Kamar da wasa complete novel - Chapter 24
Kamar da wasa complete novel Chapter 24: Kamar da wasa complete novel Chapter 24. "Kin san me? Ina raga miki nefa saboda wani dalili wanda nabarwa kaina…
3,367 words
"Kin san me? Ina raga miki nefa saboda wani dalili wanda nabarwa kaina sani amma wallahi idan kikayi wasa...."
"Kadaina raga min din, kayi duk abinda zakayi....."
Tafada cikin jin haushin abinda yayi mata, juyi daya yayi ya canja musu position ita takoma jikin bango,
"Karki damu kiyi tayi min rashin kunya akwai ranar fanshewa, duk ranar da natashi hukuntaki kisa aranki ranar sai kinyi kuka da idanuwanki...."
"Dan Allah idan katashi yin hukuncin ka kasheni har lahira...."
Murmushin mugunta yayi wanda itama dakanta saida ta fahimci hakan domin da alama bai kai har zuci ba duba da yadda ya cure baki,
"Bazan kasheki ba amma zaki wahala over..... Sai kin gane ke karamar yarinyace ranar..."
"Kaine karamin yaro bani ba....."
Wata matsa yasake yimata hakan yasata kokarin tureshi tana ta huci saboda bacin rai,
Saida yabari tayi nisa wurin kokarin tureshi ta gama sakar jiki ya murde hijabin ya yar, nan sabon fada yatashi domin da iya karfinta take kokarin dauko hijabin daga kasa shikuma yasa kafa ya take, durkushewa tayi awurin tahada kai da gwiwa bayan tasaka kukan zuci,
"Matsoraciya kawai..... " yafada yana murmushi, daga haka yafice yabarta sai faman kuka take kukan bakin cikin rainatan da fahad yayi domin yanzu tagane yagama rainata tsaf sam baya ganin girmanta gashi duk maganar da tazo bakinshi sai yafada mata sai kace wata mate dinshi,
"Ni Bilkisu naga takaina.... Wannan wacce irin rayuwa ce..."
Haka taketa fada cikin kuka har tsawon wani lokaci, saida tagama kukanta ta share sannan tashiga wanka tafito duk sai faman kumbure kumbure takeyi ita kadai ahaka su ammah suka dawo suka sameta duk bata da cikakkiyar walwala sai cika take tana batsewa ita dai ammah idone nata batace uffan ba.
Washe gari awurin aiki khulsum tabi ta dameta akan takira fahad ta tambayeshi idan yabarta sai su wuce duba Christy basai sun koma gidaba saboda idan suka bari aka sallameta har tadawo aiki ba karamar kunya zasu jiba, agaba khulsum tasata da naci dole ta tashi tafita waje itafa bama ta da no dinshi dan rainin hankali, maama takira tana dagawa tace,
"Maama kinada number din wannan dan rainin wayon ko?"
Dariya maama tayi tana cewa,
"Adda labour amarya...."
"Maama ban son rashin kunya ina tambayarki kina yimin wasa..."
"Wai number waye kike tambaya?"
"Ban saniba ai kin san wanda nake nufi munafuka, kituro min yanzu"
Daga haka ta katse wayar takoma wurin khulsum, babu jimawa taji text yashigo sake tashi tayi tafita har khulsum na tsokanarta tana cewa,
"Ohh su labour yau lobayya ce ta motsa koda yake ai amarya kike..."
Bata kulaba tafice takira number fahad tanata ringing amma ba adaga ba harta katse, sake Kira tayi anan kuma sai aka daga amma ga mamakinta sai taji anyi shiru, ahankali kamar bata so tayi magana,
"Hello... Idan natashi daga aiki zanje dubiya...."
Kafin takarasa taji wata zazzakar murya tayi magana,
"Sorry mai wayar baya nan idan yadawo zan sanar dashi...." Batare da jiran amsar da zata bayarba kawai taji ankashe wayar, wani kululun bakin cikine ya tokare mata kirjinta kawai sai taji tana dana sanin kiran da tayi masa, shine dan walakanci zai barwa mace wayarsa? To ko wannan din itace wannan yarinyar da suke yin waya da ita? Kai ba ita bace, ita can ai tasan muryarta, ita dai tasan mutane da yawa suna yaba baiwar muryar da Allah yayi mata but gaskiya ta wannan har tafi tata zaki da taushi da kuma sanyi domin kana jin muryarta kasan irin matan nanne da suka yi nutso cikin kogin daula jin dadi da hutu ya ratsa ko ina ajikinsu su akewa kirari da hurul aini na duniya,
Tsaki taketa ja tana kwafa tarasa ina zata saka ranta taji dadi amma fa abisa dukkan alamu ita wannan dinma babbace domin kamar zata girmeta, shiru tayi tana tunani, itafa takanas mutane suke wanko kafa suzo gidan radio ganinta saboda kawai dadin muryarta da sukeji to amma muryar wannan ko ita mace saida tajita har cikin kwakwalwarta, to wacece ita? Meye hadinta da fahad?
Kafin tasake yiwa kanta wata tambayar da batada amsarta khulsum tafito rikeda hand bag dinta,
"Labour yadai?"
"Nothing, na kirashi ne ban sameshi ba shine nake jira ko zai kira..."
"Ok to kafin kugama bari naje nayi voicing din report din can... Ke kinyi nakine?"
Girgiza kai tayi cikin sanyin murya da na jiki gaba daya tace,
"A'a ni koma fassarar banyiba tukunna... Jeki kiyi nakin kawai...."
Daga haka takoma cikin office ta zauna tasoma juyawa kan kujerar da take kai.
FAHAD
Sosai Bilkisu taso rikita masa lissafi yau saboda kusancin da sukayi har yayi yawa jinta ajikinshi tana half naked yasaukar masa da wata irin kasala da sha'awarta mai karfin gaske amma koda yatuna ta auri wani kafin shi ahalin yanzu sai duk yaji bacin rai da bakin ciki sun rufeshi wadanda sune sukayi sanadiyyar gushe sha'awar data taso masa shiyasa ma yabar wurinta babu shiri yanufi gida, dakyar da sauraron karatun kur'ani yasamu yaji daidai. Washe gari dayaje asibiti sunada tarin ayyuka masu wahalar gaske wadanda zasuyi shiyasa dole sai mutum ya nutsu sannan yayi taka tsan tsan wurin fitar da result din, office din Dr murja yashiga yakai wayarshi da laptop domin suna yin good time da ita tana mutukar ji dashi duk cikin daliban da aka turo babu kamarshi awurinta shiyasa sauran students din ke zargin wai sonshi takeyi gashi ahaife ma zata girmi Bilkisu matarshi, system dinshi yasaka a charge ita kuma wayar yabata ajiya yafita shiyasa lokacin da bilkisu takira bata sameshi ba Dr murja ta daga, bai samu kanshi ba sai around 3 duk agajiye yake yashiga office din Dr murja yakarbi wayarshi da laptop domin tafiya gida, har zai tafi yaji tace,
"Soul mate takiraka..."
"Ok tom zan kirata"
"Wacece ita?" Tafada bayan tazuba masa gaba daya idanuwanta wadanda take juyasu cikin salo na daukar hankali shi wallahi kunya ma yakeji idan tana yimasa wannan farin,
"Anty wife dinace fa..."
Yafada yana shafar kai, juya idanuwa tayi ta shagwabe fuska,
"Ashe kanada aure shine ban taba saniba?"
"Wallahi inada aure....."
"To amma tana kula dakai? Zo kafada min mana handsome..."
Dariya yayi cikeda kunya yafice daga cikin office din, tun yana cikin asibitin yake faman kiran wayar Bilkisu amma bata dauka ba kuma tana zaune tana fassara labarai amma taki dauka tana kallon wayar har tayi tagama bata daga ba ita tarasa dalilinta na jin mugun haushinsa yau fiyeda kullum. Wannan dubiyar dai bataje ba sai khulsum ce tatafi ita kuma tawuce gida tana zuwa gida taci abinci tayi sallar la'asar takira Abba ta gaidashi sannan tawuce toilet, wanka tayi tafito tashirya cikin kayan shan iska riga armless zuwa gwiwa da wandonta duk light purple, ta dauko system dinta ta fita zuwa dakin ammah da wayarta ahannu tana zama wayar tasoma ruri sam batayi niyyar dagawa ba saboda tasan ko waye amma sanin ammah na iya yin magana yasata dauka,
"Ke wato shine zanyita kiranki amma dan rainin wayo ki k'i dagawa ko?"
Jin abinda yace yasata tashi sim sim tafita daga dakin amma zuwa nata,
"Ba dake nake magana ba...?" Yafada cikin tsawa,
"Kaga malam ya isheka ni kar kayi min ihu aka, borin kunya kakeyi ba komai ba kuma wallahi sai kafadi wacece matar da ta daga wayarka lokacin da nakira idan bahakaba har kunnensu abba maganar nan dan bazan iya zama da mai kula mata awajeba...."
"An kula matan kiyi duk abinda zakiyi.... Meye naki aciki dan nakula mata? Kabarinmu dayane dake? Ban son shisshigi..."
"Wallahi duk wadannan maganganun akunnen abba, mayaudari kawai...."
Daga haka takashe wayar gaba daya komawar da batayi dakin amma ba kenan, tun daga ranar rigima takice taki cinyewa har tsawon makonni biyu suka dauka suna wannan fadan ta waya domin bai samu zuwa gidan ba ita ta damu akan lallai sai yafada mata alakarsu da matar da ta daga wayarta lokacin data kirashi acewarta tana gudun sake facing irin abinda hamood yayi mata yadauko karuwa ya ajiye mata azuwan matarshi ce ita tunaninta kenan amma sam bata taba zargin kanta da yin kishinsa ba, shikuma hakan da take ta fada ne yake bata masa rai shiyasa yau yashirya zuwa gidan domin ayita takare.
Sai bayan da yayi sallar magrib sannan yaje gidan, kamar koda yaushe iya amma yasamu falonta tana kallo kasancewar mai aikinta tatafi, tashi yayi yafita cikeda kunya zuwa dakin Bilkisu wacce ke zaune kan abin salla, yi tayi kamar bata ganshi ba taci gaba da tasbihinta,
Agefen gadonta ya zauna harda kwanciya tana ganinsa bata tanka masa ba text yake turawa shiyasa shima baiyi magana ba bayan mintuna biyu da tafiyar text din saiga kiran husnah dama ita yaturawa yana yimata barka da shan ruwa kasancewar yau alhamis,
"Husnah ta....kinsha ruwa lafiya..."
Kamar acikin mafarki Bilkisu taji tace,
"Ya fahad bayan azumin karyewa yayi bayan sallar la'asar saida nagama shan wahalat...."
Bai karasa jiba yaji bilkisu taja tsaki da karfi tamike tana nannade prayer rug dinta,
"Malam idan kagama karufe min kofar bayan kafita", ganin dagaske fitar zatayi tabar masa dakin yasashi ajiye wayar yamike dasauri yasha gabanta,
"Wai me kike nufine? Karfi da yaji nema kikeyi ki goga min kashin kaji ko bakin fenti...."
"Allah ko?"
Matsarta yayi yana kallonta fuskarta gaba daya babu annuri,
"Wai ke mai kike nufi? Dan kawai kinji mace ta dauki wayata? Waima ina ruwanki ne, budurwata ce wadda zan aura sunanta Dr murja medical Dr ce a asibitinmu she's 35 years old, ita kuma wannan husnah ce itama budurwata ce nurse ce yanzu haka tana yin bsc nursing dinta a BUK she's 22 years old nanda yan watanni zan aureta,sai me kuma kike son ji....?"
Ita kanta a lokacin nan tasan bata cikin nutsuwarta bata san dalili ba, cikin fushi da bacin rai tace,
"To kasan kana da duk wadannan meye naka na damuwa da lallai saika aureni? Ai da sai kaje kazauna dasu..."
Murmushin rainin hankali yayi mata yana jan dan gemunshi na rashin kunya,
"Waye yadamu saiya aureki? Ni? Lallai... .."
Afirgice ta kalleshi cikeda mamaki, idanuwansu ne suka sarke da juna cikin fada tace,
"To ai ba adole.... Kana iya sawwake min kowa sai yahuta tunda bakaine ka damu da aurenba"
"Hmmm Bilkisu kenan....!"
Haushine da mamaki suka sake kamata har ta daga kai ta kalleshi akaro na biyu, har lokacin yana wasa da gemunsa,
"Da kike cewa in sawwake miki da nine na aureki? Ai bani na aureki ba ina zaman zamana aka ce an aura min ke, tunda bakida ra'ayi kamar yadda nima banida interest akai kina iya zuwa kisamu wadanda suka daura kisasu su warwareshi....." Yakarasa maganar yana daga kafada,
"Ni kake fadawa haka?"
"Yes ai gaskiya nafada miki ni ban nemi aurenki ba sadaka aka aura min saboda ance wannan tsohon dan duniyar yaudararki yayi daga karshe ya sakeki..."
Kwallace taciko mata ido takai hannu zata dakeshi yarike yana yimata murmushi mai kona zuciya,
"Fahad sakeni... Ka sakeni.....ko ana aure dole ne?"
"Oho ni nasani ne? Nima ai dolen aka yimin tunda inada wadanda nakeso aka tashi aka bani matar sadaka"
Wannan Kalmar ba karamin kona mata rai tayiba dan har saida tanemi sliver abakinta tarasa saboda dimuwa wai ita yakirada matar sadaka, shikuwa gegewa yayi ta gefenta yadauki wayarshi yafice nan ta durkushe tasoma kuka, tunda tazo duniya bata taba jin bacin rai irin nayau ba, tamkar zata mutu haka takeji, kwana tayi tana kuka wannan dalilinne yasa dasafe ta tashi da matsanancin zazzabi da ciwon kai sai kakkarwar sanyi take yi ga wani irin lafiyayyen ciwon kai asibiti ammah tasata agaba suka tafi suna zuwa akace jininta ne yayi kasa bama hawaba kasa yayi nan aka bata gado sai rawar jiki takeyi idabuwanta faful da hawaye duk sun kumbura.....
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:21] Hafsat Rano: JIYA IYAU...
*Wannan littafin na kudine me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
43***Tafi mintuna goma cikin bathroom din bata ko motsa ba kawai hawayen bakin ciki da takaicine ke fita daga idanuwanta ba abinda yafi tsaya mata arai irin iko da isar da yake neman fara nuna mata, danme zai sakata agaba yana yi mata tsawa? Bude kofar bathroom din tayi tafito ko zama bata yiba ta nufi falon ammah wacce ke zaune suna gaisawa da Abba amma kafin Bilkisu takarasa har sunyi sallama kasancewar su lokacin salla yayi acan,
Zama tayi idanuwanta duk sun sauya cikin bacin rai tafara magana,
"Ammah gaskiya yakamata kijawa fahad kunne..... Naga abin nasa yana nema yayi yawa, ni bana son nuna isa da gadara...."
"Wani abu yayi miki?" Ammah ta bukata bayan ta zuba mata ido tana sauraronta,
"Ammah waifa har nagama shiryawa zamu fita nida khulsum dubiyar abokiyar aikinmu shine zai wani ce wai baza niba...."
Murmushi ammah tayi kafin tace,
"To ni mai gado menene nawa? Shine dama yakeda ikon yabarki ko ya hanaki kuma tunda ya hana ba shikenan ba?"
Wasu zafafan hawaye taji sun zubo mata sakamakon abinda taji ammah tafada, wato shikenan haka za abarshi azuba masa ido yayita yin abinda ya gadama?
"Amma ammah haka za abarshi....?"
"Mai gado to me kikeso nayi akai? Shine yakeda iko dake bani ba... Akan ya hanaki fita unguwar shine zaki zauna kina kuka? Allah ya kyauta to"
Tashi ammah tayi tafita zuwa kitchen domin ganin wacce wainar Rabi mai aikinta take toyawa ganin haka yasa Bilkisu tashi tafita zuwa dakinta. Tana shiga taji wani abu yatsaya mata arai musamman da ta shaki kamshin turarenshi wanda yatafi yabar mata adakin, karar wayarta ne ya katse mata tunani nan ta daga cikin sanyin murya,
"Haba labour irin wannan jira haka? Kin barni tsaye fiyeda 30 minutes.... Nidai tuni nakoma cikin gida gashi inata kiranki baki daga ba hope u are doing good?"
Ajiyar zuciya Bilkisu tasauke cikin sanyin murya mai kunshe da zafin rai tace,
"Am very sorry kawata,kin san me? Hanani zuwa yayi dan rainin wayon nan har saida yabari nagama shiryawa ina kokarin fitowa yace bazan jeba...."
"Wai wa kike magana ne?" Khulsum ta bukata,
"Fahad fa...."
Dariya khulsum tayi sannan cikin kara tace,
"What? Wowwww.....fahad again? Wonderful... Tofah, kice love kuka zauna yi shiyasa nayita kira kika ki dagawa..."
Cikin fushi Bilkisu tace,
"Malama bana son wulakanci... Abinda yafi love a'a kin manta sex...."
Dariya khulsum tayi cikin tsokana tace,
"Ai shi dinma bazance a'a ba may be kunyi tunda mata da mijinta ai komai na iya faruwa...."
"God forbid...." Daga haka takatse wayar cike da takaicin khulsum, yanzu tasan ba khulsum kadai ba kusan kowa haka zai rinka kallonta fanko ana yimata kallon tayi tarayya da kanin kaninta, kwanciya tayi cikeda bacin rai sai kuma wayar da yakeyi yi tafado mata,
"To wai aure yayi ko kuma budurwarsa ce?" Shine tambayar da tayiwa kanta bata samu amsarta ba tasoma kukan bakin cikin da ya kunsa mata, saida tasha kukanta ta more sannan taji zuciyarta tayi sanyi kadan kawai sai taji bata son sake ganin koda mai kamarsa ne, gaba daya wani irin haushinsa takeji, da haushinsa ta kwana ranar washe gari kuwa bayan tadawo daga aiki harda kulle kofarta gudun kar yashigo mata kamar jiya amma kuma sai taji shiru baima zo ba.
FAHAD
Tunda yabar gidansu Bilkisu yake jin nishadi atare da shi bawai bata mata ran da yayine yafi burgeshi ba a'a yadda yafara sata tayi laushi tun ba aje ko inaba shi yafi bashi dariya, sannan bawai yahanata fita bane dan ya kuntata mata sai dai kawai yana son ya nuna mata tsakaninsu shine jagora kuma shine shugaba koda kuwa shekarunta sun ninka nashi sau dari, dole awannan zaman nasu sai ya gyara mata zama kuma ya nuna mata karfin power din da yake da ita.
Da niyyarshi yaje gidansu husnah amma sam taki yarda yasan kunyarshi takeji sakamakon abinda yafaru tsakaninsu rannan shima kansa kunyar yakeji but babu yanda ya iya saboda mai faruwa ta rigada tafaru. Daren ranar yana kwance kan katifarsu ya tasa kanshi da pillow yadora laptop dinshi kan cikinshi yana kallon wani Nigerian film kawai sai yaga film din yayi kama da irin rayuwarsu shida Bilkisu saboda shima guy din cikin film din matar ta girmeshi amma yadda take tarairayarshi abin gwanin burgewa, lumshe ido yayi yana tunanin to ko sai yaushe shi zai samu irin wannan tarairayar wurin hajjajun tashi, murmushi yayi kafin yace,
"Mai gado rigima..."
"Kai kuma kaida waye kake magana?" Abba yace dashi wanda shigowarshi kenan cikin dakin,
"Ya Abba kallo nake yi, kasan wani lokacin idan mutum yana kallo ko yana karanta novel kamar me aljanu yake zama saboda zakaji yana magana shi kadai...."
"Gaskiya kam... Allah yabada sa'a"
Har yagama kallon baibar tuna bilkisu ba hakama lokacin da yazo yin bacci murmushi yarinka yi shi daya. Washe gari bai samu zuwa gidansu ba saboda sunsha aiki sosai a lab shi kansa bai samu tasowa ba sai 6 shiyasa kawai yayi zamansa agida yahuta dan ko salim basu haduba ranar,yana so yakira Bilkisu amma bayason tasamu dama dayawa akanshi shiyasa ya shareta yakira husnah suka raba dare suna hira, washe gari kam da wuri yadawo gida domin lokacin da yadawo ma 3 batayiba, shago yawuce bayan yayi wanka domin akwai wasu dinkuna da aka aiko masa daga abuja tun shekaran jiya wata yar makarantarsu shiyasa can yaje yafara yankawa saboda cikin week dinnan takeso, karfe biyar daidai yabar dinkunan yafita yauma yana son yaje yaga dramar da zasuyi shida mutuniyar tasa, duk da kananun kayane ajikinsa haka yatafi gidan surukai, yana zuwa su ammah na fita itada driver da Rabi mai aikinta shi da yazaci ma Bilkisu ce sai yaga ba ita bace,
Dama yana jin kunyar zuwa ahaka ammah taganshi da kananun kaya maroon din riga mai rubutun yes ajiki har sau uku sai bakin wando da p cap, koda wasa Bilkisu bata zaci zaizo ba da bazatayi saken barin kofarta bude ba, yauma baccin takeyi kamar mai shan wani abu domin sun daura itada baccin yamma yanzu tunda ba nadare takeyi sosaiba zama yayi gefen gadon dan mugunta maimakon ya kyaleta amma sai yafara neman hanyar da zai tadata. Tv yakalla da alama da kallo takeyi before baccin ya dauketa volume yakara Wanda tajishi har tsakar kanta babu shiri ta bude idanuwa tana laluben remote,
Ganinshi zaune yasata hade rai sosai kamar yadda shima yayi,
Hijabi ta yayima ta saka tana harare harare, baki yatabe cikin ranshi yace,
"Nadai gani..."
Daga shi har ita babu wadda yayi magana suna zaune shiru shidai hankalinsa nakan tv ita kuma ta dauke kai gefe daya cikeda jin haushinsa,diff nepa suka dauke wuta zamansa yagyara akan gadon sosai ya jingina bayan yadauki kafafuwansa gaba daya ya azasu bisa gadon, wayarshi yaciro yakira mukhtar saboda dazu lokacin da yafito daga shago yaga miss called dinshi yasan lokacin da yabar wayar a charge ne yakirashi,
"Ango howfar?" Mukhtar yafada yana dariya, dariya shima fahad yayi sannan yace,
"Kajika wannan ai tsohon zance ne abinda ba yau aka daura auren ba bakuma jiyaba..."
Bilkisu na jin yafadi haka tamike daga kan gadon ta sauka saboda tasan duk yadda akayi maganarta akeyi matsalar auren yaro kenan komai zai iya kwashewa wanda yashafi sirrinsa da iyalinsa yafadawa friends dinshi ta ayyana hakan cikin ranta, bathroom tashiga babu jimawa tafito fuskarta jike da ruwa alamun wanketa tayi lokacin yagama wayar yana dai cigaba da latse latse awayar,
"Karka kara shigo min daki ahaka, sannan karka kuma gigin tashina idan ina yin bacci...." Tafada cikin muryar dake nuna fushi karara bai tanka mata ba taji yana kiran waya domin a speaker yasaka, laptop dinta ta dauka ta matsa can kan prayer rug dinta ta zauna,
"Yanmatanah ya azumin?" Taji yafada cikin karya harshe,
"Babu wahala ya fahad... Ankusa ansha ruwa ma ai"
"To me zan kawo miki?"
"Kanka...." Tafada muryarta ahankali,
"Ko baki fada ba ai dama ni nakine ke kadai...."
"A'a ya fahad badai ni kadai ba bayan kayi min kishiya da tsohuwar matarka bayan kuma...." Saurin cire wayar daga hands free yayi sakamakon jin husnah na neman yimishi baran barama, duk abinda yakeyi Bilkisu najinsu shiyasa bata san lokacin da ta mike afusace ba taje gabansa ta tsaya tana huci,
"Tashi kafice min daga daki....I said get out from my room...." Katse wayar yayi sannan ya kalleta fuskarshi atamke,
"Daina yimin tsawa aka.... Ban son hayaniya"
"Anyi din... Katashi kafitar min adaki kuma karka sake dawowa..."