Kamar da wasa complete novel - Chapter 25
Kamar da wasa complete novel Chapter 25: Kamar da wasa complete novel Chapter 25. Yi yayi kamar baijita ba, hakan yasake kular da ita,
3,369 words
Yi yayi kamar baijita ba, hakan yasake kular da ita,
"Fahad katashi kabar cikin dakin nan nace..., akanme zakazo kana kawo min nonsense anan...."
Tun kafin takarasa yatashi yahadata da bango ya matse,
"Wa kike yiwa shouting aka? Ni sa'anki ne?"
Wata uwar harara ta dalla masa kafin ta tureshi tana cewa,
"Kai waye da baza ayi maka shouting akai ba? Ubana ne kai? Zaka wani zo min har cikin daki ina baccina katada ni sannan kazauna kana damuna, bazanyi tolerating wannan ba...."
Tsayawa yayi yana kallonta har saida tagama sannan yace,
"Ki gama fadin duk abinda ke ranki amma idan kika bari na kamaki ko...."
"Idan katashi dukana bayan ka kamanin ka dakeni da ice ko da dorina mai baki dubu..."
"Ni ai ba mahaukaci bane ko jahili da zan zauna ina dukan mata... Koda yake su wasu shashashan matan ai sunfi son mijin da zai dakesu...."
Haushin da ya rufeta yafi na dazu shiyasa tasake tunzura ta hayayyako masa cikin zafin rai da kunar zuciya tace,
"Ai maganar ciki ba magana bace idan har ba tsoro akejiba afito fili afada amma bawai ayita magana atukunkune ba... Idan anso masu dukan ai sun cancanta asosu dinne..."
Baki yatabe sannan yace,
"To ai dadin abin dai su babu wata soyayya da za anuna musu sai ta duka, akamasu a lakada musu duka idan dare yayi kuma arabesu amma da rana babu marabarsu da jakuna while wasu matan suna can ana riritasu ba ason ko kuda yasauka akansu...."
"Kafita min adaki nagaji da wannan hayaniyar taka..."
"Baza afita dinba..."
"Saboda kai...."
Bata karasa ba taji ya shako ta, idanuwansa cikin nata yake kusanta fuskarshi kan tata tayadda kusancin nasu har yai yawa, lumshe idanuwa tayi tana jiran jin bakinsa kan nata dan taga kamar hakance manufarshi amma sai taji sabanin haka dal taji ya dalle mata baki yana cewa,
"Wannan bakin naki na rashin kunya nakusa nayi maganinsa....sai na kasheshi murus tayadda bazai kara fada min bakar magana ba...." Ita kanta saida taji tsikar jikinta tana tashi saboda yadda yayi maganar, su da suke fada amma voice dinshi tayi sanyi takoma cool sosai sannan tasauya tana fita a rarrabe sabanin dazu kodan kusancin dake tsakaninsu ne oho,kasa bude idanuwanta tayi sai dai tana ta kokarin kwace kanta daga rikon da yayi mata saboda hatta bugun da zuciyarshi keyi tana jinshi kamar yadda shima yake jin nata kasancewar manne suke da chest din juna wani karin takaicin ma shine babu fa komai ajikinta sai iya yar doguwar rigar da ta zira sai hijabi....
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:21] Hafsat Rano: *me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
45***Taimakon gaggawa aka fara neman bata domin inbanda kadawa babu abinda jikinta keyi kamar wacce ke tsakiyar kankara, bayan kamar wasu mintuna wadanda bazasu gaza 30 ba nurses din suka zo wurin ammah suna yimata bayanin yakamata fa suje su samo jini saboda su basuda shi anan, duk da ammah bataso ta sanarwa su Hindu to amma babu yadda za a yi dole sai sun sani, wannan gayawa wannan da haka duk zancen ya yadu a junansu babu bata lokaci duk suka yiwa asibitin tsinke,text maama ta turawa fahad amma kasancewar yana cikin lab yana aiki bai ganiba.
Tun abinda yafaru jiya tsakaninsa da Bilkisu da zarar yatuna sai yayi murmushi ita daukar kanta takeyi watta babba bayan shikuma awurinshi mararbarta da jaririya kadanne gaba daya yagama rainata sanine bata gama yiba, dayake yau juma'a manyan kaya yasaka saboda ta can zai wuce masallaci, duk da cewar karshen makone hakan bai hanasu samun ayyuka da yawa ba shiyasa bashi yasamu kansa ba saida lokacin sallar juma'a yayi. Har saida yafito daga salla sannan yaga text din maama tana sanar dashi Bilkisu babu lafiya sannan ana bukatar jini, harda kwatanccen asibitin da take kwance, batare da yakoma asibiti ba yawuce inda maama tafada masa an kwantar da Bilkisu, wani dan karamin asibitin kudine dake nan unguwar tasu sai dai da dan tazara tsakaninsu da gidansu, a reception yaga meenah wacce taje kiran wata nurse wadda zata auna jinin mijinta aga ko zaiyi daidai da na Bilkisu,
"Ya fahad sannu da zuwa..."
"Yawwa meenah, ya mai jikin?"
"Dasauki tana ciki muje"
Tare suka karasa wurinsu ammah wadanda ke tsaye akofar dakin da Bilkisu take harda mijin meenah ganin fahad yasa amma gyara lullubinta suna gaisawa kuma tawuce tabar wurin, shi dinma hakan yafi sakewa shiyasa yasamu damar cemusu abar jinin mijin meenah shi sai adebi nasa dan baya ko tantama nashi zaiyi mata saboda shi jininsa irin wanda zai iya bawa kowa ne, tare suka tafi lab da nurse akayi komai da yakamata aka debi jininsa leda daya da rabi bai samu tashi ba awannan lokacin ya dan kwanta sai bayan kamar mintuna ishirin sannan yatashi yana dai dan jin jikinsa babu karfi but babu wani jiri ko hajijiya, wurinsu Hindu yakoma dama sunata zuwa suna lekashi suna komawa, suna zaune su uku daga Hindu sai maama sai meenah ammah tatafi gida da yan jikokinta haka shima mijin meenah yatafi, sannu suke tayi masa yana amsawa shi idanma banda yar yunwar da yakeji ai da zai dan jima a asibitin,
"Tafarka ne?" Ya tambaya yana kallon kofar dakin da Bilkisu ke ciki,
"Ehh amma yanzun dai gaskiya bacci takeyi...amma ai zaka iya shiga"
Juyawa yayi yashiga, tana kwance tayi fayau da ita ana kara mata jinin wanda har guda dayan yakusa karewa, jingina yayi ajikin bango ya harde hannuwanshi akirjinshi yana kallonta, hijabi ne ajikinta saboda sanyi sai doguwar riga ta atamfa, fuskarta ya kalla yaga ta wani bata fuska kamar irin idonta biyun nan ba bacci takeyiba, murmushi yasaki mai kayatarwa sannan ahankali yafurta,
"Hajjaju ana fada da jinina kenan......"
Ahankali yakarasa gaban gadon duk fuskarta akode amma idanuwanta luhu luhu akumbure ga bakinta ya bushe sosai irin yadda yake yi dinnan idan mutum yana cikin halin jinya,
"Am very sorry soul mate... Nasaki kuka ko? Am sorry kiyafe min...."
Kamar tana jinsa yaga tasake bata rai harda dan turo baki,
"Are we fighting?" Yafada yana murmushi, bakin da ta dan turo yakai nashi kai ya tsotsa sannan yadago yana murmushi,
"Ai nace miki am sorry.... Stop fighting with my blood Mana baby.... I said am very sorry about what i did... Pls forgive me kinji.... Ki yafewa dan kaninki...!"
Goshinta yayiwa light kiss sannan yasake yiwa lips dinta wadanda ada suke abushe amma tun lokacin da ya tsotsesu suka dawo kamar anshafa musu lipstick, sakin hannunta yayi wanda da yakama yana murzawa cikin nashi saboda tsabar taushinsa,
"Tunda kin ki hakura am going, anjima zan dawo kinji...."
A kumatu yasake bata wani kiss din sannan yatashi yana kallonta murmushi yasake yi saboda yadda taketa hade rai tana motsa baki kamar mai yin fada alhali kuma bacci ma takeyi yasan abinda ke zuciyarta ne taketa amayoshi lokacin baccinta. Da baya da baya yake tafiya yana murmushi har lokacin idanuwanshi na kan fuskarta, saida yazo daf da bakin kofa sannan yayiwa tafin hannunshi kiss ya hura mata, ganin yana kokarin juyowa yasa su maama dake leke ta glass din kofa saurin guduwa kowaccensu kunshe da bakinta dan kar yaji, bude kofar yayi yafita yana kallon su maama wadanda ke tsaye cirko cirko kamar marassa gaskiya,
"Maman hudah lafiya dai ko?"
"Lafiya lau ya fahad, mun dan fita ne dawowarmu kenan..."
Dan bata fuska yayi sannan yace,
"Ku da kuke da patient ina kuma zakuje dan Allah?"
"Ahhh ya fahad bafa nisa mukayi ba..." Inji Hindu,
"Nidai dan Allah ga amanata nan zanje gida idan huta anjima zan dawo, pls and pls ku kular min da ita... Idan tana bukatar wani abu akirani.. " yakarashe maganar yana kallon maama wacce ke dariya,
"Insha Allah zamu kula da ita kamar kana wurin..." Inji meenah,
"Yawaa nagode, bari naje..."
Juyawa yayi yatafi suna sake yimasa sannu, shi sai yanzu yafara jin dan ciwon kai kadan kadan da dan jiri jiri yasan bawai dan andebi jinin bane may be saboda ciwon dake tare dashi ne, tunda yabar wurin su meenah ke gulmar abinda suka gani,
"Ya fahad dinnan kamar wani salihi ashe shima number 1 ne..." Hindu tafada tana dariya,
"Ai kibari kawai adda labour fa tahuta amma takasa ganewa.." Mamaa tabata amsa,
"Gentle dashi wallahi..." Inji meenah, hirar dai suka bata lokaci sunayi kasan idan kaga mai son wanda ya shafeka kaima sonshi kakeyi watakila dalilin kenan da yasa suke kaunar fahad.
Daurewa yayi yakai kanshi gida duk da jirin da yakeji, yana shiga yawuce ciki baiko kalli dakinsu ba dake soro,
Falon ayiyah yashiga yawuceta zaune gaban murhu tana karasa daka kuli kulin da zata yiwa baba kwadon zogale wanda idan yadawo daga masallaci zai ci, ita kuma mamuh tafita zuwa gidansu salim,
Anan tsakar falon ya kwanta yayi pillow da damtsen hannunshi, ahaka yaji motsin shigowarsu mariya daga makaranta,
"Sai yanzu kuke dawowa daga makaranta ko? Kun tsaya wasa ahanya ko?"
"Allah ya fahad sai yanzu muka samu napep..." Maryam tafada tana cire sandal din dake kafarta,
"Bari natashi nakamaku zama ku fadi gaskiya..."
Sun fara rantse rantse kenan ayiyah tashigo dauke da kwanukan zogalen da ta dafa,
"Kai da naga kamarma bakada lafiya amma shine zakazo kafada yara da fada ko fahad?"
Murmushi yayi sannan yatashi zaune,
"Ayiyah lafiyata kalau fa kawai dai jinina aka dan diba..."
"Jini? Meya faru?" Ayiyah tafada tana mikewa tsaye daga durkushen da tayi tana ajiye kwanuka,
"Babu komaifa... Bata da lafiya ne wai kuma ana bukatar jini shine aka debi nawa"
Yana fadar haka ayiyah tagane Bilkisu yake nufi,
"To Allah ya sawwake yabata lafiya.... A asibiti take kenan?"
"Ehhhh, ayiyah taimaka kibani zogalen nima inci..."
"Allah ya sawwake, gashi ai dama babanku na dafawa..."
Hado mishi tayi cikin plate harda su tumatur da sauran kayan lambu, zama yayi sosai yaci sannan yakoma ya kwanta babu jimawa bacci yayi gaba dashi bai farkaba sai daf da la'asar, yafito tsakar gida domin yin alwala,zama yayi yasa maryam takawo masa ruwan alwala, yana yin alwalar mamuh tazo tana tambayarsa awanne asibitin su Bilkisu suke domin suna son suje dubata yanzu fada mata yayi yakoma falon ayiyah, yana salla yaji tafiyarsu suna yimasa sallama shi kadai aka bari agidan domin harda su maryama aka tafi. Bayan ya idar da salla yasake kwanciya sai lokacin yamika hannu yadauko wayarshi yana dubawa text din husnah na barka da friday yagani sai kuma miss called dinta da nasu bashir, daya bayan daya yarinka bin miss called din yana kira bayan yagama yatashi ya yafita kofar gida yazauna yana jiran dawowarsu ayiyah.
Yafi mintuna talatin zaune awurin sannan suka dawo, maryam na rikeda babban warmer mai kyau,
"Maryam me kika samomin?" Yafada yana kokarin tashi tsaye,
"Surukarka ce tabayar akawo maka wai kaci ka maida jinin jikinka...."
Jin abinda mamuh tafada yasashi yin dariya saboda yazaci wasan da tasaba yimasa yauma tayi, binsu yayi suka shiga cikin gida,ga mamakinsa kuwa sai yaga ashe dagaske ne domin agabansa maryam ta ajiye warmer din tana cewa,
"Ya fahad wai gashi..."
Budewa yayi nan kamshi ya bugeshi mai dadi, farfesun hanta ne cikin warmer din yaji kayan kamshi sai kamshi ne ketashi,
Kallonsu mamuh yayi sannan yakalli maryam yace,
"To kuma ni zaki kawowa ki ajiyewa? Mika musu..."
Dauka tayi takai gabansu mamuh ta ajiye, cikin plate mamuh ta zuba masa ta mika masa,
"Wallahi mamuh wannan yayi yawa... Rage"
"Ba ragewar da za ayi, kaida kabada jini har leda daya da rabi ai dole kaci abubuwan da zasu kara maka jini dannan...."
"Mamuh dazufa da bakya nan wallahi naci zogale dayawa..."
"Saifa ka cinye fahad, dauki maza ina kallonka..."
Dauka yayi yafara ci ita kuma taci gaba da raba nasu, yana ci yana hadawa da ruwa har ya cinye saboda ita hanta akwai cikawa mutum ciki shiyasa yajishi yakoshi over, tashi yayi yafita bayan ya gama yakoma dakinsu, salim yaturawa text yana sanar dashi anjima zai rakashi su dubo Bilkisu, wanka yashiga domin yanzu ya danji karfin jikinsa.
Bayan sallar magrib suka tafi asibitin su uku saboda harda ya abba,dukkaninsu sunsha dogayen kaya, babu kowa adakin sai iya Bilkisu da meenah suna zaune kan gadon Bilkisu na shan tea har lokacin tana sanye da hijabinta, jin sallamarsu yasata sake kasa da kanta bata ko dagoba saboda bata son ganin sun hada ido da fahad saboda tasan yanzu bata da wata martaba a idonsa tunda ashe sadaka aka aura masa ita tasan ba kowane yakitsa wannan abunba sai iyallo saboda dama itace ke cewa zata aurar da ita sadaka, yanzu gashi anja mata reni da wulakanci a idon yaro,
Tana ji su Abba na tambayar yamai jiki suna yimata sannu dakyar ta iya amsawa sakamakon kukan da ke kokarin taho mata, lokacin da taji meenah na gaisawa itada fahad sai taji kamar da biyu yake yin gaisuwar nan ta shareshi bata ko dago ba daga karshe su Abba suka fita suna yimata fatan samun sauki haka itama meenah sai ta tashi tafita yarage su biyu kadai cikin dakin,
"Sannu... Yajikin? Ke daga fada miki gaskiya shine zaki kwanta ciwo...?"
Jin abinda yace yasata dagowa ta zuba masa harara saboda ta tsani ke dinnan kafin ta dauke idonta yarama,
"Ni ai ka kira da matar sadaka ko?"
"To da matar meye? Sadaka aka bani kuma nakarba..."
"Wallahi karya kake yi..."
Nuna kanshi yayi da yatsa,
"Ni kike cewa ina yimiki karya?"
"Ehh din...."
Kafin yayi magana meenah tashigo rikeda waya nan ta mikawa Bilkisu tana cemata,
"Adda labour gashi su elmustapha ne..."
Karba tayi suka fara gaisawa dasu elameen suna yimata ya jiki, bata saurari fahad ba wanda ahankali yace,
"Yarinya kuma sai kin biyani jinina da na baki dan ba kyauta nabayar ba..."
Shima bai sake bi ta kanta ba yayi waje abinshi yabarta da kunar zuciya domin maganganunshi sosai yanzu suke bata mata rai,wayar nan kawai tanayi ne bawai dan tana fuskantar abinda take cewa ba......
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:21] Hafsat Rano: *Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
46****Daren ranar ma haka ta kwana batayi bacciba saboda tsabar bacin rai da damuwa da zarar ta tuno maganganun da ya yayyaba mata sai taji kwalla ta ciko idonta. Washe gari dasafe aka sallameta suka koma gida, suna zuwa tasamu tashiga wanka tafito domin shiryawa kamar tasaka hannu aka tayi ihu haka takeji idan har tatuno da maganganun fahad, ahaka ta daure tashirya tana cikeda damuwa tana gamawa Hindu takawo mata abin karyawa nan ta zauna tasoma dan kurbar ruwan zafi bawai dan tanaso ba amma sauran kayan karyawar ko tabasu batayi ba ahaka Hindu tadawo ta sameta tana rikeda sultan a hannunta,
"Adda mai gado yabaki ci abincin ba? Saifa kin dan daure..."
Jin abinda Hindu tace yasata dagowa ta kalleta da kodaddun idanuwanta wadanda ko kwalli babu,
"Hindu banida apatite abakina wallahi, sam bana jin dadin komai..."
"Duk da haka ki dan daure mana, sannan dan Allah ki gyara fuskarki kisaka koda powder ne da kwalli... Amma ya fahad yazo yaganki ahakan nan ai akwai matsala..."
Harara ta watsawa hindu sannan tamaida kallonta kan sultan wanda ke miko mata hannu yana yimata gwaranci, mika hannu tayi zata karbeshi amma Hindu taki sakinshi tana cewa,
"Kai bari kar kaje ka karasa mana addarmu kaga dazun nan tadawo daga gadon asibiti..."
Murmushi Bilkisu tayi ta karbeshi sakamakon kukan da yafara yi, ita kuma haka Allah ya dorawa yaran kannenta kaunarta duk sun shaku dasu babu wanda yake yimata kiywa,
"Dan Allah adda labour ki daure kici abincin nan kar yayi sanyi sannan ki gyara fuskarki saboda tsaro..."
"Ke hindu idanma fa akan fahad kiketa wannan damun nawa bazan yiba..."
"A'a wallahi Adda labour ni basaboda shi bane kawai dai ai kinga idan kika saka kwallin fuskarki zatafi fitowa amma yanzu Allah baki ganki ba duk kin canja kin sake fadawa..."
Bata sake yin magana ba ta jawo abincin gabanta ta bude tafara ci tanayi tana bawa sultan, saida tagama tsaf ta zauna gaban mirror tana shafa powder sai tajiyo sallamar khulsum, tana jiyosu sunayi itada hindu atsakar gida hindu nacewa bazasu amshi uzurinta ba tunda bataje asibiti ba saida suka dawo gida. Anan gaban mirrior din khulsum tashigo ta sameta tana zizira kwalli,
"Labour patient har an warke anfara coda ado za atari oga?"
Harararta Bilkisu tayi ta taso daga gaban mirror din tadawo gefen gado kusa da khulsum,
"Zaki fara ko? Allah yakawo ki ai kuma..."
"Ah to ai gaskiya ce anwarke mana me kuma yayi saura banda akoma bakin daga..."
"Sai kiyi kuma..."
"Yawwa wai ke yaushe zaki tare ne? Allah kinga labour ki tare tun kafin abinnan ya bayyana dan wallahi ni harga Allah ban yarda da wannan ciwo ciwon nakiba.... Laulayi kika fara ko?"
"Wai ke meyasa ba a abun arziki dake ne? Ni dan Allah kinga karki bata min rai..."
"To yi hakuri, sorry kinga jiya banzo asibiti na dubaki ba ko? Wallahi khalifa ne nima baida lafiya... Amma yaji sauki yau"
"Babu komai ai da kinyi zamanki ma kin kula dashi"
"Ai yaji sauki yana can tare da babanshi"
"Allah yakara masa lafiya..."
"Amin... Yawwa wai mutuniyar kin kuwa taba gwada hadin nan dana turo miki rannan?"
Dariya Bilkisu tayi saboda ita wallahi ma sai yanzu tatuna da sakon da khulsum din ta turo mata,
"Madam kedai kije kiyi tayi amma ni wallahi bazan yiba..."
Kallonta khulsum tayi cikin jin haushi,
"Allah yashiryeki labour maza dai ki tsaya kallon ruwa kwado yayi miki kafa wallahi idan baki kama mijinki a hannunba... Hmmm zaki ganene"
"Toh Anty..."
Dariya khulsum tayi sannan tayi kasa da murya tace,
"Wai dan Allah laulayinne da gaske?"
"Ban saniba..."
Kafin khulsum tasake magana suka jiyo sallamar fahad atsakar gida amma ahankali kamar wani marar gaskiya, mikewa khulsum tayi tana cewa,
"Bari na kwashi yanmatan kafafuwana inbarku kusha morning show dinku, ga wata gumba idan kinaso sharp sharp ce wallahi...."
"Banaso akai gaba..."
"Kedai kika sani wallahi, ni sai anjima"
Mikewa tayi ta kwanta bayan fitar khulsum tana jiyo lokacin da khulsum din suke gaisawa da fahad atsakar gida mintuna kadan tsakani taji shigowarsa ta hanyar bude kofa da yayi bata ko motsa ba ayadda take bare ta dago ta kalleshi, daga dan nesa yatsaya yana kallonta, riga da skirt na leshi tasaka wanda aka yiwa simple style yayi dass ajikinta, dakin gaba dayanshi sanyayyen kamshine ke tashi cikinsa,
"Yajiki......?" Yafada yana murmushin da bazata ganeba,
"Da sauki" ta amsa kamar bataso domin badan shi din mai jin magana ce komai kankantarta ba da bazai jiba,
"Dama nazo dubaki ne, hope kinji dadin jinina dake jikinki?"
Juyowa tayi afusace ta harareshi,
"Dadinta ma dai banice nanemi da kabani jinin ba, badanma lokacin da aka saka min bana cikin hayyacina ba da me zanyi da jininka.... Wa yasani ma ko guntun sikila ne..."
Murmushi yayi yana kallonta yasan dai maganar dayace wannan matar sadakar da yakirata dashi ne yaketa sosa mata zuciya har take neman hanyar mayar masa da martani,
"Kiyi hakuri bani na kar zomon ba rataya aka bani, kuma ratayar ma ban karba ba......"
"Idanma ka karba idanma baka karba ba ruwanka, sannan da kake cewa sadaka aka aura maka ni ai yanzu ma kanada damar da zakace kafasa... Tunda ba adole"
"Akan me zance nafasa? Ai narigada na karba"
"Duk da ka karba ai kasan hanya mafi sauki wacce tadace da zakabi ka mayar da sadakar...."
Tabe baki yayi yasamu kan bedside drewar yazauna yadora kafa daya akan daya,
"Ni yanzu ba wannan ne yakawo ni ba inada abin yi dubiyace ta kawo ni..."
Wani kallo tayi masa yana sanye da kananan kaya amma yadora lab coat asama kafarshi rufe cikin bakar safa, takula akwai shi da saka safa akafa sai kace wani marar lafiya,
"Yanda kake da abinyi haka nima nake dashi, nidai kawai ka datse igiyar auren nan kowa ya huta..."
"Ban ganeba.... Wai kina nufin ni fahad na sakeki? Idan hakan kikeso zan yimiki amma abisa sharadi guda daya..."
Mikewa yayi daga kan bedside drewar yaje yatsaya mata aka dukkan hannahensa yasaka su cikin aljihu,
"Kifara sanar dasu Abba irin zaman da mukayi dake dafarko da irin gangancin da kika sakani nayi harna sakeki lokacin da wannan shedanin tsohon dan duniyar yake tsaka da hure miki kunne, sannan sai kisake fada musu abinda ke faruwa ayanzu idan har kikayi haka to wallahi zan yimiki yadda kike so...."