Kenza eBookz

Kamar da wasa complete novel - Chapter 8

Kamar da wasa complete novel - Chapter 8

Kamar da wasa complete novel Chapter 8: Kamar da wasa complete novel Chapter 8. Saida ya cinye gyadar nan tsaf sannan yatashi yafita, yaci sa'a salim na…

3,300 words

Saida ya cinye gyadar nan tsaf sannan yatashi yafita, yaci sa'a salim na gida dan haka Babur dinsa yaje yakarba yanufi gidansu bilkisu duk da baida tabbacin ko tana nan, dawowarsu kenan daga kasuwa sun siyo furnitures tana kokarin rage kayan jikinta yakirata yace yana waje, ita wallahi bataso wannan zuwan nashi ba haka dai ta daure ta zura doguwar riga da hijabi tafita....

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:17] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA...!*💖

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*16*

*Littafin kamar da wasa na kudi ne yar uwa idan kinada bukata kibiya ki karanta.*

***Ba dan tanasoba haka ta fito ta sameshi yana compound din gidan tsaye jikin wata bishiya,

"Baby..."

Batare da ta kalleshi tace,

"Yakake?"

"Lafiya lau ranki yadade, ya mutanen gida?"

Atakaice ta amsa da,

"Lafiya"

"Am dama namanta ne ban fada miki wani abuba shine yanzu nazo sanar dake, mu a family dinmu idan anyi aure sai ankai amarya gidansu ango acan za aware mata daki har sai tayi tsawon kwanki bakwai ko wani abu mai kamada haka..."

"Wannan al'adar wanne garine kenan?" Ta tambaya batare data kalleshi ba,

"Fulanin kura..."

"So yanzu dai kana nufin gidanku za akaini acan zan zauna har na tsawon 1 week?"

"Ba lallai yakai hakaba dama kawai al'adace amma yana yuyuwa ma bazaifi 3 days ba ko 2"

Jijjiga kai tayi ta jingina jikin bishiyar flower tana kallon gefe,

"Babu damuwa..., ya maganar dinkuna ne wai? Naji shiru kuma tun ranar fa nayi maka maganar"

"Bani intafi dasu adaren nan zan yanka, abubuwane suka yimin yawa wallahi baby ko bakiga har nayi baki ba na fada...?"

"Bafa na son sunan nan nafada maka, so kadaina"

Murmushi yayi shi wlhi drama din da zasuyi da bilkisu kawai yake hangowa,

"Am sorry bazan sakeba amma seriously na dan rame fa"

"To ya za ayi ai situation ne"

Daga haka tawuce ciki ta dauko masa kayan da zai dinka mata takoma wurinsa,yana tsaye a inda tabarshi yana yin waya ganin tana jiranshi yakatse wayar yamaida hankalinsa gareta,

"Gashi duk riga da skirt zaka yimin..."

"Banda doguwar riga?"

"To Kaduba dai kagani idan akwai wanda zaiyi kyau da doguwar rigar sai kayi min"

"Shikenan to, kigaida su ammah"

"Zasuji"

Fita yayi yatafi ita kuma takoma ciki wurin khulsum wacce ke jiranta tayi wanka su fita gidan da za ayi mata gyaran jiki saboda yau za afara.

Cikin kwana biyu yagama dinkunan bilkisu kala takwas ne shadda guda biyu leshi guda biyu sai material da atamfa suma duk kala bibbiyu amma abinda yabashi mamaki duk cikin kayan babu na cikin lefenshi wanda yasaka amma bai kawo komai aranshi ba tunda watakila wannan din agidansu aka yimata, bai samu damar Kai mata kayan da kansa ba sai salim ne yakai saboda shi ranar yana can gidanshi ana saka masa tile da sauran abubuwan da ba akarasa ba, washe gari aka karasa komai na gidan akayi fenti gida yafito rangadau dama unguwar shiru take babu gidaje da yawa ma domin sabuwar unguwace bata fara yawaba, agajiye yakoma gida bayan sallar ishah wanka kawai yayi ya kwanta ko abinci bai nema ba babu bata lokaci baccin gajiya yace muje zuwa, koda Abba yashigo yaganshi baje yana bacci dariya yayi yace,

"Dole kayi bacci ango, irin wannan commitment Haka?"

Dasafe garau yatashi sakamakon baccin da yasha sosai adaren jiya, miss called din bilkisu yagani har guda uku hakan yabashi tabbacin akwai dalili shiyasa yayi gaggawar calling dinta back,

"Fahad dakuna nawane agidan, kofofi nawane sannan windows nawane? Muna wurin masu dinka cuttens ne"

"To hajjaju bari naturo miki gaba daya pics din gidan ki ganshi"

"Yawwa dan Allah hanzarta"

Katse wayar tayi nan yashiga whatsapp yatura mata aranshi yana cewa,

"Akwai rikici nasani"

Bai kara jin duriyarta ba sai text tamishi akan yabasu keys din gidan saboda masu zuwa jeren kaya gobe nanma aiken yayi mata aka kai musu, sai ana igobe kamu ta kirashi tana yimishi maganar itafa baza suje wata dinner ba walima kadai zatayi da friends dinta dan haka shima ya hada reception da friends dinshi kawai ya isa, tayi hakane saboda kunyar yaje dinner mutane su ganshi take,bai musa ba yace to.

Tana zaune tayi uban tagumi bayan mai kunshi tagama yarfa mata jan lalle da baki, khulsum tashigo agajiye itama daga kunshin take, zama tayi kusa da bilkisu wacce ke kallon masu shigowa da masu fita tayi tagumi,

"Wallahi fahad dinnan yayi yaro da yawa, Allah mai yadda yaso..."

Dariya khulsum tayi,

"Baiwar Allah ki rungumi kaddara kiyi hakuri, haka Allah yashirya ko jinjirine dai shine mijinki uban yayanki..."

"Tab.... Allah ya kiyaye, nifa wallahi baki ma san wani abuba, kunyar nunashi nake a matsayin mijina"

"Sai kiyi kuma malama, wai inasu maama?"

"Suna can gidanshi karasa jere"

"Gidanki dai, kyace wani gidanshi"

"Kinga malama ni idan kina tashi kitashi mutafi kitson nan idan kuma baki zuwa ki sanar dani"

"Ahh kinga karki fada min bak'a, shirya muje amma wallahi da retouching kikayi zaifi kitson nan, kinga kanki yanzu fa kullum sai yaji ruwa"

"Kanki akeji, ni tashi mutafi dan bamuda lokaci"

Hijabinta tasaka har kasa suka tafi bayan tayiwa ammah sallama iyallo sai jaraba take wai yakamata ta daina fita hakanan amma tunda tazo gidannan bataga ta yini agida batare da ta fita ba, batace komai ba tabi khulsum suka tafi,

"Shagon ma da babu wani nisa nan bayane fa amma shine iyallo sai tayiwa mutane ihu aka, kai Allah yakyauta"

"Ai keda iyallon nan taku kuna sani nishadi wallahi, gaskiya i have been missing my grandma"

Dariya bilkisu tayi,

"Uhm ai iyallo bata haduba sam wallahi, hajjaye kakarmu ta wurin uwa tafi kirki"

"Kya hadu da Abba wallahi"

"Bawani nahadu da abba ai gaskiyace"

Har sukaje shagon hirar iyallo suke yi. Kitso hadadde aka yarfawa bilkisu dan har la'asar lis suna shagon ita kuma khulsum akayi mata retouching, tun suna hanya taga su meenah nata kiranta, koda tashigo gida suma suna gidan ana yimusu kunshi har angama musu yanzu hindu ake yiwa itama ankusa gamawa,

"Wai wai wai... Gaskiya yakamata yaya fahad yaga wannan kitson da lallen" inji Hindu bayan bilkisu tacire hijab din kanta,

"To ke gaggawar me kike ko kin mantane nanda jibi suna jone ana..." Maama tafada cikin shakiyanci, tun kafin tarufe bakinta bilkisu takai mata duka ta gudu,

"Allah adda labour idan ya fahad yaga kunshin nan da kitson nan zaucewa kawaine bazai yiba" meenah itama ta karbi zancen,

"Wai dama haka kuke bakuda kunya?" Khulsum tafada tana rike haba,

"A'a wallahi Anty khulsum ai kin san Adda labour kakarmu ce fa dole mu rinka janta" inji meenah,

"Adda mai gado ki fada masa angama komai yatura wadanda zasu jire gidan saboda anjima suma su yafendon zasu taho"

Bata tanka ba takarasa shiga cikin daki wanda yanzu kayan ciki suka zama sai saura domin duk su maama sun shirge mata kayanta sunyi mata gaba dashi sai wanda zata nema kawai aka bari, zama tayi gefen gadonta tana kallon tv domin wani Indian film ake haskawa atashar MBC Bollywood mai suna a gentleman, wayar fahad takira ringing biyu yadauka,

"Ranki yadade..."

"Am yawwa kaga angama jeren nanne shine zan fada maka katura wasu sai su kwana agidan"

"Angama ranki yadade"

Katse wayar tayi tamike tafita waje wurinsu khulsum. Kamar yadda yafada da daddare su salim da Abba ya tura domin su kwana agidan,lokacin da zasu tafi jan salim yayi yace masa,

"Allah karku kwanta mana agado kasan dai babu kyau..."

Dariya salim yayi yakai masa duka,

"Allah ko fitsararre? To ai ya Abba yadace ka fadawa tunda shine babba amma baniba"

"Shi ai nasan bazaiyi hakaba sai kai...."

"To kuwa kwana bisa gadonku daram..."

"Wallahi karka kuskura..."

"Sai kayi kuma...."

Daga haka yayi gaba abinshi, fahad kam neman wuri yayi ya zauna nan kofar gida domin cikin gidan cike yake da mata yan uwa da abokan arziki, saida yakira bilkisu yasanar da ita yatura wadanda zasu yi gadin gidan sannan hankalinta ya kwanta.

Washe gari da shirye shirye aka tashi kasancewar ranar za ayi kamu, kuma anan compound din gidan za ayi kamun domin ita bata da ra'ayin zuwa hall, kowa kagani acikin hidima yake fuskarsa dauke da farin ciki ba ma kamar ya mahaifiyarta ammah wacce ke jin kamar ancire mata k'aya, yanzu kam tasan zasu huta da wadannan maganganun da habaice habaicen da ake yimusu acikin dangi, mutane sukan manta da cewa Allah shine gwani wurin iya tsara komai na rayuwar bayinsa kuma duk yanda ya tsara to hakance zata faru ko anaso ko ba aso, ko anshirya ko ba ashirya ba. Su meenah dai ana can wurin masu decoration ana nuna musu muhallin da yadace asaka kowacce kwalliya domin gudun kuskure, amarya fa? Ana can daki tareda bakinta wadanda suka zazzo daga sassa daban daban na jihar Kano musamman ma wadanda sukayi secondary school tare da wadanda sukayi Jami'a shiyasa itama yau tasamu nasarar warewa ta cika da farin ciki saboda ganin wadanda tajima bata ganiba amma da har masifa tayiwa khulsum lokacin da ta turawa class mates dinsu invitation card ta group chat dinsu dake Facebook da whatsapp tana cemusu ga labour prefect dinsu fa zatayi aure dan haka su daura damarar zuwa shan shagali, ai kuwa sunyi mata kara domin kusan duk wadanda ke zaune acikin kano sunzo,anyi bushasha babu laifi domin chicken pepe da lafiyayyar fried rice aka dafo aka kawowa friends din nasu wanda wannan yana daya daga cikin gudunmawar khulsum banda kayan sanyaya makoshi cikin manya manyan kuloli, ba karamin kyau amarya tayiba tun kafin tayi shirin zuwa wurin kamu, karfe uku tayi wanka da ruwan lalle da turare, tana yin sallar la'asar kuma mai kwalliya tafara aikinta, wanda suka dauki tsawon lokaci sunayi,

"Masha Allah...masha Allah" shine abinda kowa ke fadi lokacin da amarya tafito domin ba karamin kyau tayi ba, tayi kyau na bugawa ajarida, komai na jikinta golden colour ne kama tun daga material din jikinta wanda akayi kyakkyawar doguwar riga irinta amare zuwa head din dake nade akanta da takalminta,pose da komai da amarya ke sakawa har sarka da dan kunne, kidanta daban aka saka mata lokacin da ta karasa wurin khulsum na rike da hannunta, fuskarta abude take amma da akwai wani net me kyau akanta, kujerar da aka tanada musamman dominta taje ta zauna babu bata lokaci aka fara gudanar da abinda yadace daidai lokacin dangin ango suka karaso nan aka tarbesu aka basu wurin zama suka zazzauna. Babu karya kamun yayi kyau domin babu tarkacen shirme aciki kawai dan abinda ba arasa ba aka gudanar daga nan su iyallo suka zo suka sakawa amarya lalle lokacin magriba takusa, dangin ango basu tafiba saida aka gama komai, suka daddauki pics da amarya da danginta sannan suka tafi bayan anware musu manyan jakunkunan da aka rarraba awurin. Ango kuwa yana can gidansu salim adakinsu amma yana ganin duk abinda yake faruwa awurin kamun domin yatura mutane biyu daya zaiyi video coverage dayan kuma zai rinka turo masa ta whatsapp, hakance kuwa tafaru domin komai kamar akan idonsa akeyi....

*_Ummi Shatu_*👌🏻 [11/28, 08:17] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO*

*KAMAR DA WASA...!*💖

*_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

*18*

***Tunda fahad yakwanta bacci bai ko juya ba sai da asubah, tashi yayi yaje yayi alwala yafito yafita masallaci tareda baba suka shigo gidan lokacin harsu mamuh sun fito suna kokarin hada wuta, dakin yakoma bayan sun gaggaisa dasu,har lokacin bilkisu na kwance ta tukunkune acikin mayafi tanata sharar bacci, tashinta yafara yi tatashi tayi salla amma taki tashi dole sai kyaleta yayi ya janyo wayarshi wadda ke jikin sucket tana charge yasoma matsata. Sai karfe shida saura sannan ta farka, akwatinta ta janyo ta bude taciro soson wanka da sabulu sai brush da toothpaste tajiyo ta kalleshi yayi saurin dauke idonshi yamayar kan wayarshi,

"Malam dan bani wuri zanyi wanka..."

Kamar bazai tashiba zuwa can dai yamike da wayarshi ahannu yayi waje, saida ta tabbatar da ficewar yayi sannan ta kwashi duk abubuwan da zata bukata tashiga bathroom, harta fito tashirya tsaf tasaka wata pink din shadda riga da skirt bai shigoba, turarukanta na alfarma da sanyaya zuciya ta dauka ta shafe jikinta dashi sannan taciro mayafi ta zauna mayan ta maida akwatinta mazauninshi, handbag dinta ta bude ta ciro chingum ta saka abakinta ta dauko wayarta ta kunna. Bata dade da kunnawa ba kiran maama yashigo suka gaisa daga nan su Hindu suma suka kakkarba suka gaggaisa, bayan sun gama wayar dasu meenah saiga kiran khulsum,

"Amarya bakya laifi... Amarya kinsha kamshi"

Murmushi bilkisu tayi,

"Zan ramane wallahi, Allah yakaimu lokacin"

"Au danma na kiraki naji ya kika kwana?"

Kafin tabata amsa fahad yashigo direct bathroom yawuce tabishi da kallo,

"Ni lafiya lau natashi malama"

"Shikenan haka akeso ya angon namu?"

"Lallai kam, yana nan lafiya"

"To agaidashi ace sako injini nace ya kular min da kawata"

"Wannan sakon yafi karfina sai dai idan kun hadu ki fada masa da bakinki"

Khulsum nata tsokanarta tana ramawa daga karshe dai sukayi sallama takashe wayar, haka kawai sai kuma tunanin gida yafado mata nan taji kamar tafashe da kuka, Allah sarki rayuwa yanzu idan banda aure me zai rabata da gidansu, dakinta ne yafado mata arai da gadon da take kwanciya da komai nata dake cikin dakin, kiran da yashigo wayar tatane yakatse mata tunanin da takeyi, goggo maigado ce kanwar mahaifiyar Abba wacce aka yimata takwara da bilkisu, dauka tayi cikeda farin ciki domin goggo bilki halinta daban yake tafi iyallo kula da faran faran,

Har yafito daga wankan waya takeyi, tagaisa da wancan ta gaisa da wancan, kayanshi ya dauka yakoma toilet zuwa can yafito yana rataye kayan da ya cire saman kofar toilet din, cumb yadauka yagyara sumarsa sannan yajuya yana kallonta lokacin da yake kokarin shafa turaren amirul hub, ido suka hada ta wani janye nata cikeda sigar harara yana jinta lokacin da tagama wayar,

Zama yazo yayi gefen katifar domin saka sabuwar bakar safar dake hannunshi,

"Hajjaju kin tashi lafiya?"

"Alhamdulillah..."

"Ya bakunta?"

"Lafiya"

Murmushi yayi ya kalleta,

"Bari naje nakarbo miki breakfast anjima sai na rakaki kishiga cikin gidan ku gaisa dasu"

Jijjiga kai kawai tayi amma bata yi magana ba hakan yabashi damar mikewa yafita, yana shiga cikin gidan masu tsokanarshi suka fara suna fadin,

"Ga ango ga ango..."

Su Mariya kuwa rugowa sukayi suka rirrike hannunshi,

"Ya fahad muje mugaida Anty yanzu?"

"A'a Mariya ba yanzu ba, yanzu hutawa take zan kai mata abinci taci idan tagama zata shigo ku ganta"

Dakin ayiyah ya furmutsa yashiga duk da dakin tafare yake da baki amma haka ya tsattsallakesu ya isa gareta, cikeda farin ciki ta amsa gaisuwarsa sannan tace yaje yasamu yaya asabe yakarbi abincin karin kumallon bilkisu, fita yayi bai tsaya jin dan bikin da abokan wasa keyi masa ba wadanda ke cikin dakin, wurinsu anty fauzy yaje suna zazzaune kofar kitchen suna dama kunun farar shinkafa can gefe daya kuma masu suyar fanke nayi ga kosai shima anata sakawa,

"Ah kaga shalelen ayiyah ango..."

Dariya yayi yaduka agabansu yana cewa,

"Kai yaya asabe bari kiran angon nan dan Allah"

"To ya kwanan amarya?"

"Tana nan lafiya, yanzu ma abincin ta nazo karba"

"Dakyau ango mijin amarya..."

Mikewa yayi tsaye yana kallon anty Fauzy wacce rufe bakinta kenan,

"Anty fauziyya kema haka zakice? Shikenan bani abincin natafi"

"Za abaka ai daina gaggauta, da alama gaba daya hankalinka na can..." Anty juwairiyya dake cikin kitchen itada anty kubra tafada tana dariya, shi sam baima gansu ba wallahi sai yanzu ashe suna ciki suna hadawa amarya breakfast,

"Ohh God....,ashe yan sa ido ana ciki..."

"Mudai ga abincin amaryarka sai ka sakar mana Mara muyi fitsari" Anty kubra tafada lokacin da take fiffito masa da abincin, kayan sunyi masa yawa dole sai su mariya yakira suka tayashi dauka domin bazai yuyu yadauka shi kadai ba, har cikin dakin suka kai masa abin mamaki sai yaga bilkisu ta sake dasu sosai harda cemusu su zauna suci abincin tare, harara ya zabga musu babu shiri suka fice simi simi, tabe baki tayi tagyara kishingidar da tayi, shi wallahi wannan mulkin nata dariya yake bashi, abubuwan da aka girka yafara dubawa, chips ne aka yimasa wani hadi na musamman da dan salad sai farfesun kayan cikin saniya sai bread da ruwan zafi,

"Ranki yadade ga abincin... Bismillah"

"Ok..."

A flate daya ya zuba musu komai yasa fork yafara ci, wayarshi ce ta katse masa hanzari, husnah ce bai san lokacin da ya girgiza kai ba yace,

"Allah sarki husnah bakiyi fushi ba?"

"A'a prince banyiba, angama biki lafiya? Allah sanya alkhairi yabada zaman lafiya agaida min da ita"

Jin abinda husna tace sai tausayinta yasake kamashi bai san da biyu ta kirashi ba dan saida kawayenta suka tirsasata sukace tayi masa kirsa irinta mata ta nuna bata dauki auren da yayi da zafiba karta nuna masa komai amma da zarar burinta yacika ta nuna musu tafisu iya wulakanci, wannan dalilinne yasata dannar zuciyarta ta kirashi amma fa can kasan ranta kishine fal dankare da tsanar bilkisu wadda bata ma san da ita ba,

"Amin husnah nagode sosai..."

"Babu komai Prince ai kafi haka agareni"

Ita dai bilkisu kallonshi ta tsaya tanayi yayinda shikuma keta yiwa husna godiya, cin abincin shi yaci gaba dayi zuwa can wayarshi tasake yin kara ya dauka yana dariya bayan yasaka a hands free,

"Kai gwauro ya akayi...?" Yafada yana dariyar shakiyanci, daga can bangaren salim yace,

"Malam wallahi yau kasan wanda zaiyi maka gadin gidanka nidai nagaji tahowa zanyi"

"Karka damu yau masu gidanne zasu kwana aciki, insha Allah yau anan zamu kwana kai kuma kaje ka karata da tsohuwar katifarka..."

"Ohh hakama zakace? To babu komai ai akwai gaba..."

"Wasa nake abokina... Yanzu kadan bada jimawa ba za akawo muku breakfast kaida babban yaya, dan Allah amika min gaisuwa"

Kit yakashe wayar yana yiwa salim dariyar shakiyanci, ita kallonshi ma kawai ta tsaya tana yi tana mamakin yanda yake da bakin tsiya,

"Hajjaju ya akayi ne? Nace kizo kici abinci kin ki ban saniba ko kina jin nauyina ne, amma ai ko za ayi fulako bai cancanta ayiwa mijiba domin shi sirrinka ne...."

Wani kallo tayi masa wanda ita kadai tasan ma'anarsa,

"Miji...? Miji kuma?"

Tsayawa yayi da cin abincin da yakeyi ya kalleta,

"Ina da wani sunanne da wuce wannan awurinki? Duniya da sauran jama'ar cikinta sun gama shaidawa ni fahad mijinki ne asalima harda sadaki na baki naira dubu talatin lakadan ba ajalan ba right....?"

"To ko in dawo maka da abinka?"

Girgiza kanshi yayi ya langabe kai yaci gaba da cin abincinshi,

"A'a, ni ai ban baki dan kisake dawo min dashi ba ranki yadade..."

Shiru tayi taci gaba da danne dannen wayar da takeyi tun dazu, zuwa can yasake kallonta yace,

"Kefa nake jira ki karya mu fita, dagaske yau zamu bar gidan nan mukoma namu..."

Tsam ta tsaya da abinda takeyi itama takai kallonta gareshi,

"To yanzu idan nashiga ciki me zanyi? Kasan dai ni ba sanin al'adarku nayi ba..."

"Karki damu zaki sani sannu ahankali"

"Dan rainin wayo...." Tafada acikin ranta sannan ta ajiye wayar hannunta ta janye flate din gabanshi zuwa gabanta ta dauki fork tasoma ci, kallonta yatsaya yi kafin ya nisa,

"Ranki yadade ai ba koshi nayiba..."

"Duk abincin da kaci daga daren jiya zuwa yanzu?"

"To ai na kwana biyu rabona da abinci fa"

Kafada ta daga,baiyi kasa agwiwa ba yasake mayar da nasa cokalin cikin flate din yaci gaba da ci atakaice dai shi yaci fiyeda rabin abincin, yarigata tashi dan haka yasake kintsawa sosai yasha hula sai kamshi yake, abokanshi sai kiranshi sukeyi awaya ana tayashi murna da fatan alkhairi, hannayensa duka biyu ya zuba cikin aljihun rigarshi yana zagaye dakin yana jiranta tagama, saida tagama jan ajinta da shan kamshinta sannan ta mike bayan tasake gyara fuskarta sosai,turare tasake fesawa jikinta sannan ta dauki babban mayafi tayafa tarufe fuskarta, dariya yafarayi ahankali wayarta kawai ta dauka amma yace mata,

"Da dai kin dauki handbag din naki da zaifi..."

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull