Kamar da wasa complete novel - Chapter 18
Kamar da wasa complete novel Chapter 18: Kamar da wasa complete novel Chapter 18. Bai kara magana ba yafada saman gadonta yakwanta rub da ciki, ko takalmin…
3,364 words
Bai kara magana ba yafada saman gadonta yakwanta rub da ciki, ko takalmin kafarsa bai cireba, gaba daya tayi mutuwar tsaye ita kam ganin irin marin da hamood ya zabga mata she can't believe wai yau itace acikin wannan rayuwar itada hamood, tajima tsaye kamar wadda aka kafa kafin tanemi wuri ta zauna tana kallonsa yanata sharar baccinsa cikin maye,
"Ohhh Allah.... Ya Allah kayi min maganin wannan masifa...."
Dakyar da sudin goshi tasamu bacci ya dauketa saboda tajima bata samu bacci ba kai rabonta da bacci isasshe kuma mai dadi tun kafin bikinta. Asubar fari ta tashi tayi salla tsakanin mata da miji sai Allah hakan yasa tasoma tashin hamood akan yatashi yayi salla amma fafur yaki tashi daga karshe ma da ta matsa masa afusace yabude ido yadago ya daka mata tsawa,
"Malama wai sallar nan ubanki zan yiwa? Karki sake ki kara tashina..."
Jin abinda yace yayi mutukar razanata, wai ita hamood ke fadawa haka? Rabuwa dashi tayi saboda taga kamar har lokacin mayen bai gama sakinsa ba, anan ita kam taci gaba da zama har gari yagama wayewa, wanka tayi tashirya ta sauka kasa ta shiga kitchen duk ranta adagule zuciyarta a cunkushe wato dama ance zauna da mutum kaga halinsa wato shi hamood wadannan ne nasa halayen kenan? Ahaka ta kammala hada breakfast dinta tanata zancen zuci bayan ta kammala takai kan dining takoma sama lokacin karfe goma tawuce, sai lokacin hamood yatashi bai ko kalleta ba yashiga bathroom babu jimawa yafito yawuce dakinsa domin shiryawa bin bayansa tayi agabanta yashirya yasake fitowa tana ganinsa baiyi salla ba nan abun yasake daure mata kai, kai tsaye dining yaje tana biye dashi yaja kujera ya zauna itama haka,
Chips yasoma ci da spoon yana kunna wayarsa wadda bilkisu bata san da itaba sai yau,
"Hamood ina kwana....?" Takatse shirun nasu,
"Lafiya lau sweetheart...."
Shiru dukkaninsu sukayi sai zuwa can ta saki ajiyar zuciya dama ita ba abincin take ciba kawai tana jujjuyashi ne,
"Hamood meyasa dan girman Allah ka dauki dabi'ar da ban sanka da itaba ka yabawa kanka....? Hamood dama kana shaye shaye ne? Jiyafa da daddare har marina kayi sannan da asuba ka zagi ubana, gashi yau ko sallar asubah banga kayi ba...."
Saida ya ja wasu seconds sannan yadago ya kalleta,
"Kiyi hakuri sweetheart wallahi duk wadannan abubuwan ban san lokacin da nayisu ba, amma hakan bazai sake faruwa ba, jiyane kin bata min rai dayawa wallahi, duk yanda akayi tsohon mijinki dinnan banzan yaron nan baiso aurenmu dakeba shiyasa yayi min asirin da zan kasa kusantarki..."
Ajiyar zuciya taja ta sauke tana kallonsa,
"Bana tunanin fahad zai aikata abinda kake fada nidai ashawarata kaje asibiti sannan ka binciki wannan matar taka...."
"Matata bata aikata komai ba bilkisu ni nafi danganta matsalar dake tunda ita ko yaushe naje gareta lafiya lau nake gabatar da al'amurana kinga kuwa idan hakane matsalar daga gareki ce..."
Shiru tayi saboda ta fuskanci hamood bazai taba ganewa ba tunda bai san kaidin mataba, har ya kammala babu wanda yasake cewa komai mikewa tsaye yayi,
"Ni nafita.... Zanje office"
Bai jira cewarta ba yafice, tagumi ta rafka bayan tasauke ajiyar zuciya, ranar ma bai dawo gidanba sai 12 amma ba acikin mayeba.
Haka dai aka cigaba da zaman doya da manja domin ta fuskanci salla kwata kwata bata dameshi ba gashi da saurin fushi abu kadan zai hau yafara zagin mutun ko zagin iyayenshi, satinta biyu agidan ranar da yamma daf da magriba sai gashi rikeda babbar trolley wasila na biye dashi tasha attach da wani siririn mayafi, tana zaune afalo suka shigo dama gama girkinta kenan tayi tuwon semo miyar agushi wacce taji busasshen kifi, ganinshi tareda wasila abin yayi mutukar Sosa ranta shiyasa ta dauke kanta. Cikeda rashin damuwa suka karaso ciki hannunsu sarke cikin na juna, wani kallon banza wise kebinta dashi amma ita bata saniba saboda bata ko kalleta ba, gabanta hamood yakarasa yana kallonta,
"Sweetheart dan Allah wasila zata dan zauna damu na tsawon wani lokaci....."
Dagawo tayi ta kalleshi kallo mai kunshe da ma'anoni daban daban batare da ta tanka masa ba tawuce tanufi sama, ajiye trolley din yayi yabi bayanta,
Tana zaune kan stool din dake gaban dressing mirror tayi tagumi tacika tayi famm, tsugunnawa yayi agabanta,
"Haba sweetheart bai kamata fa kiyi hakaba, menene abin damuwa anan? Wasila fa bazata wuce 2 weeks ba zata tafi...."
Harararsa tayi sannan ta kawar da kai gefe,
"To meya hana tazauna anata gidan da zata biyoka nan?"
"Dan Allah kiyi hakuri gidan nata ake dan gyara mata kin san kuma mata da neman fitina musamman wadanda aka yiwa kishiya kiris suke jira suce kayi musu laifi...."
Dakyar dai yasamu ya lallasheta ta sauko,
"To tashi muje kasa..."
"Kaje ina zuwa, sallah zanyi"
Tashi yayi yafita ita kuma tashiga toilet tayi alwala tazo tayi salla tasake gyara fuskarta sannan tasauka kasa, wani karin bakin cikin ta tarar domin hamood ne da wasila kan dining sun gama cin abincin da tasha wahala ta girka kuma ita girkinta batayi da wise ba iya daidai cikinta da na hamood tayi tunda bata san da zuwan wise dinba, fuskarta adaure ta bubbude flasks din nan taga wayam sai ko gutsattsari nanfa tasake hasala ta kalli hamood yayinda ita kuma wise ke kallonta up and down,
"Hamood meye haka dan Allah? Waye yasa ku cinye min abinci?"
"Ayya sweetheart ai nazaci kinci naki wannan nawane shiyasa muka ci...."
"Koda nakane ai kamata yayi kujirani nasauko bawai kawai ku saka agaba ku cinye ba"
"To dai aikin gama yagama just kawai kisake shiga kitchen and find something sharp sharp sai kici ko indomie ne...,bari ni naje nayi salla"
Daga haka yamike yafita ita kuma wise tatashi tawuce bedroom din kasa, kallon wurin da suka ci abincin tayi duk sunyi kaca kaca dashi da miya kamar kajine suka ci kokuma masu bulallen baki, cikeda bacin rai tagyara wurin taje kitchen ta dafa tea taci da snacks takoma daki. Tunda wise tadawo gidan sai abubuwa suka sake kazanta domin ko abinci taci anan zata bar flate din bazata daukeba sai dai bilkisu ta dauke sannan baza tayi girki ba sai wanda bilkisu tadafa zata ci da bilkisu tasamu hamood tayi masa complain sai cewa yayi ita wise bata iya girkiba dan ko shiga kitchen wahala yake mata tayi hakuri har sai ranar da wise din takoya, maganar matsalarsu kuma da ta tuntubeshi akan suje asibiti sai cewa yayi shifa lafiyarsa kalau dan haka babu asibitin da zaije saboda awurinta ne kadai yake fuskantar wannan matsalar amma awurin wise rass yake, ita dai adaddafe tazauna da wise har na tsawon sati biyu kowa harkarsa yakeyi ba ruwan kowa da kowa aikin gidanta kuwa ita keyin kayanta amma wise ko cokali bata dauke mata wani lokacin ma idan tagama cin abinci haka zata yi ball da kwanon komai tsadarsa shiyasa daga ranar da tazo gidan zuwa yanzu ta fasa kwanuka da dishes babu adadi ita dai bilkisu bata taba yimata magana ba saboda badashi tazo ba kayan hamood ne kawai dai ansiyane da sunanta. Satin wasila biyu da yan kwanaki bilkisu tasamu hamood akan maganar tafiyar wise, karkatar da hular kansa yayi ya kalleta,
'Gaskiya kiyi hakuri dan ko zata tafi ba yanzuba saboda amfaninta yafi naki yawa agareni domin awajenta nake samun nutsuwa..."
Daga haka yasa kai yafita dama lokacin ficewa zaiyi, wannan maganar ba karamin ciwo tayi mata ba dan har kuka tasata daga karshe ta rarrashi zuciyarta aranar da yamma sukayi waya dasu elmustapha suke fada mata saura kwana biyu su koma Sudan shiyasa ta daura aniyar zuwa gida gobe domin suyi sallama,tun adaren ranar ta sanarwa hamood shiyasa washe gari tayi asubancin zuwa gida domin 9 acan tayi mata koba komai zata samu sassaucin zaman kuncin da take ciki, kowa nagidan yazaci laulayi ne yamaida ita yanda take ayanzu ita kuma bata sanarwa da kowa ba, acan duk su hindu suka sameta shiyasa tasake cikinsu sunata cafta sai daf da magrib takoma gida tana shiga bedroom dinta tayi turus saboda gaba daya aburkice yake akwatunan lefenta babu ko daya sannan laptop dinta dake kan bedside drewar itama wayam gashi da alama komai nata mai daraja dake cikin dakin anyi gaba dashi......
*littafin Kamar da wasa na siyarwane me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:19] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*💖
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*32*
*Littafin kamar da wasa na saidawa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
***A mutukar razane tafita daga dakinta ta nufi na hamood shi dai bata ga wata alama dake nuna cewar anshigar masa dakinba sai dai bata da tabbas, sake fitowa tayi tanufi wurin mai gadi hankalinta atashe nan ta fara tambayarsa suwaye da waye suka shigo gidan amma yace mata babu kowa yau kwata kwata ma basuyi baki ba wasila ma tun safe itama tabar gidan har yanzu kuma bata dawoba haka shima hamood,
Cike da damuwa takoma cikin gida ta nemi wuri ta zauna afalo tana jimami duk kuwa da kiraye kirayen sallar da ta jiyo anayi a masallatai daban daban, to kenan barawon ko kuma barayin ta katangar baya suka shigo? Ta tambayi zuciyarta asirrance, bata samu ta motsa daga inda take zauneba su hamood suka shigo shida wise kamar kullum hannunsu sakale cikin na juna, mikewa tsaye tayi,
"Hamood yau gidan nan babu lafiya... Barayine suka shigo, gaba daya sun kwashe min kayana na lefe da laptop dina harda agogona na gold...."
"What....?" Yafurta da karfi, ai tun kafin tasake magana yanufi upstair da sauri gudu gudu, yana zuwa yashiga bedroom dinshi mintuna kadan yasauko hankalinsa amutukar tashe,
"Kai... To ai nima harda dakina suka shiga, kudin wata mota da na siyar shekaran jiya nazo dashi gidan nan sun dauke.... 7 hundred thousands cash..... Ohh my God"
Wani wulakantaccen kallo wise ta watsa musu su duka biyun kafin ta yi gyaran murya,
"Hmmmm haba dear... Wai kai baka gano game dinba har yanzu? Tab..."
Kallon wise yayi idanuwanshi sun fara yin jaa,
"Me kike nufi?"
"To ai wannan abune abayyane kuma afili... Kawai dai matarka sun hada baki da barayi sun shigo gidanka sun yasheka idan bahaka ba tayaya akan san kashigo da kudi? Sannan tayaya zasu iya haurowa gidannan har su shigo batare da anyi guiding dinsu ba.....?"
Zaro ido bilkisu tayi cikeda tashin hankali sakamakon jin sharrin da wise ke neman kulla mata, shi dai hamood bai sauraresu ba yayi waje da sauri,
"Ke mahaukaciyar inace? Me mijina yayi min da zan hada kai da wasu har in cutar dashi?" Bilkisu tafada tana huci,
"Karyar banza, mijina mijina... Mijinki a ina? Mijin da bai damu dakeba.... Sannan ni kika kira da mahaukaciya ko? To bari innuna miki ni din cikakkiyar mahaukaciya ce...."
Kafin Bilkisu tayi wani yunkuri sai jin abu tayi agoshinta tauuuu take hankalinta ya bar jikinta na wucin gadi, jin duka kawai tayi tako ina, ita ba ma'abociyar fada bace domin rabonta da dambe harta manta,ko lokacin da tana yarinya batayi rayuwar fada ba bare yanzu shiyasa wise tasamu galaba akanta kafin hamood yashigo tayi mata laga laga duk ta kumbura mata fuska ga goshinta dake tsiyayar da jini sakamakon kwada mata flate din silver da tayi awurin, dakyar hamood ya iya banbare Bilkisu daga hannun wise wacce keta faman gwarata abango duk ta yayyaga mata kayan dake jikinta, cikin bedroom dinta ya turata ya rufe sannan yazo ya kama Bilkisu yashigar da ita dakinta dake sama, suna shiga tafashe da wani irin kuka mai cin rai gamida ban tausayi.
****
Sosai jikin fahad yayi kyau kuma ya samu sauki sai dai har gobe akan magani yake kullum sai yasha wasu kwayoyin magani kanana guda uku, yana kwance shi kadai acikin daki domin ya abba yakoma makaranta wayarshi na hannunshi ya tsurawa pic din Bilkisu ido wanda aka yimata ranar bikinsu,
"Wai dagaske Bilkisu kin barni...? Dagaske shikenan narabu dake? Dan Allah Bilkisu kidawo gareni,ki tasheni daga wannan mummunan mafarkin da nakeyi.... Dan Allah ki tasheni kice mafarkine ba gaskiya ba, Bilkisu kice min duk abubuwan da suka faru acikin mafarki ne, wallahi ina sonki.... Ina sonki Bilkisu....."
Salim dake tsaye akansa kawai ido yazuba masa yana kallonsa aransa yana tambayar kansa wannan wacce irin jarrabawa ce abokinsa ke fama da ita? Wai har yanzu yakasa daina son Bilkisu, ohh Allah....,
Fauce wayar dake hannun fahad yayi sai lokacin fahad din yayi firgigit alamun dawowa daga duniyar tunani, kan screen din wayar salim ya kalla hoton Bilkisu ne rangadadau gashi nan tasha mutukar kyau girgiza kai salim yayi yazauna kusa da fahad wanda ke goge hawayen idonshi cikin dabara gudun kada salim din yagani sai dai kashh ya makaro domin salim din yajima da ganin hawayen da yake zubarwa tun lokacin da yashigo cikin dakin,
"Kasan Allah? Zaka kashe kanka abanza akan wata aba banza wai ita soyayya.... Ya zaka zauna kayita kukan zuci da na fili akan so? Wallahi idan baka daina wannan tunanin ba kadai ji abinda Dr yafada maka ko jiya da na rakaka yace idan har baka bar damuwa da tunane tunane ba wannan hawan jinin naka zai janyo maka ciwon zuciya...."
Sake goge hawayen yayi da bayan hannunshi yakawar da kanshi gefe batare da ya kalli salim ba ya runtse idanuwansa,
"Salim wallahi nayi kokarin yin hakan amma nagaza, nakasa cireta araina, nakasa daina tunaninta, nakasa daina ganinta acikin mafarkina, nakasa salim, nakasa, nakasa daina sonta..... Meyasa Bilkisu zatayi min haka?"
"Kai ai banza ne wallahi, anfada maka haka ake so? Anfada maka haka ake soyayya kamar za amutu idan aka rabu? Wallahi ka maida hankalinka, matar da tajima da mantawa ma dakai shine zaka zauna kana westing din time dinka abanza kana tunaninta..."
Tashi zaune fahad yayi yana fuskantar salim,
"Malam karka sake ka zage ni ko ka zagar min mata..."
Dariya salim yayi wacce tasake kular da fahad,
"Lallai kuwa, kasan wani abu? Ai dai pics dinta kake zama kullum kasaka agaba kana kallo ko? To insha Allah daga yau zaka daina, kai wai mekakeson jawowa kanka ne? Ciwon zuciya ko tabin hankali? Anya wannan bilkisun ba asiri tayi maka ba kuwa? Wallahi karaba kanka da soyayya..."
Daga haka yamike zai fita daga dakin,
"Dallah malam ban wayata..."
Juyawa salim yayi ya kalleshi,
"An hanaka, ai wallahi ko zan baka wayar nan sai nagoge hotunan Bilkisu gaba daya...."
Tun kafin yakarasa fahad yadaka tsalle yabishi amma ina bai iya cimmasa ba domin aguje yabar gidan har kofar gida fahad yabishi ganin bazai iya kamashi ba yasa ya hakura yatsaya yarike waist yana haki gashi baya son fita cikin unguwa ahaka domin daga shi sai gajeren wando da t shirt, cikin gida yakoma yashiga daki yayi wanka yashirya sai faman fushi yake, aransa yana cewa idan har salim yagoge masa hotunan Bilkisu to zasu samu babbar matsala, yana shiryawa yana tunani, adaki yayi sallar la'asar sannan yashiga cikin gida wurinsu ayiyah, mariya na shirin tafiya islamiyya yayinda maryam tuni har ta dade acan, dundu ya zuba mata yana fadin,
"Uwar nauyi kullum kece karshen tafiya makaranta kiga maryam tajima da tafiya amma ke sai kinyi makarar da kika saba..."
"Ya fahad Allah hadda na tsaya yi idan naje ban iyaba dukana za ayi.."
"Wai zaki wuce kitafi ko sai nayi ball dake..."
Dasauri tawuce tabar gidan bayan tasaka takalminta, falon mamuh ya leka tana kwance tana jin shirin wasan kwaikwayo mai suna madubi hoton kowa wanda ake gabatarwa atashar freedom radio,
"Mamuh dan Allah me zan samu? Allah yunwa nakeji"
Dagowa tayi ta kalleshi,
"Au ai nazaci baka janye yajin aikin cin abincin da kakeyi ba, shiyasa yau ban raba dakai ba tunda naga ko anbaka baci kakeyi ba..."
Dariya yayi yasaki labulen bayan yakarasa shiga cikin dakin,
"Nidai dan Allah abani wani abu inci kar kuma ulcer ta kamani"
Mikewa zaune tayi tana rage karar sautin radion ta,
"Ai dole abaka abinci dan auta, gaka kuma shagwababbe.... Ohh su fahad ankasa daina baci..."
Shidai yana jinta baice komai ba har ta miko masa kwanon abincin, dan waken fulawa ne subil subil dashi kanana kanana nan tamiko masa robar yaji da ta mai da maggi, dama yau ayiyah bata nan tana can kura tatafi biki kuma sai gobe zata dawo,
"Wai mamuh dan Allah meke rage damuwa ne? Menene maganinta?"
Saida tagyara zamanta takashe radion da take sauraro gaba daya sannan ta amsa masa,
"Fahad hakuri da addu'a sune suke jagorancin maganin kowacce damuwa, duk abinda yasamu bawa mutukar zaiyi hakuri kuma zaiyi addu'a to da yardar Allah zakaga ubangiji ya yaye masa damuwarsa... Kowa na duniya da kagani yanada damuwarsa daban wacce ke damunsa sai dai kawai fadane bazai yiba amma idan da ace wani zai fito yafada maka damuwarsa sai kaga kai taka damuwar bata kai kazauna kana damuwa ba... Hakuri da addu'a sune mafita acikin rayuwa"
Rufe kwanon dan waken yayi yana gyada kai alamun gamsuwa, kallonsa tayi tana harararsa,
"Meke nan kayi? Wai kana nufin har kaci?"
Ashagwabe yadaga kai yana bata fuska saboda yasan halin mamuh yanzu sai tace sai yacinye shikuma yanzu kwata kwata baya iya cin abinci sosai domin ba dadinsa yake jiba,
"Wallahi sai ka cinye abincin nan fahad... Shiyasa dama ban bayar ankai maka dakiba dan ba lallai kaciba kokuma kaci kwaya biyar kabaiwa almajirai sauran kazo kayi karyar kaine ka cinye..."
Tamkar zaiyi kuka yanata yamutsa fuska yasake jan kwanon gabansa yana ci, mamuh sai kara yimasa Nasiha take cikin hikima kan muhimmancin hakuri da kuma yarda da kaddara, kamar yadda tace saida ya cinye dan waken nan tass sannan yatashi cikinsa acunkushe dan tsabar koshi, ai fasa hawa babur dinsa yayi sai akasa yafita, shagonsu yaje fuskarsa babu yabo babu fallasa dama yanzu haka yakoma bai cika walwala ba, yana saman tebur din da suke yanka dinkuna tj yana yanka wani swiss material shikuma fahad yana guiding dinshi yanda yadace yayi yankan salim yazo, sallamarsa kadai fahad ya amsa daga nan yadauke kai dariya salim yayi yadafa kafadarsa,
"Abokina ga wayarka..."
"Ai da ka rike gaba daya kaga saika kasheni da hujja..."
Dariya maganar tabawa salim ya kalleshi,
"Ga dai mai neman kasheka can shiyasa nagoge hotunanta dan nafuskanci wallahi sonta na iya zama ajalinka idan har kayi wasa..."
"To idan tazama ajalin nawa sai me? Ina ruwanka?"
"Da ruwana mana tunda mu zata jawa asara kullum baka da aiki sai dai kasa hotonta agaba kullum kayita kallo kana hawaye... Allah prince kashiga hankalinka karage son nan da kake yimata saboda ina tsoron kar ciwon nan naka yasake tsananta..."
Banza fahad yayi dashi yawarci wayarsa yasoma duba folder din da hotunan Bilkisu suke amma duk empty wato salim dagaske yake yagoge din kenan? Goshi yadafe yana jin bacin ransa yana karuwa, duk maganganun da salim keyi masa baya tankawa dan yadau fushi sosai dashi daga karshe ma bar masa wurin yayi yasauka kasa yashiga masallaci yayi kwanciyarsa sai da lokacin salla yayi sannan yafita yayi alwala, bayan an idar da salla yafito salim na bayansa yamika masa hannu suyi musabaha amma yaki, shi salim ma dariya fahad kebashi wallahi, sanin idan yaje gida tunanine zai addabi ruhinsa yasashi tunanin inda yadace yaje kamar yaje wurin husnah sai kuma yatuna ashe sufa yan school of nursing 6 nayi ake rufe musu gate bashiga ba fita, majalissin marigayi sheikh ja'afar yaje inda wasu dalibansa guda biyu ke gabatar da darasi kowacce rana daga bayan sallar magrib zuwa lokacin sallar ishah sosai hakan yadebe masa kewa bayan an idar da salla yatashi zuciyarsa wasai sai dan abinda ba arasa ba, salim sai kiran wayarsa yakeyi amma yaki dagawa daga karshe kuma kiran husnah yashigo itama bai dauka ba har saida kiran yakatse sannan ya kirata, a dakalin dake kofar gidansu yazauna sunata waya da husnah basu taba doguwar waya irin ta yauba har wurin karfe 9,baya son shiga gida yanzu domin yasan muddin sukayi ido hudu da mamuh sai tasashi yaci tuwon dare shikuma akoshe cikinsa yake, yana kokarin tashi yaya Auwal yafito daga cikin gidan wato babban yayansu mijin anty fauziyya,
"Lahh.... Yaya yaushe kashigo gari?"
"Ba tun dazu naketa jiranka agida baka shigo ba... Wai yanzu me kake shiryawa ne?"
"Yaya karatu fa zan koma"
"A ina?"
"Wai da maryam abacha nakeson tafiya ko Ogun state ance akwai wata private university acan..."