Kenza eBookz

Kanwar matata complete - Chapter 8

Kanwar matata complete - Chapter 8

Kanwar matata complete Chapter 8: Kanwar matata complete Chapter 8. Sai da ya isa k'ofar gidan sannan ya d'auko wayarsa dake gefensa ya lalubo number Sarah…

4,278 words

Sai da ya isa k'ofar gidan sannan ya d'auko wayarsa dake gefensa ya lalubo number Sarah da yayi saving da *_My endless bliss_* yayi dialing, ringing uku ya amsa kiran tare da fad'in, "Hello, Assalamu alaikum." Tab'e baki yayi kamar tana kallonsa tare da amsawa da, "Hi, wa'alaikissalam." Da sauri Sarah ta cire wayar daga kunne tana k'arewa special number d'insa kallo wanda ya k'are da 3 guda shidda a k'arshe. Turo baki tayi don sarai ta gane muryansa, gashi kuma tana tsoran yanke kiran don bata manta da deal d'in su na d'azu ba. "Wake magana!" "Bugun zuciyarki!" Kai tsaye ya bata amsa yana mai sakin murmushi. Sarah kuwa yana fad'in hakan zuciyar nata ta soma bugawa. Shuru tayi bata k'ara cewa komai ba. Sun d'au lokaci har na tsawon mintuna biyar babu wanda ya sake yin magana. _Khalil_ ya ciro wayar daga kunne, kamar yanda itama Sarah ta fiddo nata domin ganin is he still their. Sai taga yana reading kamar yanda shima ya gani daga can, mayar da wayar yayi kan kunnansa tare da fad'in, "Tun ba'a je ko ina ba, har kin fara karya dokar ko?" K'ara turo baki Sarah tayi daga can tare da fad'in, "To ni ai kai ne baka yi magana ba, kuma ni ban san mai zan ce ba." Gyara zama yayi cikin motar tare da fad'in, "Ki fito ina waje." Waro idanu Sarah tayi tare da fad'in, "Waje kuma? Ni dai......." Sai kuma tayi shuru bata k'arisa ba. "K'arisa maganarki mana, ke dai baza ki fito ba ko?" Kwanciya tayi rigingine tare da fad'in, "Ni dai Allahna yana sama yana kallo ba haka nayi niyyar cewa ba." D'age gira yayi kamar tana kallonsa tare da fad'in, "Au Allah d'in naki ne ke d'aya mai son kai. To idan ba tsoro ba ki fad'i abunda kika yi niyyar fad'i daga farko mana." Sai da ta juya idanuta sannan tace, "Ni dai so nake in ce maka, ni dai gaskiya.... Gaskiya, ummm-ummm...." Dariya ya saki tare da fad'in, "Kin ga k'aryar ma ta kasa fitowa. To bari na juya kawai kin ga kenan deal d'in mu ya rushe." Waro idanu Sarah tayi tare da mik'ewa da sauri tana fad'in, "Wallahi a'a, wallahi ni dai a'a ba haka nake nufi ba. Gani nan zuwa yanzu." Sosai ya saki dariyarsa tare da fad'in, "Matsoraciya, ana so ana kaiwa kasuwa." "To mai ake so d'in." Ta tambaya tana hararar wayar. " _Khalilullah_ mana." "Khalilo." Ta fad'i cikin zuciya har da Allah ya kiyaye. Bata san cewar a zahiri tayi maganar ba sai da taji yace, "Ni ne _Khalilo_ d'in?" "Na shiga uku na!" Ta fad'i jin ashe a bayyane tayi maganar. "Ki fito maman twins kar ki b'ata min lokacina." "Mene? Ni wallahi ba maman Twins bane. D'aya kawai zan haifa maka. Shima don babu yarda zanyi ne. Ai don dai zubar da ciki haramun ne, kuma tamkar kisan kai mutun yayi, da zubarwa zanyi wallahi." Fad'in Sarah. "Don Allah ki gwada! Da na baki tsan-tsan mamaki don kin san Allah sai na kuma yi maki real ciki kin haihu." Kuka Sarah ta saka tare da fad'in, "Kuma ba zan fito d'in ba. Mugu kawai!" "Dan Allah ban rok'eki ba, kar ki fito d'in cikin mintuna biyu rak." Yana gama fad'in haka ya katse wayar. "Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wannan wani irin jaraba ce haka? Ga duka ga tsinke jaka." Fad'in Sarah tare da share guntun hawayen da suka zubo mata ta nufi wardrobe ta d'auki Vail madaidaici ta yafa a kan riga da skirt d'in jikinta wanda ya amshi k'irar jikinta cif-cif. Babu ko hoda a fuska sai wani d'aure fuska take yi tare da fita waje ba tare da ta kalli y'an uwanta dake tsakar gidan ba. Babu mai shigar arziki a cikinsu. Marfu'a ma shayar da y'arta Fadwa take yi y'ar shekara d'aya da wata biyu. Ko kasheta za ayi baza ta iya nuna uban y'ar ba saboda yawan samarinta. Ga y'ar fara tas kyakkyawa kamar mahaifiyarta. Don duka Y'ay'an Lami kyawawa ne, duk da Lamin ita ma ba laifi tana da kyau, Sai dai ita bak'a ce, hasken Baba suka yo da kamannin fuskansa shiyasa gaba d'aya suke kama da juna sai dai wancen tafi wancen dogon hanci, ko kuma k'irar jiki. Wata kuma dimple gareta, wata kuma wushirya. Masu dimple d'in sune, Sarah, Na'ima da Hassana, masu wushirya kuma, Aina'u, Nuratu da Marfu'a, Lukman ne kawai ya d'auko Lami kaf, kamanni da hasken fata. Sai Aina'u da itama ba fara bace sosai kamar sauran y'an uwanta. Kuma ita tana da d'an jiki irin na mahaifiyarsu. Da kallo suka bi Sarah dukkan su, kuma babu wanda ya tambayeta ina zata je. Tura k'ofar gida tayi tare da fita ta coge a k'ofar gidan tana k'arewa motar da yake ciki kallo ta gefen ido tana mamaki shi motoci har nawa gare shi haka. Shima kuwa ta cikin tinted glass window d'in yake k'are ma halittar jikinta kallo yana mai jin wani irin matsanaicin kishi na taso mata. Domin gyalen dai bai da maraba da babu don babu abunda ya b'oye a jikinta. Ga shape d'inta da ya fito kamar zanata aka yi. Hannu ya kai ya d'auki glasses d'insa ya mak'ala a idanunsa tare da bud'e motar ya fito, luckily sai ga wasu almajirai su biyar zasu wuce, da hannu ya yafito tare da bud'e boat ya nuna masu abunda zasu kwashe su kai gidansu Sarah. Sarah na ganin uban kayan da ake fitowa dasu a cikin boat, back seat da kuma front seat ta bud'e ido tana mamaki don kamar za'a bud'e shago. Sai da aka gama kwashe kayan tsaf ya sallamesu sannan ya nufi wajenta don tuni ta bawa almajiran nan waje ta koma gefe. Fuskan nan b'utu-b'utu ya kalleta tare da zare glasses d'in fuskansa. Lokacin da Sarah ta d'ago ta saka idanunta cikin nasa, sai da gabanta ya fad'i ganin yanda launin idanunsa suka canza, duk lokacin da ta kalli idanunsa a wannan yanayin, tuno mata da ranar da aka samu cikin jikinta yake yi. "Ke har yanzu baki yi hankali ba ko Sarah!" Duk lokacin da ya furta sunanta, sai taji duk duniya babu wanda ya iya kira kamarsa. "To ni kuma mai nayi yanzu?" Ta fad'i tana mai turo baki. Ko kamun yayi wata magana, Lami ta turo k'ofar gidan tare da fad'in, "Sannu-sannu! Sannu da k'ok'ari yaron arziki! Wannan irin uban kaya haka? Kai an gode sosai. Ai irin ku ake so masu hannu a bud'e. Allah yayi maka albarka." Fad'in Lami tana washe baki. Sarah kuwa ji tayi kamar ta kwalla ihu tsabar takaici. Don Lami ta riga ta gama zubar mata da mutunci. Shi kuwa _Khalilullah_ ko kallonta bai yi, sai cewa kawai yayi, "Ameen." Yana kallon fuskan Sarah da ta gama b'ata masa rai. Juyawa Lami tayi ta koma ciki. Sarah kuwa sunkuyar da kai tayi tana jin hawaye na taruwa a idanunta. "Kar ki yarda wannan hawayen su zubo _Mine_, kar ki yarda su zubo don idan suka zubo nayi maki alk'awari sai na lashe su tsaf kuma a titin nan." Da kyar Sarah ta iya maida hawayenta suka koma, don ta san tabbas duk abunda _Khalil_ ya fad'a zai iya yin fiye da haka tun da dai yanzu haka cikinsa ne a jikinta. "Dan Allah kayi hak'uri da halin mahaifiyata." Mai makon yayi sharhi akan maganar da tayi, sai cewa yayi, "Sarah idan kina son zaman lafiya dani, kuma kina gudun abunda zai je ya dawo, to kar in kuma ganinki da irin d'an iskan gyalen nan. Wai ke baki san ba irinku bane suke saka gyale ba? Wallahi yawancin mata ku kuke ja ana yi maku fyad'e. Kin san cewa Allah yayi ku ma Sha Allah ta yanda ba kowani namiji zai iya had'iye miyansa akan ku ba, amma sai ku rik'a fitar da surar jikinku. Wasun ku ma har k'ari suke yi don kawai su burge samarin. To ni wallahi ban so, kuma ban so na sake ganin irin haka. Ki kiyaye ni _Mine_. "Wai wani _Mine_ sabida kinibibi. Ko ta ina na zama na shi oho!" Fad'in Sarah amma a zahiri sai cewa tayi, "Zan kiyaye daga yau in Sha Allah!" Politely ta fad'i maganar. Shi kuma _Khalil_ yace, "That's very good. Allah ya baki iko. Yanzu menene kike buk'ata?" "Turaren jikinka." Ta fad'i a cikin zuciya saboda yanda k'amshin yake fizgarta, don na yau ma yafi mata dad'i akan wanda ya saba sakawa. Amma a zahiri sai cewa tayi, "Babu komai. Ni babu abunda nake buk'ata. Abunda ka kawo yau ma yayi yawa." Harararta yayi tare da fad'in, "To ke na kawo mawa? Ni su Baba da mama da y'an uwanki da kuma babyna dake cikinki na kawo mawa. Akwai chocolate, wannan duka naki ne, au na baby na. D'an kai hannu cikinki ki fad'awa babyna daddynsa na gaishe sa." Ko kallonsa bata yi ba, balle tayi abunda yace, kuma dama shima ya san ba yi za tayi ba. Yana kallonta sosai, bini-bini zata shak'i iska ta lumshe idanu, ya karanci psychology, hakan ya fahimtar dashi abunda Sarah take shak'a. Murmushi yayi tare da fad'in, " _Mine_ akwai abunda kike so amma jik'imarki ta hana ki bud'e baki ki fad'a min ko?" Bud'e idanunta tayi a kansa tare da fad'in, "Ni babu abunda nake so. Kawai zuciyarka ce ta fad'a maka gaibu." Kallonta yayi na second hud'u sannan yace, "Ki rantse da girman Allah turaren jikina baya fizgar hankalinki har yake saka ki lumshe idanu." Mamaki ne ya kashe Sarah ganin ya d'ago jirginta. Sai ta diririce ta rasa mai zata ce sai kawai tayi shuru tana kallon k'asa. Komawa mota yayi, mintuna biyu sai gashi ya dawo da kwalin turaren *_Imperial Majesty_*, bakinsa kuma yana taunar masoyin nasa _Mastika gum_. "Wai kai baka gajiya da cin chewing gum ne?" Fad'in Sarah wacce bata ma san lokacin da tayi masa wannan tambayar ba. "Kin tuna wancen ranar haka kika ce min mai d'abi'u _KARUWAAA_?" Sai da ya,ja waa d'in yana dariya. Rufe fuska da hannunta Sarah tayi tare da fad'in, "To ai kai d'in ne ka cika cin chewing gum." "Shikenan kuma duk mai cin chewing gum ya zama karuwa ko? To ai gashi kin tunzurani kin saka nayi maki halin karuwan har gaki da tsaraba." Da gudu Sarah ta juya zata gudu ya rik'e hannunta tare da saka mata kwalin turaren a hannunta sannan yace "A sauka lafiya, a kuma gaishe min da Baba." Yana gama fad'in haka ya sakar mata hannu ita kuma ta shige cikin gida da sauri. Da gudu Lami ta rungumeta tare da zabga gud'ar da ya karad'e gidan, hatta Baba dake d'aki sai da ya toshe kunne yana fad'in, "A'uzu billahi minash shaid'anir rajim!" Lami kuwa sai ta hau yiwa Sarah kirari, "Yarinyar mai goshin arziki, yarinya mai k'irar matan manya! Gabanki fari bayanki fari k'al, d'awisu duk inda kika gitta sai an kalleki. Wuhuhuuuu ina gwanin wani ga nawa gwanar. Ni na san banyi asarar haihuwa ba wallahi. Kai jama'aa." Tana fad'in haka sai ta hau rawa da wak'a irin na matan zumunta, sai dai bata kiran sunan yesu almasihu sabida kar Y'ay'an su b'aro jirginta don duk da basu sallah, sai sun ga dama, baza suji dad'i ba idan suka fahimci ta koma addinin kiristanci wanda take ganin shine addinin gaskiya a gareta. Sarah kuwa sarai ta faminceta, a zuciyarta sai addu'ar shiriya take nemawa mahaifiyar tasu akan ta gane gaskiya ta natsu. Aina'u kuwa wani dogon tsaki tayi tare da fad'in, "A dai yi mu gani idan tusa zata hura wuta." A cikin zuciyarta. Sarah kuwa kaucewa tayi ta shige d'akinsu ta kwanta a kan gado tana tuno ranar data fara ganin _Ibarahim Khalilullah_ a rayuwarta. Tun da ta taso k'awa d'aya tal tilo take dashi a rayuwa, Muniba. Muniba na d'aya daga cikin mutanan da suka d'aura ta a kan hanyar madaidaiciya domin if not because of her she would have joined her siblings. Amma kasancewar Muniba ta taso gidan mutunci da tarbiya, don babanta shine limamin masallacin _Mai duguri road_, kuma an d'aura su akan ingantacciyar tarbiya. Makarantar bokonsu d'aya tun daga primary five har suka kammala secondary school, Muniba tayi k'ok'ari sosai wajen saita Sarah a kan hanya madaidaiciya, don farko itama ta soma d'auko rawan kai da y'an gidan. Irin su shigar banza, zagin d'an Adam duk tsufansa, rashin kunya da saurarsu. Muniba ita tayiwa Sarah registration na islamiyar da take zuwa *_MADARASATUL TATBIQUT TA'ALLIMUL ISLAMIYA_*, kuma makaranta ce da ba'a wasa ko kad'an. Kuma da ikon ubangiji sai da Sarah tayi sauka sai dai bata samu damar cigaba ba kamar yanda Muniba ta cigaba. Baba Nuhu sosai yaji dad'in haka, don ko a wancen lokacin, Sarah ita mai k'aunar mahaifinta, kuma tana jin maganarsa sab'anin Lami. Don ita b'ata tab'a sha'awar karuwanci ba kamar yanda sauran y'an uwanta suke yi. Burinta shine tayi aure ta zauna a d'akinta k'ark'ashin kulawar miji. Sai dai Baba Nuhu bai da k'arfi sosai wanda zai iya biyawa Sarah kud'i both islamiya da boko don lokacin ta kammala secondary school har ta yi jamb kuma ta samu admission a polytechnic na tudun wada, kuma Evening. Kuma registration kawai 63thousand ne. An buga an buga babu ta inda kud'in nan zasu fito, kuma Lami tayi rantsuwa da Allah kwandala baza ta biya mata ba, tunda ita bata taimaki kanta ba, babu yanda za'ayi ita ta taimaka mata. Haka Sarah tayi ta fad'i tashi har ta samu aiki wa wani babban restaurant wanda zasu rik'a biynata 20k duk wata. A kuma wannan lokacin wani babban yayan Muniba ya gansu tare da Sarah a bakin titi lokacin zata tafi restaurant inda take aiki, ita kuma Muniba zata tafi poly don ita ba evening lectures take yi ba. Ai kuwa yana dawo gida ya fad'awa mahaifinsu yaga Muniba da yarinyar gidan karuwai. Bayan ta dawo daga school aka mata dukan tsiya kuma ana zama mata jan layi akan idan ta ketara ta kuma had'uwa da Sarah kashinta ya bushe kuma baza ta k'ara zuwa makaranta ba sannan aure za ayi mata kamun ta jawo masu abun kunya kuma da ko wanene aka samu za ayi mata auren. Wannan shine dalilin rabuwarsu da Muniba. Ko a hanya basu k'ara had'uwa ba tun bayan da Muniban ta fad'a mata abunda mahaifanta suka yanke. Don ko a wannan lokacin Sarah bata daina saka k'ananun kaya ba shiyasa kowa yake mata kallon y'ar iska. A restaurant d'in nan ta soma ganin _Khalil_ yaje cin abinci. Shi kuma idan bai ci abinci a gida ba, babu inda yake zuwa yaci abinci hankalinsa a kwance kamar wannan restaurant d'in. Don abincin gargajiya suke yi kala-kala mai dad'i da tsafta. Sau uku ana aikenta kai masa menu, kuma duk taje sai sunyi fad'a don kallon y'ar iska yake mata, ita ma kuma kallon da take masa kenan don kullum da chewing gum a bakinsa, duk da kuwa ba k'as-k'as-k'as yake yi ba. Amma ganin duk lokacin da tazo kawo masa Menu wani harara take jifansa dashi tana magana k'asa-k'asa, shi kuma sarai yana jin ta sarai, don ce masa take yi karuwa. Shi duk wajen babu wacce ya tsana irinta, haka itama. Dad'inta ma sai ya kwashi watanni bai zo ba. Ta kwashi tsawon shekara biyu tana aiki a wajen har ta kammala diploma d'inta. Ranar da suka yi sign out, bak'ar skirt ta sanya iri straight d'in nan mai tsagu ta baya, sai fara k'al d'in shirt da mutane suka yi signing da maka ta ko'ina a jikin rigar gaba da baya. Kanta kuma tayi parking d'in gashinta a tsakiyar kai da yaci uban acuci maza na attachment, babu d'an kwali a kanta, sai wani siririn Chantilly Vail da ta yafa. K'arfe shidda ta tashi a aiki, bayan ta gyara jikinta ta kuma fesa turare sannan ta nufi wajen madam za tayi mata sallama don ita take bata kud'in motar komawa gida. "Aunty na gama zan wuce." "Yauwa Saratu, karb'i wannan hanyar wucewa gidanku ne, zaki kai wannan sak'on *Golden diamond hotel*, wani customer d'in mu ne ke son tuwon shinkafa miyar egushi. Kuma shi abinci idan ba na nan wajen ba, bai son na wani waje. Please ki tsaya ki kiyi delivery d'in wannan sai ki wuce gida. Ga kud'in transport." Ta k'arisa maganar tare da mik'a mata 1k da kuma ledan take away a ciki. Karb'a tayi tare da juyawa ta fita daga restaurant d'in. Zuciyarta d'aya ta nufi hotel d'in kasancewar har numbern d'akin aunty ta fad'a mata. Tana zuwa reception ta samu wani inyamuri tayi masa magana, duk a tunaninta shi zai karb'a ya kai masa abincin. Amma sai taga inyamurin ya daga waya ya kira can d'akin yayi magana da wanda zata kaiwa abincin. "Ok Sir!" Shine kawai abunda taji ya fad'a tare da yanke wayar sannan ya kalleta tare da fad'in, "Madam you can go in!" Da kamar za tayi musu, sai kuma ta nufi hanyar da zai sadata da matattakar da zai kaita room number d'in da yake ciki. Knocking tayi, daga ciki aka ce "Yes come in!" Tura k'ofar tayi tare da shiga kanta a k'asa. Shi kuwa juyowa yayi hannunsa rik'e da waya yana amsa kira yana fad'in, "Hajiya Allah idan basu bar gidan nan ba bazan dawo ba. Haka kawai sun bi sun takura mana mu da gidan uban mu!" Dai-dai nan ya d'ago idanu ya sauke a kan Sara dake tsaye. "Hajiya zan kira ki ina zuwa." Yana fad'in haka ya katse wayar tare da jifan Sarah da mummunar kallo sannan yace, "Ko ina sai kin nuna rashin kamun kanki ko? Idan banda zubda da kai da rashin aji, duk mazan dake restaurant d'in naku a rasa wanda za'a aiko ya kawo min abinci sai ke." "Ni dai ba y'ar iska bace tunda de bana zaman hotel, kuma ba'a tab'a gani na ina taunar chewing gum kamar karuwa ba. Kallo d'aya za ayi maka a fahimci kai wani irin mutum ne. Kai ne mara kamun kai ba ni ba. Kuma ni ga abunda ya kawo ni hotel nan na ajiye maka." Ta fad'i haka tare da ajiye masa ledan a kan center table zata juya. Fizgota yayi tare da fad'in, "Ke wanene d'an iskan?" Fizge jikinta tayi tare da fad'in, "Kada hannunka ya k'ara tab'a jikina. Jikina yafi k'arfin ka wallahi. Ni ba gantalallun y'an matan daka saba kwanciya dasu bane anan hotel d'in. A fita a samu dai-dai da kai. Ni ba sa'ar ka bace!" A tsawace yace, "Wallahi idan kika k'ara magana sai na baki mugun mamaki anan d'akin." A tsawace Sarah tace, "Iya kaci kace zaka kashe ni ka b'oye gawata. Ni dalla malam matsa min a hanya in wuce don wari da k'arni zina ya ishe ni." Tana maganar ne gabanta na fad'uwa amma tsaurin idanunta ya hanata yin shuru. Wani gigitaccen mari ya dauketa dashi tare da fad'in, "Zan nuna maki halin karuwan da kike ambata na dashi kullum." Yana gama fad'in haka ya danna switch d'in d'akin wuta ya d'auke tare da d'agata cak ya jefa kan gado. Wani irin ihu ta saki tare da mik'ewa zata duro daga kan gado amma ya riga ta hawowa kan gadon tare da yi mata rumfa kuma ya sakar mata nauyinsa gaba d'aya a jiki sannan yayi amfani da hannunsa ya zame shirt d'in jikinta. Jin ta damesa da ihu ya kai hannu ya bige bakinta tare da fad'in, "Dama ai kin saba bin mazan, ihun uban mai kike min." Duk da tana cikin mugun tsoro da tashin hankali hakan bai hanata magana ba tace, "Mugu azzalumi, mai halin karuwai. Wallahi sai na kashe ka idan kayi min wani abu." Bai saurareta ba ya kai hannun ya d'aga rigar jikinta ya cire, jikinta sai rawa yake yi, da taga fa tabbas dagaske yake yi zai rabata da mutuncita da take tak'ama dashi, kuma ga alk'awarin da tayiwa Farouq wanda da kyar iyayensa suka amince ya turo gidansu har aka tsaida maganar aure. Sai ta fashe da kuka ta soma rok'ansa tana bashi hak'uri. Shi kuwa tuni ya cire hook d'in bra d'inta ya shiga wasa da ilahirin lallausar jikinta. Abunda bai tab'a tun da uwarsa ta haifesa, sai gaba d'aya ya rasa nutsuwarsa, don bai tab'a body contact da mace ba a tsawon rayuwarsa. Don ko side hug bai yarda dashi ba. Tunaninsa ya bar jikinsa har bai san lokacin da ya zame wandon jikinsa ba ya ware k'afafunta tare da yunk'urin shiga jikinta. Wani mahaukacin ihun da ta saki ne ya dawo dashi hankalinsa, da mad'aukakin mamaki ya kuma tura jikinsa a karo na biyu, amma still gan ya jita. Tun da yayi yunk'uri na biyu bai kuma yi ba, sai ya canza salon wasan kasancewar ya riga ya d'ad'd'ago sha'awarsa gaba d'aya. Jikinsa ya dunga gogawa a nata jikin kusan tsawon mintuna sha biyar har ya samu nutsuwa sannan ya mirgina ya bar jikinta yana maida numfashi. Ita kuwa Sarah kuka take yi sosai duk da kuwa ta san bai isa ga jikinta ba. "Mugu azzalumi kawai." Ta fad'i tana kuka. Shi kuwa idanunsa a rufe yake fad'in, "Naji, duk nine. Kiyi hak'uri ki yafe min. Kin ga ai ban raba ki da budurcinki ba." A fusace tace, "Wallahi ba zan tab'a yafe maka ba. Karuwi kawai. Mijina ma ba zai tab'a yafe maka ba don ka cutar dashi ka shiga gonarsa." "Haka be naji duk ba amince. Kiyi hak'uri amma ki min afuwa. Tsautsayine wallahi ba hali ba bane." "Halinka ne Allah kuwa. Mugu mai lalata yaran mutane a hotel." Mik'ewa yayi ya tashi zaune. Da saurin ta mirgina sai ji kake tim a k'asa ta d'auka wani abun zai kuma yi mata. "Wayyooooo Allah na shiga uku k'afata." Ta fad'i da k'arfi dai-dai lokacin da ta d'auki boxer d'insa ya saka tare da saukowa ya kunna switch d'in d'akin. Da sauri Sarah ta jawo zanin gadon ta rufe jikinta tana kuka sosai da bak'in cikin abunda yayi mata. Matsowa yayi domin yaga halin da k'afar take ciki, wani irin ihu ta saki tare da k'ank'ame jikinta. Matsawa yayi yana kallonta. Ita kuwa sai k'ara kakkare jikinta take yi tana kuka. "I'm sorry kin ji. Ina zuwa yanzu bari na dawo." Ya fad'i hakan tare da d'aukar dogon wandonsa ya saka da riga ya fita da sauri. Sarah na ganin ta fita ta mik'e da sauri ta d'auki kayanta ta saka. Ko tsayawa d'aukar jakarta bata yi ba domin kada ya dawo ya idda ita. Da sauri ta bud'e d'akin ta fice daga hotel d'in tana b'oye-b'oyen fuska. Lokacin da _Khalil_ ya dawo bai d'auka bata d'akin ba ganin ga jakarta a kan gadon. Zama yayi a gefen gado hannunsa rik'e da wani magani yana jiran fitowarta daga bayi, mintuna biyar suka shud'e yaji shuru, wani biyar d'in ya k'ara shud'ewa nan ma shuru. Mik'ewa yayi tare da isa k'ofar bayin ya soma kwankwasawa, jin shuru sai ya tura k'ofar. Wayam ya gani. Da mugun sauri ya tashi ya fita ya dunga dube-dube ko zai ganta, amma babu ita babu dalilinta. Gashi babu wani makama da zai gane inda take, ko sunanta bai sani ba. Komawa cikin hotel d'in yayi tare da bud'e d'aukar jakarta da wani abu kamar d'an kwali da ta bari ya fita ya bar hotel d'in. Tun daga wannan ranar _Khalil_ bai sake farin ciki ba, kullum cikin neman Sarah yake yi. Kuma Allah bai k'ara had'a su. Sai bayan kwanaki ashirin da uku a asibitinsa. Aina'u ba k'aramin tashin hankali ta shiga ba ganin irin uban kaya da _Khalil_ ya jido. Ji take kamar zuciyarta zata hudo k'irjinta ta fito tsabar bak'in ciki. "Hajiya tun d'azu ake kiran wayarki." Fad'in Laure tana mai mik'awa Hajiyar waya. Amsa Hajiya tayi bayan ta shafa addu'a don sallar magriba ta idar kuma dai-dai nan aka kuma kiran wayar. "Assalamu alaikum" Fad'in Hajiya bayan ta amsa kiran ta kara a kunne. "Wa'alaikissalam, dan Allah Ina magana da Hajiyar doctor _Ibrahim Khalil_ ne mai asibitin *_Khalilullah specialist hospital_*?" Kallon Laure Hajiya tayi tare da mata nuni da hannu alamar ta fita bayan ta amsa da "Eh ita ce. Allah yasa lafiya?" Daga can aka d'an yi jim kamun wacce ta kira wayar ta soma fad'in, "Hajiya akwai wani abu da d'anki yake b'oye maki mai matuk'ar muni wanda ke baki sani ba. Kuma a irin tarbiyan da kuka bashi idan na fad'a maki abunda yake aikatawa, sai kin girgiza." Hankalin Hajiya tuni yayi wani irin mugun tashi ta soma fad'in, "Baiwar Allah ya zaki kira ni kina fad'a min irin wannan maganganun masu d'aga hankali? Mai _Khalilullah_ yake aikatawa wanda ban sani ba?" "Uhm! Hajiya idan d'an ki ya dawo, ki tambayesa wacece Saratu?" Mik'ewa Hajiya tayi tana fad'in, "Dan Allah yarinya kiyi maganarki kai tsaye, mai _Ibrahim_ yake aikatawa wanda ban sani ba?" "Hajiya d'an ki dai yana da budurwa, ko kuma ince maki dadironsa! Don kuwa yanzu haka da nake fad'a maki, ki fara tanajin jiran isowar jika nan da wata takwas masu zuwa, don kuwa d'an ki yana neman wata yarinya wacce gaba d'aya gidansu karuwai ne kowa ya sani. Sunanta Saratu ana ce mata Sarah. Tana da yayyi mata hud'u, kuma gaba d'ayansu babu wacce bata ajiye shege ba a cikin gidan. Sannan kowa ya san su karuwai ne. Kuma abunda zai baki mamaki, a gaban uwarsu da ubansu suke. Idan kuma baki yarda da maganata ba, idan _Khalil_ ya dawo tambayar da zaki fara yi masa shine wacece Saratu. Yanayin da zai nuna kawai ta isa ya tabbatar maki da zance na. Na barki lafiya Hajiya." Tsabar tashin hankali da rikicewa Hajiya fitsari ta soma saki ba tare da sani ba, da rarrafe ta shiga bayi ta soma sakin zawon tashin hankali............

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull