Kamar da wasa complete novel - Chapter 10
Kamar da wasa complete novel Chapter 10: Kamar da wasa complete novel Chapter 10. "Dagaske fa nakeyi, dan naga kamar kai kadauki abin dawasa..., ga spare…
3,324 words
"Dagaske fa nakeyi, dan naga kamar kai kadauki abin dawasa..., ga spare mattress nan kadauka sannan kaduba cikin drewar akwai sabbin bedsheets da blankets idan kana da bukata...and lastly ka kashe wannan hasken domin bana bacci da haske akaina" Daga haka tamaida kanta ta gyara kwanciyarta, fasa kwanciyar yayi ya nufi drewar yabude yadauki duk abinda zai bukata yana kunkuni, pillow yazo yadauka guda daya yayi hanyar falo yana cigaba da kunkuninsa,
"Amma bar miki dakin gaba daya kije ki cinye..... Nima bana bacci aduhu.....haka kawai dan takura zaki wanice ke kadai zaki kwanta akan gado...."
Katifar yadawo yadauka yaje yayi shimfidarshi afalo sannan yasake dawowa dakin, wannan karon wuta ya kunna dan neman magana,
"Me kuma yafaru?"
Tafada tana bude ido dakyar dan bacci,
"Sucket nake nema zan saka charge"
"Acan inda zaka kwanta din babune? Pls malam kashe min wuta bacci zanyi..."
"Ehhh ai dai kin tashi...."
Yafada cikin kunkuni yanda bazata jiba, wutar yakashe yafita yana ja mata kofa dama babu wani charge da zai saka kawai son yatasheta ne yasashi kunna wuta, akusada doguwar kujera ya shimfida katifar tasa ya kwanta yadora kafarsa daya akan kujerar yakunna data awannan daren yashiga instagram daga can yafita yakoma Facebook, bashi ya hakura ba sai wurin daya da rabi a lokacin yaji bacci yaci karfinshi, ajiye wayar yayi bayan yakashe yayi addu'a babu jimawa sai bacci. Daf da asubah yatashi saboda fitsarin da ya takurashi kusan ma shine yatasheshi, bedroom yashiga mutuniyar tasa tana tukunkune sanyin asubah da na fanka na kadata duk ta takure wuri daya, fankar yarage mata sannan yashiga bathroom din yayi abinda zaiyi yafito yakoma falo yayi kwanciyarshi bai kara motsawa ba sai karfe bakwai saura, yana bude ido yakalli agogo gani yayi sun zabga makara gashi ko salla baiyi ba, bedroom din yanufa kansa tsaye yakama handle yabude tana zaune kan gadon ta ziro kafafunta kasa tana daure kitsonta da tacire ribom din cikin dare batare da ta saniba dan hatta rigarma sai yanzu ta mayar, babu zato taganshi yashigo cikin azama ta yayibi duvet tarufe jikinta tana kallonshi,
"Meye haka? Ya zaka shigo min daki batare da taking excuse ba....."
"Yi hakuri..." Daga haka yawuce zai shiga bathroom,kunkunin nasa yasoma yi shi kadai,
"Haka kawai kin saka mutane sun makara sallar asubah dan kawai kin san ke bayi zakiyi ba....."
"Magana kakeyi ne?"
"A'a..." Daga haka yafada toilet yayi alwala yafito bayan yayi brush, tana sanye da hijab har kasa da towel daure ajikinta tana gyara kan gadon, dan tabe baki yayi ya dauki rug din salla ya shimfida yatada salla, ita kuwa saida tagyare kan gadon tsaf sannan tawuce toilet domin yin wanka da kallo yabita sannan yamaida kallonshi saman gadon cikin kunkuni yace,
"Gashi dai mun dawo daya dake da kika kwana wajen kwanan mutum biyar da ni da na kwana awurin kwanan mutum biyu..."
Yana kan abin sallar azaune har tafito, handbag dinta ta dauka tanufi drewar tana cemasa,
"Dan bani wuri zan shirya..."
Mikewa yayi baice komai ba yanade prayer rug din ya ajiye saman bedside drewar yafita azuciyarshi yana cewa,
"Oho dai tunda nasan me za ayi har ake wani korata..."
Kwanciyarshi yayi saman doguwar kujera bai san lokacin da wani baccin yasake daukeshi ba. Ita kuwa bayan ta shirya wani material ta saka peach tasa sarka da dan kunne golden sannan tasaka abun hannu da agogonta na gold wanda ammah ta siyo mata last year da taje umarah, turarenta na garari na fitina tabi ta bazawa jikinta sannan tafito domin yanzune zata yiwa gidan kallon tsaf kasancewar safiya tayi dan harma rana tafito, fahad tagani kwance yana bacci nan kuma ga shimfidarsa ta daren jiya, tattara komai tayi ta dauke mattress din takai daki tazo ta kwashe sauran suma takai daki sannan tasake fitowa, ta kofar kitchen ta fita baya ta dudduba gidan wanda yake dan cicif sannan tadawo ciki sai lokacin ta lura da buhun Irish potatoes dake jingine acikin kitchen din, dayake anrigada anhada mata cylinder din gas dinta tukwane kawai tafara lalubowa dama cooker gas dinta babu ruwanta da neman ashana wurin kunnashi nan ta kunna ta dora ruwan zafi.
Dankali ta fere wanda zai ishesu su biyu ta soya bayan ta juye ruwan zafin acikin tea flask, da kwai ta hada tayi masa kyakkyawar suya yabada kala mai kyau dama bata da matsalar kayan kamshi da kayan dandano komai gashi nan a ajiye sai dai kawai ta dauka, hatta dakakken yaji gashi nan cikin karamin plastic haka su kuka,daddawa, kubewa etc duk su maama saida suka harhada mata aka dako sannan aka kawo mata, fridge din dake cikin kitchen din taduba kamar tasan yayi ajiya nan taga balangu da yoghurt da kayan marmari danginsu tufa, kankana da ayaba, balangun taciro tasaka acikin oven ta dumama bayan takara masa kayan hadi, saida ta kammala hada abin karyawarta tsaf sannan ta dauko ta kawosu kan dinning mai dauke da kujeru kwaya hudu,kayan tea dinma da alama babu dan haka tafasa shan ruwan zafin taci iya balangunta da chips din data soya. Tana daf da gamawa taga andawo da wuta mikewa tayi tanufi daki domin jona wayarta a charge da alama shima fahad yatashi domin bata ganshi awurin da tabarshi yana bacciba,akan gadonta taganshi yana cigaba da baccinshi,
"Wannan ko yasha wani abune? Bacci yaki karewa? Uhmm"
Ita kadai take maganarta tana kokarin saka wayarta a charge, handbag dinta ta dauko ta zazzage kudin data samu tafara shiryasu domin wasu yan dari darine sabbi fil wasu yan dari bibbiyu wasu kuma yan dari biyar biyar harda yan hamsin hamsin ma, hakura tayi da shiryawar tasake gwamutsasu ta maida cikin handbag din taje ta ajiye tafita falo, daga can tayi waje, flowers din da aka shuka sunyi masifar kyau ga kuma wasu kananan shukoki nan da suka dan fara fitowa kamar bishiya duk da dai bata gane menene ba,abakin slave din pop din kofar falon nasu ta zauna,
Gajiya tayi da zaman wajen tasake diba takoma cikin falon ta zauna, tana nan zaune yafito sanye da blue din shadda yana balle links din hannun rigar,
"Hajjaju barka da safiya?"
"Yawwa, katashi lafiya?"
"Lafiya lau, ya kwanan kadaici?"
Banza tayi dashi tamaida hankalinta kan agogon dake manne jikin bangon falon wanda yake tafkeken gaske mai dauke da hoton abbansu ajiki,
"Babu kayan tea ko? Bari naje nasiyo yanzu"
"Babu amma ai ga breakfast can na hada"
"Haba ranki yadade daga zuwa sai girki? Shikenan godiya nake"
Bai jira cewarta ba yayi dinning area din yazauna yaci abincin yayi dam dan babu abinda yarage yana gamawa yayi mata sallama yafice, wani takaicine kuma yafara ziyartarta shi yayi ficewarsa yanzu hakama gidansu yatafi amma ita gashi nan yabarta agida ita kadai gashi kuma tamanta ta tambayeshi taji ko anhada mata kayan kallonta, daki ta koma ta zare wayarta daga sucket ta kunna data ta fada yanar gizo wai ko zata rage zaman kadaici......
*Book dina na kudine dan Allah idan har baki biyaba karki karanta.*
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:18] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO*
*KAMAR DA WASA...!*💖
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*20*
***Fahad lokacin da yafita saida yafara zuwa gidansu yagaida su ayiyah yayi musu ban gajiyar biki sannan yawuce kasuwa duk abinda suke bukata na amfanin gida saida yasiyo daga karshe ya iyo cefanenshi na abincin rana ya hado kayan tea sannan yanufi gida, lokacin har bilkisu tagaji da chaten dinma ta kashe data tana kwance tarasa abinda yake yimata dadi, kitchen yakai kayan gaba daya ya ajiye mata sannan yanufi bedroom, akwance yaganta kamar marar lafiya tayi shiru,
"Hajjaju yadai?"
"Yawwa dan Allah wai ba ahada kayan kallon can bane?"
"Anhada mana.... Zo kigani"
Tashi tayi tabishi zuwa falo nan yajona komai saiga tashar mbc Bollywood takawo darr, ajiyar zuciya tasauke harta dan ji dadi ai kalloma ba karamin rage kadaici yakeba, yana debewa mutum kewa sosai sai yau tayarda,
"Ga kaya can a kitchen ni Zan fita.."
"Ina zaka fita? Ni kadai zan zauna agidan? Wallahi a'a kaima neman wuri zakayi mu zauna tare..."
Kujerar dake makotaka da tata yaje ya zauna, yana zama wayarshi na yin kara, cirota yayi yaduba nan yayi dariya ya daga,
"Allah yabar babban yaya, har ka tafi ne?"
Bata jin me ake cewa amma dai taji yace,
"Ehh to shikenan sai kazo"
Saida yakatse wayar sannan yajuya ya kalleta,
"Ya Abba ne wai zai koma school amma zai fara biyowa tanan kugaisa tukunna"
"To babu damuwa Allah yakawoshi lafiya"
Tashi tayi zuwa kitchen tana ware kayan da yakawo wanda zata barsu a kitchen din tabarsu anan wanda zata kai toilet ta kwasa takai sannan kayan tea din kuma takai dining area ta zuba cikin wani glass da aka tanada musammsn domin ajiya,
Saboda taji zaiyi bako shiyasa ta dora girkin da wuri sannan takoma falo ta iskeshi yana kallon spider man atashar mbc max, tana zama sukaji knocking, shine yaje yabude, khulsum ce kawarta bata hanya yayi yana cewa,
"Barka da zuwa hajiya khulsum"
"Yawwa haji fahad, ya kwanan amarya?"
Saida suka shigo cikin falon sannan ya amsa da,
"Gata nan muna bata hakuri, bai zauna ba yawuce bedroom yabar musu falon"
Kallon khulsum bilkisu tayi,
"Kekuma sai yanzu kika gadamar zuwa?"
"Kai labour yanzun bakiyi maraba da ganina ba?"
"Oho miki, ya gajiyarki?"
"Ahh gajiya ai tana tare dake hajiya, ni ai tajima da bin lafiyar jikina"
"Nima haka..."
"Gaskiyane amarsu, me kike tafasawa ne haka?"
"Wallahi girki ma na dora gashi can wai zanyi jalop din shinkafa..."
"To muje mana mu karasa, ah tashi muje"
Tare suka shiga kitchen din khulsum ta tayata suka hada komai, kayan marmarin da yakawo jiya sukayi blending dinshi suka hada banana milk shake suka saka a fridge basu kai ga sauke abincin ba Abba yazo fahad yafita yashigo dashi, kamarsu daya da fahad kuma kusan kansu ma daya dayake shima fahad din dogo ne, a falon suma suka zauna amma bilkisu tun kafin su shigo tasako hijab dinta har kasa wanda hakan ba karamin dadi yayiwa fahad ba. A mutunce suka gaisa sai lokacin takara raina girman fahad saboda koshi abban tagirmeshi kai dakyar ma idan maama kanwarta bazata fishi ba, mikewa Abba yayi zai tafi saboda yana son ya isa Maiduguri da wuri amma suka hanashi tafiya wai sai yatsaya yaci girkin amarya, dan dole yatsaya su bilkisu sukaje suka shirya table sannan tazo tace musu,
"Bismillah..."
"To godiya nake amarya" inji ya Abba,
"Ah babu komai..." Tafada tana murmushi,
"Ni gaskiya...ni gaskiya ban ganeba, ni meyasa ba agataleni" fahad yafada yana bata fuska kamar zaiyi kuka,
"Kai ai yanzu kagirma" Abba yafada cikin sigar tsokana,
"Allah ban yarda ba"
Daga bilkisu har Abba dariya sukayi ita dai tafiya tayi tabarsu saboda taga dramar tasu ba mai karewa bace kuma da alama sun saba, cikin bedroom suka shige itada khulsum suka basu waje suma suka kai nasu can, suna cin abincin khulsum na sake yimata tsiya har suka gama daidai lokacin shima fahad ya leko yace sun gama Abba zai tafi, hijab tasaka tafita sukayi sallama takoma wurin khulsum, shima fahad ta can yawuce bayan yaraka Abba, majalissar shayinsu yatafi wacce suke zama idan sun taso daga shago amma shi bawani ma cika zama yayiba sosai domin daga shago sai filin ball. Acan gidan amarya kuwa bayan fahad sun fita tareda abba babu jimawa su yaya asabe suka zo itada Anty Fauziyya fuska asake bilkisu ta karbesu takawo musu abinci da lemon da suka hada kuma babu laifi ta saki jiki da su kamar yadda suma suka sake da ita, suna nan tare sunata kallo suna hira har maman hudah tazo wato maama takawowa bilkisu kayan tarbar baki wanda yahadar da cincin, cake, alkaki sai nakiya da dubulan an dan samu tsaiko ne matar da aka bawa tayi bata gamaba sai jiya da daddare ta aiko dashi amma da tuni anjima da kawo mata,
"Ina daughter dina naganki ke daya??"
Dariya maama tayi ta zauna kan kujera suna gaisawa da su Anty Fauzy,
"Daughter ki yau tana wurin kakarta can nabarta,ya fahad baya nanne?"
"Ehh yafita" bilkisu tabata amsa tana harararta kasa masa saboda haushi suke bata idan taji sunce mishi yayan nan wallahi, ganin tasake samun yar tayin hira su anty fauzy suka yimata sallama suka tafi, ledoji ta cika musu da kayan zakin da maama takawo mata ta rakasu har kofar gida anan suke sanar da itama gidajensu zasu wuce basai sun koma gidan ayiyah ba saboda dama sun rigada sunyi sallama, wurinsu khulsum takoma bayan taga tafiyarsu nan hira ta barke bare yanzu sai su kadai har magrib suna gidan ta hanasu tafiya tace sai fahad yadawo. Bayan sallar magrib kuwa babu jimawa sai gashi yadawo yana rikeda CD flate din bikinsu da yakarbo, maama yaya sama yaya kasa ta ringa kiranshi dashi dama suna shiri sosai musamman ma dayake tana kamada bilkisu fari kawai tafi bilkisu duk dinsu ma sun fita haske saboda ammah suka biyo ita kadaici ta dauko kalar abba tayi baki amma bakin shima bawani can dayawa ba sai dai baza asata alayin farare ba, ganin yadawo suka yimusu sallama suka fita ai harda fahad arakasu kofar gida bayan sunga tafiyarsu suka koma ciki lokacin babu wuta saida fitilar wayarshi yayi amfani ya haska musu suka shiga ciki, tana shiga taga wayarta dake kan kujera tana kara tana dauka taga su elmustspha ne,kamar yadda tazata saida tagaji da surutunsu dakyar sukayi sallama ta kashe wayar tana kallon fahad wanda ke jiranta ta kammala wayar,
"Yadai?"
"Akwai abinci ne?"
"Da akwai guntu, kacinye ma kawai"
"To kekuma fa?"
"Karka damu zansha tea ya isheni"
"Shikenan..."
Dining yanufa ita kuma ta kishingida jikin kujerar tana dora rayuwar duniya a ma'auni na zahiri ba badini ba. Har ya gama cin abincin yadawo cikin falon bata bar tunani ba saida yazauna ya murza yatsunshi guda biyu asaitin fuskarta sannan ta dawo hayyacinta ta kalleshi,
"Ranki yadade lafiya kuwa?"
Ajiyar zuciya ta sauke,
"Lafiya lau kawai dai nagajine wallahi"
"To kije kici abinci mana ki kwanta ki huta"
"Gaskiya kam haka yakamata inyi bari natashi"
Tea taje ta hada tadawo falon ta zauna tasha zafi kuwa yace muje zuwa daki tashiga domin wanka zatayi ta kwanta tana cire kaya yadanno kai bayan yaturo kofa, tukwicin harara yasamu shiyasa cikin azama yafada toilet yayi alwala yafito bai yadda ya kalli wurin da takeba yafice daga dakin bayan yadauki abin salla,
"Haka kawai wai mutum da halal dinshi amma ayita nuna masa fin karfi da iko..." Haka yaketa fada cikin kunkuni lokacin da yafita falo, abin sallar ya shimfida yatada kabbarar sallar ishah. Dan neman fada bai shiga dakinba saida ya daidaici ta kwanta domin yaga yadaina ganin haske sai duhu alamun takashe fitilar data kunna, tashi yayi ya dauki abin sallarshi yanufi cikin dakin yasan bata son haske gashi tun yana salla aka dawo da wuta amma ita bata saniba,yana shiga ya lalubi makunna ya kunna nan wani fitinannen haske ya gauraye dakin, dan karamin tsaki taja tayi saurin rufe jikinta,
"Wai dan Allah menene haka? Shigo min dakin da kayi cikin wannan lokacin bai isheka ba har sai ka kunna min haske..."
"Yi hakuri dama nazaci ko baki san andawo da nepa bane..."
"To da aka dawo da ita me zanyi mata? Ko nace maka ina bukatane?"
"Ni na san abinda zakiyi da itane madam.... Nidai kawai na fada mikine"
Banza tayi masa ta juya baya tayi kwanciyarta,
"Malam idan kagama nidai ka rage min hasken nan ya takura min..."
"Nima ai kin takura min..." Yafada cikin kunkuni, bata bi takanshi ba ta mayar da idonta tarufe, saida yagama jula jularshi sannan yakashe yashiga wanka, acan yashirya yafito yana ta kukkumbura baki kamar tana ganinshi, acikin duhun ya kwashi kayan shimfidarshi yayi falo yaje ya shimfida a position din jiya sannan yakoma ya dauki pillow irin daukar nan na ehh ina cikin fushi dan kawai fincikar shi yayi yai gaba,
"Ahh malam menene haka? Karka yaga min pillow mana..."
Yaji tace yana daf da isa bakin kofa,
"Sai anyaga din" sai dai shi tashi maganar yadda bazata jiyoba yayi, bude kofa yayi yafita yaje ya kwanta,
"Haka kawai dan kinga kin fini shine zakiyita takura min.... Allah sai nima na rama wata rana tom"
Shi kadai yake maganarshi har yagaji yahakura yayi shiru, yauma kamar jiya raba dare yayi yana chaten daga bisani yasauka yayi addu'ar bacci.....
*Book dinnan na saidawa ne yar uwa idan kinada bukata ki siya saiki karanta.*
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[11/28, 08:18] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO*
*KAMAR DA WASA...!*💖
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*20*
***Fahad lokacin da yafita saida yafara zuwa gidansu yagaida su ayiyah yayi musu ban gajiyar biki sannan yawuce kasuwa duk abinda suke bukata na amfanin gida saida yasiyo daga karshe ya iyo cefanenshi na abincin rana ya hado kayan tea sannan yanufi gida, lokacin har bilkisu tagaji da chaten dinma ta kashe data tana kwance tarasa abinda yake yimata dadi, kitchen yakai kayan gaba daya ya ajiye mata sannan yanufi bedroom, akwance yaganta kamar marar lafiya tayi shiru,
"Hajjaju yadai?"
"Yawwa dan Allah wai ba ahada kayan kallon can bane?"
"Anhada mana.... Zo kigani"
Tashi tayi tabishi zuwa falo nan yajona komai saiga tashar mbc Bollywood takawo darr, ajiyar zuciya tasauke harta dan ji dadi ai kalloma ba karamin rage kadaici yakeba, yana debewa mutum kewa sosai sai yau tayarda,
"Ga kaya can a kitchen ni Zan fita.."
"Ina zaka fita? Ni kadai zan zauna agidan? Wallahi a'a kaima neman wuri zakayi mu zauna tare..."
Kujerar dake makotaka da tata yaje ya zauna, yana zama wayarshi na yin kara, cirota yayi yaduba nan yayi dariya ya daga,
"Allah yabar babban yaya, har ka tafi ne?"
Bata jin me ake cewa amma dai taji yace,
"Ehh to shikenan sai kazo"
Saida yakatse wayar sannan yajuya ya kalleta,
"Ya Abba ne wai zai koma school amma zai fara biyowa tanan kugaisa tukunna"
"To babu damuwa Allah yakawoshi lafiya"
Tashi tayi zuwa kitchen tana ware kayan da yakawo wanda zata barsu a kitchen din tabarsu anan wanda zata kai toilet ta kwasa takai sannan kayan tea din kuma takai dining area ta zuba cikin wani glass da aka tanada musammsn domin ajiya,
Saboda taji zaiyi bako shiyasa ta dora girkin da wuri sannan takoma falo ta iskeshi yana kallon spider man atashar mbc max, tana zama sukaji knocking, shine yaje yabude, khulsum ce kawarta bata hanya yayi yana cewa,
"Barka da zuwa hajiya khulsum"
"Yawwa haji fahad, ya kwanan amarya?"
Saida suka shigo cikin falon sannan ya amsa da,
"Gata nan muna bata hakuri, bai zauna ba yawuce bedroom yabar musu falon"
Kallon khulsum bilkisu tayi,
"Kekuma sai yanzu kika gadamar zuwa?"
"Kai labour yanzun bakiyi maraba da ganina ba?"
"Oho miki, ya gajiyarki?"
"Ahh gajiya ai tana tare dake hajiya, ni ai tajima da bin lafiyar jikina"
"Nima haka..."
"Gaskiyane amarsu, me kike tafasawa ne haka?"
"Wallahi girki ma na dora gashi can wai zanyi jalop din shinkafa..."
"To muje mana mu karasa, ah tashi muje"
Tare suka shiga kitchen din khulsum ta tayata suka hada komai, kayan marmarin da yakawo jiya sukayi blending dinshi suka hada banana milk shake suka saka a fridge basu kai ga sauke abincin ba Abba yazo fahad yafita yashigo dashi, kamarsu daya da fahad kuma kusan kansu ma daya dayake shima fahad din dogo ne, a falon suma suka zauna amma bilkisu tun kafin su shigo tasako hijab dinta har kasa wanda hakan ba karamin dadi yayiwa fahad ba. A mutunce suka gaisa sai lokacin takara raina girman fahad saboda koshi abban tagirmeshi kai dakyar ma idan maama kanwarta bazata fishi ba, mikewa Abba yayi zai tafi saboda yana son ya isa Maiduguri da wuri amma suka hanashi tafiya wai sai yatsaya yaci girkin amarya, dan dole yatsaya su bilkisu sukaje suka shirya table sannan tazo tace musu,
"Bismillah..."
"To godiya nake amarya" inji ya Abba,
"Ah babu komai..." Tafada tana murmushi,
"Ni gaskiya...ni gaskiya ban ganeba, ni meyasa ba agataleni" fahad yafada yana bata fuska kamar zaiyi kuka,
"Kai ai yanzu kagirma" Abba yafada cikin sigar tsokana,
"Allah ban yarda ba"