Kamar da wasa complete novel - Chapter 23
Kamar da wasa complete novel Chapter 23: Kamar da wasa complete novel Chapter 23. "Sakar min hannu, kaje kayita zama da matar taka.... Nidai kasani nafasa…
3,360 words
"Sakar min hannu, kaje kayita zama da matar taka.... Nidai kasani nafasa aurenka saboda bazan taba zama tareda itaba....."
Gaba daya hannuwan nata yayiwa ja daya sai gata kan jikinshi rungumeta yayi sosai ajikinsa wai zaiyi rarrashi amma taki bashi damar hakan daga karshe daga shi har ita basu san menene ya gifta ba kawai dai sunji sun shagala da tsotsar bakin juna abinda bai taba faruwa ba tsakaninsu asalima idan itace ta nemi taba koda hannunsa ne fada yake yimata. Kifa kanta tayi saman kirjinsa tana kuka ahankali,
"Kiyi hakuri husnah.. Bana son wannan kukan naki... Kuma kisani bafa fin son bilkisu nayi ba akanki... Kema u are always in my mind... Yanzu duk yadda zan kwatanta miki u won't understand but am assuring u idan mukayi aure gonnah show u how much u mean to me..."
Haka yayita rarrashinta da kalamai masu dadi amma taki saurararsa daga karshe ta fincike tayi cikin gida tana sharar hawaye, daddumar da suka zauna ma sai shine ya nade yamika ciki, haka yatafi babu kuzari atare dashi domin wani irin tausayinta yake ji amma kuma da zarar yatuna da cewa shine sanadin kukanta sai yaji wani iri, tun yana hanya yaketa kiranta amma taki daga wayar. Ahanya yayi salla sannan yawuce gida, yunwa yakeji sai dai yana kunyar shiga gidan musamman da su anty asabe suka kirashi suna tayashi murna harda kiransa da ango, cikin sa'a yana shiga dakinsu ya iske abba yana cin tuwon biski miyar kubewa, zama yayi suka karasa tare sai ga salim yashigo,
"Karbi system dunka..., ya kukayi da mutuniyar?"
"Tayi fushi inata kiranta taki dauka..."
"Saika rarrasheta..."
"Dolena ai... Zan gwada"
Ficewa salim yayi dama Abba yadade awaje shikam, ga mamakin fahad yana duba system dinshi yaga hoton Bilkisu kan screen din yafito radau ashe duk hotunan da salim yagoge awayarshi da jimawa ya ajiye masa sune, wani farin cikine ya sake lullubeshi nan yarinka bin hotunan daya bayan daya yana shafawa.
_BILKISU_
Dawowarta kenan daga islamiyyar da take zuwa kowacce asabar da lahdi, tana fitowa daga wanka ammah taleko tace tazo inji Abba dama yau yadawo daga garko tun jiya canma ya kwana,agaggauce tasaka doguwar riga ta dauki hijabi tafita tanufi sashen Abba, suna zaune shida Ammah tana sake shirya masa kayansa wadanda zai tafi umarah dasu yauda daddare,
"Mai gado... Karbi wannan"
Hannu tasa takarbi kudin da abba yamika mata,
"Sadakinki ne gashi nan... Jiya aka daura miki aure insha Allah nanda sati uku zuwa Hudu zaki tare agidan mijinki, kiyi hakuri kiyiwa mijinki biyayya sannan ki zauna lafiya dashi..."
"To Abba..."
"Allah yayi miki albarka... Tashi kije"
Tashi tayi kanta na sara mata yana yimata wani irin juyawa ahaka tafita daga falon tana fita Abba yadubi ammah yace,
"Mahaifin tsohon mijinta ne yazo min da maganar neman aurenta shine kawai nace yafito adaura aure takoma gidan mijinta domin da sabon gini gwara yabe..., zaman nan nata dama yana damuna wallahi shiyasa tunda Allah yakawo ai gara ayi"
"To Allah yabasu zaman lafiya yasa mutuwa ka raba" inji ammah,
"Amin, kinga ko babu komai itama iyallo yanzu zata samu zama wuri daya wannan sintirin zata hakura dashi"
"Hakane".
Tunda Bilkisu tashiga dakinta take kuka ita dai tasan bata bakin ciki da zabin Abba amma harga Allah bataso wannan aurenba, wannan wanne irin aurene za adaura ba afadawa kowa ba sannan ba abarta ta ko ga mijinba? Tunda aurenta yamutu da hamood take addu'a babu dare babu rana akan Allah yafito mata da miji nakirki mai kaunarta saboda Allah amma shiru kakeji har yau babu wanda yazo yayi sallama da ita akan yana son zai aureta, ya mudan ma lokacin da iyallo tayi masa tayin aurenta ki yayi kiri kiri yace bazai auri bazawara ba saboda yanada budurwarsa gashi yanzu har matarsa ta haihu shiyasa iyallo kullum cikin zuwa gidan take tana fada da masifar Bilkisu taki aure bayan zaman da tasha da yanzuma gashi tasake dawowa, iyallo bata yin wata daya batazo gidan nan ta tayarwa da kowa hankali ba, wannan zuwan da tayi kuwa na karshe cewa tayi Alh Ilya zata aurawa Bilkisu dama ai idan akabi salsala dan uwanta ne, kuka Bilkisu keyi sosai domin duk tunaninta alh ilya dinne aka aura mata domin irin alhajin kauyen nanne matansa uku da 'yaya rututu kai idan kaga tukunyar da ake girki da ita agidansa sai ka kalleta ka kara, gashi kuma ba acikin garko ma yakeba acan wani kauyen kayau yake shiyasa abin yake tsoratata. Saida tayi kukanta ta godewa Allah sannan tayi shiru amma fa bata da walwala, daren ranar Abba yatafi umarah ita kam da ciwon kai ta kwana washe gari ko aiki bataje ba tana daki akunshe daga karshe takira maama tana kuka tana fada mata wai Abba yadaura mata aure da alhajin kauye gashi har yau bata ga mijinba, hakuri maama tabata sannan tayi mata kalamai masu kwantar da hankali tace insha Allah auren nan zataga fa'idarsa da alkhairinsa, da ta tambayi maama ko tasan waye mijin nata maama cewa tayi bata sanshi ba haka sukayi sallama taci gaba da zama cikin fargaba gashi sam ammah taki bari ma suyi maganar dole tahakura ta zubawa sarautar Allah ido.
Bayan kwana biyar da daura auren fahad yashirya yaje gidan wai gaida su ammah dakuma yimusu godiya tun tuni yake bin salim akan ya rakashi amma yanata kawo uzururruka shiyasa yau yashirya yayi tafiyarsa shi kadai, iya ammahn ce kadai ita tayi masa lale tasa Rabi takawo masa kayan motsa baki amma baisha koda ruwaba, shi kunya ammah kunya dan dakyar ma suka gaisa daga karshe ammah tashige bedroom zuwa can takira Rabi tace ta rakashi dakin Bilkisu.
Kasancewar Rabi tasan ba a shigarwa Bilkisu daki daga waje ta tsaya ta nuna masa dakin yashiga bayan yacire takalminsa, tana kwance kan gado tayi ruf da ciki tana shan iska domin dakin cike yakeda sanyin air condition, sannan ga kamshinta nan wanda yasani tun usuli yacika dakin, kalba ce akanta kan babu dan kwali sai yar doguwar riga iya gwiwa light pink mai karamin hannu, ganinta yayi tayi masa yar karama acikin idanuwansa domin babu abinda takara saima yarinta da ta kara kai idan basani kayiba zakace yar 22 years ce saboda rashin girma......
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[11/28, 08:21] Hafsat Rano: 42***Tamkar wanda yasamu tv haka ya tisata agaba yana kallonta yafi mintina goma tsaye kanta yana kallonta irin kallon kurulla kamar wanda keson gano canjin da jikinta yasamu a kwanankin da basa tare,
Gefenta yasamu ya zauna yana cigaba da kallonta ahaka wayarshi ta dan fara kara cikin azama ya matseta ya danne karar sannan ahankali yamaida ita silent kafin ya maida kallonshi kanta, juyi tayi daga rub da cikin da take zuwa rigingine tana mikar da tasata bankaro kirji tareda sakin hamma a lokaci daya amma har time din cikin bacci take domin rabonta da bacci mai yawa tun ana igobe Abba zai sanar da ita maganar aurenta.
Sake cika yaga tayi a idanuwanshi ta chest dinta wanda ko bra babu, dan hararar wurin yayi yana jin kishi na taso masa sakamakon tunawar da yayi cewar ta taba aurar wani fa bayan shi, shikuma gashi da jarabar kishi musamman ma akanta, idonshi yamayar kan cinyarta da ta dan bayyana kadan sakamakon kwayewar da rigar tayi lokacin da take yin juyi, luwai luwai jikinta yake haka yarinka binta daga kasa har zuwa sama sannan yadauko daga sama izuwa kasa, kan kwaurinta ya tsayar da idonshi yana cije baki sam baima taba kula da singalalinta ba sai yau, anan ya tsaida kallonshi yana ta son tunowa da abinda yataba karantawa a facebook dangane da cikar kwauri sai zuwa can yatuna wani post ne da jimawa yakaranta wai ta kwauri ake gane sweetness din mace, idan sha rabanta acike yake to babu karya tayi, ga mamakinsa sai yayi hanzarin maida kallonsa kan hips dinta domin yana daya daga cikin abubuwan da aka fada acikin post din dan ranar da ya karanta ma shi kunya ya rinka ji shi kadai haka kawai wani friend dinshi tagging dinshi akan post din, yana cikin nazarin hips din nata zuwa samanta yaji wayarta ta kaure da kara ahankali tamika hannu ta daukota idanuwanta arufe ta daga wayar ta kara acikin kunne,
"Kawata nace yanaji shirune.... Nashirya fa tun dazu..."
Cikin bacci taji abinda khulsum tafada wallahi ita sam tamanta ma ashe sun shirya tafiya asibiti dubo Christy abokiyar aikinsu wadda aka yiwa cs kwana biyu da suka wuce amma babyn babu rai shine sukace zasuje dubata yau domin suna zaman mutunci da ita.
"Yi hakuri Maman Khalifa wallahi bacci ne ya daukeni... Bani 10 minutes ina nan zuwa..."
Har lokacin bata san da mutum acikin dakinba duk da tunda tafarka take jin wani kamshi ya cika dakin, tunda tafara waya yaja baya sosai yamatsa daga kusa da ita sabanin da,
Tashi zaune tayi Allah yasota atishawa ta fito mata amma da niyyarta ta kwaye rigar jikinta tashiga toilet, kamar ance ta kalli bayanta taga mutum ba karamar razana tayiba saida tayi ta maza sannan ta iya controlling kanta amma acikin zuciyarta addu'a ta kamayi ba kakkautawa jikinta har rawa yakeyi saboda tsoro, fuskarshi ta kalla tabbas fahad ne to amma meya kawoshi dakinta? Wannan itace tambayar da tafi kai kawo cikin kwakwalwarta,
"Malam lafiya?" Tafada cikin dakewa, ai ga mamakinta sai taga ko kallonta baiyiba hankalinsa na kan wayarshi dake hannunshi fuskarshi kuma daure kamar an aiko masa da sakon mutuwa, kasake tayi tana kallonsa sosai taga yacika mata idanuwa domin a yar shekara dayan zuwa da rabi da bata ganshiba yasake zama cikakken namiji duk da ba kiba yayiba amma ya dan murmure kuma har yanzu za asashi sahun sirara, gashi dan tsaurin ido har gemu taga ya tsayar na rashin kunya irin yanda samarin yanzu keyi idan suna tashen balaga, har takaraci kallonsa tagama bai daga ido ya kalleta ba, shaddace ajikinsa mai kwabo kwabo milk colour harda hula amma yacire hular tana ajiye kan cinyarsa fuskarsa tayi haske sosai da duk jikinshi gaba daya ma amma kowa yaga fuskar yasan he's still young, sosai abin yabata haushi da tayi masa magana ya shareta,
"Malam dakai nakefa? Meya kawoka dakina? Yakamata kashigo min daki any how?"
Sai lokacin ya daga ido ya kalleta amma baiyi magana ba dolenta tajanye idanuwanta daga gareshi saboda kwarjinin da yayi mata. Cikin fushi taja hijabinta tafita, dakin Ammah taje tana tambayarta me fahad keyi adakinta nan ammah tace shida dakin matarsa sai aje ana tambayar me yakaishi?
Sake komawa dakin nata tayi jiki babu kwari wato shi aka sake aura mata akaro na biyu ashe ashe zamansu bai kareba Allah kadai yasan ranar karewarsa, ita dai tasan bazata yiwa Allah butulciba amma gaskiya bahaka taso ba, ba da fahad take son gudanar da kayan kunyar nanba, bata son yaga girmanta har yakai ga rainata dama gashi yanzu tafara ganin salon rainin nashi tunda ko gaisheta baiyi ba bare tasa ran zata bashi umarni yabi kamar zamansu na baya, afusace tashige cikin bathroom bayan taja towel dinta dake kan kofa, tana wanka tana tunani yanzufa yaron nan dan baida kunya sai yace zai ziyarceta a shimfida ko?
"Subhanallahi... Allah ya sawwake... Ashe kuwa zan mutu da budurcina..." Tafada acikin zuciyarta. Shi dai yana zaune yana sauraron karar ruwan da take wanka dashi acikin bathroom, yasan jira take yagaisheta kamar yadda yakeyi ada amma abinda bata saniba shine yanzu ba da bace idan har tunaninta shine zai gaisheta to zasu shekara basu gaisa ba sannan yanzu itace ma zata rinka gaisheshi ko tana so ko bata so dolenta dan bazai dauki raini ba, jinsa yake yi yanzu a matsayin babba gaba da ita,
Yanata murmushi shi kadai sakamakon abinda yagano a facebook dama post din da akayi magana akan cikakkiyar mace dinnan ta yadda ake gane alamominta yatafi nema wanda yakai kusan shekara da karantawa amma dayake Facebook baya goge abu komai jimawar da yayi sai gashi yasameshi bayan dogon bincike, duk macen dake da kananun ido to jarababbiya ce awurin shimfida,sannan wadda dan yatsanta na kafa nakusa da babba yafi babban tsawo to tanada bukata sosai, mai hips sosai tanada nisa, haka mai manyan mazaunai, sannan mai manyan chest itama tanada yawan bukata,mai dan mitsitsin baki to halittarta ma ta ya mace hakan take, yana tsaka da sake karantawa ta bude kofa tafito daga cikin bathroom din fuskarta babu fara'a shima gimtse tasa fuskar yayi yana sake karanta post din wanda wannan shine karo kusan na biyar da yake ta tisawa yana sake maimaitawa, shi bai damu da yaga wadannan abubuwan da ya karanta atare da husnah ba amma akan Bilkisu kam sai yagane komai.
Tana cika tana batsewa ta nemi wuri ta zauna bayan ta dauki man shafawa ita duk abinda yafi bata mata rai shine rashin gaishetan da baiyiba sannan tana yimasa magana yayi wani banza da ita dan tsabar rainin wayo acikin hijab taketa nuku nukun shafe jikinta da mai saboda yanzu yanayi ya sauya duk da jiya da yau zafi akeyi amma idan kayi wanka baka shafa maiba sai kayi fururu saboda lokacin sanyine, ta gefen ido yake satar kallonta,yatsun kafarta yaketa satar kallo ai kuwa yaga nakusa da babban yafi babban tsayi, daidai lokacin ta mike ta isa gaban wardrobe dinta ta juya mishi baya tana neman kayan da zata saka,kallonta yake tayi ta baya ya kafe hips dinta da ido,
"I will find it out...." Yafada acikin zuciyarshi yana dariyar mugunta,
"Uwar son girma, ashe har yanzu halin nan yana nan ba asauyaba na son girma... Very soon Zamu banbance nidake waye babba...." Yasake fada cikin ranshi, doguwar riga ta ciro ta atamfa tanata yin kunkuni,
"Kawai zaka wani shigo min daki kasani agaba... Ban son takura..."
Daga haka tawuce bathroom tana cigaba da kunkuninta, duk abinda take fada yana jinta saboda shi jinsa akusa yake komai kankantar motsi sai yajishi shiyasa suke yawan fada da abba yayanshi domin idan yana bacci ko tari abba yayi sai yaji, jine dashi sosai kamar maciji ko kana dan nesa dashi kayi gulmarshi sai yaji sai dai kawai yarabu dakai yayi kamar baiji ba. Mintuna kadan sai gata tafito rikeda hijabinta a hannu, akofar bathroom din ta tsaya ta shanya towel dinta sannan takaraso cikin dakin daidai lokacin da wayarta tafara kara cikin sauri ta dauka tana cewa,
"Gani nanfa... Fito kofar gidanki zanzo da mai napep inyaso kawai sai mu wuce..."
Daga haka ta ajiye wayar tawuce gaban mirrior ta bulbula turare halinsu daya dashi wurin son kamshi kwata kwata bata gajiya da siyan turare ko tanada kwalba ishirin a ajiye kan mirror dinta, maroon din mayafi taciro kasancewar atamfar jikinta akwai ratsin maroon ajiki ta dauki hand bag milk ta dauki wayarta sannan tanufi wurin shoe rack tadauko flat din takalminta tasaka tayi hanyar kofa, sai da takusa zuwa kofar cikin isa da kasaita taji yace,
"Ina zakije?...."
Bata ko kulashiba tayi niyyar fita nan taji yasake maimaita ina zakije?
Kanta tsaye tabude kofar zata fita amma kawai sai ji tayi ya danko waist dinta yadawo da ita baya, sam bataji lokacin da yataso ba bare taji tafiyarsa, mayar da kofar yayi ya rufe, yanda ta sha kunu haka shima yasha kunu, kawar da kanta tayi gefe daya tana huci yayinda shikuma yake kallonta ko kiftawa baya yi,
"Wai meye haka? Wannan wanne irin wulakanci n...."
Bata kai ga karasawa ba taji ya fincikota wanda har saida kirjinsu suka manne wuri daya, numfashinsu ke haduwa kowa yana shakar na kowa, ido ta daga dakyar ta kalleshi shima yana kallonta,
"Wa kika tambaya da zaki fita?....... Ehye?.... Tambayarki nake.... Nace wa kika tambaya?" Yakarasa magana cikin tsawa,
Yana kallon yadda idanuwanta ke kadawa tamkar zata fashe da kuka, cikin bakin ciki da rawar murya tace,
"Ba asaniba..... Dallah ni ka sakeni...."
Sake matseta yayi har lokacin yana rikeda damtsenta daya tana manne kirjinshi,
"Ni kike cewa baki saniba?.... Idan kikayi wasa wallahi daga yau bazaki sake ko taka daidai da kofar gidaba.... Zakiyita zama cikin gidan nan babu fita har sai ranar da na gadamar daukarki na kaiki duk inda nakeso...."
Sake matsota yayi cikin huci yace,
"Sannan kisan irin maganar da zaki rinka fada min idan bahaka ba sai kinyi nadama...."
Fincikarta yayi wanda har kayan hannunta suna zubewa yaje ya jefata kan gado nan ta zabura ta mike wanda hakan yaso bashi dariya amma yadake,
Tsayawa tayi ta rike kugu tana haki tamkar dambe zasuyi,
Matsawo yafara yi ahankali yana cewa,
"Ko dambe zakiyi dani ne? Nace dambe kika tashi yi dani....?"
Kafin tabashi amsa wakar ali jita tafara tashi daga cikin wayarshi, _"Rana da wata suna da haske gimbiyata sai ke soyayyarmu har abada...ko rana da wata sun daina haske gimbiyata sai ke soyayyarmu har abada..... I love u baby.....Sarauniya baby...."_
Komawa yayi da baya yadauki wayar domin yasan husnah ce saboda ita kadai yasawa wannan tune din,
Zama yayi kan bedside drewar dinta yadauki wayar,
"Sweet ma'u ya akayi.... Ko har yanzu fushin akeyi dani?" Yafada yana murmushi kasancewar tun lokacin da yafada mata anmayar da aurensu da Bilkisu bata daukar wayarshi sai yau da ta kirashi,
"Ya fahad Allah kai dinne kana bani headache dayawa...."
Hands free yasaka wayar tayadda Bilkisu zataji komai wacce har lokacin ke tsaye tana rikeda waist dinta,
"Am very sorry one love... Ki yafewa Prince dinki idan bahaka ba ciwon zuciyata yatashi dama kuma kin san ata sanadiyar sonki ya kamani...."
Ajiyar zuciya husnah ta sauke sannan cikin sanyin murya tafurta,
"No ya fahad dan Allah kabari bana son inrasaka.... Na hakura, bazan sake bata maka rai ba.... Ranar ma ban san meya sameni ba har nayi fushi dakai... Am so sorry..."
"Kishi...." Yafada yana murmushi yana satar kallon Bilkisu wacce tacika tayi famm sai huci takeyi kamar bijimin sa,
"U are right.... Ni nasan inada kishi akanka bana son nayi shearing dinka da kowa amma babu yadda zanyi i will accept koma meye...."
"That's why am loving u.... I love u yanmatanah..."
Ai Bilkisu bata jira tagama jin wadannan mugayen kalmomin nashiba ta shige cikin bathroom ta bugo kofar da karfi garammm wadda hatta husnah dake kan waya saida taji, har suka gama waya da husnah Bilkisu bata fitoba, hularshi yadauka yasaka yasan acike take dashi na ya hanata fita unguwa gashi kuma yazo yana waya da wata agabanta duk da baida tabbacin ko tana kishi ko sabanin haka amma yadauki alwashin gano hakan, itace bata saniba duk maganganun da yake fadawa husnah ita yake fadawa indirectly amma yasan bazata ganeba, gaban bathroom din yaje yatsaya yakara kunnensa amma baiji motsin komai ba yasan ba komai takeyi ba,
"Kin dai ji abinda nafada miki ko? Karki sake inji labarin kin fita... Sannan ki kira ita kawar taki kifada mata nahana wannan fitar..."
Cikin jin haushi da masifa yaji tace,
"Sai anfitan... Kayi abinda zakayi... Kuma baza akiratan afada mata dinba kai ka kirata mana da kanka... Aikin ban..."
"Idan kika kuskura kika karasa ko...idan ba tsoro ba kibude kofar mana....", kwafa yayi da karfi sannan yace,
"Ni ai bana kiran matan mutane iya inda Allah ya tsayar dani na tsaya... Gobe aiki kadai nayarda kifita baya ga nan duk inda kikaje keda Allah..."
Bai jira abinda zatace ba yawuce yafita yana jin wayarta nata ringing duk da bai dubaba yasan abokiyar tafiyar tatace taji shiru shine kila take kira, duk da bai fada directly ba tagane da hamood yake da yace wai shi baya kiran matan mutane, jin yafita yasa wasu hawayen bakin ciki zubo mata, wai ita fahad kanin kanin bayanta ke yiwa haka wannan wacce irin kaddara ce? Wai meyasa zaman nan yasake kulluwa?....
*Littafin nan na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:21] Hafsat Rano: *Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
44****Dariya ma shi taso bashi saboda yadda ta runtse idanuwa tana jiran taji abinda zai biyo baya, afirgice ta bude idanuwanta tana kallonshi saboda jin yadda ya take mata babban dan yatsan kafarta, muryarta na sarkewa tana rawa tafara hankadeshi tana cewa,
"Meye haka... ? Dallah ni sakeni..."
Sake damketa yayi yana kokarin saita kanshi, rikon da yayi mata ba karamin riko bane domin da irinta guda biyar zasu hadu ba lallai su iya kwatarta ba,