Kanwar maza Book 3 and 4 Complete - Chapter 61
Kanwar maza Book 3 and 4 Complete Chapter 61: Kanwar maza Book 3 and 4 Complete Chapter 61. Da sauri Ammi ta ƙarasa ta riƙo hannun Ade, hawaye ya wanke…
3,357 words
Da sauri Ammi ta ƙarasa ta riƙo hannun Ade, hawaye ya wanke mata fuska ta ce "Dan Allah gaske ne ba mafarki nake ba, Ade ke ce a gabana? Ade ba irin neman da ban yi miki ba"
Suka rungume juna ita da ita.
Alhaji Aminu ya ƙurawa iman ido, ya ce "wannan ce ƴar ta mu?" Kamar sokuwa haka iman ke bin su da kallo.
Mahmud ya ce "Hajjaju ga ƴan uwanki, mijinki ya nemo"
Jiri ne ya fara ɗibar iman, saboda ba ta san mafarkin nan ya cigaja da yaudararta.
Umar ya riƙe ta ya ce "Iman, calm down mana menene"
"Dan Allah ka tashe ni daga baccin, kamar ba zai faru a gaske ba fa?"
"Ba mafarki bane ba fa" yayi maganar yana zama tare da ita, saboda har numfashinta ya fara sama.
Alhaji Aminu ya ƙaraso gaban iman, ya riƙe hannunta, ya ce "ƴa ta ba mafarki bane ba, mu ne ahalinki" bayan gama kukan ammi ta ce Aminu haka ka girma sosai? Iman ga Ade da nake baki labari, wannan su ne ahalin mairamu"
An sha koke-koke, Ɗan aike ammi ta tasa, aka kira wambai, sai dai yaji kunya da nauyin abubuwan da suka din ga yi wa Ammi da iman, a kan rashin sanin wacece, wanda hakan yana da alaƙa da zigar Mummy.
Nan Alhaji Aminu ya gaya musu cin amanar da jauro yayi musu, da ƙiyayyar garin da ya sanya musu, suka kasa komawa, balle su binciki abun da ya faru gaske ne ko ƙarya.
Takawa ya ce "Tabbas wannan mutumin shi ne rumaisa ta zana mini, ta ce da wa yake kama? Na ce mata iman, ta ce a yanayin da ta ganshi ne ya sanya ba zata taɓa cewa ta ga wani mai kama da iman ba, kasancewar sa mutumin banza, dan har tattaunawa da shi ta yi"
Iman ta rasa mai zata cewa mai sunan baba saboda murna, sai kuka take yi.
Bayan an nutsa, ammi ta saka aka kawo abinci, takawa ya ce "Shi da matarsa zai ci abinci, mai sunan baba ya ce shi ma haka. Mahmud ya ce "Ni za a yi wa gori? Sai in ci da ammina"
Haka suka wuni cikin raha da dariya, iman ta rasa in da zata tsoma dan farinciki.
Labari ya bazu, Mijin iman da Mahmud sun gano iyayen Iman.
Hankalin Mummy ya ƙi kwanciya, sai da ta zo ta ganewa idonta, Ade ga jikarta, amma ta yi ram da rumaisa, saboda yadda yarinyar ta yi mata.
Da yamma ammi ta ce ruma ta tafi gida, tun da jego take yi, takawa ya ce ta ƙyaleta, duk tare za su zauna, su taya iman murna.
Mai sunan baba ma barin iman yayi a gidan, ya tafi gida dan ya huta.
Iman da rumaisa gami da nusaiba, sun kewaye Ade, sai dariya take basu, suna yi mata tambayoyi, har bacci ya kwashe su.
Takawa dama yana ɗakinsa na sashin Ammi, fitowa yayi, kusan sha ɗayan dare yana nunawa ammi wayarsa, ya ce "Ammi ina mimi, a taso mini ita"
A daren aka wallafa labarin kama Khalifa wakili a Mexico da cocaine.
Ammi ta ce "Bacci take yanzu, ka bari da safe"
Ya ce "Ammi ba zan iya jira ba, a taso mini ita dan Allah"
Haka Ammi ta je ta taso masa ruma, ya ja ta ɗakinsa ya nuna mata.
"Ban gaya maka ba papa, duk wani azzalumi da ya fi ƙarfinka, bai fi ƙarfin Allah ba, ka zuba ido zaka ga yadda Allah zai ɗaiɗaita azzalumai, yanzu ma ga ta in da ɗan nasa zai yi takara, kuma wannan abun da aka kama ɗan sa da shi, ya isa ya saka baban nasa ma su faɗi zaɓe".
Alwala takawa yayi, ya din ga salla yana godewa Allah, ko wannan tashin hankali ya isa hana wakili sukuni, ɗan sa yayi laifi da ƙasar da bashi da halin yin cuwa-cuwa.
Ruma kasancewar jiya ba ta yi bacci da wuri ba, ya sanya take ta bacci da safe.
Ammi ta saka aka ɗorawa ruma ruwan zafi.
Ade ta ce lallai a kai su su gaida iyayen mai sunan baba ma, Ade ta yi wa Ammi addu'a da iyalan ta da fatan alkhairi, bisa jajircewa kan riƙe amana.
Takawa ne ya je yana tashin ruma, ta buɗe ido ta tashi zaune, ya ce "Ammi ta ce ki tashi haka, ki yi wanka sabuwar kakar ki ma tana nemanki".
Wani irin zilllo ruma ta yi tana haki, ta yakushi takawa a wuya ta fita da gudu daga ɗakin, bayan ta ya bi yana kiran sunanta, ta baya ta ɓulla in da ake girki idan da baƙi a gidan, ta kefa wani abu a cikin murhu.
Kan ya ƙarasa wurin kuma ta faɗi, cikin tashin hankali ya ɗauke ta, ya kaita ɗaki, sai dai a sume take.
Ammi ya je ya gayawa abun da yake faruwa, hankali tashe suka nufi ɗakin da take.
Kasancewar iman nursing take yi, ta dudduba ruma, amma babu wani abu da yake nuna akwai matsala a vitals ɗin ta.
A hankali ta yi juyi, ta ta da kai da hannunta kamar mai bacci, Ammi ta ce "Alhamdilillah, iman ku ɗaukko mp a kunna karatun Alkur'ani, ko wani abun ne ya sameta" iman ta jinjina kai ta aiwatar da abun da Ammi ta ce.
Mutane na ta zuwa ganin dangin iman, su Ade sai godiya suke yi musu na riƙe musu ƴa.
Ade ta dame su da tambayar ina rumaisa, iman dai ta fito ta gaya mata halin da ake ciki.
Har kan rumaisa Ade ta je, ta dafa kan rumaisa ta ce "Wannan ai kamar shaiɗanu ko sihiri"
Tun sanin da Ammi ta yi wa Ade, mace ce mai ibada da yawan addu'a, duk da kasancewar ta ba wata mai ilimi mai zurfi ba.
Ta dafa kan rumaisa tana ta yi mata addu'a, a hankali ruma ta ce "papa"
"Na'am mimi"
"Wata mage ce za ta sha maka jini a wuyanka, ta kasa"
"Babu wata magge fa, tsorata ki ka yi, bacci ki ke yi"
"A'a ta yakushe ni a hannuna, idonta hayaƙi ma yake yi" ta nuna musu hannunta, in da aka karta mata farata.
Ade ta ce "yarinya na jego kun barta tana yawo ko ina, gashi ba ta son ɗan kwali, idonta ne ya buɗe take gane-gane ai". Aka samu dai ruma ta farfaɗo, sai dai ba ta magana sosai.
A yammacin ranar su Ade har gida suka je, suka gaida mama, dan a washegari suke son komawa.
Mai sunan baba ya tabattar musu da yardar Allah, zai kawo musu iman, ta ga dangin ta.
Har gida suka sake bin mai girma wambai, suka sake yi masa godiya, turaki kuma a lokacin yana Germany.
Hajiya Lubabatu wani irin ciwon kai ta din ga fama da shi, mai tsananin gaske, da har ta kai ba ta gane mutane sosai, kuma ba ta son haske sai duhu, tayi ta surutai na fita hayyaci, haka aka kaita asibiti aka ajiye.
Ranar da su Ade suka koma, ranar mai sunan baba ya koma lagos shi ma, sai dai mahmud ya rasa sukuni, amma bai gayawa kowa abun da yake damunsa ba, iman ta yi wa mahmud godiya, daga shi har mijinta, bisa ga namijin ƙoƙarin da suka yi mata
Still a yammacin ranar, wani tashin hankalin ya sake afkuwa, Allah ya yi wa galadima rasuwa, wato mahaifin jabir, Senator wakili kuma ya hau jirgi domin zuwa Mexico, sun samu plane crash, da shi da wasu manya-manyan ƙusoshi a Nijeriya, wanda galibin su tare suke harƙallar smoke duk suka mutu.
Duk mutuwa mutuwa ce, takawa yana jimamin rashin ɗan uwan mahaifinsa, gefe guda kuma yana farincikin hukuncin lokaci ɗaya, da Ubangiji Allah ya haɗa azzalumai yayi musu.
Ahalin masarautar kuwa suka shiga taradaddi da damuwar gagarumin rashin da aka yi, turaki ne ya yi clearing komai, ya taho da gawar Kano. Ga matarsa na can kwance a asibiti, ɗan sa kuma aka kawo shi cikin sarƙa, sai a lokacin mutane hankalin su ya koma kan cewa matar galadima ba su suka yi jinyarsa ba, baro shi suka yi a can, aka din ga Allah wadai da ita.
Kwanaki uku da rasuwar galadima, ba a ga Mummy ba, mutane suna ta tambayar Ammi, wai ba su ga Mummy ba.
Kwana na huɗu mahmud ya je ya samu ammi, ya roƙeta dan Allah ta kira takawa da rumaisa da iman, su haɗu a sashin Mummy.
Ammi ta ce masa ba damuwa, dan kuwa yanzu ba ta ƙaunar duk wani abu da zai sanya mahmud ɗin damuwa.
Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba, da suka ga Mummy, gaba ɗaya jikinta a ƙone, sai ihu take tana kiran sunan rumaisa, ruma kawai ta fashe da kuka ta rirriƙe takawa saboda tsoron da Mummy ta bata.
Wambai ya kalli Mummy ya ce "Jamila, ya aka yi ki ka ƙone haka?".
Cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali, ta din ga faɗar miyagun abubuwan da ta aikata ita da Hajiya Lubabatu, babu wanda yafi ɗaga musu hankali, irin yadda ta kai Adam wurin boka a ka zuƙi jininsa, kuma duk shekara irin bala'in da yake shiga saboda asirin da tayi masa.
Kasancewar sa da runaisa ne, ya sauƙaƙa masa wasu abubuwan, kuma a wannan karon ma, aljanar ce ta zo shan jini da take duk shekara, ta kasa ta sanya ruma naƙudar dole ta kashe ɗan, still ta cigaba da bin adam ta sha jinin da ta saba, saboda ba zata iya cigaba da aikin da aka bata ba, sai da jininsa, shi ne take ta dambe da rumaisa, ta fito a suffar mage, rumaisa ta jefata a murhu. Shi ne ta shiga jikin Mummy, ta ce sai dai tayi jinyar a jikinta, idan mutuwa ce su mutu tare tun da tsayin shekaru ita take yi wa aiki. Wannan matar da rumaisa take gani, da hayaƙin da idonsa ke yi, aljanar take gani. LA ILA HA ILLA ANTA SUBHANAKA INNI KUNTU MINA ZALIMIN, da rumaisa ta riƙa, tun da lokacin da ta san falalarta, take ganin fa'idarta a rayuwar ta.
Wambai ya ce "Anya ba surutan ciwo ne ya sanya take maganganun nan ba".
Mahmud ya girgiza kai ya ce "Ba zafin ciwo bane, muna bibiyar duk wayar da Mummy take yi, kuma tun asali na san wasu abubuwan, ba abun da zan iya yi a kai ne"
Kuka ammi take kamar ta fita a hayyacinta ta ce "Jamila me nayi miki haka a rayuwa ne? Haba Jamila shikenan bawa ba zai ɗau ƙaddara ba, duk saboda marigayi ya fara aure na?"
Mahmud ya zube a gaban Ammi ya ce "Ammi, dan girman Allah ki yafewa Mummy, na sam ta cutar da mu, amma ta riƙe ni kamar ita ta haifeni, dan Allah ki yafe mata"
Ruma ta ce "Wallahi ba zata yafe ba, nima ban yafe ba, dukkanin mu bamu yafe mata ba, dare na din ga bi, ina kai ƙarar ku wurin Allah, sunayenku na din ga gaya wa Allah, kuma yayi mana maganinku, yau na cika alƙawarin da na ɗauka".
Su Fauziyya sai kuka suke yi, wambai ya ce "Jamila baku yi wa kanku adalci ba, ki ka saka na din ga ganin baiken Binta, ina goyon bayanki, kanki ki ka yi wa. Binta ki ɗauki yaranki ki tafi da su, Allah ya haɗa miki kansu, mun yi magana da mai martaba da ƴan majalisar sarki ma, Adam ne zai gaji kujerar galadima. Binta ki yafe mini abubuwan da suka din ga faruwa, ke kuma wannan yarinya rumaisa Allah ya ƙara haskaka rayuwarki, kin kawo sauye-sauye da tarin alkhairi a wannan gida".
Ammi ta rungume Mahmud tana rarrashinsa, sosai yake kuka yana Ammi ta yafe musu baki ɗaya.
Su Fauziyya sai kuka suke yi, ruƙayya na gefe ba ta iya magana, dan tun da Mummy ta fara rashin lafiya abun ya shafeta, take abu kamar taɓaɓɓiya.
Kwanaki uku aka yi bikin naɗin sarautar takawa zuwa galadima, shi kuma ya yi wa rumaisa sarautar garkuwar galadiman kano.
Kwananta arba'in da haihuwa, ya biya musu umara, shi da ita da ammi da mama, suka tafi domin nuna Godiyar su ga Allah.
Kamar yadda mai sunan baba yayi alƙawari, Iman ta je ta ga danginta, mutane masu karamci da tarin dukiya.
Kamar yadda ammi ta yi alƙawari, sabir na isa shiga makaranta, ta basu ɗan su, lokacin ruma ta kammala secondary school, sai dai da laulayin wani cikin ta shiga makaranta, take karantar criminology. Kamar yadda suka yanke shawarar hakan ita da takawa.
Cike da tausayawa mai sunan baba yake kallon iman, ta shirya ranar graduation ɗin su, cikin ta kamar yayi magana saboda girma, scaninc ya nuna tagwaye ne a cikinta.
Mai sunan baba in dai yazo baya bari ta yi aikin komai, manyan mutane sun halarci bikin kammala karatun su iman.
Hajiya Lubabatu brain cancer ta samu, kanta ya din ga ɗurar ruwa, aka fita da ita ƙasashen ƙetare, sai dai duk da an saki Jabir, bai iya zuwa yayi jinyarta ba, sai ƴan uwanta.
Mahmud ya koma aiki, idan ya zo kuwa, kullum sai ya je duba Mummy, sai dai abun nata babu cigaba, kullum ciwo ƙara jagwalewa yake yi, an kai ta asibiti dressing ake yi, amma ƙuna sake jagwalgwalewa take yi, tana wani irin wari.
Turaki ya tattara iyalin sa yayi watsi da su, duk wani abu na kyautatawa tsakanin su, ya daina yi musu, Jamil aka din ga iƙrarin ya mutu a hannun DSS saboda babu wanda ya san a in da yake.
Mai sunan baba kan Iman ta haihu, ya canza musu gida, gida mai kyau sosai da sosai, daga Lagos yake sayo kaya yana aiko wa da Usman da Aliyu kayan takalma, computer da yadiddika da lesuna da ga Aba yana aiko musu da shi, iman da ruma da nusaiba suka haɗa kuɗi, suke tura masa suma suna karɓar takalma da laces.
Yaya Abubakar da yayi aure, jigawa ya koma, saboda a can yayi karatu ya saba da mutane, kuma cikin ikon Allah ya samu aiki a can.
Alhaji Aminu ya din ga jan mai sunan baba a jiki, yana koya masa yadda ake importing kaya daga ƙasashen ƙetare, mai sunan baba ya ce a koyawa su Aliyu, sune suka fi ga harkar kasuwanci, kar son rai ya shiga lamarin tun da yana aiki da hukumar hana fasa ƙwauri.
Tagwayen mata aka yi wa Iman aka ciro mata, masha Allah kyawawa tamka su suka yi kansu, lokacin mimi ma ta yi nauyi sosai, aka sha shagalin suna, an yi wadaƙa da shanu da nono a haihuwar nan, mai sunan baba ya sanya sunan Ammi da mama.
Abdallah ma a DSS ya samu aiki, yana abuja tare da Bashir, cikin ikon Allah babu wanda Allah bai ɗaukaka a ƴaƴan mama ba, kuma galibi duk a sanadin rumaisa ne.
Kasuwanci ya buɗewa su Yaya Aliyu, suka tattaga aure, mama ta ce duk su yi Allah ya taimaka.
Mahmud ma yayi aure, Yasir kuwa sai ƙarshen shekara yake samu yazo ya koma, zaman canada ya yi masa daɗi yana ta karatunsa, ga wata irin shaƙuwa tsakaninsa da ƴar anty laila. Mijin anty laila yana ta jaddada mata, shifa idan Yasir ya kammala karatun sa, a nan zai samu aiki su cigaba da zamansu, sannan kuma da ya kammala karatun ya bashi anam.
Ƴan mazan mama, gidaje uku suka saya, a jikin nasu, suka faɗaɗawa mama shi, dan cewa tayi dan Allah yayi musu arziki ba zata bar unguwar nan ba, tana fatan suma su ci albarkacin ruma da ƴan uwanta.
Hakan ya sa suka gyara layin, aka yi masa kwalta da kwalbati, aka sassaka sola, wannan ya shiga da abun alkhairinsa wannan ya fita.
Mummy ta koma tamkar mushe da rai, saboda wari, kuma tana ji tana gani, gida ya koma hannun ammi, ta malleke komai da take ta ƙoƙarin hana faruwar hakan. Ba tare da ƙyashi ba, ammi ta din ga nemawa ruƙayya magani, ta ce in dai tana raye ba zata bari ɗan marigayi galadima ya wulakanta ba.
Adam ya sauyawa ruma gida, manyan motocin take ja, da ƙananun shekarunta sai ta birgeka, saboda har a lokacin ba ta haɗa shekara ashirin ba, ta saka ya ɗaukko mata ɗan mai unguwa mai hanata shiga lambu sata, yake kai Sabir makaranta ana biyansa kuɗi mai yawa.
Adam ya ɗauke mata komai, dan haka kuɗin kasuwancin ta a sama suke, sai dai tayi ta kyauta kasancewar ta mai kyauta ce. Ba ƙaramin girmama rumaisa suke yi ba, saboda rawar ganin da taka a rayuwar Adam, dan shi kansa duk wani abu da zai taɓa mutuncinta, ko tayar mata da hankali fito na fito yake da shi.
Ƴan unguwarsu ruma har murna suke su ga danƙareriyar mota a ƙofar gida, sun san akwai kaɓakin alkhairi ranar.
Hajiya Lubabatu ce ta fara mutuwa, ba tayi arba'in ma Mummy ta bita, ammi ta ji mutuwar nan ba kaɗan ba, hakan ya sa ta ce duk ta yafe musu, kuma ta rungumi Fauziyya da ruƙayya ta cigaba da riƙo, baba uwani a can garin su mahaifinta aka ganota, Cancer ya kama mata ƙafafuwa ita ma, babu kuɗin da za ayi mata aiki, ammi ba ta yi shawara da wani ba ma, ta tura sidi aka biya kuɗi, aka cire mata ƙafafuwan ta saya mata keken guragu tare da bata jarin sana'a.
Rumaisa kafin ta gama makaranta sai da ta haifi ƴan maza biyu, ta din ga Addu'a "Allah kar ka sa na yi irin ta mama na haifi ƙanwar maza, ba zan iya ba" takawa ya din ga yi mata dariya ya ce ashe kina sane ki ke tsiyata ku.
Idan ta tuna wasu rashin hankalin da tayi a baya, ta ji kamar ta yi wa kanta duka, babban abun da ya bata mamaki, bai wuce duk shekarun nan takawa yana ajiye da wasiƙar da ta rubuta masa, na cewar ya taɓa mata nono, yayi ta tsokanarta yana dariya.
Samha kuwa rayuwa ta juya mata baya, dan abun da Jamil ya aikata, da wanda tayi ita ma, ya zame mata baƙin fenti, aka rasa mai aurenta, duk gayu da ƙwalisar samarin duk suka watse.
Runaisa ba ta bar harkarta ta zane-zane ba, dan har rubuce-rubuce take yi, kamar wasa ta zama popular manyan mutane suke sayen zane-zanenta.
Cikin ikon Allah rumaisa ta zama criminal lawyer, sunanta ya shahara sosai, ga ta lawyer, ƙwararriya wurin zane-zane da rubuce-rubuce, kuma ƴar kasuwa. A duk lokacin da aka yi hira da ita, ta kan ja hankalin mutane a kan cewa a duk lokacin da aka samu ɗa mara ji kamarta a cikin al'umma, kar a tsangwame shi, a ja shi a jiki a duba wace irin baiwa Allah ya yi masa a dafa masa a kanta, saboda Allah baya halittar abun da ba shi da amfani. Kamar dai ita da tun a tasowarta ko makaranta ba ta so saboda rashin jin ta, amma cikin ikon Allah a yanzu, ilimi na addini da na zamani sai dai ta koyar da wani bisa jagoranci da jajircewar mahaifiyarta yayyenta da kuma mijinta ta zama abun da ta zama a yanzu.
TAMMAT BI HAMDILLAH!!!
GODIYA TA TABBATA GA UBANGIJIN TAIKAI MAI KOWA MAI KOMAI, DA YA BANI IKON FARA RUBUTUN NAN YA BANI ARON RAI DA LAFIYA NA KAMMALA SHI. ALLAH YA SANYA A AMFANA DA DARUSSAN DA KE CIKI, AKASIN HAKA KUMA ALLAH YA YAFE MANA.
SAƘON GAISUWA TA MUSSAMAN, UWAR KIRKI UWAR ALJANNA UWA TA TA KAINA, MALAMA NAFISU ADAMU, DA MUKA FARA TARE HAR NA KALLAMA ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MIKI HAR GADON BACCINKI.
GODIYA TA MUSAMMAN GA ƳAN UWANA. ZEE KUMURYA NIMCY LUV, TARE DA SAURAN MARUBUTA MAIMOON, MARYAM MAI ƘOSAI ANTY ZEETY, KUNA DA YAWA GASKIYA DUK INA JI DA KU DAI.
BAN MANTA DA KU BA, MUTANEN DA SUKA BANI TALLACE TALLACENKU MAMAN MEENAT COLLECTION MAMAN KHADIJAH MAI SABAYAR ƳAN GAYU TARE DA MAMAN ILHAM KUN GA DAI YADDA SUKA KANKARO RUMA A GIDAN AURENTA, KAR A GAJI DA CIGABA DA PATRONIZING KAYANSU, TESTED AND TRUSTED RUMA TA YI AMFANI DA SU KUN GANI.
WAƊANDA SUKA YI SUPPORTING ƊINA, WURIN SAYEN LITTAFINA, ƳAN NORMAL GROUP, SPECIAL DA AKE TURAWA TA PC, ƳAN AREWABOOKS DUK INA GODIYA, DA SUPPORTING ƊINA ALLAH YA ƘARO MUKU ARZIKI DA BUƊI MARA YANKEWA.