Kenza eBookz

Kamar da wasa complete novel - Chapter 28

Kamar da wasa complete novel - Chapter 28

Kamar da wasa complete novel Chapter 28: Kamar da wasa complete novel Chapter 28. Daga haka sukayi sallama yakatse wayar dama tun lokacin da suka jone da…

3,206 words

Daga haka sukayi sallama yakatse wayar dama tun lokacin da suka jone da husnah ko ba ya gari idan zata fita saita tambayeshi shiyasa har sun dade da sabawa da wannan tsarin sam basa kallonsa asabon abu. Irin zaman da su Bilkisu suka faro shi suka cigaba da yi na ba ruwan kowa da kowa, gaisuwa kuwa tab rabon da taji fahad ya gaisheta har ta manta gashi yanzu wani sabon salon wulakanci da ya koya shine sai yarinka kiranta da Bilkisu, idan zaiyi mata magana sai dai yakira sunanta, yauma da zai fada mata sakon su ayiyah tana daki tana ware kayan sawarta tana karasa shiryawa cikin drewar, zama yayi gefen gadonta yace,

"Am Bilkisu ayiyah tabani sako.... Tace wai gobe za akai lefen ya Abba gidansu salim idan kinada lokaci kije akai dake...."

"Naji...." Tafada atakaice saboda tasoma kosawa da wannan rashin kirkin nashi akan me zai rinka kiran sunanta kai tsaye? Duk da bawai yau yafara ba amma yau kamar hakan yafi kona mata rai. Washe gari da yamma bayan tadawo daga aiki ta shirya tatafi gidansu fahad sai kaffa kaffa ayiyah takeyi da ita, dama tasan bata da matsalar uwar miji dan ayiyah na mutukar sonta hakama sauran yan uwan mijinta kawai dai abinda ta lura shine matar ya sunusi wato anty juwairiyya bata faran faran da ita tun wancan lokacin har yanzu dan tun aurensu nafarko taketa kukkushe Bilkisu tana cewa ai fahad tsohuwar yayarshi ya auro dan wannan a haihuwar kajima ai ta haifeshi, ko yauma da ta shigo gidan kowa yanata murna da lale marhabun da ita amma banda Anty juwairiyya shiyasa itama takama class dinta daga gaisuwa bata kara cewa komai ba,tarba ta girmamawa aka yimusu agidansu salim akwatuna shida masu kyau suka kaiwa nusaiba bayan an karbi kayan da babu jimawa suka koma gidansu fahad lokacin magriba tayi, Bilkisu tafito tsakar gida tana alwala sai ga fahad yashigo daga masallaci yake anty juwairiyya na ganinshi tafara cewa,

"Kaga sabon ango....kaima nanda wani satin zamuje Kaduna mukai maka naka...."

Baiyi magana ba sai murmushi kawai duka hannayenshi na cikin aljihun rigar farar shaddar da take jikinsa,gun Bilkisu yakarasa ya tsaya kusa da ita tana alwala,

"Zaki tafi yanzune injiraki ko sai anjima sai indawo in daukeki?"

Jin abinda yace ba karamin dadi yayiwa Bilkisu ba saboda tasan dai ko babu komai anty juwairiyya zata gane fahad na yinta kuma tanada wani matsayi na musamman agareshi,rausayar da kai tayi ta kalleshi sannan tace,

"Da sallah nake son nayi... Ko sauri kakeyi?"

"A'a kiyi mana... Kiyi sai mutafi"

"Yawwa nagode" tafada tana kokarin shiga falon ayiyah inda anty juwairiyya ke tsaye tana kallonsu sai jan fahad take da maganar bikinsa shida husnah amma yaki biye mata suyi saboda shi yanada wani abu guda daya akan Bilkisu, idan daga shi sai itane baya raga mata ahalin yanzu amma idan agaban mutane ne ko wani to yana nuna har gobe yana sonta yana martabata, shiyasa abun bai cika damun Bilkisu ba saboda sai idan iya shi da itane yake nuna shine oga dole ta girmamashi. Har ta idar da salla bai bar kofar falonba yana tsaye da wayarshi a hannu yana dannawa, lokacin da take yiwa ayiyah sallama tana jiyo anty juwairiyya nace masa,

"Ko da amaryar ake soyewa ne dan kanina...."

"Kai anty nifa gaskiya kin saka min ido da yawa..." Yafada yana dariya, sosai Bilkisu taji dadin amsar da yabata, fitowa tayi rikeda irin kayan snacks din da aka basu agidansu salim wanda anty asabe ta zubo mata, karba yayi daga hannunta yawuce gaba tana biye dashi abaya har waje, su ya Abba na zaune akofar gida shida salim sai taji duk kunya ta kamata musamman ma lokacin da zata hau bayan babur din nashi dole saida ta dafa kafadunshi duka guda biyun, har sukaje gida babu wanda yace da wani ci kanka sai dai idan sun dan shiga kwari ko gargada yaji ta rikeshi da haka suka je gida. Cikin yan kwanakin aka kammala komai na zuwa kd domin kai lefenshi komai iri daya yayi ma husnah da Bilkisu bai banbanta ba ita Bilkisu ma bata san wacce wainar ake toyawa ba, ita dai kawai abinda tasani shine bazata taba daukar raini ba nashi ko na matarshi, ranar da aka tafi kai lefen ma bai fada mata ba saboda har gobe irin zaman da ya zabar musu sukeyi, ita anata ganin ai ba ita yadace ta rinka shan kanshi ba ko kuma ta nemi shiri dashi, shiyasa gaba dayansu ba wani dadin zaman sukeji ba saboda kowa baya sakarwa kowa, har aka kai lefen aka saka rana wata biyu babu wanda ya gaya mata batama saniba gaba daya, shi kam fahad shirin komawarsa makaranta yasaka gaba yana kammalawa ya tafi bayan yabar mata duk abinda yasan zata bukata. Wani lokacin Mariya ko maryama ayiyah ke turo mata su tayata kwana amma ba kullum ba, tunda yatafi kuma bai kirata ba sai bayan kwana hudu da tafiyarsa nan dinma iyakarta gaisuwace daga nan ya tambayeta ko da akwai abinda take bukata tace babu shikenan yace mata sai anjima, hakace take faruwa har yayi sati uku da tafiya a lokacin ne yazo gida weekend, tun ranar Thursday yazo yana son komawa Monday ko Tuesday,lissafin bikinsu kuwa saura sati hudu babu yan kwanaki, a wannan zuwan da yayi yai niyyar fadawa Bilkisu maganar aurenshi da husnah, ranar ya fada mata da safe tana karyawa zata tafi aiki saboda Monday ce shikuma yana kwance kan three sitter yana kallo, a laptop dinshi,

"Bilkisu aure zanyi fa...., yau saura sati uku da kwana biyu..."

Saida ta dan ja numfashi sannan cikin halin ko inkula tace,

"Allah yabada sa'a... Ko akwai wani abu da zanyi baya ga haka?"

Girgiza kai yayi yana murmushin takaici bai san sai yaushe Allah zai karbi addu'arshi yasa Bilkisu ta soshi kamar yadda yake sonta ba, ita kuwa tsabar takaici da bacin rai ko gama cin abincin ba tayiba tabarshi ta tashi ta dauki wayarta da handbag dinta tafita dama tun dazu mai napep din dake kaita aiki yazo. Fahad kwanciyarsa yaci gaba dayi har saida husnah ta kirashi tace yataimaka yazo ya dinka mata atamfarta domin da ita take son tatafi gida jibi, jibi zata gama exams dinta kuma idan tatafi bazata dawoba sai bayan bikinsu saboda hutun session ne, tashi yayi duk jikinsa babu karfi yayi wanka yashirya cikin kananan kaya, bakar riga da milk colour din trouser, zama yayi ya karya sannan yafita yasamu husnah a shagonsu salim tana jiransa, tsokanarsu salim yafara yi yana waka yana cewa ga amarya ga ango, tare suka haura saman shagonsu fahad inda zaiyi mata dinkin.

Bilkisu kam tana can office tarasa me yake yimata dadi, ita dai tasan ba kishine ke dawainiya da itaba kawai dai bata son yarinya karama tazo ta nemi rainata shiyasa bataji tana farin ciki da auren da fahad zaiyi ba, duk zuciyarta babu dadi take gudanar da ayyukan dake gabanta, lokacin da taje yin voicing din news kuwa kasawa tayi saboda sai tafara tiryan tiryan sai ta tsaya tana inda inda kamar yaune tafara koyon aikin daga karshe dai sai hakura tayi ta mayarwa head of news din tace kanta ke ciwo bazata iyaba, haka ta tarkata nata inata tafito domin tafiya gida dama yau khulsum bata zo ba, abin bakin ciki saida taje gida taga ashe yau bata fito da keys dinta ba wato mantaso tayi aciki da safe bata dauko ba koda yake da safenma acikin kunar zuci take saboda maganar da fahad yafada mata na aurenshi ko ina ruwanta da zaizo yasata agaba yana wani cemata aurenshi yakusa? Tsaki tayi ta tsayar da mai napep dinta dama Allah ya taimaketa bai tafiba, wayar fahad taketa kira amma bai dagaba har sau uku, tasan duk yadda akayi baya tare da wayar saboda bai fiya kin daukar wayaba matsawar yana kusa, yanzu bata da zabin da yawuce tabishi plaza shagon dinkinsu ta karbo nashi mukullan, hakan tayi tashiga napep tatafi plaza dinsu, lokacin shikuma yana zaune shida husna dasu tj yana yiwa husnah dinkinta su tj kuma sai hirar siyasa sukeyi shidai dariya yakeyi kawai saboda ganin yanda suka hakikance suke tada jijiyar wuya saida cikin kowa yafara kugi saboda yunwa kowa yadare yatafi neman abinci yarage saura su biyu ashagon, ahaka Bilkisu tashigo ta samesu, da mamaki fahad ya dago yana kallonta ranta abace fuskarta adaure amma shi sai ya fadada tashi da murmushi saboda husnah dake zaune,

"Hajjaju yadai? Lafiya kuwa?"

"Inata kiranka baka daukaba...., keys dina ashe ban fita dasu ba... Bani na wajenka"

"Kashhhh, bari salim yadawo, dazu wallahi yazo ya karba yaje siyo fetur ne a Babur dina kuma duk keys din tare suke... Sorry fa..."

"To ya zanyi da mai napep dake jirana?"

"Ba matsala bari na sallameshi sai na mayar dake gida nima nakusa tashi,have a sit" yafada yana nuna mata wurin zama kan wani benchi dake ajiye shi kadai babu komai akai, tashi yayi da kanshi ya sauka kasa domin sallamar mai napep din, daga ita har husnah babu wadda yayi tari ita husnah ma wayar hannunta take latsawa yayinda Bilkisu ke bin shagon da kallo har ta dire kallonta kan husnah wacce ke sanye cikin riga da skirt na leshi c green taci daurin zahra buhari hakan yabawa kitson dake kanta damar lekowa ga dan siririn mayafinta kalar kayanta kan kafadarta barima guda ukune jere akunnenta kallo daya zaka yimata ka fahimci yar jami'a ce dan tsantsar wayewar da take tare da ita sam bata san cewa itace budurwar fahad ba amma ita husnah tuni tagane Bilkisu itace matar fahad hakan yasata dan kallonta ta gefen ido tabbas black beauty ce kuma ita dinma babu raini tun daga dressing dinta pink din materia ne ajikinta mai tsada shiyasa komai nata pink tayi amfani dashi ciki kuwa harda hill din takalmin kafarta saboda ita ba ma'abociyar saka flat bace.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:22] Hafsat Rano: *Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

50***Kuka take yi harda shessheka gaba daya ta jike pillow din da take kai, ga wani matsanancin ciwon kai wanda yafara damunta har tsawon karfe daya da kusan rabi takai tana wannan kukan, Dai dai wannan lokaci shi kuma fahad na can tare da husna, lokacin da yashiga kishingide ya isketa ta dan fara bacci, tashinta yayi ta hanyar kama yan kafarta wadanda sukasha jan lalle da baki yana jansu ahankali, bude ido tayi tana kallonshi cikeda gajiya da tarin bacci,

"Ya fahad... Sai yanzu kadawo?"

"Wai har kin fara bacci asma'u? Oya tashi kici abinci sai ki kwanta..."

Yafada yana janyo hannunta, kafada ta noke tamaida kanta ta kwantar saman pillow,

"Ni bana jin yunwa, kaci kayanka..."

Murmushi yayi ya matsa jikinta, ahankali yace,

"Ko kema kina jin tsorone?"

"Name?" Tafada tana bata rai,

"Kar kici min kazata kuma nace sai kin biyani......!"

Daga shi har ita dariya ce ta subuce musu ta harareshi sannan ta gyara kwanciyarta izuwa rigingine,

"U kid yourself sweetheart.... Good news da zan baka yanzu shine am off, soo allow me to sleep pls....."

Murmushi yayi yana shafar lallen hannunta,

"To kinga dadinma zagewa kici kaza kenan tunda ba biyana zakiyi ba, wake up pls"

Girgiza kai tayi tana lumshe idanuwanta,

"Na koshi wallahi, sai da safe zanci...."

"Ok, sleep tight my love, good night...."

Bata amsaba ta gyara kwanciyarta ta hanyar juyawa daya bangaren, shikam yunwa yakeji sosai saboda yau da yunwa yawuni throughout shiyasa ya zauna yaci rabin kaza yasha madara, tashi yayi yashiga bathroom yayi wanka yafito ita dai husnah ko kayan jikinta dakyar ta iya canjawa saboda tsabar bacci da gajiya,shiryawa yayi cikin kayan baccinsa maroon colour masu santsi sannan yatashi yafita, dakin Bilkisu yanufa saboda haka kawai yake jin zuciyarshi bata nutsu da yanayin da Bilkisu ke cikiba shiyasa yasake niyyar komawa dakinta yaganta,

Kamar amafarki taji bude kofa babu shiri ta hadiye kukanta ta toshe bakinta da hannunta guda daya, fitila ya kunna sannan cikin sassarfa yakarasa gaban gadon da take lullube ta wani tukunkune wuri daya,

"Billy....." Taji yafada cikin son jan magana amma sai tayi shiru kamar mai bacci,

"Billy tashi kiji.....kinji"

Nan dinma shiru tayi masa tana shasshekar kuka azuciyarta,

"Wai kina nufin kema kinyi bacci? Ok shikenan good night.....have a nice sweet dream"

Daga haka yajuya yaje ya kashe mata wutar yafita bayan yarufe mata kofa. Yana fita ta cigaba da shasshekar kukanta,kusan daren gaba daya bata samu runtsawa ba har saida asubah takawo jiki lokacinne bacci yasamu nasarar yin gaba da ita, su fahad kuwa tunda yabar dakin Bilkisu yana zuwa ya kwanta kusa da husnah babu jimawa yabi sahunta wurin yin bacci saboda tsabar gajiyar dake tattare dashi sallar asubah makara yayi dan sai wurin 6 sannan ya tashi, yana yin salla yasake kwanciya daidai lokacin ita kuma husnah ta tashi, wanka tayi ta caba ado ta sake kwanciya gefen fahad tana kallonsa yana ta sharar bacci hannunsa kan cikinsa, hamdala ta shiga yi ga ubangijin rahma dan ko yanzu ta mutu tasan Allah ya cika mata burinta, kasancewar jiya da yunwa ta kwana yasata jin cikinta yafara kiran ciroma babu shiri ta tashi tajanyo ledar da fahad yazo da ita adaren jiya, kaji guda biyune aciki amma yaci rabin guda daya sai fresh milk kwali biyu, fresh milk din tafara sha sannan taci rabin kazar da ya ajiye, rasa abinda zatayi tayi gashi takasa komawa bacci kuma lokacin karfe bakwai da wasu mintuna wadanda bazasu gaza biyar ba, tana nan kwance tana kallonsa har shima yafarka hada ido sukayi tayi masa gwalo, hannu ya mika mata amma sai ta gagara kama nashi saboda yau jinta take awani takure duk da ba yau tafara kama hannunshi ba amma dai na yau ya banbanta da na kullum, jikinsa ya matso da ita yana tsokanarta da idanuwanshi,

"Kin ci abinci?" Ya tambayeta ahankali, daga kai tayi sannan tace "ehh"

"Husnah kenan wai duk kinyi laushi why? Dan Allah kidaina tsorona,bari ma ki gani wanka zanyi infita..." Daga haka yatashi yawuce toilet kafin yafito ta dan gyaggyara dakin duk da babu wani datti da yayi sai dai dan abinda ba arasaba. Falo ta dan leka tana sa ran ko zata ga matar gidan amma shiru babu motsin kowa, kafin takoma daki fahad yashirya saima da ta daidaci cewar ya shirya sannan tashiga dakin, yana tsaye gaban mirror dinta yana karya hularshi da zai saka,

"Ya fahad ina kwana?" Tafada tana murmushi sannan tana kallonsa,

"Lafiya lau husnatah, ya bakunta?"

Dariya tayi tazauna agefen gadon tana kallonsa ta cikin mirror shima kallonta yayi yasakar mata murmushi sannan yajiyo,

"Bari induba hajjaju ko ta tashi..." Kai ta daga masa hakan yabashi damar wucewa yafita, dakin Bilkisu yabude yashiga da sallama akan labbansa, tana zaune gefen gado tana shafa mai da alama daga wanka tafito sai dai fuskarta duk a dan kumbure,

"Ashe kin tashi? Yakike?", dan tsuke fuskarta tayi saboda tasan rainin wayon nashi yazo yimata inbanda haka menene nashi na wani cemata yatake, jin bata tanka masa ba kuma taki kallonshi yasashi dan matsawa gab da ita,

"Billy yakika tashi...?"

Sam kin yarda ta kalleshi tayi saboda bata son yaga yanayin da idanuwanta ke ciki, har yagama neman maganarshi yafita bata tanka ba kuma bata kalleshi ba, wurin husnah yakoma yayi mata sallama yafita. Fitarshi babu jimawa su Anty Fauziyya sukazo da sauran yan uwan husnah wadanda suka kwana agidansu fahad, food flask din da aka zubowa kowa breakfast dinshi daban, anty asabe ce tashiga wurin Bilkisu takai mata nata, basu dade agidanba suka tafi sai lokacin da zasu tafi sannan Bilkisu tafito ta rakasu bakin kofa sannan takoma ciki tayi kwanciyarta, haka tawuni adaki a kwance dolece kawai take tadata ango kuwa bashi yadawo gidanba sai dare saboda anata baki yan uwa da abokan arziki duk wanda yaje gidan ya Abba to gidan fahad zai zarto shiyasa husnah yau tasha baki har ta godewa Allah amma fa Sam bata ga bilkisu ba hakan yasa mata tunani aranta na anya kuwa ko lafiya?.

Lokacin da yadawo dakin Bilkisu yashiga har lokacin tana kwance bakinta akekashe alamun bata ci komaiba, zama yayi saman bedside drewar yana kallonta,

"Kinci abinci ne?" Wani kallo tajuya tayi masa sannan takawar da kanta duk sai yaga tayi masa wani iri kamar marar lafiya,

"Dan Allah kici abinci rabin raina..." Yafada yana dariya shiru tayi masa, tashi yayi yafita yana fita taja dan siririn tsaki tagyara kwanciyarta, shi kam yana can suna zuba love da husnah dan yana kwance dare dare akan kafafunta tana bashi labarin irin bakin da tasha yau, daga nan bai sake fitaba sai dai idan salla zaije, ana yin sallar ishah kuwa yarufe gida yashiga gida yana tunanin ya kamata ya hada husnah da Bilkisu inyaso ko gaisawace suyi, yana shiga dakin husnah yaga tasha wata kwalliyar kamar bata kwanciya bacci ba, saida suka gama hira suka ci abinci yayi shirin bacci sannan yashiga dakin Bilkisu, itama tuni tayi shirin baccin tana zaune tsakiyar gadonta tana cin abincin da aka kawo musu daga gidansu fahad,

"Billy husnah zata zo ta gaisheki..."

"Ina ciwo ne?" Ta tambaya batare da ta kalleshi ba,

"A'a" yabata amsa,

"To bana bukata, ko zamana takeyi agidan?

"Allah yabaki hakuri, inzo muci abincin?"

Nan kuma bata tankaba saboda taga nema yake ya maidata wata bi ta nan, yana fita ta tashi tamayar da kofarta ta kulle, daren yau dai babu laifi ta dan samu damar yin bacci da wuri saboda jiya batayi ba yayinda ango da amarya ke can suna debewa junansu kewa danma dai har yanzu amaryar bata samu tsarki ba amma duk da haka an aikata abinda ba arasa ba, fahad baiyi bacci da wuriba yanata tunani wato dan adam yana nashi ne Allah na nasa, shi ko acikin mafarki bai taba zaton cewa zaiyi tarayya da wata mace koma bayan Bilkisu ba ashe husnah matarsa ce bai saniba sai yanzu. Washe garima haka Bilkisu tawuni curr adaki abinci kuma daga gidansu fahad ake kawowa, gaba daya zaman gidan ya isheta ya gundireta yakuma gama fita akanta, saida husnah tayi kwana uku gidan sannan suka hadu, ita Bilkisu tafito ita kuma husnah na zaune falo da waya a hannunta tana yin game, sama sama suka gaisa Bilkisu tawuce kitchen tayi abinda zatayi tafito, daren ranar fahad ya sameta da maganar girki domin yakamata husnah tafara girkinta adaina kawo musu daga gidansu fahad acewarta shine yake tambayar Bilkisu ya abin zai kasance,

"Ni zan dafawa matarka abincin da zata ci? Tabdijam to wallahi bazai yuyu ba, kowa yayi girkinsa final.... "

Shifa yagama lura da Bilkisu yanzu akusa take abu kadan ke bata mata rai tayita surfa masifa, baice komai ba yabar maganar sai da yakai 12 adakinta suna zaman kurame sannan yatashi yakoma dakin husnah,washe gari tunda sassafe Bilkisu ta tashi ta shirya saboda ankirata awaya wai Hindu ta haihu ansamu mace amma suna asibiti saboda yarinyar ba lafiya ansakata cikin kwalba, ganin shiru ango bai fitoba yasata kiranshi awaya amma wayar akashe, tsaki taja ta dauki handbag dinta tafita falo daidai lokacin shikuma yafito daga dakin husnah,

"Ya naganki haka? Lafiya?"

Batare da ta kalleshi ba tace,

"Asibiti zanje Hindu ce ta haihu"

"Masha Allah, Allah yaraya.... Zan kaiki ne?"

"A'a kayi zamanka zan hau napep" tafada ciki ciki saboda harga Allah haushin fahad takeji irin karshen nan,

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull