Kamar da wasa complete novel - Chapter 19
Kamar da wasa complete novel Chapter 19: Kamar da wasa complete novel Chapter 19. "Kai dalla rufewa mutane baki, kaje kayi applying a federal university…
3,313 words
"Kai dalla rufewa mutane baki, kaje kayi applying a federal university Kaduna kacike D E saboda karka makara, kaga kusa da gidane kacike duk course din da ranka keso...,sai da safe"
"To shikenan yaya agaida su anty"
Daga haka sukayi sallama yawuce shikuma yaci gaba da zama awurin yana jin baida mafitar da tawuce abinda yaya auwal din yafada yazama dole yabar garin kano koda zuwa kadunan ne.......
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:19] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA...!.*💖
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*Littafin kamar da wasa na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
*33*
***Cigaba yayi da zama awurin bai shiga gidaba har saida yaji sauro ya takura masa da cizo sannan yatashi yashiga ciki, bai shiga wajensu mamuh ba yashige dakinsu kawai yayi shirin bacci ga mamakinsa sai yau yaji baccin ya kauracewa idanuwansa domin aduk dare yasaba yasa hoton bilkisu yayi ta kallo har sai bacci ya daukeshi amma yau gashi babu salim yagoge masa komai,
Juyi yayi cikeda takaici sannan yaja wani guntun tsaki, haka yayita juye juye yana faman zuba tsaki har wurin karfe 12 ganin baccin yaki zuwa yasashi kiran ya abba bugu uku zuwa hudu kuwa yaji yadauka,
"Kanina bakayi bacciba? Ina fata dai ba damuwace ta hanaka bacci ba?"
Sai da yajuya daga kwancen da yake zuwa rigingine sannan yayi murmushi mai dan sauti,
"Ya Abba wallahi al'amarinne sai ahankali yau fari gobe tsumma...."
"Fahad hakuri zakayi fa, kayi kokari karage damuwa kaga condition din da kake ciki ayanzu haka...."
"Insh Allah, yanzuma kasa bacci nayi shine nace bari natabo abokin kwanana inji ya yake ciki...." Yakarashe maganar cikeda tsokana hakan yabawa Abba dariya,
"Ni test guda biyu gareni gobe shiyasa nazauna ina dan taba boko....."
"Allah yabada sa'a, yi bokonka nima bacci zanyi.... Saida safe"
"Shikenan amma pls karka yawaita tunani.."
"Insha Allah babban yaya..."
Daga haka sukayi sallama yajefa wayar karkashin pillow ya lumshe idanuwansa, yasan har yamutu bazai daina son bilkisu ba domin sonta acikin jinin jikinsa yake mutukar za arabashi da sonta to sai dai arabashi da numfashinsa wannan dalilinne yasashi yin mafarkinta awannan daren irin mafarkin da bai taba yiba wai ga mutane nan cike dam akofar gidansu bilkisun koda yaje sai yahango bilkisu tsugunne a tsakiyar mutanen ta hada kanta da gwiwa ba aganin fuskarta agabanshi wani yazo ya kama hannunta yatafi da ita alhalin fahad yanata kiranta fuskarsa sharkaf da hawaye amma bata ko waiwayo ba, shiyasa lokacin da yafarka da asubah jikinsa jike sharkaf da gumi duk kuma asanyaye, haka yatashi babu kuzari yashiga toilet, bayan yafito yana kokarin saka jallabiyarsa yaji baba na buga masa kofa, fita yayi suka fita masallacin tare, sai da yadawo daki yakwanta bayan yadawo daga masallaci sannan mafarkin da yayi yasoma dawowa cikin kwakwalwarsa,
"Meke faruwa da bilkisu.... ?" Shine tambayar da yake ta yiwa zuciyarsa, kasa komawa bacci yayi haka yazauna shiru yanata sakar zuci zuwa can yajawo wayarshi yasoma bincikar ajiyayyun muryoyin da ya adana nata amma su dinma wayam babu ko daya kwafa yayi da dukkan karfinsa yana jin haushin salim na sake turnikeshi,
"Wato har voice din nata ma duk yahada yagoge? Sai nayi maka wulakanci salim.... "
Daga haka yakunna radion wayarshi ko zai dan debe kewa yarage kadaicin da yake ciki, har ya dan fara bacci sama sama yaji kamar amafarki acikin radion ana cewa,
_"Zamu yi amfani da wannan damar wurin taya abokiyar aikinmu wato Bilkisu Lukman Aliyu murnar daurin aurenta tareda zankadeden angonta wato ma'arufi sha guda Hamood Ahmad barewa, muna addu'ar Allah yabasu zaman lafiya yakawo kazantar daki....!"_
Shiru yayi yana saurare har aka kammala sanarwar wasu zafafan hawayene suka ziyarci fuskarsa yana sake maida hankalinsa kan wakar nazifi asnanic wacce ke tashi,
_Na barki ya zan da raina.... Ban kwana...,sai watara na cewar bakina...., ban kwana...., amma kamarki ni ban mancewa.....,ban kwana, ko dare ko ko da rana, sai wata rana nasake fada ban kwana sai wata rana rabin jikina... Ni dake ayau muyi ban kwana sai wata rana rabuwa ba mutuwaba yar uwa rabin raina ban so muyo rabuwa.....!._
Kashewa radion yayi nan yadaga wayar da niyyar bugata da bango amma kuma ko me yatuna oho sai yafasa ya cillata gefenshi,hawayen takaici yaci gaba da zubarwa har na tsawon wani lokaci.
Yana nan kwance jikinsa babu kuzari yaji wayarshi tana vibrating kamar bazai dauka ba sai kuma yajawo yadauka yana goge hawayen idonshi,
"Yan mata...." Yafada muryarshi asanyaye, jin abinda yace yasa husnah murmusawa,
"Ya fahad ina kwana...?"
"Morning dear, how was ur night?"
"Fine sweet heart, dama nakiraka ingaidaka ne...."
"Nagode, me kikeyi yanzu?"
"Na shirya ne zan fita lecture amma ba zama zanyi ba saboda ina son zan shiga kasuwa insiyo lace zan kawo ka dinka min,ranar friday zanje Kaduna..."
"Bari nayi wanka zanzo inrakaki.... Idan kin fito daga lecture din just call me"
Daga haka yatashi ya shiga wanka domin yanzu ya kudurtawa ransa mantawa da bilkisu tunda har itama tamance dashi to babu amfanin yazauna yana damuwa akan wanda bai damu dashiba,da yardar Allah wannan zai kasance karo na karshe da zai zubar da hawaye akan soyayyarta. Wanka yayi yashirya yasha turare sannan yashiga cikin gida yanata kokarin danne damuwarsa sunata raharsu da mamuh ya karya da wainar shinkafa miyar taushe da ruwan zafi yana gamawa yatashi yafice, cikin plaza yaje ya ajiye babur dinsa sannan yataka da kafa zuwa school of nursing domin daga nan din zuwa can baida wani nisa yana hanya husnah ta kirashi tana sanar dashi gata nan fitowa,
Yana zuwa daf da gate din makarantar ya hangota sanye cikin uniform dinta fari tass da dan farin hijabinta marar girma sosai sai bakin toms akafarta da side bag dinta itama baka, jingina yayi da jikin bangon gate din yana kallonta tana tahowa gareshi tana magana awaya, tana zuwa ta tsaya gabanshi suna kallon juna kowannensu fuskarshi dauke da murmushi ahaka tagama wayar tana kallonsa sanye cikin kananan kaya jar t shirt da bakin wando da bakar p cap sai jan sau ciki akafarsa da jan agogo yana sakale da earpiece acikin kunnenshi, sosai yau dinnan yatafi da ita over duk da idanuwanshi sun danyi luhu luhu, can kasan makoshinta tafurta,
"Prince kayi kyau sosai..."
Saida ya lumshe idanuwansa sannan yabudesu akanta,
"Kin fini yin kyau ai..., muje ko"
Tare suka jera akafa suka nufi plaza har shagon da zata siyi leshin saida tazabi wanda yayi mata aka fada mata kudinshi tana niyyar ciro kudin fahad ya biya, shagon sayar da kayan dinki suka shiga yasai duk abinda zai bukata wurin dinka mata leshin, suna daf da shagonsu salim ya kalleta,
"Bakya bukatar kayan kwalliya.....?"
"Inada kayan kwalliya prince..."
"Turare fa? Ko kina dasu muje akara wasu"
Shagon su salim suka shiga nan fahad yayi tamkar ma bai san salim dinba saboda wani irin dauke kai yayi yana zaro wasu turaruka yana dorawa saman teburin dake gaban salim din,
"Nawa wadannan turarukan?"
Dariya salim yayi,
"Koma nawane ai kaima kasan dole inrage muku tunda budurwarmu za asiyawa..."
Harararsa fahad yayi yana motsa baki kamar mai son cewa wani abu amma baiyi magana ba,
"Husnah kiyiwa saurayinki fada yabar gaba dani, daga kawai nayi masa fadan gaskiya shikenan yake fushi dani...."
"Ayya ya fahad kayi hakuri ku shirya..."
Kallonta yayi nan suka hada ido tayi saurin janye nata domin ba kowacce macece zata iya jure kallon kwayar idanuwanshi ba domin akwai wani sirri na musamman aciki duk da idanuwan nashi farare ne tass,
"Babu ruwanki husnah kirabu dashi ai yasan laifin da yayi min babba ne...."
"Tom shikenan nidai nazama yar kallo tunda kunfi kusa da juna..."
Dariya salim yayi yana saka musu kayan acikin Leda,
"Abokina ashe yau soyayya ce tatashi shiyasa naganka cikin farin ciki...."
"Oho maka dan sa ido kawai..."
Da wasa da dariya suka rabu suka haura sama shagon su fahad, atake ya yanka leshin yana kallonta,
"Me Zan dinka miki? Riga da skirt ko da zani?"
"A'a kayi min da skirt"
Murmushi yayi ya dan harareta,
"Da zani zanyi miki zaifi yimiki kyau..."
Matsawa tayi kusa dashi inda yake kokarin karasa yankan kayan,
"Ya fahad banfa iya daura zaniba...."
"Ohhh husnah case... Zan rinka daura miki to"
Kafadarshi ta dan buga tana turo baki, tare sukayi yankan suka koma ciki duk inda yayi tana biye dashi kamar jela yan shagon sai dan kus kus sukeyi duk da dama sun saba ganinta wurin fahad dan indai kaganta ashagon to wurinsa tazo, har azahar suna tare lokacin sallah nayi duk suka fice sallah sai ita kadai bayan an idar fahad ne kadai yashigo amma duk sauran sun wuce sabgoginsu yana zama ta matsa tana karkade masa sumarsa,
"Ya fahad wani abune fari akanka..."
Hannunshi yasa ya kade wurin sannan yaci gaba da dinkin tanata yimasa hira zuwa can ta nisa tana niyyar yin magana yayi saurin janye hannunshi wanda allura taso datsewa,
Hannun tayi saurin kamawa tana shafa masa wurin daga ido yayi ya kalleta,
"Husnah meyasa bakya jin magana ne? Na hanaki tabanin nan amma kinki yarda nanfa ba bayelsa bane..."
"Haba ya fahad kuma dan na tabaka menene? Ai is nothing,normal..."
Saida yataka keken taku biyu sannan yadakata ya kalleta,
"Kina son wata rana nayi disvirgin dinki acikin shagon nan ko? Idan bakya so to kidaina tabani amma idan kika cigaba da tabani komai na iya faruwa dan zan iya baki baby batare da andaura mana aureba, kiyi hakuri har muyi aure sai ki tabani son ranki... Harma sai ankai level din da zakiji na isheki baki son tabanin...."
Ai tana jin abinda yafada tayi saurin rufe fuskarta ta hanyar kifa kanta kan keken da yake dinki, murmushi yayi yana cizon lips dinshi yasan dama dole taji kunya amma shi iyakar gaskiyarshi yafada mata domin idan ba haka yayi mataba to zasu cigaba da taba juna daga karshe har lamarin yayi kokarin kazanta,
"To ki daga kanki inkarasa hada miki intafi gida yunwa nakeji..." Yafada yana murmushi,
"Bari naje nakawo maka abinci...."
Kafin yayi magana tatashi tafice cikeda kunya dan har lokacin bata yarda ta bude idanunta ba, tana fita kuma saiga salim shi yaci gaba da tayashi hira har yan shagon suka dawo kafin 3 yagama dinka mata hadaddiyar skirt da riga yana kokarin mikewa sai gata tashigo itada kawarta hafsa tasha kwalliya cikin doguwar riga ta atamfa da dan mayafi, ahankali yafurta,
"Kinyi kyau princess......"
Murmushin jin dadi tayi ta ajiye masa abincin tana furta,
"Thank you"
Basu wani bata lokaci ba takarba tatafi yau dai yayi niyyar cin girkinta shiyasa yakira salim awaya yazo suci tare, jalop din macaroni da dankali yaji sadden sai kamshi yake tare sukaci shi dai fahad tsakura kawai yake saboda baya zagewa yaci abinci yanzu. Sosai al'amarinsa da husnah aka samu cigaba domin yana sakar mata fuska yanzu sabanin da ammafa har gobe bai taba jin sonta yana yawo acikin jininsa ba kawai dai yana biye mata ne kuma yanajin shakuwa mai karfi tsakaninsu.Duk da baya son karatu kusa da gida yacike D.E kamar yadda Yaya auwal yace yanzu kawai zaman jiran admission yakeyi.
***
Bilkisu kam ranar da sukayi fada da wise tayi kuka kamar me dakyar hamood yashawo kanta ta canja kaya yakaita chemist aka yimata plasta awurin aka manne da audiga da bandeji, suna dawowa kuma yakalleta yana fadin,
"Shawarar da zan baki babu ruwanki da shiga sabgar wise domin ita dambe awajenta ba komai bane sannan tafi karfinki saboda harda maza dambe take...."
Cikin masifa da jin haushi bilkisu ta kalleshi,
"To yanzu me kake nufi? Nufinka kenan wannan ciwon da taji min taci bulus bazaka tsawatar mata ba?"
"Kinga bilkisu dan Allah kibarni naji da bakin cikin satar da akayi min, nidai nafada miki babu ruwanki da ita idan kuma bahaka ba to jiki magayi...."
Tsabar bakin ciki kasa cewa komai tayi har yafita daga dakin, tagumi ta rafka tama rasa wanne irin tunani yadace tayi. Tun daga wannan rana takoma rayuwar daki domin bata fitowa sai idan wani abu zatayi shiyasa zaman gaba daya ya dameta kuma ya gundireta wannan dalilinne yasata yanke shawarar tunkarar hamood da maganar komawarta aiki ko tasamu tarage kadaicin da take ciki tunda ko babu komai fitar zaiyi keeping dinta busy, aranar da daddare bayan yashigo ta sameshi da maganar wani kallo yayi mata irin na yan iska sannan yaci gaba da abinda yakeyi yana cewa,
"Mai gado kenan, wai ke wacce irin macece? Atunaninki zan amince dake har inbarki kifita aiki bayan alhalin nasan har yanzu wannan karamin yaron ba daina sonki yayiba? Ai sai kuhada kai kurinka ha'intata..."
Cikin bacin rai ta kalleshi bakinta har rawa yake yi,
"Hamood kallon da kake yimin kenan? Wannan itace sakayyar da zaka yimin? Idan har Zan iya hada baki da fahad inci amanarka to meya hana inzauna tare dashi tun farko?"
"Look mai gado dan Allah karki nemi yimin hayaniya yanzu saboda agajiye nake i have to rest so pls walk out....."
Bakinta abude da mutukar mamaki tajuya tafice zuwa dakinta rasa wanne irin fassara zata yiwa wadannan kalaman na hamood tayi, wato dai yanaso yace mata bai yarda da itaba? Kasa bacci tayi a wannan daren shiyasa tunda sassafe takira abbanta awaya ta sanar masa nan yace zai kira hamood din tabashi number dinsa, wurin 9 yashiga dakinta yace tatashi zasuje gidansu abbanta na nemansu duk wannan maganar yana yinta ne cikin daurewar fuska, haka suka je gidan babu wanda ke cewa ko uffan Abba yana zaune falonsa yagama karyawa amutukar ladabce hamood yagaida Abba da Ammah kowannensu ya amsa fuska asake sannan Abba yayiwa hamood maganar da yakirashi dominta wato na komawar bilkisu aiki,
"Hamood mai gado ta kirani tace tana son zata koma aiki amma da tayi maka maganar kanuna kamar baka aminceba domin ma tamkar har yanzu baka gama yarda da itaba hakane....?"
Sosa keya yasoma cikeda ladabin karya yace,
"Abba wallahi bahaka nake nufiba, nidai kawai banida ra'ayin matata tayi aikine nafiso tazama full hause wife"
"To shikenan ke mai gado kinji abinda yace, tunda baya bukata kiyi hakuri... Kibari anjima zan turo miki kudi a account dinki sannan duk sanda kike da wata matsala ki sanar dani..."
"Shikenan Abba, nagode madalla"
Tafada tana share hawayenta, anan hamood yatafi yabarta zata wuni bayan yatafi su amma Nasiha suka yiyyi mata har tasaki ranta, tun kafin tabar gidan taga abba yatura mata dubu dari biyar cikin account dinta, bayan sallar magrib tana niyyar tafiya saiga Abba yadawo shida ya mudan wanda yakawoshi gida daga garko domin yau can abban yaje kuma cikin rashin sa'a motar da suka tafi da ita tasamu matsala ganin zata tafi Abba yace ya mudan yakaita gida, baya tashiga suka tafi lokacin da sukaje kofar gate din gidan anan ta sauka suna yin sallama da ya mudan hamood yadanno motarsa shida wise hakimce agaba kamar kullum tayi daurinta na ture kaga tsiya.........
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:20] Hafsat Rano: *Wannan littafin na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
34 ***Tana shirin barin wurin hamood yakaraso shida wasila wani mugun kallo ya watsa musu ita da ya mudan sannan ya danna hancin motarsa zuwa cikin gida, bata kara ko mintuna ukuba tashiga itama tabar ya mudan zaune yana jimami tambayar zuciyarsa yake tayi,
"Wai dama wannan shine mijin da bilkisu ta aura?"
Yayiwa kansa tambayar nan tafi sau dari kawai tunani yake shin yafadawa bilkisu gaskiya ko kuma karya fada saboda ko babu komai ai yar uwarsa ce daga karshe dai yabi shawarar zuciyarsa na kawai yaja bakinsa yayi shiru domin gudun abinda zaije yazo jan motarsa yayi yabar wurin yanufi gida.
Bilkisu adarare tashiga cikin gidan saboda iya kallon da hamood kadai yayi musu ya isa sanar mata cewa there is something wrong, tana shiga falo suna tsaye shida wise juyowa gaba daya yayi yana harararta,
"Daga ina kike? Maigado bafa zan lamunci yawon ta zubar ba acikin gidan nan..."
Ita tsabar takaici ma sakin baki tayi tana kallonsa, har saida yadiga aya sannan tayi magana,
"Lallai hamood, ya mudan nefa dan uwana abba yasa yakawo ni tunda kai bakaje ka daukoni ba..."
"Ni bawanki ne da zanje na daukoki ko kuwa ni driver dinkine? Kishiga hankalinki kin gane ko..... Aikin banza kawai Malam haka kawai najawa kaina masifa naje na jajibo yar matsiyata...."
Zaro ido bilkisu tayi tana kallonsa,
"Hamood ni kake kira da yar mutsiyata? Wallahi karyar mutum yakira iyayena da wannan sunan, yayan matsiyatan dai suna inda suke..."
Daga haka tawuce sama tana shiga daki tazauna tana ta surutu ita daya cikin masifa,
"Haba wannan wacce irin rayuwace wai? Mutum kullum idan banda cin mutunci da jaraba bashida zance.... Ni wallahi zaman gidanka yafita akaina gaba daya nagaji da igiyar aurenka haba...."
Tun daga ranar tsakaninta da hamood babu daddadar magana abu kadan sai zagi ita dai ji take ankusa zuwa gabar da dole zata bar gidansa domin gudun kada cutar hawan jini ta kamata saboda kullum cikin bacin rai take da damuwa idan yau basu debota da hamood ba to sai sun haura da wise shiyasa duk tabi ta lalace ta fige, tana cikin wannan halin bikin khulsum yazo bilkisu nason taje ayi komai da ita kamar yadda khulsum din tayi mata amma fafur hamood ya hana sai bikin dai yabarta ranar da za afara bikin tun sassafe tabar gidan domin dama jinta take kamar akan kaya, gidan hamood ya zame mata tamkar kurkuku, duk ankon da aka fitar ta turawa khulsum kudi ansiya mata dama ko takan hamood bata bi ba domin wani wulakanci yake ji kwana biyun nan, zuwanta gidan bikin cikin mutane yasata mancewa da damuwarta domin ga kawayensu nan yan makarantarsu da abokan aikinsu, kwana uku aka dauka ana yin bikin sai da aka kai amarya gidanta sannan bilkisu tasamu zama. Lokacin da ta koma gida babu kowa agidan daga hamood har wise din asalima ita daya ta kwana agidan, washe gari ma haka kai saida tayi kwana uku ita daya ce kwal cikin gidan tana rayuwarta takira hamood yace mata yana abuja amma yau ko gobe zai shigo so take yadawo ayi wacce za ayi domin yakamata su nemi magani saboda tagaji da wannan zaman na cuta domin akwai cutarwa acikinsa. Tana zaune falo tana kallon tashar zee world mai gadi yayi mata knocking, hijab tasa ta leka cemata yayi sunyi bako wai hamood ne ya aiko shi, fita compound din gidan tayi, kamar a mafarki taga dr Abrar wato tsohun saurayin khulsum kawarta domin kamarma shi zai auri khulsum din Allah ne dai baiyiba kawai,
"Ahhhh likita... Yau kai nake gani?"
Murmushi yayi yafito daga cikin motarsa,
"Hajiya Bilkisu yan jarida..., ya aikinku? Ina kawarki ashe tayi aure ta kini ko?"
Dariya bilkisu tayi,
"Likita ba kinka tayi ba kawai dai Allah ne baiyi zaku zama ma'aurata ba..."
"Adai yimin dadin baki irin na yan jarida..."
"Ba dadin baki bane gaskiya ce kawai Dr..."
"Wai dama kece wacce hamood yace inkawowa sakon nan?"
"Ehh nice..."
Tafada cikin murmushi,
"Ok to amma meyasa ban taba ganinki a asibitinba? Ai akwai tarurruka da ake shirya muku domin wayar muku dakai da kuma shawarwari da ake baku na musamman domin kula da lafiyarku... Idan har zakubi ka'ida to ko mai lafiya bazai fiku walwala da tsawon kwana ba...."
"A'a likita wai meke faruwa ne? Wanne ciwo kenan?"
Gyara tsayuwarsa yayi, cikin murmushi yace,
"Karki damu bilkisu u know am a Dr,wai dan nasanki ko kin sanni isn't something bad duba da yanayin aikinmu am always confidential soo feel free, wallahi da asibiti ma kikazo bazan taba nunawa cewar nasanki ba that's the rule.... Mu a ka'idar aikinmu koda ace kasan mutum when he comes to u with such case zaka nuna kamar ma baka taba ganinsa ba sai ranar unless shine yayi maka magana i hope u understand?"
Goge fuskarta tayi da gumin dake tsattsafowa tasake kallon Dr abrar dakyau,
"Likita dan Allah fada min in a simple way da zan fahimta saboda ni duk wadannan maganganun naka babu wanda na fahimta am confuse...."