Kanwar matata complete - Chapter 9
Kanwar matata complete Chapter 9: Kanwar matata complete Chapter 9. *👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa…
3,820 words
*👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262*
*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*
*_MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜
*PAGE 13*
*👭GARKUWAR MATA* *Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci* *GA* *Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa* Rage tumbi💯 Nono💯 Sanyi💯 Karin kiba💯 girmar hips💯 Ni'ima💯 Sabulai💯 Humra💯 Turarukan wuta💯 Matsi💯 Miski💯 Dilka💯 Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI *08089965176* *07084653262*
Abu kad'an ke saurin d'aga mata hankali. Babu mamaki yanzu idan aka duba BP d'inta aga ya hau. Ta jima duk'e a bayin kamun ta iya cire kayan jikinta tayi wanka sannan ta sake d'auro alwala ta fito ta sauya kaya. Tuni wani zazzafan zazzab'i ya rufeta sai kakkarwa take yi a bakin gado. Dai-dai nan Laure ta shigo bakinta d'auke da sallama tana fad'in, "Hajiya a kawo maki zogalen yanzu?" Da sauri ta k'arisa shigowa d'akin tana fad'in, "Hajiya lafiya? Mai ke damun ki? Yanzu fa na barki lafiya kina amsa waya." Dakyar Hajiya tace, "Tafi ki kira min Maryamu yanzu a b'angarensu." da sauri Lauren ta juya ta bar d'akin har da had'awa da gudu ta nufi side d'in aunty Maryam tare da danna doorbell. Mijinta Yaya Abdul-Hakeem ne yazo ya bud'e k'ofar tare da fad'in, "Lafiya Laure na ganki a rud'e?" Ya fad'i don shima dawowarsa kenan daga wajen aiki. Yanzu nan kuma yake son shiga wajen Hajiyar. "Yaya Abdul Hajiya ce ba lafiya shine tace in kira mata aunty Mar....." Ko kamun ta k'arisa maganar har ya tureta ya fito da sauri ya nufi side d'in Hajiyar kamar zai tashi sama. Aunty Maryam ma da sauri ta fito don fitowarta kenan daga kitchen taji abunda Laure ke fad'awa mijin nata. Bin bayansa suka yi ita da Lauren hankali tashe. Ko da yaya Abdul ya isa d'akin Hajiya, gaba d'aya ta gama firgicewa. Jikinta yayi mugun zafi musamman ta wajen kanta. Zama yaya Abdul yayi tare da tallabo Hajiyar yana fad'in, "Inna lillahi! Hajiya mai ya same ki. Ai bamu ga ta zama ba. Mu tafi asibiti kawai." Dai-dai nan aunty Maryam d'in ta shigo ita da Laure. "Abdul-Hakeem d'au wayarka yanzu ka kira min _Khalilullah_." Hajiya ta fad'i hakan da kyar. Yaya Abdul bai kawo komai a ransa ba sanin k'anin nasa ai doctor ne. Maybe don yazo ya duba tane don Hajiya ta tsani zuwa asibiti. Wayarsa ya fiddo tare da kirar _Khalil_ d'in. Ringing yayi har ya katse ba'a d'aga ba, zai sake kira kenan sai ga shigowar kiran _Khalil_ d'in. D'agawa Abdul-Hakeem yayi tare da fad'in, "Kana ina?" Daga can _Khalil_ yace, "I'm sorry yaya, na fito da wayar kenan zan d'auka sai katse. Gani kusa da gida." "To kayi maza ka shigo yanzu. Hajiya ba lafiya." Yana gama fad'in haka ya katse wayar. _Khalil_ kuwa ji yayi gaba d'aya hankalinsa ya tashi. K'ara gudun motar yayi duk da yana gab da layin. Mintuna biyar suka k'ariso dashi gidan. Ko parking mai kyau bai yi ba ya shigo gidan ya nufi d'akin Hajiya kai tsaye. Nan ya tarar dasu sun yi curko-curko. "Hajiya mai ya same ki, taso mu tafi asibitina dan Allah." Da kyar Hajiya ta d'ago kanta ta zubawa _Khalilullah_ idanu tare da fad'in, "Abdul-Hakeem ku d'an bamu waje." Tana fad'in haka gaban _Khalil_ ya yanke ya fad'i. Don har ji yayi wani k'aramin zufa ya gangaro daga goshinsa. Abdul-Hakeem babu musu ya mik'e ya fita, aunty Maryam da Laure suka bi bayansa tare da rufo masu k'ofa. _Khalil_ shuru yayi kamar ruwa ya cinyesa, don hakanan jikinsa Hajiya ta gano abunda yake b'oyewa. " _Ibrahim_" Hajiya ta kira sunansa da muryanta da yayi rauni. Hankalin _Khalil_ ta tashe yace "Na'am Hajiya." "Wacece Saratu?" A mugun furgice duk da kuwa zuciyarsa na bashi ta gano ko kuma wani ya fad'a mata ya d'ago bakinsa na rawa yace, "Haj..... Hajiya ban gane abunda kike fad'i ba." Hannu Hajiya ta d'aga ta wanke masa fuska dashi tare da fashewa da kuka tace, " _Khalilullah_ ka b'ata wayanka. Baka kyautawa kanka ba. Dadiro _Ibrahim_? Yanzu har kayi rik'an da zaka ajiye dadiro a waje _Khalil_. Kana da kud'i, kana da wajen zama, duk wani abu da namiji zai mallaka kamun yayi aure, ka mallaka _Mu'azzam_, amma shine sabida shaid'an ya buga maka gangi, giyar kud'i na janka, shine zaka butulcewa Allah ta hanyar yin abunda ya haramceka dashi. Ka bani mamaki _Khalil_. Ashe irin tarbiyan da muka gina ku a kai ni da mahaifinku, watsar dashi kayi? _Khalil_ baka yi wa kanka da mu adalci ba. Ka b'atawa zuri'ar suna. Ashe dai da gaskiya su Ameeru da suke cewa ka ajiye dadiro. Shiyasa a kullum burinsu shine suyi maka aure sabida sun san lalatar da kake yi a waje. Baka min adalci ba _Mu'azzam_!" Ta k'arisa maganar tana mai fashewa da kuka takaici. Shima _Khalil_ d'in kukan ya soma yana fad'in, "Hajiya dan girman Allah kar kiyi mani kuka. Kukanki bala'i ne a gare ni. Ki tsaya inyi maki bayani. Duk wanda ya fad'a maki na ajiye dadiro wallahi sharri yake min kawai yana son shiga tsakanina dake ne. Wallahi tallahi ban tab'a ajiye dadiro ba a rayuwata. Kuma Hajiya ban tab'a ratsa jikin wata y'a mace ba. Ban san ta yanda zan yi maki bayani ba ki fahimceni ni." Hajiya tsagaita kukanta tayi tare da fad'in, "Kenan sharri ake maka baka san wata Saratu ba." Girgiza kai yayi tare da fad'in, "Na santa Hajiya, amma ba ta yanda kike tsammani ba. Ita ce wacce nake fad'a maki ba tsayar matsayin wacce zata zama uwar y'ay'ana." Wani ajiyar zuciya Hajiya ta saki, sai kuma tace, "To maganar ciki fa? An ce kayi mata ciki in tsammaci zuwan jika nan da wata takwas. Ya matsayin wannan maganar take?" Shuru _Khalil_ yayi yana kallon k'asa. Sai kuma ya d'ago tare da kama hannayen Hajiya duka biyun yace, "Hajiya dan girman Allah kiyi hak'uri da abunda zan fad'a maki yanzu. Amma ki saurare daga baya sai ki yanke hukuncin da kika ga ya dace. Dagaske Sarah tana d'auke da ciki, kuma nawa ne." Tass Hajiya ta sauke masa mari tare da nuna masa k'ofa tace, "Fita! Fita nace ka bar min d'aki yanzun nan!!" Ta kuma fad'i a tsawace. Da sauri ya mik'e tsaye tare da fad'in, "Haj......" "Fita _Khalil_ kar ka sa nayi abunda zan dawo ina dana sani. Fita nace kar in fad'i mummunar kalma a gare ka." Fad'in Hajiya tana matsar hawaye. Da sauri _Khalil_ ya fita tare da rufo mata k'ofar. Shi babban tashin hankalinsa, kar jininta ya hau. Yana fitowa daga d'akin ya nufi waje ya zauna tare da kama kansa har akai kiran sallar Isha sannan ya mik'e ya nufi masallaci. Hajiya kuwa kuka tayi sosai har da majina. Bayan ta idar da sallar isha'i wanda tayi sa da kyar, sannan ta lalubi wayarta ta dannawa babban wansu soja mai muk'amin *_LTG (Lieutenant general)_* dake zaune a abuja, a can yake da iyalansa gaba d'aya kasancewar aikinsa a can yake. Bugu d'aya yayi rejecting tare da karanta, "Assalamu alaikum Hajiya." "Amin wa'alaikassalam." Tun daga yanayin yanda ta amsa kiran ya tabbatar babu lafiya, mik'ewa yayi d'aga kwancen da yake ya zauna tare da fad'in, "Hajiya lafiya? Mai ke faruwa?" Kuka Hajiya ta fashe dashi tare da fad'in, "Marmari daga nesa (Bata kiran sunansa kasancewarsa d'an Faari) duk abunda kake yi ka d'auki sakuis (excuse) kazo gida gobe, kuma ka kira wancen yaron na Kano shima ina son ganinsa har da k'anwarku Aisha. Duk kuzo ina neman ku gobe." Gaba d'aya tunanin _LTG Abdallah_ akan maganar gadonsu ne, don wani lokacin haka uncles suke sako mahaifiyar nasu a gaba duk akan dukiyar da mahaifin nasu ya bari. "Dan Allah Hajiya ki kwantar da hankalinki, in Sha Allah gobe zan biyo jirgi ni da Aysha. Zan kira mijinta yanzu ina gama waya dake." Fad'in LTG Abdullah don Aysha d'in a nan Abuja tayi aure, kusan a hannunsa take, don shi ya aurar da ita. Ita ma soja take aure ana Abujan. Katse wayar Hajiya tayi tare kifa kanta a kan pillow tana zuciyarta na mata zafi, gaba d'aya Y'ay'anta daga maza har matan lafiya k'alau ta aurar dasu, Nafeesa ta je gidan mijinta lafiya, haka Aysha. Mazan ma gaba d'aya babu wanda ya d'auko mata abun kunya sai _Khalilullah_. Kuma duk cikin y'ay'anta shi, yana da wani special guri a zuciyarta. Don shi d'in favourite d'inta ne. Duk da kuwa ba shine auta ba. Nafeesa ce autarta. B'angaren _Khalil_ kuwa yanda yaga rana, haka yaga dare. Abun duniya duk yabi ya ishesa. Sam ba ta haka yaso hajiya taji wannan maganar ba. Yaso ya shaida mata da kansa ta hanyar da ko zata jijjiga ba kamar haka ba. Tunani ya dunga yi wanene ya san abunda ke faruwa har ya d'aga waya ya kira Hajiya, "Doctor Kamal!" Fad'in _Khalil_ a bayyane. Da sauri ya mik'e zaune yana jin wani irin matsanaicin b'acin rai da tsanar doctor d'in. "Wallahi sai na baka mamaki Kamal. Ni zaka had'a da mahaifiyata. Zaka san koni wanene. Daga kai na baza ka k'ara irin wannan munafurcin ba." Saukowa yayi ya nufi bayi yayi alwala tare da fitowa ya shimfid'a darduma ya dunga yin sallah yana rok'an Allah sauk'i da sassauci akan lamarin. Bai tashi daga kan darduma ba sai da yaji kiran sallar asubahi na shiga masallaci sannan ya mik'e ya fito. Sai da ya fara bi ta d'akin Hajiya tukun, da sand'a ya murd'a k'ofar a hankali tare da bud'ewa. Karaf suka had'a idanu da Hajiyar dake zaune a kan darduma, don kamar yanda ya kwana sallah haka ita ma. Da sauri ya jawo k'ofar ya rufe tare da barin wajen ya nufi masallaci. Sai bayan da aka idar da sallah har fito zai koma cikin gida yayansa Abdul-Hakeem ya tare sa, bayan sun gaisa yake ce masa, " _Khalil_ mai ke faruwa Hajiya tayi kiran kowa na gidan nan cikin gaggawa? Yaya Abdullah ma yana hanya zuwa anjima zai biyo jirgi shi da Aysha. Kuma nima Hajiya ta saka na kira mijin Nafeesa akan ha kawo ta gobe. Wani irin meeting kuma za ayi yau a gidan nan? Allah yasa ba dai akan rigimar gado bane. Nifa wallahi abunda Papa ya tafi ya bari bai tab'a d'ad'ani da k'asa ba, abun na tara da gumina ma ya ishe ni zaman duniya." Tun da ya fara maganar _Khalil_ jinsa kawai yake yi amma kwakwalwarsa da tunaninsa sun yi nisa tun lokacin da yace masa yaya Abdullah na hanya. Wannan masifaffan mai bak'ar zuciya kamar da taurin kai. Don shine ya d'auko Papa sak. Shi kaifi d'aya ne, idan yace yes, to ko duniya zata tashi yes d'in ne, idan kuma yace no, tofa ko ana ha maza ha mata babu mai canza shi. Kuma duk gidan tsoransa ake ji. Shine babba kuma zai iya kaiwa shekaru hamsin da biyar a duniya. Daga shi sai yaya Barrister (Muhammad Kabir) kenan, shi yana da sanyi hali. Ba k'aramin abu ke b'ata masa rai ba. Idan kaga yana zafi da magana sosai, to fa a kotu ne musamman idan Shari'a ake yi akan fyad'e. Shi yaci gajiyar Papa don tun yana k'aramin yake fad'in "Papa idan na girma irin aikinka zan yi in rik'a Yankewa mugaye hukunci. Daga Barrister sai Abdul-Hakeem wanda shi kuma SSS ne, (D'an sandar farin kaya). Daga shi sai _Doctor Khalilullah_, sai Aysha, sai auta Nafeesa. "_Khalil_ kana jina kuwa." Fad'in ya Abdul yana tab'a hannunsa ganin yayi zurfi a tunani. "No, babu komai ina zuwa." Fad'in _Khalil_ tare da nufa part d'in Hajiya. Kai tsaye d'akinsa ya shige yana safa da marwa. Kwankwasa k'ofar d'akinsa aka yi, da sauri ya juya yana kallon k'ofar. Hannu ya kai ya danna wani switch sai ga Laure ta bayyana akan screen d'in dake saman k'ofarsa. Ajiyar zuciya yayi tare da nufa k'ofar d'akin ya bud'e, "Yaya _Khalif_ ina kwana?" Saude ta fad'i a sanyaye don tun jiya take jinta wani iri ganin uwar d'akinta babu lafiya. "Lafiya k'alau ya aka yi?" Ya amsa tare da jefa mata tambaya. "Hajiya ce tace in fad'a maka yau kar ka bar gidan nan akwai bak'in da zasu zo anjima." Shuru yayi yana kallon Laure kamar ita ce Hajiyar, can kuma ya nisa tare da fad'in, "Ok, to jeki." Yana gama fad'in haka ya rufo k'ofar tare da zama a bakin gado ya rik'e kai. Gaba d'aya natsuwa ta bar jikinsa. Gabansa sai dukan tara-tara take yi. Bai isa sakawa cikinsa ko ruwan Lipton ba har k'arshe sha d'aya yana nan zaune a d'aki yana sak'awa da warwarewa. Su aunty Maryam da Laure kuwa, sai kaiwa da komowa suke yi a kitchen suna had'awa bak'i abinci. Nafeesa ta riga kowa zuwa kasancewar ita mazauniyar Kaduna ce. Ana tayi aure a kabala shooting range. Hankalinta sosai ya tashi ganin halin da mahaifiyarsu take ciki. Don har a wannan lokacin jiri hajiye take gani, kuma idanunta sunyi luhu-luhu alamar taci kuka. "Hajiya dan girman Allah mai ke faruwa? Idan dai akan su uncle ne, dan Allah ki fitar da damuwarsu a zuciyarki. Har kuka gama zaman ku da Papa bai saka maki ciwo ba, sai y'an uwansa ne zasu buwayeki. Dan Allah Hajiya ki bari." Girgiza kai Hajiya tayi tare da fad'in, "Uhm, baza ki gane ba Nafeesa, bari dai sauran y'an uwanki su iso. Ni ba akan y'an uwan mahaifinku bane. Da sune ne abun da sauk'i." Shuru Nafeesa tayi tana tunani a zuciyarta to mai ya faru idan har ba su uncle bane. K'arfe sha d'aya da mintuna arba'in, yaya Barrister ya iso gidan shi da matarsa aunty Khairat da yayansu uku, Sam'an, Sahla da Nu'aima. Nan aka dunga oyoyo-oyoyo. Ko mintuna goma basu yi da zuwa ba, soja marmari daga nesa, LTG Abdullah ya iso shi da Aysha da kuma tawagar sojojin da suka yiwa unguwar k'awanya. Don gaba d'aya unguwar sai da suka shaida *_Lieutenant General Abdullah Nurudden Muhammad_* ya shigo unguwar. Tun da _Khalilullah_ ya lek'o ta window ta can saman d'akinsa yaga uban sojojin sun gewaye gate d'in gidan, wasu ma har ta cikin gidan yaji kamar an cire lakar dake jikinsa. Laure gaba d'aya ta rud'e don har wani zawo-zawo take ji sabida ba k'aramin tsoro da shakkar _LTG Abdullah_ take yi ba. Don shi fuskansa ma bata cika fara'a ba. Kai tsaye gaba d'aya suka wuce d'akin Hajiyar ban da _Khalil_ da ko lek'owa parlor bai yi ba. Har k'asa k'asa ya _LTG_ ya duk'a gaban gadon da take tare da fad'in, "Hajiya ina wuni, mun same ku lafiya? Ashe baki ji dad'i ba. To menene amfanin _Ibrahim_ a cikin gidan nan da ba zai iya kai ki asibiti ya duba ki ba. Wallahi wani irin iskanci ne. Ina yaje?" Hawaye Hajiya ta soma yi tare da fad'in, "Ni na hana a kai ni asibitin, don ciwon dake damuna, _Khalil_ d'in ne sanadiyarsa. Marmari, _Khalil_ ya b'ata mana sunan famili. Ya rusa duk wani tarbiyar da muka ginasa akai. So mu had'u mu duka a parlor, bayan anci abinci, sa muyi maganar." Kai a k'asa zuciyarsa na tafasa ganin mahaifiyarsa na hawaye yace, "Hajiya abinci ba zai ciwu ba, har sai naji abunda yake damunki nayi maki maganinsa tukun." Gaba d'aya su Barrister, Aysha da Nafeesa har da yaya Abdul suka ce, "Hajiya abinci tabbas ba zai ciwu ba har sai munji matsalarki." "Ku aika Laure ta kira _Mu'azzam_ a d'akinsa ya fito mu tafi can parlor ayi maganar a can." Mik'ewa Nafeesa tayi tare da nufa corridor d'in da zai sadata da d'akin yayan nata tana mamakin wani irin laifi ya aikata da har Hajiya take cewa ta b'ata masu sunan family. "To ko zubar da ciki yake yi a asibitinsa?" Fad'in Nafeesa cikin zuciyarta dai-dai lokacin da take knocking d'in k'ofar d'akina. Bud'ewa yayi, kallon fuskansa kawai za kayi ka tabbatar yana cikin tashin hankali. Kuma ba komai ke d'aga masa hankalin ba irin fushin Hajiya. "Nafeesa!" Ya fad'i a hankali yana kallonta. "Na'am yaya _Khalil_. Tun d'azu gaba d'aya muka zo amma babu kai a wajen. Hajiya tace kaje parlour duk muna can." Fitowa yayi gaba d'aya tare da kullo k'ofar yace, "Muje Nafeesa. Hankalina ne gaba d'aya a tashe. Har da ya Abdullah ko?" Gyad'a masa kai tayi suna tafiya a jere tare da fad'in, "Yaya _Khalil_ wai don Allah mai ke faruwa ne Hajiya ta kira mu gaba d'aya? Wani abun kayi ne?" Bai ce mata komai ba har suka k'ariso parlourn. Bai iya d'aga kai ya kalli kowa a cikinsu ba. Neman waje tayi daga gefe ya zauna kansa a k'asa tare da fad'in, "Ina wuni ya Abdullah? Sannu da zuwa ya Barrister. Kun zo lafiya?" Babu wanda ya amsa gaisuwarsa. Bai damu ba don dama ya san dole hakan zata kasance. Ya Abdullah kuwa duk ba sai ainahin abunda _Khalil_ d'in ya aikata ba, sai jifansa yake yi da wani irin mugun kallo. Su kad'ai ne a parlor, don ko Barrister da yazo da matarsa, tana can ita da Y'ay'anta a part d'in ya Abdul-Hakeem. Sune kawai isu-isu a parlourn. Don maganar tasu tana buk'atar privacy. "Abdul-Hakeem bud'e mana taro da addu'a." Fad'in Hajiya wacce ke hakimce a kan kujera tana girgiza k'afa. Sai bayan yaya Abdul-Hakeem d'in ya gama addu'ar sannan Hajiya tace, "Na kira ku ne anan wajen ba don komai ba, sai don saboda _Ibrahim_. Na san dukkan ku kun san bak'ak'en maganganu da kuma zagi da nake jurewa daga wajen dangin ubanku. Tun yana da rai suka kafa min k'ahon zuk'a har ila yau da ya kasance babu shi a raye. Kuma kun san cewa iyayenku suna son had'a _Khalil_ aure da Nina wanda shi kuma yak'i bada fad'in kai a cewarsa bata da kamun kai ita mazinaciya ce." Da sauri yaya Barrister yace, "Hajiya idan dai a kan wannan maganar ce ta Nina, to ba wai bane. Don ni da kaina na tab'a ganinta a wani babban hotel a Kano ita da wani sa'an mahaifinta." Da k'arfi Hajiya tace, "Kayi min shuru! Ai ita da _Khalil_ d'in zani ce ta tadda muje." Da sauri _Ya LTG_ yace, "Hajiya ban fahimta ba." Gyara zama tayi tare da fad'in, "Yanzu kuwa zaka fahimta. Kai _Khalil_ yi masu bayani abunda ka aikata." Kansa a k'asa gabansa na fad'uwa ya d'ago ya kalli Ya Abdullah, wata uwar hararar da ya watsa masa ya saka yayi saurin sunkuyar da kai k'asa." Wani mahaukacin tsawar da yayi, ba _Ibrahim_ kad'ai ba, hatta ita kanta hajiyar sai da ta tsorata. "Za kayi magana anan wajen ko sai na taso na taka cinyarka tayi dagwa-dagwa!" A razane _Khalil_ yace, "Hajiya wallahi, tallahi wa billahil azim ba halina bane. Tsautsayine ya saka nayi mata fyad'e har ta samu ciki." A mugun mamakance da bak'in ciki ya Barrister da ya Abdullah suka ce "Fyad'e!" Wani mik'ewa _Lieutenant Abdullah Nurudden Muhammad_ yayi tare da isa inda _Khalilullah_ yake tare da............
*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*
*_MATAR SAYYADEE_* [9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜
*PAGE 14*
Here are the list of my books: 👇 1. Anya uba nane? 2. Auren cikin gida (paid) 3. Ni da shi abu d'aya ne 4. Zina babbar bala'i ce 5. Bani da gata (paid) 6. Garwashi 7. Sai a lahira (paid) 8. D'an Faari (First born) (paid)