Kenza eBookz

Kamar da wasa complete novel - Chapter 4

Kamar da wasa complete novel - Chapter 4

Kamar da wasa complete novel Chapter 4: Kamar da wasa complete novel Chapter 4. Washe gari aka daura aure kuma ranar ne zasu gabatar da dinner party dinsu…

3,297 words

Washe gari aka daura aure kuma ranar ne zasu gabatar da dinner party dinsu a al-mukarram event center,tun safe amare basu samu zama ba hakama bilkisu bayan an idar da sallar juma'a a babban masallacin dake cikin unguwar tasu ta hotoro aka daura auren, auren Hindu da angonta Mus'ab aka fara daurawa kasancewar itace babba akan sadaki naira dubu talatin sannan aka daura na meenah da angonta Isma'il itama akan naira dubu talatin,gidansu kancame yake da hada hadar jama'a koda akazo yin albishir din daura auren iyallo yada magana tai tayi da habaice habaice duk inda bilkisu tawuce kuwa ko amma ko su Hindu sai ta rakasu da harara su kam basu san tanayiba domin sabgar gabansu sukeyi, maama cema da hudah tayi kashi taje tana cire mata pampers iyallo tazo zata isheta da fadan akan me zatazo gaban rijiya tana yiwa mutane kazanta, ita kuwa maama ta gurmuda mata baki tana farfara ido rankwashi iyallo takai mata tana fadin,

"Fitsararriya yau dinma fitsarar zakiyi min abainan nasi?"

Maama bata kulataba ta sabi yarta tayi falon amma wadda ke can itada danginta da abokan arziki sukuwa su iyallo tasu tawagar ta yan garko suna sitting room.

K'arfe takwas da rabi aka fara tafiya wurin dinner,amare da angwaye ba karamin kyau suka sha ba haka itama bilkisu ta hade cikin material din da fahad ya dinka mata tayi masifar kyau tasha head golden dama yau babu maganar mayafi daga ita har kawarta khulsum basu samu zama ba domin sune masu tsara komai.

Cikeda doki fahad yasha wankansa cikin blue din tissue sabo fil da hularsa samfurin minister wacce ta saku da asalin dinkin hannu yayi kyau har yagaji, turaren Amirul oad yayi amfani dashi ya gauraya da turaren black xxs nan fa yafito tsaf dashi saurayi kalar birni, bakin takalmi sau ciki yasaka yadauki agogo yafita lokacin karfe takwas daidai na dare, sai da yashiga cikin gida yayiwa su ayiyah sallama mamuh sai tsokanarsa take tana cewa yagaida budurwar tasa, su Mariya kam saida ya cafki Maryam ya zuba mata rankwashi sannan yafita domin sashi sukayi agaba da dariya da kus kus, yayansa Abba yana zaune akofar gida yafito, shi dinma kallonsa yayi cikeda tsokana yace,

"K'anina yau hira aka nufa ne?"

Dariya yayi yawuce yana fadin,

"Wallahi wani biki zanje"

"To adawo lafiya"

Saida ya amsa sannan yawuce, koda ya isa almukarram event center tuni har wurin ya dinke da jama'a sai kawo mutane akeyi a motoci yayinda wasu sukazo a keke napep wasu kuma da kafarsu ma suka shigo cikin wurin, abangaren fahad shima yabi sahun wadanda suka shigo da kafarsu domin tafe yake hannunshi daya cikin aljihun wandonshi dayan kuma yana latsa wayarshi ta hannu, duk wanda ya kalleshi kallo daya baya iya gamsar dashi har sai yakara na biyu.

Yana isa gaban hall din yayi tozali da yanmatan amare sunsha anko kowacce naji da kanta, ido yashiga ciccilawa yana son yaga ta ina zai hango tauraruwar tasa amma bai samu damar ganinta ba har aka gama shigewa cikin hall din nan shima yamaida wayarshi aljihu ya shiga, kusa da wasu samari su uku yaje ya zauna dama mazaunin mutum hudune domin kujerun guda hudune, gefensu kuma wasu matane suma zaune su hudu, bai kai minti biyu da zamaba ya hango bilkisu tana rikeda hannun khulsum da wasu abubuwa a hannunsu wanda bazai iya gane ko menene ba, ji yayi yana dana sanin yimata wannan dinkin domin jikinta babu ko mayafi amma fa tasha kyau har tagaji kayan sunyi mata dadas ajikinta dukkan shape dinta yafito masha Allah, goshinsa yadafe ya sunkuyar da kai sakamakon sara masan da yaji kan nasa yayi, hankalinsa bai kara tashi ba sai da ya hangota kan step taje wurin amaren suna yin kus wadda babu wanda zai fahimci me suke cewa domin wurin sautin kidane yake tashi ahankali cikin wakar Umar m Sharif ta ranar kuke jira....!, yayi nadamar yimata dinkin nan domin gani yake kamar kowa na wurin ita yake kallo, sai da kowa ya nutsu sannan aka fara gudanar da shirye shiryen da aka tsara, taro da addu'a aka fara budewa sannan aka gayyaci babbar yaya wato bilkisu domin tabada tarihin amarya amma guda daya daga ciki, abunku da yar jarida wacce tasaba nan tazo ta zayyano tarihin Hindu daga karshe tajuya tana kallon isma'il angonta,

"Ango amaryarka tana da kiriniya sosai ada musamman wurin zane domin gaba daya bangon dakinsu da jikin wardrobe dinsu zanen tsintsaye ne da ciyayi, muna addu'ar Allah yasa bazata Zane muku bangon dakunanku da zanen tattabaru ba...."

Kowa na wurin saida ya dara nan ta sauka tabada abin maganar aka kira maama itama tabada tarihin auta minah. Duk inda tayi idanun fahad na kanta ji yake kamar yatashi yaje ya kareta mutane su daina kallonta amma babu damar hakan, lokacin da aka fara raba abinci da abin sha hirar matan dake zaune kusa dasu taja hankalinsa,

"Yanzu dai Yahanazu tagama auren yaranta saura maigado kuma babbar banza ko kunya bataji duk takai kannenta daki ita tana zaune agida..."

"Bakiga harda sake gyaran dakiba domin a tabbatar mana da ba ranar aure"

"Ai uwar tata ke daure mata kugu, idan taki fito da miji basai su hadata da duk wanda suka so ba..." Daya matar tafadi cikin takaici, idonshi ne yakai kan bilkisu wacce ke tsaka da hidimarta khulsum ta miko mata wayarta nan ta Karba ta nufi kofar baya, zip din rigarta ta baya ya dan sauka har hannun farar bra din jikinta ta dan leko amma saika lura dakyau zaka gani, cikin azama, kirjinsa yana fat fat yabi bayanta tana tsaye tana waya gadon bayanta duk awaje, cikeda kishi karara yatsaya abayanta ya kareta, jin tsayuwarshi yasata juyowa ta kelleshi bayan ta maida wayar kunnenta......

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:15] Hafsat Rano: © _HASKE WRITERS ASSO._

*KAMAR DA WASA....!*💖

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*8*

*Mai fitarmin da book kiji tsoron Allah haka kuma wadanda ake turowa kuji tsoron Allah kudaina karanta min mutukar ba siya kikayi ba saboda kamar da wasa wannan karon na kudine,idan kina so ki biya ki karanta.*

***Sai da idanuwansu suka sarke da juna sannan tajanye nata ahankali bayan ta juya masa baya, bayan nata yake bi da kallo kasa kasa, jin takun tafiya abayansu alamun wani na zuwa yasashi saurin kai hannu kan zip din yayi sama dashi hakan yayi daidai da karasowar khulsum wurin, saurin matsawa baya yayi yayinda ita kuma Bilkisu tajuyo atsorace amma ganin khulsum tsaye bayanta tana waya yasata sauke ajiyar zuciya domin tagane itace taja zip dinta ko kadan bata kawo cewar fahad ne ba, ita kuwa khulsum bata ma san abinda ke faruwa ba kawai dai ta iskesu tsaye ne, yayinda gogan ke tsaye yayi mata kurr da ido hannayensa sanye duka cikin aljihun wandonsa.

Kusan tsawon mintuna biyar ta dauka tana wayar daga bisani sukayi sallama da hamood dinta takatse wayar tajuyo tana kallon fahad dan tuni khulsum tabar wurin,

Langabe kai yayi yana kallonta tamkar wani yaro,

"Kazo ashe?..."

"Uhm hajjaju nazo tun dazu"

Murmushi tayi tana duba wayar dake hannunta,

"Zaka jira atashi ai ko?"

Girgiza kai yayi har lokacin kansa langabe yake,

"Idan nayi dare sosai zaneni za ayi agida...!"

Ita abinma dariya yabata yanda yake yi mata wani shagwaba sai kace hudah,

"To yanzu ya za ayi?"

"Muje ciki amma nanda 10 minutes zan tafi"

"Ok babu damuwa muje..."

Sai da ya dan rausayar da kai sannan yawuce tabishi abaya, kai idan kaga yanda suka basar sai abin yabaka sha'awah tamkar wasu saurayi da budurwa,duk da hill din dake kafarta akafadarshi tsayinta ya tsaya ahaka suka kai tsakiyar hall din wanda tuni ya kancame kasancewar amaren sun fito suna takawa mc kuwa sai kiran sunan Bilkisu yake yana cewa yana son ganin babbar yaya wato adda bilkisu yayar amare.

Bilkisu ai jaka ta balle tashiga cikin kannen nata tana yimusu ruwan sabbin nairori suma suna yimata, su hudu gwanin sha,awa domin harda maama kamar abin hadin baki kuma sai hudah da mina suka soma kuka harda maama, ita kanta ji tayi kwalla tana taho mata shiri tabar cikin filin ta nufi hanyar fita, daga inda yake zaune yana ganin duk abinda ke faruwa abisa dukkan alamu akwai shakuwa mai girman gaske tsakaninta da kannen nata, tashi yayi yabi bayanta, kamar yadda yazata kafin ya cimmata har ta ida ficewa. Abakin kofar hall din yaganta kan baranda ta jingina da bango,

"Haba hajjaju da girmanki..."

Juyowa tayi suka hada ido idanuwanta har sun danyi ja,murmushin karfin hali tayi,

"Badai har zaka tafiba?"

"Ehh gaskiya wucewa zanyi kar gida su rufe min kofa"

Wannan yaron yanada abin dariya ta ayyana hakan acikin zuciyarta bayan ta sake murmusawa,

"To shikenan nagode, yanzu muje gaban waccan motar inbaka naka hasafin..."

Dan kada idanuwanshi yayi,

"Nidai gaskiya kibarshi, yanzu sai kowa yasan nazo biki? Bana son daukar kaya..."

Murmushi tayi tajuyo sosai tana kallonsa,

"To shikenan Allah ya kiyaye hanya nagode"

"Ba rakiya?"

Wani murmushin tayi har saida hakoranta suka bayyana tasauka tana nuna masa hanya alamar suje, jerawa sukayi har kusa da gate nan tajuya takoma ciki amma me tana zuwa gaban hall din taji yace,

"Saida safe atashi lafiya"

Juyowa tayi cikeda mamakin sake biyota din da yayi amma kafin tayi magana har yajuya yatafi, ciki takoma inda aka cigaba da hidima ba atashi daga wannan dinner ba sai karfe goma sha daya saura ahakanma dan abbansu ya iyo waya yace lallai lallai atashi haka ne nan aka rufe taro da addu'a aka tashi kowa yanufi gida. Fahad kuwa koda yakoma gida raba dare yayi yana sakawa da kuncewa kawai tunanin bilkisu ne ke azalzalar ruhinsa, harga Allah yakamu da mugun sonta to amma bashida tabbacin ko akwai wanda ta tsayar amatsayin mijin aure, yajima yana juyi har dai daga karshe yaji muryar yaya Abba yana cewa,

"Yau meke neman hana dan kanina bacci??"

"SO" yafada acikin zuciyarsa amma azahiri sai yajuya ya kalleshi ta cikin hasken kwan lantarkin da basu kasheba,

"Babu abinda zai hanani bacci kawai dai nagajine..."

"To idan kahuta sai ka kashe mana wutar muyi bacci ko?"

Murmushi fahad yayi bayan yatashi zaune,

"Gaskiya nifa bazan iya bacci aduhu ba harga Allah.."

"To nikuma bazan iya bacci da haskeba, Allah yakawo mu kuma..."

Dariya fahad yayi yana jan pillow dinshi,

"Kuma ahakan kasan har kaguwa nake kazo weekend saboda mu cigaba da fada akan rufe kofar toilet da budewa duk da dai kana hanani bacci..."

Dariya shima yaya Abba yayi yagyara kwanciyarsa yana fuskantar fahad din,

"The same thing da yake faruwa dani kenan duk time din da nakoma school wallahi wani lokacin har dariya drama dinmu kebani abokaina suyita tambayata idan sunga ina dariya ni kadai daga karshe dai nasanar dasu kai natuno kullum sai munyi fada saboda ni bana son haske kai kuma baka son duhu sannan ni bana iya kwana har gari yawaye ban shiga toilet yakai sau uku ba gashi kaikuma k'ara kadance ke tada kai daga bacci gashi kofar k'ara take dashi..."

Dariya fahad yayi yana kokarin kwanciya,

"To ai idan baka nan alla alla nake kadawo kaci gaba da bude kofar"

Dariya sukayi gaba daya nan suka cigaba da hirarsu kamar abokai dama ko tsaye abban bawani fin fahad yayiba haka suka taso tare kamar twins, wannan hirarce ta daukewa fahad hankali dan kafin su farga har 12 da rabi takusa, tashi Abba yayi yanufi toilet nan fahad yasa pillow yatoshe kunnenshi lokacin da yaji kofar tafara kara kiiiiyyyyyyyy, Abba na fitowa yakashe wutar dakin duk da haka saida fahad yakunna light awayarshi sannan ya iya bacci.

*** Su Bilkisu yau zasu gama biki domin kuwa yau za a mika amare gidansu, tun safe Bilkisu take tattara musu sauran kayayyakinsu da ba akai ba kafin kace me gida yacika da yan kai amare ita kam Bilkisu batayi niyyar zuwaba amma khulsum ta matsa sai sunje domin saurayinta zaizo yakaisu, ana yin sallar isha'i akayi haramar kaisu saida aka gama zagawa dasu wurin iyaye sukayi musu fada sannan aka tafi kaisu gidajensu. Hudah aka fara rakawa unguwar jan bulo sannan aka raka Mina sharada, duk inda sukaje Bilkisu bata shiga domin tasan gidajen asalima kayan ciki sune suka jera. Misalin karfe goma suka dawo daga rakiyar amaren, yanzu kam yan biki saura kadan domin dama yau duk wasu suka tattafi sai najiki irinsu iyallo da yan uwan amma harda mahaifiyarta hajjo, ba karamin dadi tajiba ganin dakinta fayau babu kowa nan ta dauko hudah bayan tayi mata wanka itama tayi tabi lafiyar gado domin maama na can wurinsu amma acan zata kwana. Wani lafiyayyen bacci tayi domin tunda ta kwanta bata motsa ba saida 6 nasafe tayi nan tatashi tayi salla tasake komawa har 9 sama sama tajiyo muryar hajjo kakarta tana fadin,

"Ohh maigado ai sai asaceki dake da katifar da kike kai batare da kin saniba, kowa yatashi banda ke"

"Ai dole tayi bacci hajjo wallahi tagaji dayawa tasha zirga zirga" Inji maama wadanda suka shirya tsaf domin zuwa gidan amare suda su iyallo, sai bayan sun tafi da dadewa sannan bilkisu tatashi ganin babu hudah akusa da ita ya tabbatar mata da tabi tsohuwarta, wanka tayi ta caba kwalliya tasha gown ta atamfa dark blue, wurin ammah ta nufa wacce ke can dakinta ita da baki yan Allah sanya alkhairi, gaisawa dasu kawai sukayi tafito tawuce kitchen koko da kosai ne akayi na karin kumallo sai dankali da kwai wanda aka soyawa abba, dankali da kwan ta diba ta zauna tayi nak sannan tafito sai lokacin wayoyinta suka fado mata dan rabonta dasu tun ranar dinner da daddare, daki takoma ta daukosu gaba daya ta kunna su nan sakonni suka yita shigowa rututu kusan 10 amma aciki guda biyu na hamood ne wanda ke sanar da ita zai dawo Nigeria jiya idan yazo zai kirata dan Allah tazama mai rike masa alkawari domin itace matar aurenshi, dariya tayi tana jin farin ciki yana ratsata, sauran massages din kuwa duk na fahad ne wanda bata da masaniyar cewa shine, daga karshe ajiye wayoyin tayi ta dauko laptop dinta tayi downloading din wani Indian series mai suna Rangarasiya ita kam Allah yadora mata kaunar Indian film tana tsaka da kallo khulsum tayi sallama,

"Au ke baki tafi gidan amaren ba?"

Murmushi tayi,

"Me zanje inyi musu kuma"

"Ai shikenan, bani ruwa insha"

Kawar da laptop din tayi daga gabanta ta mike ta dauko mata ruwan ta miko mata,

"Ya labarin mutumin ne?"

"Yataho ai may be ma yanzu ma yasauka"

"Ahh lallai abun yazo amarya"

Shiru bilkisu tayi saboda tasan kawai neman magana ne irin na khulsum.

Dasu iyallo sukaje gidajen amaren kowacce aciki babu wacce batayi cikiyar bilkisu ba amma babu ita sai maama itace ma ke cemusu kila da yamma bilkisun zataje musu nan ta gyaggyara musu abubuwan da yadace sannan suka tarkato suka dawo iyallo dai sai sakawa danta albarka take kan irin rawar daya taka wurin zubawa yayansa kayan daki nagani na fada. Har suka dawo gida bilkisu natare da khulsum suna kallo saida rana tafara yi sannan tatafi domin tanada karanta labaran rana.

Da yamma dukkan baki suka tafi amma banda iyallo ita kam tana nan Allah kadai yasan ranar tafiyarta, haduwa sukayi maama da bilkisu suka gyare gidan tsaf yadawo yanda yake da, suna kammalawa Abba na dawowa daga garko dama duk karshen wata yake zuwa ya duba garin nasa a matsayinsa na hakimin garin manya manyan kaji da zabbi aka shigo dasu sai kwan zabbi cikin bokitin roba dama duk ranar da yaje haka yake dawowa da kaya niki niki domin jama'ar kauye akwai kara banda su yalo, gwaiba da sauransu, nan dai su bilkisu suka shiga aiki baji ba gani ita dai iyallo tana zaune tsakar gida kan tabarma ta kishingida tana ganin mai shiga da mai fita domin mutane sunata zuwama amma Allah yasanya alkhairi. Sai dare maama ta tattara tatafi bayan mijinta yazo daukarta, bilkisu rufe kofarta tayi tai kwanciyarta nan taga text din minah da na Hindu kamar hadin baki duk suna yimata korafin rashin zuwanta murmushi kawai tayi ta ajiye wayar tafada kogin tunani.

Washe gari bata tashi dawuri ba sanin acikin hutu take ba aiki zata fita ba, koda tafito tuni har anhada abin karyawa kowa yaci sai nata kadai dauka tayi takoma dakinta taci tana kammalawa kiran abba yashigo wayarta cikeda ladabi ta daga nan yace taje yana kiranta, hijab ta dauka tafita jikinta na bata lallai akwai abinda ke faruwa bare iyallo trouble maker tana nan.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:15] Hafsat Rano: © _HASKE WRITERS ASSO._

*KAMAR DA WASA...!*💖

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*Dan girman Allah na rokeku kudaina fitar min da book, ku kuma wadanda aka turowa kuji tsoron Allah idan baki siyaba karki karanta.*

*9*

***Falon tsit sai fadan iyallo dake tashi duk tabi ta cikashi da hayagaga,

"Haba yarinya tadade da kawowa misali amma kun zuba mata ido sai dai garin Allah idan yawaye tayi wanka ta saba jaka tatafi wani wai aikin gwamnati, to wallahi ya isa haka sam bazan lamunta ba kannenta duk gasu can adaki amma ita tana gida, wannan ai ba dabara bace karatunnan tayi ta dada tayi ta dada wai shin karshen biro da takarda zata gani? To wallahi wata biyu kacal na bata ta fito da miji idan ba hakaba ga dan uwanta nan mudan ai tushensu daya sai a aura mata shi...."

Zama bilkisu tayi tana sauraron fadan iyallo har saida tayi shiru sannan Abba yayi magana yabata hakuri yace insha Allah za ayi yadda tace, ita kam amma shiru tayi batace komai ba har akayi aka gama. Juyawa Abba yayi ga bilkisu yace,

"Uwata kinji abinda hajiya tafada lallai lallai kifito da miji cikin wata biyu ayi miki aure"

Daga kai tayi yayinda iyallo ta bude murya,

"Yawwa gaya mata da kyau, wannan yawon karatu ya isa haka"

Sallamarta abba yayi tatashi tatafi takoma dakinta ta zauna, sam bata sa abin aranta ba domin karma ya dameta taci gaba da harkarta. Kwana biyu da faruwar hakan iyallo ta tattara takoma garko kuma aranar maama tazo nan bilkisu take bata labarin abinda yafaru,

"Iyallo jaraba, ai wallahi adda labour da kin wanketa tas kafin tatafi"

"Ke maama kar nakara jin haka, ba mahaifiyar babanku bace? Itama fa tana da iko daku infada muku gaskiya, kedai mai gado kawai kiyi abinda tace ki fidda miji kiyi auren nan kihuta muma mu huta da maganganunsu"

Bilkisu dai batace komai ba domin har yau bata samu hamood ba shima kuma bai kirata ba, sai yanzu hankalinta yasoma tashi ganin ankusa wata daya domin har hutunta yakare takoma aiki, agefe daya kuma iyallo kullum cikin bugowa abba waya take tana kara jaddada masa maganar auren mudan da bilkisu, ita kuwa bilkisu ji take akan ta auri ya mudan gara ta auri koma waye.

Wasa wasa lokaci sai tafiya yake amma shiru babu labarin hamood duk ta inda take tunanin zata sameshi tarasa domin daga Facebook dinshi har Twitter da instagram duk shiru, yanzu kam tashiga mutukar damuwa gashi wanda ke damunta batare da tasan ko wayeba bai fasaba kullum yake kiranta kuma yaturo mata text ganin wankin hula na shirin kaita dare yasata nemarwa kanta mafita. Daren ranar kwana tayi batayi bacciba tanata sakawa da kwancewa daga karshe shawarar khulsum ta fado mata inda take cemata,

"Ni kawai ina ganin ki baiwa bawan Allahn nan dama wallahi yafito ya bayyana miki kansa idan yayi miki kawai ki aureshi ki manta da wani hamood tunda har yanzu babu wani labari game dashi...."

Lumshe idanuwanta tayi bayan ta dafe kanta dake sara mata, tabbas yazama dole ta dauki shawarar khulsum mutukar tana son hakanta ya cimma ruwa,wayarta ta jawo ta duba agogo karfe 2 da yan mintuna na dare, text ta soma rubutawa wannan guy din da har yau bata san ko wayeba, bayan yanuna mata yatafi ne ta kashe wayar gaba daya tana jiran zuwa gobe sai ayita takare.

***

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull