Kamar da wasa complete novel - Chapter 14
Kamar da wasa complete novel Chapter 14: Kamar da wasa complete novel Chapter 14. Yabude baki zai sake magana kenan sukaji wata tsawa mai mutukar karfi dan…
3,259 words
Yabude baki zai sake magana kenan sukaji wata tsawa mai mutukar karfi dan hatta dakin da suke ciki saida ya girgiza, bata san lokacin da kankameshi ba shima haka, jikinta gaba daya rawa yake ga ruwa da ake kwararawa kamar da bakin kwarya, ahaka suka yi bacci suna kwakume da juna har asuba, shine yafara farkawa har lokacin ruwa akeyi, kallonta yayi tana bacci cikin kwanciyar hankali rungume akirjinsa tayi matashin kai da kirjin nasa,
"Su hajjaju iyayen son girma amma kuma ana tsoron tsawa...."
Pillow yajawo zai kwantar da ita akai domin ya fahimci tana fashin salla duk da boye masan da take tayi domin idan bata salla bata son yasani idan asubah tayi saita tashi taje tayi alwala sai tazo ta zauna kamar irin ta idar da salla dinnan tana tasbihi bayan kuma tun lokacin da ya fara kwana adakin ya fuskanta saboda duk lokacin da zata tashi sai yafarka domin abu kadanne ke farkar dashi abacci,
Bude idonta tayi wanda ke cike da bacci kamar jaririya ya kwantar da ita ya mike, ga mamakinta sai taji tana bala'in jin sanyi bayan yatashi babu jimawa ciwon kai yasata agaba, sam fahad bai san abinda yake faruwa ba har saida rana tayi duk da har lokacin anata yayyafi yashigo dakin da niyyar yin alwala tayi masa magana,
"Dan Allah ko zaka samo min maganin ciwon kai"
Matsawa yayi kusada ita ya dafa goshinta,
"Da zazzabi?"
"A'a iya ciwon kanne"
"Sannu, Allah ya sawwake bari naje na samo miki"
Sai bayan da yatafi sannan ta janyo wayarta ta kunna ta tura masa text domin pad dinta yakare abinda ya hanata ma wanka kenan tun dazu,
Yana gidansu wurinsu ayiyah zai karba mata abinci text din nata yashigo yana dubawa yaga tace,
_Dan Allah ka dan taho min da pad._
Murmushi yayi aransa yana cewa,
"Wato baza dai afada min baki da bakiba wai kunya akeji hajjaju kenan"
Saida yajira aka karasa abincin rana sannan aka zuba ma bilkisu cikin food flask, maryam yadauka zasu tafi da ita domin ta ragewa bilkisu aiki tunda yau suna gida ruwa ya hanasu zuwa makaranta, ta wani chemist suka fara biyawa yashiga domin siyo mata maganin ciwon kan kuma cikin sa'a yaga harda pad dinma gashi nan ana saidawa kala kala, guda biyu ya siyo mata yakarbo mata maganin suka wuce shida maryam. Har yakoma tana kwance rikeda kanta wanda ke azalzalarta, afalo yabar maryam yashiga cikin bedroom din ya taimaka mata ta tashi zaune,
"Kiyi wanka sai kici abinci kisha maganin ko?"
Kai ta daga masa tana jiran yafita daga dakin sannan sai tatashi domin tana kyautata zaton tayi staining, tun kafin ta koreshi ya fahimta dan haka yamike yafice bayan ya ajiye mata maganin da pad din agefenta, lallabawa tayi ta tashi cikin sa'a taga staining din bai taba bedsheet dinba iya kayan jikinta ne, wanka tashiga tayi da ruwa mai dumi wanda ke cikin babbab tea flask dinta, har lokacin kanta bai sarara mata ba, body spray kadai ta fesa ta saka kaya riga da wando na Pakistan, ta lallaba tafita falo, yana kwance a kujera maryam na mopping din falon ganinta yasa bilkisu fadada murmushinta,
"Maryam daga zuwa kuma sai aiki"
"Ehh anty, ina wuni? Yajiki?"
Zama tayi akujerar nesa da fahad tana amsawa, da kanshi yatashi yaje ya dauko mata abinci da flate yakawo mata, saida tafara hada tea tasha sannan tabude abincin, dashishi ne yaji kayan hadi da albasa ga mai nashe nashe ai kuwa taji dadin ganin dashishin nan domin taci da yawa dama yau bata ci komai ba, kwanciya tayi bayan tasha magani bacci yayi gaba da ita sai lokacin fahad yasamu yafita yabar maryam atare da ita, koda yaje shagonma hankalinsa na gida domin bini bini sai yakirata yaji yajikin nata har magrib tayi bayan yayi salla ya koma gida yadauki maryam ya maida ita gida daga can ayiyah tabashi tuwo yatafiwa da bilkisu. Tsawon kwana biyu ta dauka tana fama da ciwon kan kafin tasamu sauki tafara fita aiki amma da ko aikinma bata zuwa, khulsum har gida tazo ta dubata haka ma maama masu jegone kadai basu zoba tahanasu tace taji sauki basai sunzo ba kowa yadauka laulayin ciki tafara basu san bahaka bane. Shi dai fahad yanata iya kokarinsa na ganin sun zama abu daya amma taki amincewa shikuma baya son yanuna mata karfinsa shiyasa yake kyaleta, yauma kamar kullum saida sukayi rikici daga karshe ya sauka kasa yayi shimfidarshi ya kwanta wai yayi fushi,can cikin dare tafara jin nishinsa yana murkususu kamar bazata kulashiba amma sai taje inda yake ganinsa tayi duk ya jigata sai gumi yake baccin da basu komaba kenan domin abin ya tsananta zuwa asuba yasamu ya lafa masa, bayan gari yafara haske yatashi ya dingisa yayi alwala yayi salla yana dafe da gefen mararsa na hagu, akwance agida yawuni ranar gashi yakasa cin abinci sai ruwan tea kadai yake sha bilkisu tayi tayi akan yaje asibiti yaki daren ranar halin da yashiga har yafi najiya babu shiri ta dauki wayarsa ta dangwala dan yatsanshi tashiga neman contact ya abba takira lokacin karfe 12 nadare yana tsaka da bacci yadauka,
"Kanina ya akayi?"
Cikin tashin hankali bilkisu tayi magana, dama abban yazo gari yana nan cikeda tashin hankali shima yasako kaya yafito ko cikin gida bai shigaba saboda kowa na gidan yayi bacci. Bilkisu na can tanata fama dashi domin kuka yake ta yimata wiwi yana rike mararsa ahaka Abba yazo gidan yasoma kwankwasawa da azamarta taje ta bude shida salim ne sukazo a motar ya baffa ai basu jira komaiba ahaka suka daukeshi sukayi kama kama, itama dogon hijabi kawai tasaka ta daura zani tabisu,asibiti mafi kusa suka je wani dan karami na kudi, wajen karfe dayan dare Dr yafito yace aiki za ayiwa fahad domin k'arine a mararsa kuma yagirma dole sai ancire nanda zuwa safe za ayi masa aikin matsawar sun biya kudin aikin amma ahalin yanzu aunyi masa allurar da zata sakashi bacci dan yasamu saukin ciwon,azaune su bilkisu suka kwana da ita da Abba da salim, zuwa asuba Abba yasanar da gida abinda yake faruwa kafin gari yagama wayewa su baba duk sunzo dasu ayiyah har su yaya asabe sun zo nan aka biya duk wani kudi da ake bukata,wurin karfe 9 nasafe ake sa ran yimasa aikin shiyasa kowa ya zauna yana zaman jiran tsammani,kafin lokacin da za ayi masa aikin anty kubra da anty juwairiyya suka zo dauke da abincin da suka shiryo amma dayake hankali ba akwance yakeba babu wanda yakula balle har yaci.
Karfe tara da wurin rabi aka shiga da fahad theater ayiyah sai addu'a akeyi itada mamuh abin tausayi, tunda aka shiga dashi basu suka fitoba sai sha biyu na rana kallo daya zakayi masa kagane amutukar wahale yake sannan yajigata,sai faman baccin wahala yake, wani daki aka kaishi gado biyune adakin amma daya gadon babu kowa akai, wuni yayi yana bacci bai farfado ba sai la'asar sai lokacin hankalin kowa ya dan kwanta yanyameshi akayi kowa nayi masa sannu bilkisu dai daga dan baya ta tsaya saida kowa yagama sannan tamatsa itama bayan taga fitarsu mamuh yarage saura abba da salim kadai, duk wanda yayi masa sannu sai dai yadaga masa kai amma baya iya amsawa, koda bilkisu ta matsa idanuwanshi yazuba mata wadanda suka sake girma sakamakon dan fadawar da yayi,
"Sannu... Yajikin.... Allah yabaka lafiya"
Kai yadaga mata sannan ahankali yakamo hannunta cikin nashi yana mai yimata alamar da ta zauna agefenshi, batayi musuba ta zauna tana kallonshi, lumshe idanuwanshi yayi har lokacin yana rike da hannunta, sunata zaune ahaka har anty Fauziyya tashigo ta kirata wai tazo inji ayiyah, tashi tayi tafita bayan yasaki hannun nata, koda taje ayiyah matsa mata tayi tasata agaba dole sai taci abinci domin wuni guda bata ci abincin kirki ba, daurewa tayi taci abincin tuwon shinkafa miyar wake bayan tagama ci tayi alwala tayi salla sannan takoma cikin dakin tare dasu Mariya wadanda suka biyo anty fauziyya suka taho tare.
"Sannu ya fahad....." Inji su mariya kai yadaga musu sannan yamaida kallonsa ga bilkisu hannu ya mika mata amma sai taki kamawa saboda ganinsu mariya awurin gaban gadon taje ta zauna amma sai ya dan dungureta koda ta kalleshi sai taga yana yimata alama da ta zauna asaitin kanshi matsawa tayi ta zauna tana zama yamaida kansa kan cinyarta yana ciccije lebe sakamakon amsawar da wurin da akayi masa dinki yayi hannunta ya damke cikin nasa yana rumtse idanuwa duk sai yabata tausayi domin tasan abinda zaisa kaga namiji na kuka to bafa karami bane abin ahaka suka kasance har wani baccin ya dan daukeshi kowa ya leko yaga ayanda suke baya shigowa saiya koma shiyasa duk nauyi da kunyar duniya tataru ta dabaibaye bilkisu musamman ma da taga su ayiyah sun leko amma sai suka koma har magrib yana kan cinyarta saida ya farka sannan abba yataimaka mata ya kwantar dashi saman pillow, salla taje tayi daga can tazauna wurinsu ayiyah har karfe 9 nadare suna asibitin da su ayiyah zasu tafine lokacin da mijin anty fauziyya yazo daukarsu sukace bilkisu ma tatafi gida sai su mariya subita su tayata kwana shikuma fahad abba yakwana awurinsa, turo baki fahad yayi ya bata rai yana kallon mamuh wadda itace ke tsara hakan, kallonshi ya mayar kan bilkisu ganin ta mike daga kujerar da take kai azaune acikin zuciyarshi yanata masifa,
"Ga matata ga komai maimakon abarta mu kwana tare shine kawai za awani ce ya Abba ya zauna ya kwana awurina, ni wallahi mamuh baki kyauta minba..."
Haka yaketa fada acikin ransa amma afili babu bakin magana domin tamkar andinke masa bakin baya iya magana gashi duk jikinsa kamar ba nashiba musamman ma daga mararsa zuwa babban yatsunshi na kafa,
Jin kowa nayi masa sallama suna tafiya yayi saurin yiwa salim alama da ya kira bilkisu,
"Hajjaju oga fa yana magana"
Murmushi tayi ta koma da baya tana cewa,
"Lallai salim kaima din hajjajun zakace"
Tana zuwa yayi mata alama da ta sunkuyo taji, duk atunaninta magana zaiyi mata akunne amma tana mika fuskarta saitin tashi taji yabata hot kiss a kumatunta mikewa tayi tana harararsa shima harararta yayi murmushi ne ya subuce mata batare da ta shirya ba, hannunta ya riko yana yimata alama da wai shima tayi kissing din kumatunshi,
"Dan Allah kaga ni sakar min hannu gasu can ni kadai suke jira kar kasa azargi ko wani abu mukey...."
Murmushin karfin hali taga yayi kafin yagirgiza Mata kai alamun bazai sakar mata hannun ba, hannunshi tayiwa kiss tana kokarin fita abba yashigo ganinsu ahaka yasashi saurin komawa da baya, hararar fahad tayi,
"Kagani ko...."
Bata saurareshi ba tafice daga dakin, binta da kallo yayi yana yimata dariya acikin zuciyarshi, dama ita kadai ake jira tana zuwa suka tafi,itada maryam da mariya aka sauke agidanta tana shiga wanka tafara yi sannan tayi sallar ishah domin batayi ba a asibitin acikin wannan daren takira maama da ammah duk ta sanar dasu rashin lafiyar fahad da asibitin dayake kwance ahalin yanzu sannan takira khulsum wacce har tafara bacci itama tasanar da ita, dayake jiya batayi isasshen bacciba shiyasa yau tunda ta kwanta bata tashiba sai da asubah duk da hakama ta makara sallah domin har masallatai sun jima da idarwa......
*Littafin kamar da wasa na siyarwa ne yar uwa idan har kinada bukata ki siya ki karanta domin yana dauke da dunbin darrusa na rayuwar da muke ciki yau, ka karanta halak dinka yafiye maka alkhairi akan karanta hakkin wani.*
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:19] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA...!*💖
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*25*
***Kitchen tashiga bayan ta idar da salla sukuma su mariya suna kokarin gyara mata gidan, saida ta shirya lafiyayyen abincinta tazuba a flask wanda zata kai asibiti sannan ta zubawa su mariya suka ci daga nan tabasu kudin napep saboda sai sun koma gida sannan zasu shirya su tafi makaranta danma dai sunyi wanka agidanta da sunje gida uniform kawai zasu saka, bedroom tashiga bayan ta sallami su maryam sun tafi, tana kokarin daura towel idonta yakai kan wayar fahad dake ajiye saman bedside drewar tana karar neman agaji, koda taje gaban wayar sunan husnah tagani ajiki nan wayar takatse wani kiran yasake shigowa, ko kadan bataji tana sha'awar daga wayarba har tayi tagama sai lokacin ta dauka ta jona masa a charge kasancewar akwai wuta. Wanka tashiga tayi tafito ta kintsa adan hanzarce sannan tayi breakfast kafin ta hada komai wanda zata tafi dashi tarufe gidan tatafi, shatar napep ta dauka yakaita har asibitin lokacin karfe bakwai da wurin rabi,iya ya abba ne kadai awurin da alama babu wanda yazo tunda yanzu garin yawaye, saida suka gaisa ta tambayi yamai jiki sannan tashiga ciki, idonshi akan kofa shiyasa tana shigowa idanuwansu sukayi arangama da juna, murmushi taga ya sakar mata kasalalle yana kwance rigingine kanshi tallafe bisa hannunshi na dama,
Har gaban gadon takarasa zata zauna, hannu yamika mata yakamo nata, zama tayi tana kokarin ajiye handbag dinta bayan ta dire kayan da tazo dashi. Kallonta yake tamkar yau yafara ganinta domin ba karamin haduwa yau dinnan tayiba, leshi ne ajikinta dark pink anyi mata gown tasha lafaya itama pink duk ta lullube jikinta, juyawa tayi ta kalleshi,
"Sannu yajikin?"
Daga mata kai yayi yana matsa mata yatsunta bata kai ga sake yin wata maganar ba Abba yashigo dauke da brush da toothpaste,
"Gaskiya mijinki jinyarsa akwai takurawa.... Ni yanzu ma gida zanje anjima zan dawo"
Murmushi bilkisu tayi ta dan karkatar da kai tana kallon fahad wanda idanuwanshi ke lumshe,
"Meya faru yayanmu?"
"Shifa idan yana ciwo nafarko bazaiyi bacciba sannan na biyu bazai ci abincin ba na uku bazai sha magani ba sannan komai sai anyi masa kamar wani jariri, yanzu gashi yanace sai ankawo masa brush kuma bari kigani ko yayi brush din bafa cin komai zaiyi ba kuma Dr yace zai dan iya cin abinci kadan kadan bawai dayawa ba"
"Sannu da kokari, Allah yabada lada....,ayi mana afuwa amma"
Bude idanuwa fahad yayi ya kalleta yana jin wani irin sabon sonta yana shigarshi,
"Yanzu dai gashi sai kusan yanda zakuyi kiyi masa brush din"
"A'a babban yaya ai sai ka taimaka min"
Da taimakonshi suka samu yayi brush din sannan ta zubawa abba abinci yafita waje yaci, Dr ne yashigo shida wasu nurse maza guda biyu yaduba jikin fahad sannan yafita yabar nurse din domin su gogewa fahad wurin da aka yankashi, ai ana saka audugar da aka tsoma cikin ruwan spirit ya runtse idanuwansa tareda sake damke hannun bilkisu tun nurse din Suna tsokanarsa sun zaci shagwaba ce har kowa ya fahimci dagaske yake domin kuka yasaka musu saida aka gama suka fita Abba yashigo tsayawa yayi yana kallon fahad wanda har lokacin bai daina kukanba,
"Kai wai menene amfanin kukan ne? Dallah malam tashi kaci abinci saboda ni tafiya zanyi"
Ko motsi baiyi ba bare asaka ran zai yarda yaci abincin, shi dama idan lafiyarsa kalau yana son abinci sosai amma idan bashida lafiya to shida abinci sai ahankali, gyara zama bilkisu tayi tafara lallashinshi,
Gefen lifayarta tasaka tafara goge masa fuskarshi, kanshi tashiga shafawa sannan ahankali ta sunkuya daidai kunnenshi tafara yimasa rada,
"Kaifa yanzu ba yaro bane kagirma, kayi hakuri.... Yi shiru katashi kaci abinci, dan kadan zan baka dama kai na dafowa..."
Ahankali ahankali yasoma rage kukan nashi har yadaina gaba daya sai ajiyar zuciya da yake ajiyewa, mikewa tayi da niyyar yiwa ya abba magana amma sai taga wayam wato yafice yabasu wuri kenan, tea ta hada masa mai kauri bai kai rabin cup ba ta taimaka masa ya dan tashi yanata cije lips, yana hawaye yana shan tea din wai ahakanma dan itace amma da wanine da sai ansha fama dashi kafin yasha, wainar kwai guda daya da dankali guda biyar ta sake bashi yana ci yana yamutsa fuska yana gamawa ta mayar dashi ya kwanta, wayarshi ta ciro ajakarta tabashi yakarba ya ajiye agefen pillow din da yake kai, su ayiyah ne suka shigo harda baba lifayarta taja tarufe fuskarta kadan tasauka kasa ta gaidasu bayan sun gaisa tafice waje ta zauna bisa bencin dake kofar dakin anan ammah ta sameta itada Rabi mai aikinta, tare suka shiga ammah ta dubashi sannan tafito itada rabi suka bar ammah acan wurunsu ayiyah. Sunata hirarsu da Rabi har khulsum tazo itama tashiga ta dubashi tafito tatafi saboda wurin aiki zata tafi. Wurin misalin karfe 10 saiga maama dasu meenah abban hudah yakawo su anan suka shantake kamar ba dubiya suka zo ba domin anan ammah tatafi tabarsu,kowaccensu rikeda yarta har su anty fauziyya sukazo suma dauke da girke girken da suka iyo, shikuwa marar lafiyar yana daki kwance shida salim suna hira amma dayake jiya baiyi baccin kirki ba da daddare yanzun sai hamma yake danyi.
Bayan anyi sallar azahar suna gama cin abinci salim yaleko yakira bilkisu tashi tayi batare da ta bude warmer din da rabi takawo ba yanzu, dakin tashiga fahad na baje sai faman lumshe idanuwa yake, hannu yamika mata yajata gefenshi,
"Zo ki tayani baccin rana luv"
Ita abinma maimakon yabata haushi kunya yabata saboda ga abokinshi zaune kan gadon marassa lafiyar dake makotaka da na fahad amma babu patient akai, maganarsa tasake juyowa ahankali domin tunda aka kawoshi asibitin ma sai yanzu ne sukaji yayi magana amma da ko me yarike maganar oho,
"Zo muyi baccin rana hajjaju"
Dan satar kallon wurinda salim yake tayi amma sai taga shi hankalinsa ma ba awurinsu yakeba domin yana ga kan wayar fahad dake hannunsa, jin kunyar gwasaleshi tayi agaban abokinshi domin tasan babu wanda yasan irin zaman da sukeyi kusan kowa yazaci zaman aure sukeyi na hakika, tana can duniyar tunani ya hardota da hannunshi zuwa kan kafadarshi bai tsaya ananba yashiga shafar bayanta kamar wata jaririya, lumshe idanuwa tayi tai shiru kamar mai yin baccin da gaske shi dai mutumin abu biyune suka taru suka hadar masa lokaci guda ga ciwo ga kuma wani abu dake sauka asassan jikinsa gaba daya wanda yafi kamada kasala kasala, gajiya gajiya, ji yayi bazai iya jure wannan kamshin nata dake barazanar tarwatsa tunaninsa ba, bakinshi yakai kan goshinta yabata kiss mai sanyi sannan ya soma kokarin lulluba da lifayar jikinta anan ne kuma taso bashi matsala amma sai ya shagwabe fuska,
"Allah sanyi nakeji fa..."
"To akawo maka bargo?"
Girgiza kai yayi harda makale kafada,
"Ni naki nakeso, dan wannan mayafin naki zai isheni.."
Yar kokawa sukayi kafin ta farga yashige cikin lifayar tata ya kwakuma akirjinta amma fa duk abinnan dake faruwa bai motsa kafafunsa ba iyakacin hannayensa da kanshi ne yake motsawa, salim dake zaune yana jin duk abinda ke faruwa tunda ya kallesu sau daya bai sake iya kallonsu ba sai bayama yajuya musu domin sunyi mutukar bashi kunya. Mintuna kadan taji jikinsa ya dan saki alamar yayi bacci da dabara da komai tasamu ta zare jikinta ta tashi tafita bayan ta gyara masa kwanciyarshi yadda bazai takuraba, tana komawa wurinsu maama sai kuma duk ta tsargu da kus kus din da sukeyi musamman ma da ta kama Hindu na gulmarta da ido itada meenah,
"Adda labour ya mai jiki?" Inji maama, banza tayi da ita ta karbi Minal dake hannun hindu ta rike tana lakutar kumatun yarinyar,
Duk dan bikin da suke tayi tana jinsu bata tanka ba daga karshe ta jawo warmer din da ammah ta aiko musu da ita tabude domin bata san ko wanne irin kalar abinci bane, farfesun koda ne cikin warmer din sai tashin kamshi yake wannan dalilin ne yasata niyyar baiwa fahad yaci domin naman ya dahu ligif zai iya ci,
"Maman hudah zuba muku kuci ni ba ci zanyiba sai dai shi ku bar masa"