take da kallon so cikeda burgewa domin sosai yau yayi mata kyau,
Yana dinka kayansu Hindu sai labari take bashi na garinsu shi dai kawai jinta yake amma bawai yana son labarin bane.
Yan shagon nasu kuwa kowa sai kallonsu yake yana yiwa fahad dariya kasa kasa,ganin bata da niyyar tafiya shi kuma ta takura masa yasashi fitowa fili yace taje ta tafi da yamma saita dawo, ai tana tafiya babu jimawa yagama abinda zaiyi yabar shagon, shagon su saleem yaje acan suka sha hirarsu wadda kusan rabi ta Bilkisu ce da take can bata san yana yiba. Saida sukayi sallar la'asar sannan suka nufi gida, koda yaje gida abinci kadai yaci daga nan ya kwanta baccin nasa na sabo nan yayishi har na tsawon rabin awa, karfe biyar da wani abu yafarka yayi wanka yafita filin ball duk da yau baya sha'awar buga kwallon amma yana son ya zauna ya kalli masu bugawar, ear piece yasaka acikin kunnenshi yafita yana sauraron wakar fall in love, kamshin oad kawai yake zubawa da haka ya isa filin kwallon yakama katanga yahau ya zauna yabi sahun wadanda ke zaune suna kallo, wayarshi ya ciro yayi dialing number din Bilkisu domin amatse yake da jin muryarta lokacin da ya kirata tana tsakiyar hayaniyar jama'a domin yan kawo lefen basu tafiba suna dai niyyar tafiya matsawa gefe tayi tai sallama cikin muryarta mai mutukar zaki wadda ta saukar masa da kasala mai nauyi cikin sanyin murya ya amsa bayan ya lumshe matsakaitan idanuwanshi sannan yabude su akan masu buga kwallo,
"Mai gado i really loves u...."
Jin abinda yace yabata mamaki duk da bata fahimci wayeba amma tagane itace number din da aketa damunta da turo mata massages dinnan, yanzu kam tagama yarda cewar ba yaya mudan bane wani ne daban wanda bata saniba.
"Uhmmm.kefa? Kina sona?"
Jin abinda yace ta dan nisa kadan sannan tace,
"Yanzu ina cikin wani uzurine amma idan anjima zan kiraka"
Kitt ta katse wayar takoma taci gaba da abubuwan dake gabanta yayinda shikuma tabarshi da faduwar gaba domin bugawa kirjinsa yashiga yi da sauri da sauri......
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:15] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO*_
*KAMAR DA WASA.....!*💖
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*6*
***Bilkisu bata samu kanta ba sai dare bayan sallar isha domin har karfe 9 saura na dare mutane basu bar shigowa kallon kayan ba, sai tara da wani abu ta samu tayi wanka tayi shirin bacci domin a mutukar gajiye take jinta yau tsabar busy din da ta shiga sau daya kawai sukayi waya da hamood, yanzunma bata jin zata iya kiranshi shiyasa kawai ta kwanta taja bargo. Tafara bacci sama sama taji karar wayarta,idonta cikeda bacci ta kara wayar a kunnenta,
"Love..... Bacci kikeyi?"
Jin muryar da bata saniba yasata katse wayar tareda kasheta gaba daya domin bacci take so tayi. Wurin sau biyar fahad yana gwada kiranta sai yaji akashe daga karshe dole sai hakura yayi shima ya kwanta din yana tunata acikin ransa.
Washe gari misalin karfe 10 nasafe ta sauka agaban shagonsu ita kadai domin ta baro khulsum a office tana fassara labaran turanci zuwa hausa itama kawai bikin nan da ya karato ne m d yake daga mata kafa, anutse take takawa babu hayaniya ta nufi shagon su fahad, yana daga waje kofar shagon gaban wani tebur yana yanka uniform din husna da ta kawo masa wuyansa rataye da tape na aunawa, sallamarta ce tafara shiga cikin kunnuwansa yayi saurin waiwayawa ganinta yasashi fadada murmushinsa yana sake bude kofofin hancinsa domin shakar kamshinta dakyau,
"Shiga ciki mana hajiya"
Murmushi tayi tanufi cikin shagon tana cewa,
"To nagode, Allah dai yasa ka cika alkawari"
P cap dinshi ya maida baya yabi bayanta yana murmushi,
"Ah haba hajiya ai ni bana magana biyu"
Kanta tabawa mazauni agaban kekenshi tana kallon cikin shagon wanda babu kowa aciki yau da alama sauran yan shagon sunyi nisan zango.
"Am nace nawane ma ragowar cikon kudin dinkin gaba daya?"
"Dubu biyar banda naki"
Tana kokarin bude jakarta batare da ta kalleshi ba tace,
"Ban gane banda nawa ba, ni baka dinka nawa kayan bane ko yaya?"
Zama yayi a mazauninsa yana wani murmushi mai kayatarwa,
"Na dinka miki, kawai dai ni ka'idata ce haka"
Dan dakatawa tayi daga binciken cikin jakarta da takeyi ta dago ta kalleshi cikin rashin sa,a idanuwanshi suka sarke cikin nata domin shima lokacin tsaka yake da kallonta, ahankali ta janye nata idanuwan ta maida kan jakarta tana cewa,
"Haka ka'idarka take kamar yaya?"
Tallafe kumatunshi yayi da hannunshi guda daya,
"Akaron farko nakan yiwa customer dina ragi ko indinka masa kyauta saboda ina son yakara dawowa so idan yadawo sai infara yimasa na kudi..."
Murmushi tayi tana jijjiga kai alamar gamsuwa murmushin da yakusa sumar da fahad azaune, kasa koda motsi yayi sai uba uban kallon da yake faman binta dashi har ta ciro kudin ta mika masa, karba yayi yana lumshe idanuwana sakamakon kamshinta da ya kusantoshi mutuka.
Sam ita bilkisu bata san abinda yakeyi ba dayake ma lokacin wayarta tana karar neman agaji alamar ana kiranta, ciro wayar tayi ta daga domin amma ce, tana dauka taji muryar meenah na cewa,
"Adda labour ba amma bace nice, dan Allah ko zaki taho mana da kayan kamshi?"
Agogon hannunta ta kalla na silver wanda yayi mata das,
"Meenah kufa matsala gareku,sakonku baya karewa, bari zan dubo"
Bata jira abinda meenan zata ceba takatse wayar ta cilla cikin jaka sai lokacin fahad ya dauke idonshi daga kanta,
"Am muga dinkunan...."
Fito dasu yashiga yi daya bayan daya, nan bilkisu tasoma santinsu tana yabawa dasu domin ba karamin tsaruwa sukayi ba koda tazo kan nata ai sai ta raina nasu mamaa domin har na amaren bafin nata kyau yayiba gashi dinkin yafitar da shape mai kyau,
"Kai amma fa dinkin sunyi kyau gaskiya nasamu tailor insha Allah daga yanzu kai zan rinka baiwa dinkuna na"
"To hajiya Allah yakawoki"
Daga haka yadauko babbar leda yafara ninke kayan yana zubawa aciki tana tayishi sai yabon dinkin take, daf da zasu gama zuba dinkin cikin leda ya dubeta ta kasan ido,
"Hajiya ba zaki gayyaceni bikin ba kuma?"
Murmushi bilkisu tayi,
"To ai sai dai ingayyaceka daurin aure"
"Ai ban san angwayenba"
"To zan gayyaceka dinner"
Sai da ya dan bude idanuwanshi sosai sannan ya marairaice murya,
"To ai idan nazo baza abarni inshiga ba tunda babu wanda yasanni"
Murmushi ta kumayi ta mika hannu zata dauki ledar kayan amma sai ya hanata yaci gaba da rikewa,
"Karka damu kowa zai shiga tunda bamu raba gate pass ba"
"To shikenan zanzo insha Allah hajiya.... Kodan inga yanda kayan nan zasuyi miki domin zanso ingansu ajikinki"
Ya karashe maganar ciki ciki ta yadda bazata jiba, ai kuwa bata ji dinba tadai ji abinda yafada dafarko amma daga karshe bata jiba, tana kokarin daukar kayan ya hanata ya daukar mata yana fadin,
"A'a hajiya bari na rakaki dashi"
"Ok nagode amma ina son shiga kasuwa ne akwai abinda zan siya"
"Karki damu babu komai muje"
"To nagode"
Handbag dinta ta dauka suka fito yana biye da ita, suna fitowa hamza na zuwa dan haka fahad bai rufe shagonba yawuce yabi bayanta, har cikin kasuwar ya rakata ta kammala siyan kayan kamshin sannan suka fito bakin titi inda zata hau napep, shine yatsaya domin tare mata amma duk wanda yatare sai yaga da namiji aciki sai yace suje da haka har yatare kusan guda uku ana hudunne yaga namiji daya mace daya, cemata yayi ta zagaya ta saitin macen saita zauna, hakan kuwa tayi ya kinkimi kayanta ya mika mata tana yimasa godiya, baice mata komaiba sai murmushin da yake aika mata dashi can akasan ranshi kuma yana cewa,
"Zanyi missing dinki"
Yana tsaye har saida yaga sun kule sannan yakoma shago, yana shiga da kamshinta yasoma yin arangama nan ya lumshe idanuwanshi aranshi yafurta,
"Kamshinki yafi na kowacce mace"
Zama kawai yayi saman benci yakasa cigaba da aikin da yafara, sai hamza yake tayawa hira wanda ke kan kekenshi yana dinka wani leshi, ahaka yar nacin nasa husna tazo ta sameshi, shifa yarinyar nan har mamaki take bashi kamar ba daliba ba yawonta yayi yawa yakan kasa gane lokacin da take shiga class, yana mata dinkin yana daddaure fuska ita kuwa ko ajikinta dan sai zuba take kamar kanyar da bata da zaki.
***
Haka al'amura suka cigaba da tafiya, abangaren su bilkisu dai kowa kagani acikin hidima yake domin biki yazo gaba daya gidansu angyarashi ansake masa sabon fenti sannan kayan falon amma suma ansakesu tun daga kan kujeru har tv da labulaye da sauransu, ada carpert ne malale afalon amma yanzu tiles akasa mai tsada sai katuwar plasma tv da aka manna abango ga kujeru kirar royal chairs nan falon ammi ya dawo tamkar na yarinya duk da tanata rokon Abba akan yabar gyaran haka yaji da kayan dakin yara domin aurar da yanmata biyu lokaci daya ba wasa ba amma yace itama so yake yadawo da ita amarya ai kuwa hakance tafaru domin gidan ba karamin kyau yayiba dan hatta dakin bilkisu Abba yagyare mata shi ansake mata labulaye sabbi sannan ansaka mata tv yar madaidaiciya abangon dake kallon gadonta sannan gefe ga dan fridge dinta ga uban fenti da dakin yasha nan daki yafito yayi fes dashi. Ana saura kwana biyu biki dakyar bilkisu tasamu ta tafi saloon da kunshi itada kawarta khulsum ba ita tadawo gidaba sai karfe biyar saura tana shiga dakinta tajiyo sallamar mutanen garko wato su iyallo, kasancewar daga ita sai daurin kirji yasa bata fitoba domin tana jiyo maganar ya mudan da alama shine yakawo su. Kai tsaye iyallo dakin bilkisu tashiga lokacin ita kuma tana toilet, ganin irin gyaran da dakin yasha yasata rike haba tana tafa hannaye tana zuba salati,
"Ah lallai wannan shine zama daram wato babu ma ranar tashi, irin wannan daki haka kamar agidan miji? Tab... To Allah yasawwaka, iye... Lallai.... Duniya sabuwa"
Juyawa tayi tabar dakin tafita ta nufi cikin gidan wato falon amma wadda ke can tana gaggaisawa da baki domin iyallo ba ita kadai tazo ba su wurin takwas sukazo ciki harda yayarta inna maigado takwarar bilkisu da kuma yayanta guda biyu wato kannen Abba gwaggo uwa da yafendo sai "yayansu,nan tazauna tana tabe taben baki da harare harare, sama sama ta amsa gaisuwar amma nan da nan aka cikasu da ruwa, lemo da abinci tunda dama ansan da zuwansu, shi dai ya mudan bai wani jimaba yakoma yabarsu anan. Bilkisu sarai taji abinda iyallo take fada lokacin da tashigo dakinta, tana wanka tana zancen zuci,
"Su iyallo trouble maker ansauka, haka kuma za ayita fama har sai ranar da kika bar gidan nan, Allah yarabamu lafiya"
Da zancen zuci tagama wankan tafito, ta shirya agaggauce tana saka kaya su Hindu na shigowa shiyasa koda tafito tare suka rankaya falon amma........
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:15] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO.*_
*KAMAR DA WASA....!*💖
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*7*
***Su maama sai yaba kunshin nata sukeyi yayinda ita kuma take yaba kwarewar mai gyaran jikinsu domin kwana uku kacal da fara yimusu har ta sauya musu kamanni, Hindu da maama sarakan rashin kunya ganin takalmansu iyallo tuni suka tura dan kwali gaban goshi duk da hararar da bilkisu keyi musu haka suka dauke kai, itace tafara shiga cikin falon uwar harara iyallo ta tarbeta da ita tana tabe baki sabanin inna mai gado da ta washe hakora tana yimata lale tamkar zata goya bilkisu dan murna da tsantsar kaunar da take yimata, suna tsaka da gaisawa su maama suka shigo, maganar iyallo ita ta katse kowa daga gaishe gaishen da akeyi,
"Ke samodara daga ina kika tafi kika bar yar labibiyar yarinya dan tsabar rashin hankali?"
Dauke kai maama tayi saboda tasan da ita take bata amsa mata ba ta nufi inna maigado domin duk sunfi sakewa da ita,
"Yanzu ke kuma dan Allah bakiji kunyaba? Kiduba ki gani duk kannenki sunyi aure sun barki, gaku nan ku hudun duk kanku daya" Iyallo tafada tana hararar bilkisu, ai rufe bakin iyallo keda wuya Hindu ta dora,
"Kuji iyallon nan da takura, to dan munyi aure mun barta sai me? Kuma ma naga ba wuce shekarun auren tayiba..."
"Ke kika kulata ma, wai wani nan munyi kai daya da ita to ai halittar tatace mai kyau shiyasa har ba a iya banbance itace babba cikinmu....kum...."
Tsawar da ammah ta daka musune yasa maama yin shiru bata karasa fadar abinda tayi niyya ba nan amma tashiga yimusu fada ta inda take shiga bata nan take fitaba, ita kuwa iyallo cewa take,
"Rabu dasu kibarsu su zageni kamar yadda suka saba, fitsararru dama me suka iya inbanda rashin kunya da rashin arziki? To wallahi bari uban naku yazo..."
Inna maigado ce tasoma tausarta tana bata hakuri ita dasu yafendo, su Hindu kuwa ko ajikinsu asalima tashi sukayi suka bar wurin suka wuce dakinsu.
***
Tunda su iyallo suka zo kowa yashiga takura acikin gidannan gata da fadan tsiya ga sa ido gashi bata iya gani tayi shiru komai tagani sai tayi magna,abinda inna maigado bata iyaba kenan shiyasa kullum cikin yimata fada take wannan dalilinne yasa su bilkisu basa son zuwa garko wurin iyallo saboda fadanta da masifa su maama ne kadai daidai da ita domin basa bar mata.
Haka dai aka cigaba da lallabawa, gida ya cika dam da yan uwan Abba da amma domin itama ana igobe sa lalle yan uwanta suka zo daga dawakin tofa, mota uku suka ciko da yayyenta da kannenta da sauran 'yayan yan uwa, bilkisu kam yanzu tazama ba zama domin har tafi amaren zama busy, ko hamood dinta sai yar hi hi sukeyi, haka shima fahad yanzu bai fiya samunta ba duk da hakan yana sakashi cikin damuwa amma yazaiyi dolensa ya hakura.
Ranar alhamis aka fara gudanar da biki domin ranar ne sakun lalle anan unguwarsu gidan aminin babansu mai sabulu anan akayi kamun kamar yadda al'ada ta tanadar,amare sunsha kyau mutuka cikin shigar da sukayi ta ruwan bula, itama bilkisu itada mama wani leshi suka saka dan ubansu sai walwali suke, an cashe mutuka sannan anwarwasa haka aka tashi kowa cike da farin ciki, agajiye likis bilkisu takoma gida bayan sallar magriba ga dakinta ma cike yake da baki dole sai dakin Abba taje tayi shirin bacci dayake har lokacin shi bai shigoba, ko takan wayoyinta bata biba taje ta kwanta adakinsu meenah domin ta huta.