Kamar da wasa complete novel - Chapter 6
Kamar da wasa complete novel Chapter 6: Kamar da wasa complete novel Chapter 6. Ita dai bilkisu dariya tayi daga nan sukayi sallama tashige gida sukuma…
3,338 words
Ita dai bilkisu dariya tayi daga nan sukayi sallama tashige gida sukuma suka tafi.
Adaren ranar bayan fahad yakoma gida yasamu baba da maganar a turakarshi, dafarko shi kansa kunya abin yabashi shiyasa yarasa ta inda zai fara sanar da baba, kawai sai yaji kunyar yacewa baba aure yakeso yaje ya nema masa dakyar dai yadaure yace,
"Baba dama.....dama akwai wata..... da nake zuwa wurinta..... to yau naje ingaida mahaifinta...... shine.....shine.... yace wai yana son ganinka...."
Shiru baba yayi ya zuba masa ido hakan yasashi kara yin kasa da kansa, mamuh kuwa dake tsaye bakin kofa wacce shigowarta kenan kuma da alama taji komai tafa hannu tafara yi tana rafka salati.....
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:16] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO* _(Home of expert & perfect writers)_
*KAMAR DA WASA....!*💖
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*12*
*Kamar da wasa na siyarwa ne yar uwa idan kinada bukata kisiya saiki karanta.*
***Ji yayi jikinsa yayi mutukar sanyi hakan yasashi yarda aransa cewar iyayen nashi ba lallai su amince da batun nasaba,
"Yanzu kai fahad har kafara maganar aure? Ahh lallai zamani yazo...." Inji mamuh, kasa yasake yi da kansa, dariyar baba yajiyo daga bisani yaji yana fadin,
"Ai ba auren akace za adaura ba kawai dai mahaifin yarinyar ne ke son ganawa dani, menene na saurin karaya kodai baki shirya aurar da d'an nakiba?"
Dariya itama tayi takarasa shigowa cikin dakin ta nemi wuri ta zauna,
"Bahaka bane baban asabe ko gobe akace mu fito muna iya fitowa tunda yarona ba zaman banza yakeba yana da sana'arsa"
"Gashi babarsa tana adashi..." Baba yafada cikin raha,
"Ni yaushe rabona da adashi baban fahad?"
Jin su baba sun mayar da abun raha yasashi zare jikinsa zai fice har yakai bakin kofa yaji baba yace masa,
"Gobe idan Allah yakaimu zanje sai ka sanar musu"
Daga kai kawai yayi yana shafa sumar kanshi batare da yace komai ba, ganin sun cigaba da maganar su yasashi karasa ficewa dasauri.
Bayan fitarshi baba yadubi mamuh cikin nutsuwa,
"Abinda nakeso daku idan har dagaske auren aka bashi to mu mara masa baya yayi tunda har yafurta, yin hakan yafi fiyeda mu bada gudun mawa wurin lalata tarbiyarsa da ruguza rayuwarsa, saboda yaran zamanin nan da kike ganinsu sai dai abarsu kawai shiyasa komai kankantar yaro ko yarinya idan suka nuna aure sukeso kawai yimusu ka huta domin idanfa baka yimusu ba to watan hanyar zasu bi ta daban,... Ai mu da muke fita waje mune muke kallon abubuwan dake faruwa Rahmatu"
Gyada kai mamuh tayi cikeda gamsuwa tace,
"Hakane Baban asabe ubangiji Allah ya shirya mana zuri'a da sauran al'ummar musulmi"
Daga nan sun jima suna tattauna maganar atsakaninsu.
Abangaren fahad kuwa ko zama baiyi adakin ayiyah ba yadauki abincin shi dake rufe yafice, dakinsu yabude yashiga sai lokacin yaji nutsuwa tazo masa domin da alama su baba bazasu hanashi wannan auren ba zama yayi bayan yarage kayan jikinsa ya zamana daga shi sai vest da gajeren wando, abincin yabude yafara ci nan kuma hankalinsa yakoma kan lissafin abubuwan da zaiyi tofa account dinshi yaduba yaga nawa yake dashi daga nan lissafe lissafe yatashi wanda ya daukeshi tsawon lokaci daga karshe abincin ma barinshi yayi. Sai da yasamu nutsuwa bayan yayi wanka sannan yakira bilkisu wacce tuni harta kwanta amma ba bacci takeyi ba,
"Kaje gida lafiya?"
Shagwabe fuska yayi kamar tana kallonshi,
"Ni wallahi bazan amsa ba tunda ai baki kirani kin tambayeni ba...."
"To ai sai kayi min uzuri dai ko"
"Nayi miki ranki yadade, dama mai gidane yace zaizo gidanku gobe wurin Abba"
"To Allah yakaimu, amma da yaushe zaizo?"
"Da safe naji yace,sai ki sanar dasu"
"Babu matsala Allah yakaimu"
"To saida safe? Ko zamuyi hira?" Yafada dan jan magana,
"A'a saida safen dai" tabashi amsa tana yatsina fuska,
"To kihuta lafiya baby...."
"Thanks" tafada cikeda bacin ran kiranta da baby da yayi,
Daga haka takatse wayar juyi tayi ta gyara kwanciyarta aranta tana cewa,
"Wannan shine Abu kamar da wasa yana shirin zama babba,hamood meyasa kayi min haka? Amma babu komai tunda ban san abinda ke faruwa ba sai dai nayiwa kaina alkawarin zama injiraka har lokacin da Allah zai sake hadani dakai..."
Sake muskutawa tayi cikeda damuwa,
"Lallai yaron nan ni yake kira da baby? Tab ai kuwa dolene ma na yanka masa serious warning wallahi...."
Da bacin rai tayi bacci wanda bata san ko na menene ba amma tafi alakantashi da rashin sanin takamaimai halin da hamood ke ciki da kuma kiranta da baby da fahad yayi.
Koda gari yawaye bayan tafito suna karyawa da ammah take sanar da ita batun zuwan babansu fahad wurin Abba, ai ammah farin cikine ya mamayeta harta kasa boyeshi saida ya fito fili bilkisu tagani,
Shiru tayi aranta tana jin tausayin ammah domin azahirin gaskiya bata jin zata iya zaman aure da wannan karamin yaron kawai dai aure ne na wucin gadi za ayishi da zarar abin sonta yadawo zata koma gareshi domin shine yadace da ita ba fahad ba.
A bangaren fahad kuwa tunda ya kwanta bayan yayi sallar asubah bai tashiba har 9 saida ayiyah tazo ta buga masa kofa tace baba na kiranshi sannan yataso da hanzarinsa yana kokarin zura doguwar rigar jallabiyarsa wadda yacire bayan ya idar da salla. Lokacin da yashiga dakin baba yasameshi yana karin kumallo da kakkauran koko da kosai nan ya durkusa yagaidashi baba ya amsa cikin fara'a kana yace,
"Nayiwa babanka Alhaji Nuhu magana mahaifin salim yanzu haka yashirya ni yake jira zamuje gidansu yarinyar, a ina gidan yake?"
Sunkuyar dakai fahad yayi sannan yasanar dashi, dayake sanannen mutum ne mahaifinsu bilkisun shiyasa baba bai wani wahala wurin gano inda gidan yakeba daga karshe yace fahad din yatashi yatafi. Yana kwance adaki yajiyo fitar baba hakan yasashi jin faduwar gaba babu kakkautawa dakyar yasamu yaji yakoma daidai amma baccin da bai komaba kenan hakane ma yasashi fadawa toilet yayi wanka yafito yashirya sannan yasaka kananan kaya yanufi cikin gida, yana shiga su mamuh na waje suna gyaran waken suya wanda zasuyi awara dashi da rana, ji yayi kamar yakoma dan kunya gashi yau sai yaji duk ya tsargu dasu saboda yanda daga ayiyah har mamuhn suka zubo masa ido gefe daya ga mariya tsugunne arakabe,
"Yaya fahad tattabarunka sunyi sabuwar kinkisa Allah leka kagani"
Dama mafaka yake nema dan haka yanufi dakin barun batare da yakarasa wurinsu ba yana cewa Mariya,
"Haba? Ashe zan baki biyu tunda kece kika fara yimin albishir"
Zuwa yayi ya lelleka nan yahangosu sun doshi goma koma fiye da haka, ma'ajiyar abincinsu yanufa yaje ya ciko musu kwano da hatsi yazo ya watsa musu sannan yakoma wurinsu ayiyah yana hararar Mariya,
"Ke meyasa bakije makaranta ba? Kema gardamar karatu zakiyi ko?"
Kafin Mariya tayi magana ayiyah ta amsa,
"Ka ganta nan da zazzabi tatashi da asibiti ma zan rakata babanku yace inbari anjima inkaita wurin murja nurse makotanmu ta dubata tunda can asibitinma idan anje layine kuma ba lallaima aga likitan ba watakil nurse din za agani"
"To Allah ya sawwake, ina kwananku?" Yafada bayan ya durkusa,
"Lafiya lau ango" inji mamuh, ai baice komaiba yamike yana murmushi yafada dakin ayiyah domin karyawa yanaji mamuh nacewa ayiyah,
"Sai mufara asusu tunda danmu ya lakato aure"
Dariya ayiyah tayi sannan tace,
"Atoh bikin auta guda ai dole anuna bajinta"
Agurguje ya karya yafito yabar gidan yanufi shago saboda yanada ragowar dinkunan da bai karasa ba kuma yaga har masu dinkin sun turo masa kudin dazu da asubah. Acike yasamu shagon kowa yafito harda yan karbar dinki da masu zuwa zaman hira shagon, hamza ya iske asaman kekenshi dan haka yanemi wuri yazauna yana jiran yagama yabashi wuri,
"Yau mutuniyarka zuwanta biyu nemanka ta dubaka taga ko ka fito amma shiru"
Duk da Tj bai fadi sunaba amma yasan husna yake nufi,
"Yar naci kenan, ni garama da ka tuna min bari inyanka atamfar can tata kafin inhau keke"
Atamfar yadauka da almakashi da sauran abunda zai bukata yafita domin yankawa.
Kamar yadda baba yafada shida mahaifin salim sukaje gidansu bilkisu a motar yayansu salim din baffa wanda shine yakaisu, lokacin da sukaje bilkisu tafita wurin aiki sun samu kyakkyawar tarba awurin Abba wanda ya karbesu hannu bibbiyu cikeda girmamawa da mutuntawa, kasancewa abune na manya masu ganin mutuncin juna anan aka kulla magana inda Abba yace yabaiwa fahad bilkisu sannan shi baya son wadannan bidi'o'in masu hana aure yayi karko dan haka nanda watanni biyu sai adaura musu aure yafi ayita dogon zancen nan suna sake shakuwa da juna daga karshe kuma ba asan me zai faruba, duk da baba yana ganin kamar hakan bamai yuyuwa bane duba da su ba karfine dasu kamar gidansu bilkisun ba amma haka yakarbi maganar Abba hannu bibbiyu aranshi yana cewa idan da yuyuwar su daga lokacin bikin sa sake dawowa su nemi alfarma, cikeda mutunta juna sukayi masa sallama suka fito inda yayi musu rakiya har gaban motarsu,wannan fa shi ake kira da babu zato babu tsammani daga zuwa tambaya ansaka ranar aure alhalin shi angon bai tanadi komai ba na biki.
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:17] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*💖
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*13*
***Daga fahad har bilkisu babu wanda yakeda masaniyar abinda yake faruwa, shi fahad baima koma gidaba sai bayan sallar la'asar wannan dinma yunwa ce ta addabeshi shiyasa yana zuwa gidan ta kan abinci ya fara saida yaji ya koshi sannan yawuce dakinsu yayi wanka daga ayiyah har mamuh babu wanda yayi masa maganar kowa acikinsu kama bakinsa yayi yai shiru, bayan yagama shiryawa yafito yana kokarin rufe daki baba yashigo, kayan hannunsa yakarba sannan yashiga cikin gida baba yana biye dashi, bai san wa zai kaiwa kayanba kasancewar bai san wacce keda girki ba domin su al'adar gidan nan baka gane wacece ke girki saboda komai tare sukeyi wannan dalilinne yasashi ajiye kayan a kofar dakin baba yajuya yana kallon maryam da mariya wadanda ke ta faman kallonsa suna yar dariya kasa kasa,
"Ke Mariya kin warke zaki fara munafurci ko? Bari nazo nakama yarinya sai nayi ball da..."
"Ya akayi kuma? Dawa za ayi kwallo?" Baba yafada bayan yashigo,
"Ahh babu komai baba" fahad ya amsa yana shafa kai,
"To zo ina son ganinka..."
Bin bayan Baba yayi cikin turakarsa, sai da yajira Baban yazauna sannan shima yazauna bayan ya dora habarsa kan gwiwarsa,
"Muhammadu tofa karamar magana tazama babba, naje wurin mahaifin yarinyar nan kamar yadda ya bukata kuma mun tattauna dashi, ya yabeka iya yabo haka kuma ya kaunaceka domin duk mutumin da yaso hada zuri'a dakai to mai kaunarka ne, kuma naji dadi domin gidan da kaje gidane na mutunci da karamci saboda bana tunanin duk nahiyar nan bama cikin kano ba babu wanda bai san mahaifin yarinyar nanba..."
Shigowarsu ayiyah da mamuh ne ya katsewa baba maganar da yakeyi sukayi masa sannu da zuwa sannan suka nemi wuri suka zauna suna saurarensa,
"Yanzu dai zancen da nake maka fahad mutumin nan yabaka yarsa yace baya bukatar komai daga gareka domin har yama sanya ranar aurenku watanni uku, duk da nasan kanada sana'ar yi amma sai nake ganin kamar zaka shiga wani hali saboda aure abune mai wahalar gaske musamman ma a wannan lokacin..."
Shiru fahad yayi yana jin abun kamar amafarki wai shine zai auri bilkisu matar da yake mutukar kauna, maganar babace tadawo dashi cikin hayyacinshi,
"Yanzu menene abinyi? Kaga dai nafarko bakada muhalli domin baka gama ginin da kakeyi ba, na biyu rikon gida dole sai anshirya duk da nasan Allah shine da kowa amma mu ta bangarenmu zamu taimaka maka da abinda zamu iya sannan zan tattaro yayunka ma duk in sanar dasu"
"Baba nida tunanin da nayi ko insaida dayan filina dake digar maharba sai inkarasa ginin?"
"A'a kabar filinka bari dai zamuga abinda za ayi, tashi kaje, zamu shawarta da iyayenka"
Tunda yafito sai yarasa me zaiyi yasan dai yau yana cikeda wani farin ciki wanda bai taba jin irinsa ba, tafe yake ahankali domin zuwa yasanarwa da salim saboda magana awaya bazata yuyu ba, idonshi ne yakai kan yaran dake tsugunne gaban wata yarinya wacce ke soya awara agefen titi, wurin yakarasa yazaro dari biyar ya mikawa yarinyar,
"Ki rabawa yaran nan sadakar ta dari biyar..."
Daga haka yawuce yanajin yaran sunata murna da yimasa godiya. A shagonsu salim ya sameshi yana kwance shi kadai bayan wasu mata sun gama siyayya sun tafi. Shiga yayi ya zauna agefenshi yana fadin,
"Washh..."
Kallonsa salim yayi, "yadai abokina?"
"Katashi kaji wani labari, ansa min ranar aure yau?"
Ai kuwa tun kafin yarufe bakinsa salim yatashin yana kallonsa,
"Dawa?"
"Da hajjaju mai gado"
Dariya sunan yabaiwa salim shiyasa saida ya dan dara sannan yace,
"Lallai mutumin nan kadage sai kayiwa Abba overtaking..."
Dariya fahad yayi,
"To ya za ayi lokaci nane kawai yazo"
Dariya salim yayi,
"Allah yasanya albarka tareda alkhairinsa, ya kuma zakayi da maganar husna?"
Canja fuska fahad yayi,
"Ya kuwa zanyi, ko na taba cemaka ina sonta ne?"
Jijjiga kai salim yayi,
"Tab akwai rikici, Allah dai ya kiyaye"
"Babu wani rikici malam"
Har dare suna tare da salim, saida salim yarufe shago sannan suka tafi gida gaba daya.
Tunda bilkisu tabar gida bata dawoba sai yamma tana dakinta bayan tafito daga wanka taji wayarta na kara, su elmustapha ne dan haka ta daga tana tsaki tasan maganar dai bata wuce ta kudi,
"Elmustapha ya akai?"
Daga can tajiyo muryar el'ameen yana cewa,
"Adda labour amarya, nine shi yashiga school"
"Amarya kuma?"
Dariya taji yayi mata sannan yace,
"To Allah yasanya alkhairi mudai aturo mana picx din babban yaya"
Daga haka yakatse wayar, ita dai kanta daurewa yayi jin abinda el'ameen yace, to meyake nufi, da haka ta kammala shiryawa ta sanya yar doguwar riga marar nauyi mai hannun shimi kalar ruwan hoda sannan tasa hijab tafita, farar shinkafa da miya tasa Rabi ta zuba mata tashiga dakin ammah wacce ke kwance tana kallon shirin dadin kowa,
"Ke, yaushe kika shigo kuwa"
Zama tayi saman rug dake gaban gadon ammah tana kallon tv din itama,
"Ammah na dan jimafa ai na leko kina bayi"
"Ehh ruwa na dan watsa saboda naji garin adaure yake"
"Gaskiya ana sheka zafi"
Har suka gama hirarsu tatashi tafita ammah bata yimata maganar ansaka ranar bikinta ba har saida Abba yadawo da daddare sannan yakirata yake fada mata, rasa wanne yanayi ta tsinci kanta tayi farin ciki ko bakin ciki? Share fahad din tayi bata nemeshi ba haka shima bai kirata ba. Har akayi kwana biyu basu magantu ba ita gaba daya haushinsa takeji kamar ba itace ta kawoshi ba shikuma barinta yayi ta sarara gashi hidindimu sun fara yimasa yawa saboda tun washe garin ranar da aka sanya ranar auren nan baba yakira yayun fahad din kamar yadda yafada suka tattauna dangane da yadda za ayi akan maganar bikin fahad, shi dai baba yace zai karasa gina masa gidanshi wanda yafara hakama yayunshi maza guda biyu wadanda ke zaune a gombe da zamfara sunce zasu bada kyakkyawar gudun mawa lokacin da baba ke sanar dasu awaya sauran yan uwansa mata kuma sukace zasu taimaka masa wurin yin lefe. Yanzu kam fahad ansamu nayi domin can wurin aikin yake wuni duk da dama ginin yadan deboshi da fadi shiyasa dole sai baba yasaka masa hannu. Kasancewar yau ba ayi aikinba yasashi zama agida domin hutawa, yana kwance adakinshi duk jikinsa ciwo yake kamar shine yake aikin ginin, alamun shigowar text yagani duk tunaninshi husna ce amma da yabude sai yaga sabanin haka domin bilkisu ce taturo masa da,
_Salam idan kasamu time kazo zaku gaisa da kakarmu._
"Tofa.. Wata sabuwa nifa kunyar gaishe gaishen nan nakeji amma ya na iya? Ai idan naki zuwama sai na fuskanci hukunci"
Shi kadai yaketa maganganunshi daga karshe ya yanke shawarar kiran salim domin yarakashi da daddare. A lifan din salim suka tafi bayan sallar isha, kayan marmari suka tsaya suka fara siya mata sannan suka karasa gidan, awaje suka jira har bilkisu ta fito fuskarta dai babu yabo babu fallasa, kasancewar yasan hali shine yafara gaisheta ta amsa sannan suka gaisa da salim wanda take kallonshi ta gefen ido aranta tana jin damuwar wai wadannan zata nuna ranar bikinta amatsayin abokan ango,
"Muje ko" daga haka tawuce gaba suna binta abaya har ciki, iyallo jaraba ana zaune dakin baki ana sharbar tuwon shinkafa miyar taushe wanda tasa aka yimata ga tv ana kallo jin baki zasu shigo yasata yin lullubi ta rufe tuwon,
Cikin barkwanci da tsokana irinta kakanni ta taresu,
"Barka da zuwa angona, ina fata dai nima ka tanadi nawa dakin dan kafarka kafata"
Murmushi fahad yayi yayi shiru bai amsa ba sai salim ne yace,
"Dama ai dakunan mata biyu yayi harda naki wanda yamafi nata kyau"
Ai kuwa nan ta cafke tana cewa bata yarda ba shikuma salim yabiyeta sunata yi, daga fahad har bilkisu basa cewa komai shiru kawai sukayi sai dai murmushi sunfi minti talatin wurin iyallo daga karshe suka ajiye mata tsarabar da suka kawo mata harda na cin goro fahad ya ajiye suka fita, godiya da albarka sun shata wurin iyallo daga nan suka gaida ammah suka fita domin shi Abba yau baya nan, a compound din gidan suka tsaya yayinda salim yafita yabasu wuri, kallonshi tayi yasha coffee din yadin kufta da hula da takalmi sau ciki sannan ta dauke kai, ita kam hijabi ne ajikinta har kasa, shiru sukayi dukkaninsu na dan wani lokaci.
"Mai gadon zinare ya ake ciki? Kinji dai yanda su Abba suka yimana wai aure nanda 2 months nikuma gani mai karamin karfe"
"To ai basai ka takura kanka ba kawai kayi abinda ya sawwaka.... Tunda aurene na wucin gadi" takarasa maganar acikin zuciyarta,
"To Allah yasa bazaki rainaba"
"Babu matsala kayi dai dai karfinka"
"To shikenan, sai gani nagaba,nabarki lafiya, I luv u!!"
Bata amsa masaba yajuya yatafi yana daga mata hannu.
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:17] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*💖
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*14*
*Littafin kamar Dawasa na siyarwa ne,yar uwa idan kinada bukata ki siya saiki karanta, ku kuma masu fitar min da book dan Allah ku hakura haka tunda ai kunyi na zumunci.*
***Wasa wasa lamari sai kara girmama yake domin biki yanata matsowa, a bangaren fahad komai yana tafiya daidai domin hatta lefenshi yakusa kammala danma yana baiwa su yaya asabe matsala saboda komai idan suka siyo suka saka idan baiyi masaba sai ya canja idan anyi magana yace shi matarshi babbar yarinya ce yar gayu ba karamar yarinya bace, tun abin yana yimusu ciwo musamman Anty Fauzy mai zuciyar tsiya amma da ta fahimci inda ya dosa saita daina damuwa daga karshe ma duk abinda zasu siya sai sunyi snapping dinshi sun tura masa ta whatsapp yagani, baba kuwa duk atamfofin da aka zuba cikin lefen shine yabada domin cewa fahad yayi yaje shagonsa yadubo duk atamfofin da suka yimasa dama sana'ar baba kenan shago gareshi a kwari na atamfofi zalla kala kala, duk da kayan sauran kadan su gama haduwa har yau bai siyo akwatuna ba saboda yace da kanshi zai siyo kuma da kudinsa, kowa agidan lamarin auren nan na fahad dariya yake bashi har baba ganin abin suke yi tamkar wasa wai fahad ne zaiyi aure, shi dai yanzu ta ginin gidanshi yake domin burinshi kawai yanzu yaga gidan ya kammala.
Bilkisu kam ta cika famm haka kawai lamarin auren nan ke bata haushi gashi kullum saita gwada number hamood amma shiru kamar koda yaushe bata shiga, yau kam amare duk sunzo gida harda maama dama hudah na gidan wurin bilkisu tun ranar da ta raka iyallo gidajensu hudah ta dankafe mata dole sai tare suka taho,
"Adda muma fa mun kwadaitu da son muga big Broz domin anty maama tace yahadu karshe ga class..." Inji meenah,
"Ehh wlhi meenah anty maama cemin tayi wai duk yafi mazajenmu kyau.... Gaskiya Adda labour kina bada kala..." Hindu tafada tana dariya,
"Yara kudai kubari zaku ganshi, wallahi big guy ne har wani suna fa ake fada masa amma ba zakuji abakina ba...."
Ai maama tana rufe baki bilkisu tatashi tabar musu wurin ta shige kitchen domin idan tazauna suka cigaba da haka tana iya make wata aciki.