Kenza eBookz

Kamar da wasa complete novel - Chapter 5

Kamar da wasa complete novel - Chapter 5

Kamar da wasa complete novel Chapter 5: Kamar da wasa complete novel Chapter 5. Ga fahad kuwa abun ba sauki domin har gobe bilkisu ce zabinsa duk da yasan…

3,369 words

Ga fahad kuwa abun ba sauki domin har gobe bilkisu ce zabinsa duk da yasan tayi masa nisa kokuma tafi karfinshi amma dayake ita zuciya babu ruwanta da duk wadannan abubuwan haka ta nace da soyayyarta, kullum aikin kenan tura mata love massages gashi tun bayan bikin kannenta bai sake ganinta ba dan program dinma da takeyi yanzu shiru sai wata bakuwar murya ce keyi gaba daya yarasa gane abinda ke faruwa. Bayan yadawo daga sallar asubah kamar yadda yasaba yazauna saman katifa yajawo wayarshi da niyyar yakirata ya tadata tayi salla yana kunna wayar yaga massage dinta jikinshi na rawa yabude domin wannan shine karo nafarko da ta taba turo masa sakon karta kwana, da sauri da sauri yafara karanta sakon nata kamar haka;

_Amincin Allah ya tabbata agareka, dan Allah idan har bazaka damuba ina son ganinka gobe agidanmu akwai muhimmiyar maganar da nake so mu tattauna, nagode._

Ajiyar zuciya yasauke yana jin tsoro yana shigarsa, tambayar zuciyarsa yafara yi to yanzu idan taganshi tace baiyi mata ba kokuma tace kar yasake kulata fa? Yajima zaune cikin rashin sanin abinyi daga karshe yabarwa Allah ya kwanta ya tura mata da reply,

_Sarauniyar mata ina fata kin tashi cikin aminci da koshin lafiya, insha Allah yau zan amsa kiranki batare da jinkiri ba amma inaso kibani time da kanki kuma kibani address din saboda ban san gidan nakuba, masoyinki ahar kullum....!_

Daga haka yatura mata ya ajiye wayar yana addu'ar samun nasara acikin wannan al'amari.

Lokacin da taga text din nashi murmushi tayi tana yabawa iya kalamansa acikin zuciyarta, babu bata lokaci tatura masa address din da time din da zaizo, koba komai tana jinta da dan dama dama yau sabanin kwanakin baya da taketa fama da kunci da bacin rai, hatta amma yau ta fuskanci walwala atattare da ita amma batace da ita komai ba.

K'arfe uku na yamma kiranshi yashigo wayarta lokacin tana shiryawa bayan tafito daga wanka, tana dauka yace mata gashi yazo nan tace tana zuwa, karasa shiryawa tayi tafita ta zira flat din takalmi,fararen kujeru guda biyu na roba ta daukar musu tafita zuwa gaban part din Abba wanda ke makotaka da gate ta ajiye ta zauna, waya tayi masa tace yashigo, har yashigo bata dago ta kalleshi ba hankalinta na kan wayarta tana turawa da khulsum text sai dai kamshinsa da ya ziyarceta.

Da sallama ya isa wurinta ta amsa batare da ta dago ba, zama yayi yana yimata kallon kurulla, ashe ita din yar babbar koface bai saniba sai yau domin mahaifinta yarike mukamai daban daban domin yanzu haka shine commissioner na ruwa ajihar sannan kuma mai baiwa governor shawara ta musamman akan harkar ciyar da makarantun kasa da secondary,

Dagowa tayi ta kalleshi idonta yashiga cikin nashi nan mamaki ya cika ta domin ganin wanda ke gabanta,

Murmushi tayi,

"Sannunka da zuwa musa..."

Murmushin shima yayi,

"Yawwa barkanki dai hajjaju amma muhammadu nake ba musa ba"

"Ayya sorry namanta ne, ya aiki?"

"Alhamdulillah"

"Allah yataimaka"

"Amin"

Shiru sukayi dukkaninsu, kafin daga bisani ta danja numfashi tace,

"Dama kaine wanda ke kirana sannan yake turo min wannan massages din?"

Babu fargaba ko tsoro ya daga mata kai,

"Eh nine..."

Murmushi tayi ta maida kanta gefe,

"Haba Muhammad to ai ni ba sa'ar aurenka bace.."

"Ko menene dalili?"

"Saboda nayi maka girma ai,inada kanne twins kamarka el'ameen da elmustapha suna Sudan suna karatu"

"A'a mutukar kin amince zaki aureni toni wallahi bakiyi min wani girma ba"

Murmushi tasake yi tana kallon Rabi mai aikin amma wadda aka kawo mata kwana biyu da suka gabata domin tayata aikace aikace, ruwan roba da lemon kwali tazo ta ajiye agaban fahad sannan tatafi hakan yabaiwa bilkisu damar cigaba da fadin abinda ke ranta,

"Muhammad wallahi ni ba mate din aurenka bace, saboda ko ahaifi na girmeka sosai, ai zakaji kunyar nuna ni agidanku da wurin abokanka amatsayin mata"

"Mutukar kin amince wallahi ni babu maganar kunya, kece dai kawai zakiji kunyar nuna ni amatsayin mijinki saboda nayi miki kankanta"

Fuskarta babu yabo babu fallasa ta kalleshi babu alamun wasa tace,

"Kasan me nake so dakai? Daga yanzun nan kar ka kuskura ka kuma zuwarmun da magana makamanciyar wannan, ada banma yi niyyar sauraronka ba amma dole tasaka na saurareka sakamakon mutuncin da kayi min abaya"

Shiru yayi yana faman aikin goge screen din wayarshi da handkerchief din dake hannunshi sai zuwa can yanisa ya kalleta kadan ta kuwa sha kunu kamar bata taba dariya ba,

"Shikenan tunda haka kikace amma ni anawa rashin hankalin idan akazo kan batu na aure wasu muhimman abubuwa ake dubawa bawai maganar ka girmi mutum ko shi ya girmeka ba dan haka nidai har gobe ina nan akan bakana dan wallahi ina sonki..."

"Naji kana sona amma ni nagama fada maka ra'ayina idan kaji fine idanma bakaji ba duk daya, sai anjima"

Daga haka tamike ta wuce cikin gida cikeda takaici wannan wacce irin lalacewa ce ace yaro karami wai yazo mata da maganar aure babu ko kunya bare tsoro lallai zamani mai yayi, dakinta tashiga ta watsar da komai dake hannunta ta kwanta kan gado idonta akan tv, gaba daya ranta abace yake meyasa hamood yayi mata haka? Duk da zuciyarta na bata yakinin tayuyu akwai gagurumin abin da yafaru dashi wanda ita bata saniba....

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:16] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA...!*💖

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*10*

*Dan Allah idan baki siyaba karki karanta....*

***Ji take kamar tafashe da kuka ko zata samu saukin damuwar dake addabarta,

"Lallai yaron nan yama raina min wayo wallahi..."

Haka tayita fada tana yin kwafa daga karshe kasa jurewa tayi har saida ta kira khulsum, khulsum na dagawa bilkisu tafara jaraba kamar khulsum din nada masaniyar abinda ke faruwa,

"Gaskiya tailor nan baida kunya wallahi saina saita masa zama"

"Wanne tailor kuma? Inji khulsum,

"Wanda yayi mana dinkunan bikinsu Hindu mana"

"Me yayi miki wai?"

"Zuwa yayi har gida wai sona yake da aure dama kuma yadade yana turo min text harda kirana awaya duk ban san shi bane dan banza,yaron da baifi su el'mustapha ba"

Khulsum najin haka me zatayi idan ba dariyaba nan tashiga kyakyatawa ita kuma bilkisu na masifa daga karshe dai kashe wayarta tayi sai lokacin taga ashe tun tuni tanada ajiyayyen sako da yashigo, cikin hanzari ta budeshi dan tana zaton ko hamood ne amma abin takaici fahad ne,

_Gimbiya kiyi hakuri na bata miki rai wanda bana farin ciki da hakan, kiyi min afuwa kuma ki gafarce ni akan abinda nayi, ni nayi zaton aure ana ginashi ne bisa yarda da amana da kuma gaskiya da kaunar juna baya ga wannan basai an hada da wani abu can waishi fin shekaru ba, ki taimaka min kiyi nazari da tunani akan maganata sannan ki sanyata a mizani na adalci kafin ki yanke hukunci, nabarki lafiya...._

Tsaki tayi ahankali marar sauti itafa yaron nan yafara takura mata kuma gaskiya, bata yi yunkurin tura masa reply ba ta shareshi taci gaba da hadiyar bacin ranta.

***

Dama fahad yasan za ayi haka yasan sai bilkisu ta raina girmansa gashi kuwa hakance tafaru amma hakan ko kadan bai karyar masa da gwiwa ba, yajima zaune a inda tatafi tabarshi yana faman zaman jiran gawon shanu daga karshe yatashi yatafi batare da yasha koda ruwan da Rabi ta ajiye masa ba. Bai sanar da kowa abinda yafaru ba domin hatta salim bai fadawa ba ubangijinsa kadai ya fadawa wanda yake da tabbacin yafishi sanin komai kuma shine zaiyi masa magani sai da yakoma gida sannan yatura mata da text daga nan yaci gaba da harkarsa shima ya shareta duk da yana son yaji daga gareta ga yar naci husna da ta sakoshi agaba kwana biyu kullum ashagon take wuni wai lallai sai ta koyi dinki awurinsa, ko ya shareta bata zuciya bare tatafi haka yake hakura suke hira.

Yau Satinta uku da komawa aiki bayan hutunta da ta cinye wanda ta dauka bayan tadawo daga aiki da yamma ammah ke yimata maganar data dan razana ta wai iyallo tace tana nan zuwa acikin satin nan gara tazo da kanta ayi maganar mudan da ita agama, kadan ta iya cin abincin da ta zubo dambun zogale da wainar shinkafa, daki ta koma ta zauna, yanzu kam yazama dole ta nemo fahad ko dan su shirya deal inyaso daga baya sai su warware, wayarta ta dauka ta tura masa text,daga nan ta wurgar da wayar saman gado tawuce bathroom.

Yana shago yana hutawa bayan yagama wasu dinkunan biki husna ta kawo masa tuwon semo miyar shuwaka amma dayake ba cin girkinta yakeba ko dandanawa baiyi ba sai su hamza ne keta kwasa yana kwance gefe yana kallonsu, wayar yazaro daga aljihunsa yaduba saboda jin sako yashigo shi duk atunaninsa ma kudinsa aka turo masa na dinkunan da yayi saboda yabawa mutanen account number dinshi amma sai yaga sako daga bilkisu tana cewa,

_Salam, yakake, kazo anjima ina son ganinka._

Murmushi yayi yamike yana tattara komatsansa domin amsa kiran gimbiya.

Saida yakoma gida yayi wanka yashirya tsaf sannan yanufi gidansu bilkisu yau kam daga waje ya tsaya ya kirata, ta kwashe kimanin mintuna goma kafin ta fito ta leko bakin gate din,yana tsaye ya jingina kafarsa da bango yana danna wayarshi,

"Bismilllah..." Tafada atakaice, bin bayanta yayi suka shiga cikin gidan inda ta tanadar musu fararen kujerun roba guda biyu. Zama sukayi ta daga kai ta kalleshi, sanye yake da blue din shadda mai kyau harda hula wacce ta saku da blue din zare amma hakan bai hana sumar kanshi bayyana ba,

Shine yakatse shirun ta hanyar cewa,

"Ina yini hajjaju?"

"Lafiya lau, kasan meyasa na kiraka?

"A'a" yafada yana girgiza kai,

"Kace kana sona zaka aureni ko?"

"Uhmm" yabata amsa,

"To nima zan aureka amma bisa wasu sharruda, kaga nafarko akwai wanda mukayi alkawarin aure dashi wanda mu duka muna son junanmu amma aka samu wata yar tangarda bama jin juna nikuma kakata ta matsawa babana akan lallai sai nayi aure acikin watanni uku kacal idan ba hakaba ta aura min wani cousin dina wanda nikuma bazan iya zaman aure dashiba,that's why nake neman taimakonka..."

"Taimakona kamar yaya?" Ya bukata yana kallonta,

"Yawwa, so nake muyi aure kamar gaske daga baya idan hamood yadawo sai mu rabu naje na auri saurayina wanda nakeso"

Murmushi yayi wanda ya bayyanar da hakoransa,

"To wannan auren namu menene sunanshi?"

"Auren taimako domin taimako na zakiyi mutukar da gasken kana kaunata"

Murmushin yasake yi,

"Gashi nikuma ban shirya aure kwana kusa ba"

"Karka damu zan baka dukkan abubuwan da za ayi amfani dashi, ni dakaina zan hada lefe inbaka akawo da komai da komai"

"Sai kace acikin shirin film ko littafin hausa? Gaskiya bazan iya wannan auren ba, da dai aure zamuyi halattacce kamar na kowa shine sai indage inyi iya bakin kokarina inga nasamo abinda zan aureki cikin watannin da kika fada amma wannan auren gaskiya ba daniba..."

Daga haka yamike yana kallon agogo,

"Ni zan wuce, nabarki lafiya"

Ya fita daga gate din gidan bata iya cemasa komai ba saboda tsananin mamaki ashe haka yake da baki da iya zance bata saniba? Ganin zaman babu amfanin da zai tsinana mata yasata tashi tashiga cikin gida, wurin ammah tawuce ta zauna anan ammah ke tambayarta waye yazo nan ta sanar da ita sabon saurayi tayi kuma dagaske yake yashirya aure, fatan alkhairi ammah tayi domin ita zabin bilkisu shine nata.

Koda ta shiga daki kasa zaune tayi ta kasa tsaye bata son damarta tawuce, ya kamata tayi amfani da wannan yaron wurin cikawa hamood burinsa,

Wayarta tajawo ta shiga kiransa, tana daf da tsinkewa yadaga,

"Hello, sorry hajjaju wanka na shigane"

"Babu komai dama na kiraka ne infada maka na amince ayi yadda kakeso din, ya kakeso ayi?"

Wata sanyayyar ajiyar zuciya ya ajiye sannan yayi magana cikin taushin murya,

"So nake muyi aure irin wanda kowa yake, sannan bana bukatar ko sisinki kibarni inyi komai kamar yadda kowanne ango keyi..."

"Na amince..." Tabashi amsa,

"Yawwa ko kefa to shikenan insha Allah babu matsala zan fara shiri daga yau dinnan, Allah yawuce mana gaba"

"Amin"

Daga haka sukayi sallama, kowannensu zama yayi yana tunanin abinda zai tunkara, ita dai bilkisu dawowar hamood take hararowa bayan tayi wannan auren na wucin gadi yayinda shikuma fahad anasa bangaren yanda zaije ya tunkari su Ayiyah da maganar aure yake tunani.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻

[11/28, 08:16] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO.*_

*KAMAR DA WASA...!*💖

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*11*

*Littafin kamar da wasa na kudine dan Allah idan har kinada bukata to kibiya kudi kisiya sai ki karanta.*

***Da tunanin ta yadda zai jewa su ayiyah da maganar aurenshi yashirya, bakin jeans yasaka da jar t shirt mai dogon hannu kamar koda yaushe saida yasha turarenshi wadanda suka zauna ajikin kayanshi sannan yafito daga dakinnsu yana taje sumar kanshi da karamin cumb wanda keys dinshi ke makale jiki. Tsayawa cak yayi yana tunanin ina yadace yanufa ahalin yanzu,

Waje yayi domin baida bukatar shiga cikin gidan yanzu, zama yayi kan dakali yana cigaba da taje gashinsa daga karshe yasaka cumb din cikin aljihu yazaro wayarsa ya leka instagram daga nan yashiga facebook, sakon husna yagani hakan yasashi jan dan karamin tsaki,

"Wannan yarinyar ko mayya sai haka..."

Chaten yaci gaba dayi har magrib yana zaune awannan wurin yana ganin masu wucewa daga can cikin gida yashiga yayi alwala yafito yawuce masallaci bayan an idar da salla yanufi gidan yaya Asabe babbar yayarsu wadda ke aure acan ladanai, tana tsakar gida itada yaranta guda biyar wasu nayin homework wasu kuma na game a wayarta ita kuma tana marking din test din yara domin malamar makarantace awata private school dake unguwar, ganinsa yasata ajiye abinda takeyi tana yimasa sannu da zuwa yaran kuma nayi masa oyoyo,

Kan babbar tabarmar da suke kai yahau ya zauna yana rikeda humaira wacce itace karama dan ko tafiya bata faraba,

"Autan ayiyah daga ina haka?"

"Anty wallahi yau takanas nazo miki dan wallahi akwai magana"

Dariya tayi takalli 'yarta mai sunan ayiyah yar kimanin shekaru 9 tace,

"Ilham jeki ki kawowa uncle fahad ruwa da lemo mai sanyi kinji sai kizo ki zubo masa abinci idan kin kawo"

Saida taga tashin ilham sannan ta maida hankalinta gareshi,

"Meyake faruwa?"

"Anty aure nasamo amma ban fada agidaba tukunna"

Dariya ita abinma yabata saboda jin abinda yace domin ai fahad yarone, nawama yake da har zaiyi maganar aure yanzu?

"Fahad aure kuma? Wai dagaske kake koda wasa?"

"Dagaske nake Allah"

Kafin takara magana ilham takaraso dauke da aiken da tayi mata nan ta karba ta mika masa gabanshi ta ajiye sannan ta kalleshi,

"Amma fahad aure yanzu anya baka ballowa kanka ruwa ba? Haba fahad inama laifin kakoma karatunka yar degree dinnan da kowa keyi kaima kaje kayi inyaso idan kagama sai kayi maganar Auren amma yanzu dududu nawa kake? Ai ko Abba bana jin zai jajibo aure yanzu bare kai, shiyasa tun jimawa nake cemaka kakoma karatu amma kaki...."

Murmushi yayi bayan ya kwankwadi lemon dake hannunshi,

"Anty inada burin komawa karatu amma gaskiya ba yanzuba..."

"Sai yaushe? Saika Tarawa kanka nauyi yayi maka yawa? Ai tun yanzu yadace kakoma da baka da nauyin kowa amma haka kawai kaki karatu?"

"Anty asabe nidai kawai kiyi min fatan alkhairi"

"To shikenan Allah ya tabbatar da alkhairi, ga abinci nan kaci"

Yajima agidan dan acanma yayi sallar isha'i sannan yatafi gida, akofar gida yaja burki yanemi wuri ya zauna yakira bilkisu,

Fitowarta kenan daga wanka tadauki wayar tana kokarin zama agefen gadonta,

"Ya akayi?" Shine abinda tace lokacin data daga wayar,

"Babu komai, ina wuni?"

Ajiyar zuciya tasauke aranta tana jin tafiyarsu zatazo daidai dashi domin da alama sai yanda tayi dashi,

"Lafiya lau dama nima ina son kiranka, gobe idan Allah yakaimu inaso kazo domin zaka gaisa da ammah sannan zakazo kagaida Abba ma"

"Babu matsala Allah yakaimu amma da kamar yaushe zanzo?"

"Koda yaushe kazo ma babu matsala koda yamma koda daddare"

"Tom zanzo da daddaren dan gaskiya kunyar zuwa da yamma nake"

Murmushi tayi amma bata bari yajiba tace,

"Shikenan Allah yakaimu"

"Amin kiyi bacci cikin aminci da farin ciki,saida safe"

"Allah yakaimu"

Daga haka takashe wayar ta ajiye gefe, koda tagama shirin bacci sai kuma tunani ya addabi ruhinta wato kamar da wasa karamar magana na shirin tabbata dakyar tasamu ta fidda tunanin aranta tayi bacci. Shima fahad da tunanin abin ya kwana aransa shi yanzu babban abinda ke fadar masa da gaba tayadda iyayenshi zasu amince yayi auren nan alhalin ga Abba nan agabanshi wanda shi yadade ma da budurwar amma har yau ba afara maganar aureba. Washe gari bilkisu bataje aikiba domin bata da aiki,tana dakin ammah tana gyarawa bayan tagama wanke toilet taji sallamar maama atsakar gida,

"Yar halak" tafada azuciyarta, babu jimawa sai gasu sun shigo itada huda wadda ke gudu dan tazo wurin bilkisu,

"Sannu Adda, kawo intayaki"

Sakar mata mooper din tayi ta dauki hudah dake rungume da ita,

"Ina kwana Adda labour?"

"Lafiya lau Maman hudah, wallahi yanzu nake tunaninki nake cewa to ko inje gidanki tunda ba fita aiki zanyi ba?"

"Wallahi nima daku na tashi shiyasa muna tashi nacewa abban hudah tare zamu fito idan zaije office yasauke mu"

"Ai kuwa kin kyauta, nasan daga nan har dare kuna nan kamar yadda aka saba"

Dariya maama tayi tace,

"Abinda kema kin sani adda labour"

Kinkimar hudah bilkisu tayi suka koma falo wurin ammah nan maama tafito ta samesu.

Da daddare misalin karfe 8 fahad yayi mata waya cewar yakaraso dama lokacin tana daki tanata faman caba ado kamar gaske, maama dai na kwance tana lallaba hudah tana kallonta, mayafi tadauka tafita tana zuba kamshi dama tun yamma ta fadawa ammah fahad zaizo gaishesu,

Kamar koda yaushe yana tsaye hannunsa daya cikin aljihu yana sanye da farar shadda sabuwa fil tasha bakin aiki wannan dalilinne yasashi sanya bakar hula da bakin takalmi,

"Yaron akwai daukar wanka babu laifi matsalarshi daya yayi yaro dayawa" tafada cikin zuciyarta,

"Barka da fitowa, ina yini?"

Yace da ita yana kallonta,

"Lafiya lau, muje ko?"

Jerawa sukayi zuwa cikin gidan, wurin ammah suka fara zuwa tana zaune afalo lullube cikin mayafi, akunyace yacire sau cikin kafarsa yashiga falon daga shi sai bakar safa akafar tashi, zama yayi kanshi akasa yana gaidata, itama ammahn kanta akasa ta amsa bata ko daga kaiba bare ta kalleshi, hakan da sukai sai yabawa maama da bilkisu dariya nan kowa yayi tasa aboye, duk jinsa yayi yatakura shiyasa ko ruwa yakasa sha daga karshe yamike yafita bayan ya ajiyewa ammah kudi, bin bayansa bilkisu tayi domin takaishi wurin Abba.

Afalon Abba sukaja birki ya kalleta fuskarsa cikeda annuri,

"Ban daiyi rashin kunya ba ai ko?"

"Da kayi me?"

"Dana zo mana"

"Uhmm zancen kakeso"

Murmushi yayi baice komaiba har Abba yashigo daga can wata kofa wadda da alama itace hanyar bedroom dinshi,mikewa tsaye fahad yayi Abba na zuwa ya durkusa kasa da niyyar gaisheshi amma sai Abban ya ruko kafadarshi yana bubbuga bayanshi ahaka suka gaisa, sannan Abba yajashi kan kujera mai zaman mutum uku, abin gwanin burgewa Abba sai janshi yakeyi da hira yana yimasa tambayoyi dangane da tushensu cikin barkwanci da dabara irinta manya daga karshe Abba yace yana son ganin mahaifinsa, duk da yaji dadin ganin Abba da hirar da sukeyi amma yakasa sakin jiki duk atakure yake jinsa dan haka cikeda girmamawa da alkunya yayiwa Abba sallama yafito dama bilkisu tuni ta dade da zamewa tafice, koda yafito tsaye ya sameta tana yin waya da kanwarta mina ganinsa yasata yiwa Mina sallama ta juyo tana kallonsa,

"Ya kukayi?"

"Cewa yayi inturo mahaifina zai gana dashi"

Ajiyar zuciya ta sauke batace komai ba tayi masa alama da hannu suje ta rakashi, shi dinma baice komai ba yawuce tana biye dashi a second gate sukayi kicibus dasu Hindu itada mai gidanta wanda yazo daukarta ganin su bilkisu sun fito yasata komawa domin yiwa Abba sallama dama su take jira sufito. Gaisawa sukayi da mijinta da fahad daga nan suka wuce waje,

"Yanzu menene next abu da kake ganin zamuyi?"

"Bari dai infara yiwa babanmu maganar tukunna inyaso sai sauran su biyo baya..."

Sallama yayi mata yahau roba roba din da yazo dashi na salim yatafi, ciki takoma ta iske Hindu na jiranta nan tafara yimata santin haduwar da fahad yayi tana cewa,

"Su iyallo masu fatan tsiya to zasuga mijinki yawuce tunaninsu"

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull