Kamar da wasa complete novel - Chapter 26
Kamar da wasa complete novel Chapter 26: Kamar da wasa complete novel Chapter 26. Sosai kalamansa suka bata haushi ta lura yanzu baida magana saita hamood…
3,372 words
Sosai kalamansa suka bata haushi ta lura yanzu baida magana saita hamood magana daya sai ya jefo hamood aciki, takasa gane tsakanin shi da hamood waye yafi wani tsanar dan uwansa saboda shima hamood din lokacin da tana gidansa baida magana sai ta ya kira fahad da karamin yaron nan marar kunya, shi kuma fahad yanzu magana kadan zaice tsohon dan duniya,tana can duniyar tunani har fahad yawuce yabar mata dakin yayi tafiyarshi kawai sai bude ido tayi taga baya nan,
Tagumi ta rafka tana tunani, ai ko giyar wake takesha bazata taba gigin aikata wannan abun da fahad yafada ba, ai idan ta kuskura abba yaji cewar itace ta kashe aurenta karo nafarko dan ta auri hamood wallahi kashinta yabushe,
"Ai yanzu bakida mafita banda wacce tawuce kiyi hakuri ki zubawa sarautar Allah ido...." Zuciyarta tafada mata, shiru tayi kawai tana tunani, yanzu ita shikenan haka zatayi rayuwarta da yaro karami wanda baya ganin girmanta? Tunfa daga yanzu ya rainata to inaga wani abu ya hadasu ai sunanta sorry kawai, tsaki taja takoma ta kwanta tana istigfari acikin zuciyarta.
Tun daga ranar har takarasa warwarewa takoma aiki fahad bai sake zuwa gidanba ita anata bangaren hakanma yafi mata kwanciyar hankali saboda baizo inda takeba bare yafada mata bakar maganar da zata hanata bacci kamar yadda yasaba, kokari ma take tayi tasamu ta yakice matsalarshi daga zuciyarta. Shi dinma yayi hakanne domin yabarta ta sarara kuma ta huta sannan shima aiki yasakoshi gaba koda yaushe cikin aiki suke mutum baida lokacin kansa,
Ana saura kwana uku abbanta zai dawo daga tafiyar da yayi masu hayar gidan fahad suka tashi wato wadannan turawan da suka karbi gidanshi dama already sun gyara gidan sai dan gyare gyaren da baza arasa ba. Ranar laraba da daddare Abba yasauka wanda da tunima yajima da dawowa dan dai kawai yabiya ta wurinsu elmustapha ne yagansu, dawowarsa da kwana biyu fahad yarako babansu domin yiwa Abba sannu da zuwa dama awurin maama yake jin komai yanzunma itace tasanar dashi dawowar Abba,
Tunda fahad yagaida Abba yakoma gefe ya zauna yana saurarensu suna tattaunawa cikin fahimtar juna da mutuntawa, ahaka ammah tazo ta samesu suka gaisa ta fita, babu jimawa saiga Bilkisu itama tasha dogon hijabi har kasa,durkusawa tayi ta gaida baba sannan tamike zata fita, hada ido sukayi da fahad ta harareshi wannan karon bai ramaba amaimakon hakama sai yayi murmushi kawai, bayan fitarta ya maida hankalinsa kan maganar da su Abba sukeyi inda abban yake cewa tunda yadawo ai sai ayi maganar tarewar Bilkisu agidanta, dan haka idan har babu matsala nanda sati biyu sai ta tare agidanta nan baba yace babu kuma anyi abu akan gaba saboda dama mutanen da suke zaune agidan fahad din sun fita dan haka ko gobe ake son tariyar babu damuwa, anan dai aka bar zancen azuwan nanda sati biyu zata tare saboda abata dama ta gabatar da dan shirye shiryenta da take son gudanarwa.
Fahad sun bar gidansu Bilkisu cikeda karramawa ga uban kayan tsaraba da Abba yabawa baba, washe gari fahad yasoma gyara gidansa gashi a lissafinsa bazaifi sati daya da tariyar ba zai koma makaranta, haka dai yake ta kaiwa da kawowa danma yayunshi na taimaka masa.
Bilkisu kuwa tun lokacin da abba yasanar da ita maganar tariyar nan take cikin kunci, kullum cikin fushi take hatta khulsum saida ta fahimta har saida ta tambayeta meke faruwa nan ta sanar da ita wai tarewa zatayi nanda yan kwanaki dariya khulsum tayi tace,
"To ai ke gata ma akayi miki wannan uban sanyin dake tunkaro duk wani mai rai ai zakifi more amarcinki tunda gaki ga mijinki.... Danma kun kwafsa kin yarda yayi miki ciki tun kafin ku tare..."
Harararta Bilkisu tayi sannan atunzure tace,
"Dallah ni tashi muje news ko intafi inbarki, ke kika san wani ciki ni ban sanshi ba"
Daga haka tafigi handbag dinta tayi gaba tanata masifa aranta ita daya.
Cikin kwanaki kadan aka gama gyarawa fahad gidansa wannan karon kam komai gaban kansa yakeyi babu maganar tambayar ra'ayin Bilkisu kamar wancan, duk abinda yayi masa shi yakeyi yanzu, babu karya gida yafito yayi das dashi kowa yagani yasan gidan amarya ne, kwana biyu atsakani su maama sukazo da motar kaya aka soma shirya mata kayanta aciki komai sabone fil aledarshi, yana shirin baro cikin asibiti maama tayi masa waya tana tambayarsa wai duka bedrooms din guda biyu nasune?
Dariya ma shi abin yabashi shiyasa bayan sun gama yarawa da maama yakira Bilkisu wadda rabonshi da ita tun sati biyu da suka wuce, har wayar ta tsinke bata daga ba wannan dalilinne yasashi tura mata text massage.
Tun tana cikin bathroom tana wanka take jiyo karar wayarta amma bata fitoba saida tagama tana zuwa taga miss called da massage guda daya massage din tabude bayan ta duba miss called din,
_Ki fadawa kannenki su zaba miki daki guda daya, dayan kuma subarshi empty saboda na matata ne...._
Ganin abinda ya rubuto mata yasata zama agefen gadon tana huci azuciyarta tana tambayar kanta wai ita zai hada da matarshi agida daya? Ai kuwa sam wannan abune wanda bazai taba yuyuwa ba....
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:21] Hafsat Rano: *Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
47**** Kamar a mafarki sai taji abun na damunta, akan me zaice zai hadata da wata agida daya? Ai wallahi bazata taba sabuwa ba idan har yadamu da dole sai yayi auren to sai dai ya nemawa matar tasa wani gidan amma ba wannan ba, cikeda masifa ta jawo wayarta wadda ta cillar kan gado saboda takaici, maama takira amma har ta katse bata dagaba dan haka ta kira meenah wannan dinma saida tayiwa meenah kira biyu sannan Hindu ta daga,
"Meenah kar ku wani bar empty bedroom duka ku saka min kayana ako ina dama ai gado biyu ne ko? So kuyi min jerena ako wanne daki...."
Bata ma jira taji maganar Hindu ba ta katse wayar saboda ita duk atunaninta meenah ce, dukansu dariya abun yabasu lokacin da Hindu ke kora musu labarin fadan da taji Bilkisu nayi,
Ita kam cikin fada da masifa take yin komai tana shiryawa sai babatu takeyi ita kadai,
"Can da iyawarku kaida matar taka...., nidai abinda nasani shine bazai taba yuyuwa ka hadani da karamar yarinya ba salon tazo ta rainani...., kuje can ku karata ka kaita duk inda zaka kaita wannan damuwarku ce ba tawa ba..."
Ahaka ta gama shiryawa tasaka blue din material fitted gown tana daura dan kwali tajiyo karar wayarta, zuwa tayi ta dauka tana ganin fahad ne tayi tsaki ta sake jefa wayar saman gado tafita daga dakin ma gaba daya zuwa dakin ammah wacce ke zaune tana waya da Rabi mai aikinta tana sake karanta mata abubuwan da zata sake hado mata daga kasuwa, zama tayi tana sauraron ammah har tagama wayar ta sauketa daga kunnenta,
"Ammah kunyi waya ne dasu maama?"
Kallonta ammah tayi tana danna wayarta,
"Meya faru?, munyi waya dasu dazu nace musu subar gado daya su saka miki daya saboda wai yace daya dakin idan matarsa tazo anan zata zauna..."
Bata rai Bilkisu tayi kamar karamar yarinya tasoma magana cikin damuwa,
"Kuma shikenan ammah dan matarsa zata zauna aciki ni sai afasa saka min gado biyuna? Ni wallahi yanemi wani gidan yakaita can..."
Girgiza kai ammah tayi tana kallonta,
"Wai dan Allah sai yaushe zaki girmane mai gado? Mijin naki nawa yake da har zakice yayi gida biyu? Shida ba aiki yakeyi ba shine zakice yanemi wani gidan? Kinga.... Tam, maza dai kibari wannan maganar taje kunnen abbanku.... Zakiyi masa bayani nidai babu ruwana..... Karki bari nasake jin wannan maganar kinji dai nafada miki..."
Jin abinda ammah tace yasata sake jin bacin rai ya rufeta yanzu shikenan babu mai goyon bayanta? Haka zata zauna gida daya da karamar yarinya amatsayin kishiyarta? Tun daga lokacin take ta fushi, fushi takeyi da kowa,komai su maama sukace tayi sai tace baza tayiba, kunshi, kitso, gyaran kai duk taki yi bare asa ran zatayi gyaran jiki. Ana saura kwana uku ta tare hajiya iyallo tazo amma wannan karon ita kadai tazo ko yafindo mai gado basu taho tareba wai tana can tana kula da jikokinta wadanda aka yiwa shayi har su shida, ko kadan Bilkisu bata so zuwan iyallo ba wannan karon kamar waccan saboda yanzu abubuwan da iyallon takawo ita ba amfani zatayi dasu ba, kuma haka kawai sai inzauna inta dirkar kayan gyaran jiki saboda wannan yaron? Haka take ta tambayar kanta, tsumi ne hadadde irin na mutanen kauye sai tukudi da gumba amma fafur taki sha sai su maama ne suka rabe atsakaninsu. Lokacin da khulsum tazo kuwa saida suka yi fada da Bilkisu saboda takawo mata hadin kankana da kwakwa sannan kuma tace mata yakamata suje ayi mata kitso da kunshi amma tayi biris, tabe baki khulsum tayi tace,
"Duk dai wannan zille zillen da kikeyi bashi zai hana mu mikaki gidanshi ba jibi ehe... Kuma dole abashi hakkinsa ta dadin rai idan anki kuma ya kwata ta karfin tsiya....."
Shiru Bilkisu tayi bata kulata ba taci gaba da abinda takeyi, nan tasake jiyo maganar khulsum tana cewa,
"Badanma ina tausayawa mutum ba kar dan karamin cikin dake jikinsa ya zubeba ai wallahi da sai na zuga fahad yayiwa mutum lisss..."
"Wai ke kika yimin cikin? Ni kidaina jamin jaraba malama..."
Bilkisu tafada cikin fushi, dariya khulsum tayi taci gaba da tsokanarta, duk yadda sukaso ta gyara kanta da jikinta ki tayi ita kuwa dama ammah bata kulaba tunda tasan rashin yin kitso da lallen bashi zai hana ta tare dinba. Shima fahad bai sake nemanta ba tun lokacin da ya kirata taki dagawa, yasan fushi takeyi saboda yace tare zasu zauna da husnah shi kanshi idan son samune zaifi son ace kowa da wajenta to amma ai baida karfin rike gida biyu shiyasa lokacin da yasamu ayiyah da maganar tace a'a karma yafara saboda bazai iyaba, itama husnan yasanar da ita tare zasu zauna da Bilkisu saboda gara tasani tun yanzu domin so yake Bilkisu tana tarewa yatura asaka musu rana da ita domin shi ya Abba yake jira shima yagama shirinsa tsaf kawai sa ranane yarage. Ranar da su maama suka yi jere agidan ya kwana adakin Bilkisu kuma akan gadonta, kawai tunani yayita yi acikin ransa yana sake jinjina girman ubangiji saboda gashi cikin iyawarsa da hikimarsa yasake dawo masa da Bilkisu akaro na biyu,
"Hmmmm ko yanzu wanne irin zama kuma zamuyi oho... M" haka yaketa maimaitawa acikin ranshi. Ranar laraba da daddare aka raka Bilkisu gidanta tun amota iyallo take zuba ruwan fada tana cewa wannan amarya akwai shashasha shine ko dan sunkuben lallen nan bata kunsa ba bare tayi kitso? Ita dai Bilkisu najinta batayi ko da tariba har suka karasa gidan inda su anty kubra dasu anty asabe ke zaune suna zaman jiransu, babu Wanda yakara koda mintuna goma acikin gidan duk tafiya sukayi lokaci guda kamar ana korarsu,yaye mayafinta tayi bayan tafiyarsu tana kallon dakinta wannan karon komai blue ne amma furnitures dinta farine tass kirar royal, bata bukatar sake fita koda falo saboda bacci take son tayi tahuta amma kuma bata son wannan dan rainin wayon yazo ya isketa tana bacci saboda jikinta na bata komai na iya faruwa.
Sai dai abinda bata saniba shine fahad yashirya zamansu yanda zai kasance, sam bazasu yi zama irin nada ba yanzu yanaji aranshi lokacin shine yazo shima, awanccan zaman Bilkisu tayi yadda takeso to yanzu shima shine zaiyi yadda yakeso shiyasa lokacin da yadawo ma bai ko shiga dakinta ba yawuce daya dakin wanda kayansa naciki dama wanka yayi yashirya cikin kayan bacci masu taushi yayi kwanciyarsa babu jimawa bacci yayi gaba dashi,Bilkisu nata jiran shigowarsa shiru shiru har tagaji da saurare tayi bacci ba ita tatashi ba sai asubah, tana kan gadon tana niyyar saukowa taji yana yimata knocking,
"Kitashi lokacin salla yayi..."
Daga haka taji shiru alamar yabar wurin, sake kwanciyarta tayi bayan tayi salla ba ita tasake tashiba sai 10 saura wannan dinma karar wayarta ne yatada ta,tsaki tayi sakamakon ganin khulsum ce me kiran nata,
"Labour har yanzu ba awartsake bane? Ko dai sai nazo ne?"
"Uwar me zakizo kiyi min? Wallahi khulsum zan ramane..."
"Shikenan sai nazo din to"
Katse wayar tayi tana hamma saboda yunwa da kuma sauran bacci baccin dake kanta, wanka tashiga tayi tafito ta shirya tsaf cikin doguwar riga ta atamfa coffee colour sai dison yellow yellow ajiki, batayi kwalliya ba dan kawai powder tashafa sai kwalli ta fita falo, dama kayan abinci tasan babu matsala domin wannan karonma kamar waccan abba ya ajiye musu komai cikin store, afalo taganshi kwance daga shi sai three quarter da yar t shirt, yana kwance kan three sitter yana lallatsa waya, kanta ta dauke kamar bata ganshiba shima haka domin yasan awannan shegen son girman nata bazata yimasa magana ba saboda jira take ya gaidata tukun, harda wani dan bata rai yayi sai kace shine babba koda yake shima yanzun jin kansa yake a babba tunda shi yake aurenta ba itace take aurenshi ba dan haka yazama tilas tayi respecting dinshi a matsayinshi na mijinta, maganar hakkinshi kuwa dama shi yanzu ba ta wannan yakeyi ba saboda aduk lokacin da yatuna cewar ta auri wani yayi tarayya da ita sai yaji baya sha'awar abun, gaba daya abun yafice masa akai saboda yatsani hamood dinnan tsana mai tsanani. Kitchen tawuce domin taga kayan tea akan table,tana neman cattle tajiyo buga gida, duk haushi yabi yakamata sakamakon rashin gaishetan da fahad baiyiba,
Fitowa tayi daga kitchen din dan ganin suwaye, daidai lokacin da su mariya suka shigo dauke da kuloli akansu fahad yana biye dasu, nunata yayi yana cewa,
"Maza ku kai mata gata can"
Nufarta sukayi suna fara'a babu shiri itama tasaki fuskarta tana yimusu murmushi gamida karbar kayan dake kansu, maryam tariko kular wainar shinkafa ita kuma maryama tariko kular miyar agushi, anty Fauziyya ce tashiryo musu wannan wainar ta musamman domin ta hutar da amarya girkin safe, fahad baiko kalleta ba yawuce dayan bedroom din wanda ke gefen nata amma akwai dan tazara kadan,
Tare ta hada musu tea din dasu Maryam suka karya, ba karamin dadi taji wainar nan tayi mata ba wannan dalilinne ma yasata zagewa taci wainar sosai tana korawa da ruwan tea, daga nan falo suka tarkata suka koma ta kunna musu kallo har lokacin fahad bai fitoba ko breakfast dinma shi bai fito yayiba har 12 saura. Misalin karfe daya saura mintuna biyar ya Abba yakawo musu abincin rana, su maryama ne suka shigo da abincin amma shi ko shigowa baiyiba yadai ce agaidata, yanzunma tare suka ci abincin ranan shinkafa da miya da salad, bayan sun gama tawuce dakinta domin lokacin salla yayi, wanka tayi tai alwala tafito tashirya tana ta mitar shine babu wanda yazo mata yau wato har khulsum dinma da take cewa zatazo shine itama tayi zamanta ko leke, da abin sallarta tafita ahannu da hijabinta wurinsu maryama, tunda tashiga falon kamshi yacika kofofin hancinta wanda ko ba afada mata ba tasan na dan mulkinne saboda da alama yau da mulki yatashi da nuna isa,
"Anty ya fahad yanzu yafita yace lallai lallai muna yin salla mutafi gida saboda zamuje islamiyyar yamma..."
"Ba yau alhamis ba, har yau kunayin islamiyyar ne?" Tafada tana kokarin shimfida rug din sallar,
"Ehh munayi ranar juma'a ne kawai ba azuwa yanzu..." Maryama tabata amsa,
"Ok, fahad din yaci abincine?" Tayi tambayar da ita kanta bata san daliliba,
"A'a baiciba" suka hada baki wurin amsawa,
Sallarta ta tayar batare da ta kara magana ba, bayan ta idar tatashi tawuce daki tana ninke hijabinta tabarsu maryama afalo suma suna yin sallar, rasa abinda zata bawa yaran tayi daga karshe ta dauko wata atamfarta wadda matar abokin abba ta aiko mata da kyautarta lokacin da tana gida amma bata dinkaba,saida ta wahala kafin tanemo ledar da zata saka musu aciki, da atamfar da dari biyar tabasu sukayi mata sallama suka tafi, wayarta ta dauka tana latsawa amma kuma can kasan ranta tunani takeyi, wato wannan yaron dan rainin wayo ya karo wulakanci shine harda wani ficewa baiko fada mataba? Ohh sai yanzu tagano dalilin dayasa jiya baiko shiga dakinta ba, wato irin zaman da ya zaba musu kenan ahalin yanzu? To azuba agani zataga tsakaninsu wanda zai sauko yabi daya........
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:21] Hafsat Rano: *Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
49***Har yadawo babu wanda yayi magana acikinsu yana zuwa yazauna a mazauninsa da yatashi dazu,
"Hajjaju nabar wayar a silent ne ashe ban saniba..." Yafada yana murmushi,
"Babu damuwa..." Ta amsa hankalinta na kan wayarta dake hannunta, karfe uku saura agogon silver din dake daure a hannunta yanuna duk tagaji kawai alla alla takeyi taganta agida tasha tea ta kwanta ta huta, tsitt shagon yayi baka jin maganar kowa sai karar keken da fahad yake dinki dashi, kowa yanada dalilinsa na yin shiru, husnah da fahad dalilinsu daya ne saboda ganin Bilkisu zaune awurin shiyasa suka kasa sakewa suyi hira ita kuma Bilkisu hayaniyarce bata so domin har wani dan ciwo ciwo kanta keyi,wayarta take dannawa tana chaten da khulsum tana tambayarta abinda yahanta zuwa aiki yau,
Ninke kayan da yagama hadawa yayi ya mikawa husnah nan takarba can kasan makoshinta ta furta,
"Thank u my prince..." Kan labbanta kawai ya kalla yayi murmushi, mikewa yayi yana yin mika saboda zaman da yasha, yana kokarin daura agogon hannunshi wanda yacire yaji husnah ta fauce,
"Dama ai nafada maka sai nasace agogon nan wallahi yafi dacewa dani..."
Kallon agogon yayi ya kalli husnah shi ba wai tsadar kudin agogonne damuwarsa ba a'a yanda yake son agogonne saboda kwata kwata wannan shine sawarshi na uku a Kaduna yasiyo shi kuma unisex ne maza da mata kowa zai iya sakawa, 7 thousands ya siyeshi amma tun ranar da husnah taganshi ahannunshi tace sai yabata shikuma yahanata yace zai saka mata irinshi a lefe amma da yake kansa yadau caji gaba daya ma yamanta da sunyi magana makamanciyar wannan lokacin da ake hada lefen.
"Hmm ya fahad sai munyi waya dai kawai..." Tafada ahankali saboda kar Bilkisu tajita,hannunshi ya mika mata,
"Bani agogona before kitafi... Bani pls"
Makale kafada tayi tajuya zata tafi nan yayi gaggawar riko rigarta ta baya babu shiri ta tsaya, duk abunnan da sukeyi Bilkisu bata san sunayiba domin abinda yake gabanta takeyi wato chaten, saida tajiyo motsin fara kokawarsu sannan ta daga kanta ta kallesu abin yayi mutukar bata mamaki saboda ita kallon salihi mutumin kirki take yiwa fahad amma yanzu sai ganinshi tayi dumu dumu yana kokawa da mace har yana hadata da jikinshi, to meye hakan? Har wajen baranda suka fita suna kokawa yana kokarin kwace agogonshi amma husnah ta hanashi wannan dalilinne yasashi turata jikin bango ya matseta yana neman kwacewa,
Ganin kamar sunma manta da ita yasata tashi ta dauki jakarta fuuu tafito, abayan kofa tagansu suna manne da juna har lokacin basu daina kokawar ba, wani dogon tsaki taja sannan tawuce, dukansu tsayawa sukayi suna kallonta tana kokarin kaiwa karshen steps din benen, sakar masa agogon husnah tayi yajuya yabi bayan Bilkisu bai ko koma cikin shagonba bare ya rufeshi cikin ikon Allah sukayi kicibus da nazifi zai koma shagon, yana sauka kuma yaganta tsaye itada salim suna gaisawa alama yayiwa salim da ido nan ya wulla masa keys din dake hannunshi ya cafe yaje ya dauko babur din yatsaya agabanta ,dauke kai tayi sannan ya karkata mata tahau, duk husnah na kallonsu daga can inda take tsaye asama, har saida taga sun tafi sannan ta sauka itama tatafi. Bilkisu kam wani irin bakin ciki takeji wanda batasan dalili ba, ganin da tayiwa su fahad manne da juna yaki ya bace daga cikin idanuwanta da zuciyarta gaba daya, ji take kamar ta shakeshi tayita dukansa ko zata huce, har sukaje gida bataji bacin ranta ya ragu ba,
"Kenan Allah kadai yasan abinda sukeyi idan su biyune kadai...." Tafada acikin zuciyarta saboda yanzuma sukayi haka agabanta inaga su biyune kacal ashagon, tsaki taja tasake ja akaro nabiyu tana kokarin rage kayan jikinta, falo tafita ta hado tea tazauna tana sha sai faman jan tsaki takeyi saboda bacin rai,
Duk tsakin da take ja fahad na jinta amma bai yi maganaba kuma yasan dashi take,
"Ita ta dazun da kaketa hada jiki da ita, ita kuma wacece?"