Kamar da wasa complete novel - Chapter 31
Kamar da wasa complete novel Chapter 31: Kamar da wasa complete novel Chapter 31. Jin motsin husnah a kitchen yasata cewa,
3,372 words
Jin motsin husnah a kitchen yasata cewa,
"Thank u my dear..."
"Adawo lafiya but kamar bakiyi breakfast ba..."
"Bana jin yunwa karka damu, idan naje office zan karasa gida"
"Adawo lafiya" yafada yana kara kwanciya, duk abinda sukeyi husnah na labe tana jinsu akofar kitchen, kwafa tayi da karfi amma shi fahad bai jiyoba Bilkisu ita kuma tafita, husnah ita kadai tasan abinda zata shirya musu saboda taga fahad yama rainata akan matarsa harda marinta? Wallahi saita rama ta wata hanyar. Kamar yadda ta fadawa fahad yau gidansu takarasa wuni sai da magriba takoma gida,daren ranar ma adakin husnah ya kwana washe gari kuma zai dawo dakinta, ranar da yadawo dakinta tunda safe garin kano yake daure da wani matsanancin zafi kowa kagani rike yake da abin fifita masu kankara da ruwan sanyi kuwa kasuwarsu ce tabude ranar saboda kowa abu mai sanyi yake bukata, karfe 3 tadawo daga office saboda yunwa gashi ita har gobe takasa sabawa da cin abinci a office sam bata iyawa, tuwon shinkafa ta tuka miyar busasshiyar kubewa da kifi, sannan ta tafasa magarya wannan dabi'artane tun tana gida abubuwan nan guda biyu duk lokacin da tagama period tana amfani dasu almiski da magarya saboda tasan yau zata samu tsarki, dama bata wuce kwana biyar ata dade tayi shida. Bayan magrib tasamu tsarki tana yin sallar magriba fahad yadawo daga filin kwallo wanka yayi ya dauki mattress yafita tsakar gida yayi shimfida saboda zafi, Bilkisu na daki bata fitoba tana dai jiyo yar hirar da sukeyi shida husnah tana cemasa ita karatun nan yafi wanda tayi da wahala saboda tulin sunayen magungunan da suke haddacewa sannan sai sun haddace class din da yake da group dinshi da dossage dinshi na manya da na yara, dariya taji yana yi yanace mata ai dama kowanne karatu akwai irin tashi wahalar domin shima hakan take yanzu wata wahala karatunsu ke zubawa saboda yakusa zuwa karshe, ita dai bilkisu tana jinsu ne kawai batada niyyar shiga shirginsu koda akusa dasu ma take bare tana nesa, tunani itama tafara yi da tunifa itama tazama nurse ko Dr dan har tasamu admission a school of nursing amma taki yi tace mass com takeso saboda shi take sha'awa tun tana karama.
K'arfe 9 saura taji su husna shiru da alama sun bar waje sun dawo ciki amma kuma ai yau fahad adakinta yake, bata kai ga gama tunaninta ba taji yar kara daga waje kuma da alama fahad ne ta zaci abin wasane sai tajiyoshi yana ta salati, atamanin ta sauka tafita daidai lokacin itama husnah tafito rikeda wayarta wadda ta kunna light,
"Kuyi ahankali kar ta harbeku.... Kunama ce..."
Husnah na haskawa kuwa sai ga kunama katuwa irin rikakkiyar nan baka kirin da ita, wata zabura husnah tayi saboda tsoro sai Bilkisu ce ta kashe kunamar cikin rawar jiki, fahad kam na kwance yadafe gefen kanshi inda kunamar ta harbeshi,
"Kira min ya Abba... Yazo muje asibiti"
"Wanne yazo ku tafi asibiti kawai ya siyo maka magani saboda kar abata lokaci...." Bilkisu tafada tana dangwala masa dan yatsanshi ajikin wayar, husnah ta mikawa bayan tayi dialling number din ya Abba, yana dagawa husnah tace zata turo sunayen magani yayi sauri yakawo yanzu kunama ce ta harbi fahad,
Dukansu arikice suke saboda wani irin nishi fahad yakeyi mai wahalar gaske duk yabi yahada gumi sai sannu suke yimasa amma baya iya amsawa. Lokacin da Abba yakawo maganin duk yagama jigata, cikin azama husnah ta karbi maganin dama harda allura tayi gaggawar yimasa sannan suka bashi maganin yasha, alama yayiwa Bilkisu da ta kaishi daki nan ta kamashi akan kafadarta suka shiga ciki kayan shimfidar tashi ma da yayi sai ya abbane yashigar musu dashi falo yatafi ita kuma husnah tabishi tarufe gidan. Sosai Bilkisu tayi nadamar kamo fahad bata bari ya Abba yakamashi ba saboda nauyin da taji yayi mata sosai dakyar ta iya kaishi dakinta suna zuwa bakin gado saboda layin da yaketa yi hajijiya na daukarsa akokarinta na kwantar dashi suka fada saman gadon tare yabita ya rufe, iya yinta tayi amma tagagara tureshi saboda nauyinshi har lokacin garin adaure yake sai dai akwai kamshin ruwa alamun anyi akusa da garin, jin gumin dake fita daga jikinsa tasan yana shan azaba cikin ikon Allah nefa suka kawo wuta nan sanyin iskar fanka tasoma ratsashi yadaina gumin, hannunta ta mika ta warware net din dake jikin gadonta pink colour nan hasken yaragu akansu, ita gaba daya mamaki ya rufeta saboda jin nauyin fahad gaba daya yasakar mata nauyi dakyar take numfashi. Baccine itama ya saceta ahaka, husna daketa kaiwa da kawowa tana dan labewa ko zataji motsinsu tun lokacin da suka shiga daki amma sai taji shiru har 12 takai tana zirga zirgar laben nan idan taji shiru sai taje ta kwanta da anjima sai tasake komawa daga karshe sai gajiya tayi ta kwanta tai bacci. Misalin karfe biyu nadare fahad yafarka, daidai lokacin ansau iska agarin sannan yayyafi yafara sauka amma bamai karfiba, juyawa yayi niyyar yi amma sai yajishi ajikin Bilkisu dafarko yazaci ma husnah ce amma yanayin kamshinsu da ya banbanta yasashi gane Bilkisu ce yana kwance dumu dumu akanta ta zagayeshi da hannuwanta ta rungumeshi tsantsan, yayi pillow da kirjinta, ahankali ya bude idonshi ya kalleta har lokacin kanshi yana dan ciwo kadan kadan,
"Ohh Allah inama yau akwana ana lafta ruwa...." Yafada ahankali kafin yarufe bakinsa ruwan ya dan fara karfi daidai lokacin kuma difff nepa suka dauke wuta, ahankali ya dan raba jikinsa da nata yana sinsinarta daidai lokacin ruwa yasake karfi kamar da bakin kwarya......
*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:22] Hafsat Rano: *Littafina na kudine me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
53****Yana fita wani wahalallen bacci yasake yin gaba da ita yau kam tasan haka zata wuni tana baccin nan saboda daren jiya kadan tayi,
Fahad kam yana fita yaga dakin husnah wallahi gaba daya ya manta da ita sai yanzu yatunata dan ko lokacin da yake cewa Bilkisu akira husnah ta dubata bawai dan husnan na cikin ranshi bane shifa idan yana tare da Bilkisu yakan manta kowa da komai,
Bedroom din husnah yashiga har lokacin tana kwance cikin bargo da wayarta ahannu tana chaten, zama yayi gefen gado yana kallonta,
"Wai ke bakya gajiya da chaten ne? Haba asma'u ga abubuwanan masu yawa wadanda zasu amfaneki...."
"Ya fahad yanzu fa na dauki wayar ina duba group din yan class dinmu ingani ko zamuyi lecture din...."
"A wannan ruwan? Tab"
"Allah ance fa za ayi, tashima zanyi infita"
"Allah yabada sa'a, zaki kira napep ko?"
"Uhmmm, ya jikinka? Yadaina zafi ko yanayi?"
"Da sauki yadaina tun lokacin da nayi bacci.... Yanzuma fita zanyi"
"Ina zaka ya fahad? Ya anty?"
Murmushi yayi,
"Ba nisa zanyiba antynki kuma ai tana daki..... Kina son ganinta ne?"
Ajiye wayarta tayi tana mika tareda yaye bargon da take lullube,
"Wacce ni? Uhm uhm idan mun hadu dai sai mu gaisa"
Mikewa yayi yana murmushi,
"Husnah kenan.... Bari naje sai nadawo"
"Adawo lafiya...."
Lokacin da yafita gidansu yafara zuwa kasancewar yau antashi da ruwa har baba yasamu agida bai fitaba sukuma iyayenshi mata suna soya fanke da miya, acikin flask aka zuba mishi yatafi dashi, chemist din dake makotaka da gidansu salim yaje yasiyawa Bilkisu maganin sannan yakira salim yafito, arumfar chemist din suka fake suna gaisawa, salim ya kalleshi cikin tsokana yace,
"Mijin hajiya kai kuma meye yafito dakai cikin ruwan nan....?"
"Kasan me iyali, hajjaju nazo saiwa magani..."
Dariya salim yayi,
"Gaskiya kai mijin tace ne, sai yadda akayi dakai, yanzu acikin ruwan nan aka aikoka..."
"Dallah tafi can kai baka san mata da miji ba, wani abinma idan kasha giyar soyayya ka bugu to basai ance kayiba zakayi.... Ni bari nawuce nasan tana can tana jirana"
"Idan andauke ruwa to zanzo"
"Ina? A'a banda yau, yau matata hutawa zatayi basai kazo ba"
Dariya salim yayi yace,
"Kai dai kasani, mijin hajiya kawai"
Dariya fahad yayi yakarasa gaban rubber rubber dinshi yana cewa,
"Naji dai, ai nafi gwauro wanda yake kwanan shago"
"Agaishesu...." Salim yafada lokacin da yake shiga cikin gidansu. Tunda fahad yafita bilkisu take kwance tana bacci cikin bacci taji fitsari kamar zatayi me dakyar ta lallaba ta tashi ta sauka daga kan gadon, hula ta dauka tasaka akanta tafita saboda dole saita nemo ruwan zafi kitchen tashiga ta dora a karamar tukunya mintuna biyu ya tafasa tajuye ta fito tana gwame kafafu daidai lokacin husnah tafito cikin shirinta na tafiya school, tsayawa tayi tana kallon bilkisu amma bata yimata magana ba tabata hanya tawuce itama Bilkisu batace mata uffanba tunda aganinta ita husnan ce yadace tafara yimata magana amma idan ita tayi mata magana ma babu mamaki ta disgata taki amsawa shiyasa ta shareta tawuce, da kallo husnah tabita,
"Ciwon kafa take yine? Ko kuma bata da lafiya to? Nashiga uku kardai cikine da ita? Wayyo ni...."
Da sanda tabi bayan bilkisu ta kuwa ci sa'a Bilkisu bata rufe kofa ba amma tadai karota, bata hango cikin gadonta sakamakon net din da yake sauke ya lullube gadon, ita kuwa Bilkisu lokacin ma tana bandaki tana gasa cinyoyinta zuwa kafafunta da ruwan zafi saboda lokacin da taje yin fitsari kasa tsugunnawa tayi sam saboda tsabar tsamin da cinyoyinta sukayi bata san lokacin da tafara kwalla ba, husnah nata sand'a har labulen ta dage tana leken cikin dakin daidai lokacin fahad yashigo kwata kwata bata ji karar shigowar machine dinsa ba, shi kuma da yaganta tana leka dakin Bilkisu sam bai kawo komai ba aransa,ji tayi yace,
"Asma'u lafiya...?"
Firgigit tayi tajuya tana kallonsa,
"Ya fahad uhmm....uhmm dama... Dama anty ce naga kamar bata jin dadi shine na leka inyi mata sannu kuma banji motsinta ba.... Inajin bathroom tashiga..."
"Ok, kije mai napep dinfa yana waje, kije zan fada mata"
Daga kai tayi tawuce zata tafi tana kallon ledar maganin dake hannunsa da flask din abincin da yake rike dashi,
"Fanke ne idan kina so..."
"A'a bana ci...."
Daga haka tawuce tana waiwayenshi shikam bai san tanayi ba saboda dakin bilkisu yashige harda rufe kofa ganin bata kan gado yasan tana cikin bathroom yana ajiye kayan hannunshi sai gata tafito tana takawa dakyar sai cije lips takeyi,
"Sannu....." Yafada ahankali, bata amsaba sai tukwicin harara da ta bashi,
"Kaida wa naji kuna magana?" Ta tambayeshi batare da ta kalleshi ba saboda yau tunda garin Allah yawaye sau daya kacal ta yadda suka hada ido,
"Nida husnah ne wai ta leko ta gaisheki kuma taga bakya nan..."
Jijjiga kai kawai bilkisu tayi batace komai ba amma ita tasan abinda husnah tafada karya takeyi tunda tagabanta tawuce amma bata ko daga kai ta kalleta ba, yarinyar nan ta lura yar sherri ce ta ajin karshe amma ita dai bata da lokacinta,
Wuceshi tayi yabita da kallo gaskiya bilkisu akwai saurin karaya da raki dan gaba daya jikinta awani sanyaye yake gashi sai tattale kafafuwa takeyi, ta cikin rigarta yagane bata saka komai ba sai iya rigar kadai saboda ga alama nan yagani na fulaninta sunyi cirko cirko suna kallonsa, gaban gado tawuce ta zauna yabiyo bayanta shima ya zauna kusa da ita,
Matsawa zatayi ya rikota,bata yarda ta kalleshi ba tajuya masa baya sosai,
"Kinyi brush....? Ga abinci ayiyah tace akawo miki"
"Nayi..." Tafada atakaice,
"Inkawo miki abincin?"
"Uhmmm" tasake amsawa atakaice, tashi yayi yaje ya dauko mata yakawo mata gabanta sannan yafita domin kawo mata ruwa, bude fanken tayi yasha miyar taushe wacce ta wadatu da gyada da tantakwashi nan tasoma ci hankali kwance, ruwa fahad yakawo mata ya zauna gefenta yana kallonta amma mafi yawan kallon a kirjinta yake duk tana ankare dashi aranta tana cewa fahad dai ko maye ne sai haka saboda ya sakawa kirjinta ido tun ba yauba tun zamansu na farko tasha kamashi yana satar kallon kirjinta amma a lokacin idan suka hada ido sai ya basar ya sunkuyar da kai ko yafara shafa keya, atakure tagama cin fanken kwata kwata ma kwaya uku taci ta dauki maganin ta balla tasha, mike kafafunta tayi saman gado taja bargo ta rufe kafafuwan nata zata kwanta da hanzarinsa ya matsa wai zai gyara mata pillow din da zata kwanta akai, babu zato tajishi ya dadimi abunda yajima yana tsole masa ido, runtse idanuwanta tayi tama kasa magana dan har lokacin hannunshi na wurin,
"Nidai kabari dan Allah.... Kabari mana...." Tafada idanuwanta arufe tana tureshi amma takasa dan bai bari dinba, kirjinshi ta buga da hannunta sannan ta tureshi ya matsa yana dariya, rasa irin kwanciyar da zatayi tayi saboda tasan kota fara bacci sai ya taba tunda tun jiya suke wannan fadan dashi dan haka kawai sai tayi rub da ciki, dariya taji yayi ahankali yace,
"Duk salon rowar ne haka hajjaju? Ba kyau fa rub da ciki, idanma saboda ni akayi to afasa ba sake tabawa zanyi ba"
Banza tayi dashi taja bargo ta lumshe idanuwanta,
"Kai yaron nan fitinanne ne na karshe wallahi..." Tafada cikin ranta bayan ta kawar da kanta gefe daya har lokacin a rub da ciki take. Shima fanken yaci yasha ruwa sannan yakoma kusa da ita, dariya yayi sannan ahankali yace,
"Ohhh su hajjaju labour angama zagaye zagaye dai daga karshe kuma andawo min dole dai nine nabude fadar...."
Dariya yayi ya kwanta akan gadon bayanta yana rera waka ahankali,
"Ko anaso ko ba aso nine nabudeta fadar...."
Cikeda bacci ta dago kanta tana tureshi daga bayanta, tashi yayi yana kallonta,
"Lafiya kake kokarin tashina da hayaniyarka bayan kasan bacci nake?"
"Ayya labour tayaki baccin fa zanyi... Nima Allah bacci nakeji..." Yafada cikin shagwaba yana wani lullumshe mata idanuwa, mayar da kanta tayi ta kwanta amma kuma sai yaga tayi saurin sake tashi sakamakon cire belt dinshi da taga yafara yi yana kokarin cire jeans din jikinshi,
"Menene haka?" Tafada tana kokarin boye tsoronta da yake kokarin bayyana,
"Karki damu trouser din zan cire saboda damuna zaiyi, bana son bacci da abu mai nauyi"
Batayi magana ba har saida taga yacire wandon ya jefashi can gefe daya ya kwanta daf da ita sannan tasake kwanciya a rub da ciki, turata yayi yafara kokarin juyata yana cewa,
"Wai ke wacce mummunar dabi'a kike Neman ki koya ne.... Babu kyau fa"
Ganin taki juyawa yasashi tashi ya dauketa cak ya juyata takoma rigingine tana kallon sama saurin saka hannayenta tayi ta harde kirjinta kwanciya yayi yana murmushi,
"Duk dai wayon amarya......"
Shiru tayi masa kamar bata jiba sannan taki bude idonta, bai sake magana ko motsiba saida ya fahimci tafara bacci sannan ya lallaba ya cire hannayen nata yamaye gurbinsu da kanshi ya kwantar awurin ahaka yayi bacci. Gaba dayansu bacci sukeyi haikam kasancewar jiya basuyi na kirki ba har lokacin sallar azahar yayi yawuce basu farka ba domin wani ruwan ake tafkawa, saida karfe 3 tayi sannan Bilkisu tabude idanuwanta ganin yanda fahad ya kanainaye kirjinta yasata tureshi aranta tana mitar nacinshi, ya takurawa kirjinta dan jaraba baccinma akai zaiyi? Bude idonshi yayi ya kalleta nan ta kawar da nata idanuwan bata bari sun hada ido ba,
"Ya zaki katse min baccina....?"
Shiru tayi masa ta yunkura ta tashi dakyar tana cije lips dinta duk da dai ciwon ba kamar na dazuba amma dai da akwai, hannunta yakama yana kallonta idanuwanshi narai narai,
"Ciwon yake yimiki har yanzu?"
Kai ta daga masa alamun ehh, tashi tayi shima yatashi yana cewa,
"Am sorry..."
Bata amsa masa ba tayi hanyar waje yana biye da ita kitchen tanufa saboda tasake dafa ruwan zafi saboda wanda ta dafa dazu duka ta yi amfani dashi, gas ta kunna zata dora ruwa yana tsaye abayanta yana kallonta, tukunyar ya karba ya debo mata ruwa yadora mata, suna tsaye ya tafasa ta sauke sannan ta dauki tea flask din tana dan buda kafa bin bayanta yayi da kallo sannan yabi bayanta da sauri yana cewa,
"Kawo inkai miki..." Sakar masa tayi ya dan kalleta sannan yace,
"Wai wannan gwamewar duk menene musabbabinta? Ko nine?"
Banza tayi masa tawuce suna zuwa falo yasha gabanta ya tsaya yana gyara short wandon dake jikinshi,
"Yanmata Magana fa nake yimiki...."
Ji tayi kamar ta makeshi kuma tafashe da kuka daure fuska tayi takawar da kai gefe,
"In dan taba dan Allah?" Harara ta watsa masa ta gefen ido ta kewayeshi zata wuce da hannu daya yadawo da ita yana yiwa kirjinta kallon rashin kunya har lokacin yana rikeda hannunta daidai lokacin husnah tabude kofa tashigo Bilkisu bata jira karasowarta ba tawuce tashiga daki,
"Sannu da zuwa husnah..."
Yafada ahanzarce sannan yabi bayan bilkisu zuwa cikin daki saboda ko sallar azahar basuyi ba gashi la'asar ta kusa, a kan pillow yasameta zaune saman gado abinma dariya yaso bashi amma yafuske, butar da ta fito da ita ta dauka tacika da tafasasshen ruwan zafin tawuce toilet saida ta dan jima aciki sannan tafito saboda saida ta sake gasa jikinta,
A bakin kofa taganshi tsaye yana jiranta, "kijira ni muyi tare", yafada cikin tsokana, bata jirashi ba tayi sallarta dan lokacin da yafito ma har takai raka'a ta biyu, tana idarwa tatashi ta kawo la'asar saboda lokaci yayi. Kan gado tasake komawa ta dauki pillow mai laushi ta ajiye wurin kafarta ta dora akai ta kwanta bayan ta saki net din dake jikin gadon, tasowa yayi yazo yayi knell down agaban gadon kusa da ita dan har tana jiyo numfashinsa,
"Da zaki yarda wallahi sai inyi miki wani taimako..."
Shiru tayi idanuwanta alumshe hannayenta rungume akan chest dinta,
"Yanzu ina yafi yimiki ciwo?"
Kafafuwanta ta nuna masa zuwa cinyarta batare da tayi maganaba sannan har lokacin idonta rufe suke,
"To tsaya in taimaka miki..."
Tashi yayi yaje ya tsiyayo ruwan zafi a flask yazo yazauna gefenta yazame hular kanta nan gashinta dake jike ya bazu tasa hannu ta sake maidashi baya, rigar tata ya dan ja zuwa sama nan santala santalan laps dinta suka bayyana sai shining suke, tun daga kan kafarta yake gasa mata har zuwa cinyarta babu karya kuwa taji dadi mutuka domin ciwon yaragu da kaso mai yawa, lokacin da yagama harta dan fara gyangyadi, tashi yayi yaje ya ajiye komai da yadauko sannan yadawo, shammatarta yayi kawai taji ya cakumo kirjinta tashi tayi cikeda masifa yayi saurin guduwa yana cewa, "Ai ba ayin aikin banza a kano nima na karbi ladan aikina..."
Batayi magana ba tajuya ta gyara kwanciyarta taja bargo, saida ya tabbatar da tayi bacci sannan yakoma kan gadon ya kwanta kusa da ita yana wasa da gashin kanta. Husnah kam yau acike take famm da fahad saboda bai taba yin hakaba gaba daya yau sun wani kule adaki shida Bilkisu sunki fitowa, to me suke nufi? Kitchen tashiga ta dafa farar taliya sannan tayi sos din kwai tafito duk ranta ajagule, zama tayi afalo taci abincin ta ganin har tagama bai fitoba yasata sadadawa taje ta dan labe amma tsitt kamar babu kowa acikin dakin, komawa falo tayi taci gaba da zama har magriba tayi sannan ta tashi taje tayi salla tasake fitowa lokacin suma su bilkisu sun tashi, tana kwance kan rug din salla da carbi ahannunta fahad na kusa da ita yana yimata maganar abinci, labewa husnah tayi tana saurarensu,
"Hajjaju me zakici to idan bazaki ci wannan fanken ba?"
Saida taja wasu sakwanni sannan tayi magana ahankali,
"Ni babu abinda zanci..."
"No, zakici wani abu gaskiya, zaki ci indomie?"
Daga masa kai tayi yatashi yafita, yana fita yaga husnah wacce babu zato taga yabude kofa yafito,
"Uhmmm ya fahad dama zuwa nayi in tasheku naga baku fitoba shine nace may be baku san lokacin salla yayiba....."
Fuskarsa babu yabo babu fallasa yace,
"Mun tashi, zo muje ki dafa min indomie...."
Hade rai tayi tajuya tana kunkuni,
"Tabdijam... Nice ma zan dafawa matarka abinci? Impossible wallahi bazai yuyu ba"
Jin abinda tafada yabashi mamaki,
"Husnah nikike fadawa haka ko? Wato bazan saki abu kiyi ba?"
"To ai naga bakai zaka ciba.... Matarka zaka kaiwa fa"
"To matar tawa ita kika yiwa bani kika yiwa ba? Zaki wuce muje kitchen ko sai nayi miki rashin mutunci"
Turje turje tafara yi tana buga kafa akasa ganin haka yasashi wucewa cikin kitchen din batare da yasake bi ta kanta ba, da kansa yadafa musu manyan indomie guda uku sannan yasoya kwai yajuye yanufi dakin Bilkisu tana kwance har lokacin tana tasbihi,
"Tashi kici abincin hajjaju..."
Yunkurawa tayi ta tashi ta dauki fork ta debo takai bakinta tafara taunawa kenan taji yace,
"Kanwarki ce ta dafa mik...."