Kenza eBookz

Karfen kafa complete rufaida omar - Chapter 8

Karfen kafa complete rufaida omar - Chapter 8

Karfen kafa complete rufaida omar Chapter 8: Karfen kafa complete rufaida omar Chapter 8. Rayuwa ta yiwa Aliyu zafi yakan ji kamar ya yi hauka duk ranar da…

3,309 words

Rayuwa ta yiwa Aliyu zafi yakan ji kamar ya yi hauka duk ranar da Babansa ya kulleshi a ɗaka ya hanashi fita ko nan da can. Makaranta dama ba labarinta don tun ranar da aka rabashi da gidan Abulle ya zuciya ya ce ya fasa karatun gaba daya. Ranar da ya ɓalle ya fice daga gidan, bai koma ba sai da ya yi mankas. A ranar Innarsa ta yanke jiki ta fadi. Tun daga wannan rana ba ta ƙara lafiya ba. Ciwon Innarsa ya sanyaya jikinsa kadan, duk da a ganinsa matar sam ba ta damu da shi ba hakan bai mantar da shi matsayinta wurinsa ba.

Bayan farfadowarta ya daukar mata alkawarin ya dainawa, ba ta ce mishi uffan ba har ya fice. A hankali kuma ya dinga ɓoye munanan halayyarsa, ya maida turare abin fesawarsa, ba ya taba yarda ya zauna na awanni da yan uwansa gudun kar a ga sauyawar leɓɓansa adalilin shan taba. Sai dai ya zama masifaffen karfi da yaji, ya daina ragawa duk wata mace da za ta gasawa Innarsa magana. Akwai ranar da ya kusan yiwa Amaryar babansa duka duk don ta zagi Inna a fakaice. Wannan ya fusata Baban ya ce ya bar mishi gidansa. Zuciya irin ta Aliyu ya sanyashi haɗa komai nasa ya koma gidan Abulle. Ba abinda ya boyemata har da karin gishiri, nan kuwa ta tara meeting ta gargadi kowa akan takurawa Aliyu da ake.

"Duk wanda ba zai bi shi da Addu'a ba kar ya zageshi ya kara bin duniya. Kai kuma Abdussalamu ba ka isa ka rabashi da gidan ubansa ba. Ko yau yaro ya ga dama zai je. Don kunga an samu ya soma gyaruwa shikenan kuma sai ku kara sanyashi ya bi duniya? Ke kuma Amarya ki ci gaba, idan dai za ki ci gaba da gasawa Amina magana, yaron nan ba zai fasa kirɓarki ba. Shashasha."

Nan yaran suka shiga ba ta hakuri gami da nunamata kuskuren Aliyu cikin sanyi. Aliyu ya ba Amarya hakuri aka ce ya ci gaba da zama anan gidan Abulle. Bayan watsewar surukan da jikoki, Abulle ta nemi shawarar ta yanda za'a inganta rayuwar yaron tunda ya ƙi boko. Nan take Justice ya kawo shawarar a dorashi kan kasuwanci. Ba musu kowa ya yi na'am. Justice da kansa ya dauki nauyin budewa Aliyu shago da komai. Nan kuwa Abulle ta yi ta sanyamasa albarka daga nan aka tattauna batun auren yanmatan da suka isa aure a zuri'ar da zarar sun kammala Sakandire don a sannan suna ajin karshe. Budar bakin Abulle ta ce.

"Banda Muhibbat, na yi mata miji."

Kalamanta sai da yasa kirjin Justice bugawa, tsoransa kar ya zamana abinda yake gudu ne zai afku. Duk yanda suka so jin waye mijin Muhibbat ta ƙi basu fuska. Asalima goronta ta hau tauna ta ce su mike su bata wuri ta sallame su. Jiki ba kwari dai Justice ya tafi.

Ita kuwa Abulle tun wani dare da ta kama Muhibbat na kallon hoton Aliyu tana kuka ta ci alwashin sai ta auramata shi. Ba ta bari ta ganta ba ta juya ta ci gaba da baccinta cike da farin ciki da tausayin yarinyar.

Cikin luɗufin Allah zaman kasuwa ya karɓi Aliyu, dakyar yake ajiye wasu kudaden don shi da za'a bar shi ya yi facaka zai fi son hakan. Bai fasa shaye-shayensa ba sai dai ya fi yi da dare wanda daga ya sha ya ɗan yi tamɓelansa zai ɓige da bacci. Taba kuwa ko a kasuwa zuƙarta yake don zuwa lokacin bai dauketa abar tashin hankali ba. A wannan lokacin ne kuma Inna ta tashi lafiya kalau, daga baccin rana ta gamu da ajalinta, ta rasu. Mutuwarta ta girgiza jama'ar gidan musamman kishiyoyinta wadanda suka cika da dana sanin zaman gaba da hassadar da suka yi da ita. Batun mijinta kuwa ba'a magana, Abdussalam ya shiga tashin hankali marar misaltawa. A gefen Aliyu da yaran Innar mata suma ba'a magana.

"Ka ji tsoron Allah." Shi ne abinda Innar ta fi yawan fadamasa a kalamanta masu tsawo, sai a sannan ya san yana son mahaifiyarsa halinta na banzatar da lamuransa kawai ya tsana. Yan uwanta daga Gombe duk sun zo. Mutuwar Inna ya karawa Abulle da Muhibbat tausayi da son Aliyu.

Suna kammala Sakandire magabata suka yiwa Muhibbat caa akan ta fiddo da miji, ita kuwa ta kasa zaɓen ko ɗaya saboda Aliyu.

Aka yi sa'a koda Abulle ta tari Aliyu da zancen Muhibbat don jin ta bakinsa sai ta ga ya hau murmushi, nan take ya nuna ya amince don dama ya jima da sanin yarinyar na sonsa. A cewarsa ko ba komai zai ƙara martaba a idon duniya kasancewar mahaifinta wani ne kuma ɗan uwan mahaifinsa.

Tashi ɗaya kowa ya ce bai yarda da auren ba, Justice dai ya yi alkunya ya yi shiru, daidai da mahaifin Aliyu bai amince a ba Aliyu auren Muhibbat ba. Ita kuwa Abulle ta rantse ko bayan ranta aka ƙi aurawa Aliyu Muhibbat ba ta yafewa yaranta ba. Kuma bakinta sai ya bi su, wannan ya tashi hankulansu, a dole suka amince.

Justice ya yi mamakin murnar da Muhibbat ta nuna. A gefe guda Mamarta Saudatu na cika da batsewa.

"Dama kina sonsa?" Ta riga Justice jefamata tambaya, ta kara sunkuyar da kai tana murmushi kafin ta mike a guje ta nufi daki. Saudatu ta dubi Justice dake hamdala da alama abin ya mishi dadi.

"Kana nufin ka amince da auren yaron da ya fitini kowa a dangi da ɗiyarka kamila?"

Yayi murmushi.

"Allah Ke shiryawa, kuma Ya shirya Aliyu sai dai a ci gaba da yi mishi addu'a. Farin cikin Muhibbat ya fiyemin komai, fargabana kar ya kasance ba ta sonsa. Tunda har tana sonsa shikenan, Allah Ya tabbatar da alheri. Ba zan ƙi bin umarnin Mahaifiyata ba."

"Tabɗijam!"

Abinda Mama ta furta kenan. Rigima sosai ta tayar akan lallai sai dai a fasa auren, karshe Justice ya zuciya ya fita harkarta, har yaji ta yi da ta gaji ta dawo ɗakinta. Abulle ta rantse ba don darajar ta haifomata sanyin idaniyarta Muhibbat da sauran jikoki ba da sai ta saka an saketa. A dole ta dangana aka yi auren Aliyu da Muhibbat wanda alokacin ya yi nisa da son Ramlat.

Muhibbat ta sauke ajiyar zuciya, ta kara maimaita sunan Ramlat da mijinta yake yawan kiranta da shi a shimfiɗa. Hannu ta sanya ta dauke hawayenta. Kauna da son Aliyu abu ne da ta fara tun ba ta mallaki hankalin kanta ba. Ba kuma ta jin za ta daina. Addu'a za ta dage da yi har Allah Ya fidda Ramlat daga ran mijinta. Ba ta santa ba ko a hoto, ta dai santa a bakin mijinta. Takan yi mamakin yanda Ramla ke aminta su yi waya da mijin aure har cikin dare. Ta rasa gane SON ZUCIYA ne ko kuwa a'a? Fatanta Allah Ya karkato hankalinsa gareta su ci gaba da rayuwa kamar yanda suka fara a farko.

***

*DAWOWA LABARI*

🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

10)

Tarr ta bude idanunta jin motsin bude kofar. A hankali ta kai hannu saman dirowa ta dauko wayarta gami da duba lokaci, karfe uku saura mintuna, mayarwa ta yi ta ajiye kirjinta na wani irin zugi tana cin ɗaci a maƙogwaro. Miƙewa ta yi ta nufi hanyar falon, kunnuwanta ba zasu iya juriyar sauraron hirarsu ba don haka ta dawo dakin. Banɗaki ta shiga ta kama ruwa gami da ɗauro alwala, nafila ta yi raka'a biyu, ta jima cikin sujjada tana zubar hawaye gami da kai wa Allah kukanta kafin ta ɗago ta sallame. Nan ma Alkur'ani ta jawo ta karanta a karshe ta yi addu'a ta shafa.

Shi kuwa Aliyu tun da ya kira ya soma zazzaga ruwan kalamai ga Ramlat mai nuni da kewa da kuma damuwar halin da za su shiga idan wani abin ya afku.

"Na kasa bacci, na kasa samun nutsuwar yi, kin kuma san ke ce. Ina tsoron na rasaki Baby."

Ya ji motsin rufe kofa, ya waiwaya sannan ya kara kishingida ya ci gaba da wayarsa hankali kwance.

Daga ɓangaren Ramlat ta kara cusa kai cikin bargo yanda A'isha ba za ta motsa ba.

"Na fi ka shiga wannan zulumin, Sweet Aliy babu ta yanda zan rasaka in sha Allahu. Ka kwantar da hankalinka."

Murmushi ya yi mai sauti. Nan kuma suka shantake suka shiga hira har da kyakyacewa.

Muhibbat zaune saman darduma ta zurfafa cikin tunani, ta ji labarin kaddarorin aure da dama, sai dai irin nata ya bambanta da kowanne. Ta yi sanadin sauyawar lamura da dama. Ta rugurguza farin ciki da dukkan tanadin da ta yi a zamantakewar aurenta. Shigowarsa dakin ya katse tunaninta, ya kai duba ga inda take, sai kuma ya dauke kai ya koma saman gadon ya kwanta gami da juyamata baya. Ta tsayar da idanunta ga kallon bayannasa, a duniya ba namijin da take so irin mijinnata, dama so na rikiɗewa har haka? Da me wannan baiwar Allahn ta fi ta? Meyasa yake ƙuntatamata saboda ita? Meyasa ta kasa samun zaman lafiya a rayuwar aurenta duk a dalilinta? Ta dauka duk mace mace ce!

Wasu hawaye masu ɗumi suka zubomata ganin halin ko in kular da yake nunamata aduk sadda irin hakan ta faru. Bacci har da sakin munshari ta tsinceshi yana yi. Ta kai hannu ta shafi cikinta ɗan watanni biyu kacal, a hankali ta lumshe ido tana addu'ar neman sassauci da kalar rayuwar mijinta.

*** Hajiya ta yi mata ƙuri da ido.

"Kwanakin nan kin fiye yawo, kin je gidan Amrah ya fi a kirga, yau kuma Muniru ki ka tuna? Yaushe sabo mai karfi ya shigeku har haka?"

Ta turo baki kadan.

"Dan uwana ne fa Hajiya."

Abba dake karanta jarida ya ɗago kai yana dariya.

"To kinji amsarki ai. Kwana nawa ne za ta tattara ta bar miki gidan ke da autarki? Ki bar ta ta sada zumunci, ta samu lada biyu. Na juma'a da kuma zumuncin."

Ramlat ta sauke ajiyar zuciya, dama tana sane ta tambaya a gaban Abban don tasan zai goyi bayanta. Tun safe Hajiyar ke cin magani tana mitar wai ta sauya daga Ramlatun da ta sani akan ta shigo tana waya ta yi shiru har ta fita daga dakin. Wannan ne kuma ya tabbatar da zargin Hajiyar cewa akwai saurayin da ke huremata kunne a yanzu. Koda Hilal bai ce komai ba, ita ta lura ɗiyar ta bar rawar kafa a kansa da komai ma.

"Ban wayarki. Idan kin dawo kya karɓa."

Maganar Hajiyar ya daskarar da ruwan jikinta, ta bude baki za ta yi magana sai dai tuni miyan bakinta ya daskare jin muryar Abba na magana cikin nuni da goyon baya.

"Ba ta idan har za ki tafin. Tunda gidan Yayanki ne ai ba damuwa. Zuwan dai ake kokarin hanaki."

Ba haka ta so ba don dama da biyu take son fitar, Aliyu na son ganinta ko ta wane hali don su tattauna su samarwa kansu mafita sai dai kuma da alama karyarsu ta kare muddin wayarta ta shiga hannun Hajiya. Ba ta da zaɓin da ya wuce ta fiddo wayar daga jaka ta miƙa wa Hajiyar.

_Idan lokacin bayyana soyayyarmu bai yi ba har yanzu, sai yaushe? Sai yaushe ne za'a san abinda muke ta ɓoyansa? A soyayya ba'a shakka balle tsoro. Idan aka yi hakan ba'a yi mata adalci ba, ba'a fitar da hakkinta ba._

Wadannan kalaman Aliyu ne, nan take ta ji wani kwarin gwuiwa. Ƙarƙari Hajiya ta bincika wayarta ta kuma bibiya shiga da ficen kiranta. To me ta aikata? Ai ba haramtacciyar soyayya ba ce.

'Nema cikin nema?'

Ta ture tunanin ta hanyar yi musu sallama ta fita, Abba ya bita da kyakkyawar addu'a yayinda hankalin Hajiya ya koma ga wayar ta yi mishi ƙuri kamar mai jiran amsa daga cikinta.

"Menene wai Rabi'atul Adawiyya? Meke damarmin ke da zuciyarki? Kwanakin nan ina lura da tsaurin da kike ƙara yi game da yarinyar nan. Ta yi wani abu ne?"

Hajiya ta yi shiru tana dan kallonsa, ta fi kowa sanin halin mijinta, yana da sauki amma idan ranshi ya ɓaci babu kyau. Bai fiye zargi ba kamar yanda bai fiye daukar magana ba idan har ba shi ya ganewa idanunsa ba ko kuma yana da hujja. Tasan idan ta furta wani abin bisa zargin zai iya yiwuwa nata ne zai yi wari don haka ta ɗan murmusa.

"Ba komai Abban yara, tunaninka ne kawai ya ba ka hakan. Ramar da take yi ne kawai bana so, a kanta aka fara aure?"

Ya riko hannun Hajiya yana murmushi.

"Kar ki damu, ko kin manta ban da auren shirin zana jarrabawa ta ke? Na dan lokaci ne In Sha Allah. Ko kin manta kalar naki zullumin dab da aurenmu?"

Da sigar wasa ta harareshi suka yi dariya gami da yiwa Ramlat din kyakkyawar addu'a.

*** Cike da fara'a Anti Bilkisu ta tarbeta.

"Lale marhabin da Amaryarmu. Yau an tuna da ni?"

Ramlat ta kama hannun Maama babbar ƴar Yaya Munir suka zauna saman kujera. Tana dariya

"Kai Anti, ko wata fa ban yi ba rabona da gidannan."

Taɓe baki Anti Bilkisu ta yi tana dan murmushi.

"Ai shikenan, nasan da mutuniyata ce har da kayan kwananta zan ganta. Kin dai wanke kanki tunda kin zo. Yau na huta da shiga kicin."

Dariya ta yi kawai sanin halinta, wato dai tana nufin A'isha don sun fi ɗasawa, dama murnar da take na zuwannata kusan da biyu ne. Wata irin mace ce mai son jiki da ba ta son aiki, burinta kawai a yi mata, wasu lokutan akwai ta da shan ƙamshi da kuma sakarwa mutum hidima duk sadda ya kai mata ziyara, wannan ta sa ba ta fiye zuwan ba. Da ace ta san ma dalilin zuwannata da sai ta ji kamar ta shaƙeta.

"Mutuminki kuwa jiya kusan wuni ya yi a gidannan, kinsan fa ni ya damƙawa haɗa lefe don haka ki min biyayya idan kina son ganin tsala-tsalan kaya."

Tsaki ta yi wanda ba ta san ma ya fito fili ba, da mamaki Bilkisu ta dubeta.

"Tsaki ki ka yi?"

Sai ta ɗan basar.

"Wayata na tuna na bari a gida, kuma ina son yin waya. Don Allah ban aron ta ki."

"Au, toh ki gama wayar a karshe ki ce ya turon kati don nasan ƙararwa za ku yi."

Ta ƙarashe tana mai sanya kai ta fice daga falon zuwa ɗaki. Da sauri Ramlat ta mike ta nufi kicin, lambobin da suka riga suka zama tamkar lazimi a wurinta shi ta shiga rubutawa kafin ta danna kira. Sai safa da marwa take yi a kicin din har kiran ya shiga.

"Assalamu alaikum."

Ta tsinci muryar mace, muryar da ba ta yi kama da ta Muhibbat ba don akwai sadda ta taɓa kiran Aliyun, ta daga ta ce ba ya kusa. Ranar ta tabbatar sun kusa yin kaca-kaca da Aliyu don har rantsuwa ya yi mata a kan idan tana so ma zai sauwakewa Muhibbat duk a dalilin kishin da ta motsamata.

"Hello."

Aka kara fada daga can bangaren sai dai ta kasa magana. Tana shirin katse kiran cike da faduwar gaba ta tsinci muryar macen.

"Kanwarsa ce Habiba, Yaya Aliyun yana ciki wurin likita su na magana."

Da wani irin matsanancin tsoro ta watsamata tambaya kamar a tsawance.

"Meya sameshi?! Wane asibitin ne?"

Habiba sai da ta ɗan yi shiru kafin ta yi magana cikin rashin wayo.

"Anti Muhibbat ce ta yi ɓari, ya bar wayar a dakin ne, idan ya dawo zan fadamasa kin kira."

Da sauri ta katse kiran ta kuma goge lambar daga wayar. Tasan ba ta son Muhibbat, ba kuma tsana ba, a'a, kishinta take. Sai dai fitar cikin ya zo mata a bazata, ba ta san sadda ta shiga fitar da hawaye ba, ta ajiye wayar a gefe ta hau fiddo kayan girki jikinta a sanyaye. Ba ta taɓa jin tausayin Muhibbat din ba sai a wannan rana.

Tana cikin gyara kayan miya ta tuna ba ta ma tambayi Antin abinda za'a dora ba, tana niyyar fita ne kuma ta ji wayar ta dauki ƙara, jiki a sanyaye ta karasa ta daga, lambar Aliyun ne.

"Ki yi hakuri, waccan ƴar rawar kan ce ta ɗaga. Ta fadamaki muna asibiti ko? Kar ki damu fa zan zo din. A ina za mu hadu?"

Ita kuwa wane irin rashin adalci ne wannan da zai sa ta nemi ganinsa a yau duk da tashin hankalin da matarsa ke ciki yanzu? Ko ba komai a yau Muhibbat ta cancanci duk wata alfarma. Don haka ba ta yi ƙasa a gwuiwa ba ta shiga girgiza kai kamar yana gabanta.

"Ka yi hakuri, nima ce maka zan yi Hajiya ta karɓi wayata har sai na koma gida sannan za ta maidomin. Yanzu haka ina gidan Yaya Munir, wannan wayar Anti Bilkisu ce."

"Kenan ba zamu hadu ba?"

"Ka yi hakuri don Allah Sweet Aliy, a yau Muhibbat na bukatar kulawarka. Ka ce ina mata sannu. Zuwa gobe zan san yanda za'a yi mu hadu ko bayan tashi daga makaranta ne."

"Yau ita ta samu wannan alfarmar a wurin sarauniyar masu kishi?"

Ya fadi cike da zolaya yana ƴar dariya. Murmushi kawai ta yi mai sauti.

"Ai ina tunanin gida zasu wuce da ita har sai ta samu lafiya. Naga yayyunnata sai wani kallo suke watsamin kamar ni na janyo zubewar cikin. Mtsw, ita kanta In-law ba don darajar Granny ba sai na fadamata maganar da za ta hanata bacci."

Ta gane In Law din da yake nufi, wato Mama mahaifiyar Muhibbat, a duniya ya sha fadamata ya tsani matar saboda ko kallo bai isheta ba har gobe. Idan ma ya gaidata amsawar kamar mai taunar maɗaci haka ake yinta.

"Allah Ya bata lafiya."

Ta furta cike da tausayi.

"Ke na yi wani karambanin. Wayarki na soma kira kafin wannan. Har kuma saƙo na aika da ban ji kin ɗauka ba."

Ta fiddo ido waje game da riƙe kirji.

"Dagaske?"

"Yes, amma ya naji kamar kin razana? Mene a ciki? Mene don Hajiya ta san da zamana? Ko kina tunanin lokaci bai ba da zamu bayyana abinda ke zukatanmu? Saboda Allah na gaji da wannan ɓoyon!"

Ta ɗan sauke ajiyar zuciya.

"Me ka rubuta a sauƙon toh?"

"Idan kin koma gidan kya gani. Sai anjima." Ya katse kiran, nan da nan hankalinta ya tashi har garin saurin ta kirashi, kiran Yaya Munir ya shigo ta katse. Sai da ya kusan katsewa sannan ya daga.

"Me za ki cemin kuma?"

Ta marairaice.

"Ka yi hakuri. Wallahi nima yanzu bana tsoron kwan ya fashe kowa ya ji. Kawai dai na tambaya don na sani, amma ka yi hakuri."

Sai da ta kwashi mintuna uku tana bada hakuri, karshe ya hakura ya shiga karfafamata gwuiwa akan kar ta kusa ta ji shakkar komai akan abinda yake ƴancinta. Ya na kara nunamata muddin ta bari ta auri mijin da ba ta so za ta tafka kuskure. Ita kuwa ƙara hawa take gami da hango gaskiyar hakan. Tana ji kira na faman shigowa ta ƙi maida hankali a kai, sai da aka soma warning na karewar kati sannan ta tuna ita ta kira suka yi sallama bayan ya dorata kan hanyar da za ta bi ta fidda abinda ke ranta idan Hajiya ta mata zancensa. Ba tare da ɓata lokaci ba ta goge dukkan shiga da fitar da lambarsa ta yi a wayar. Hamdala ta yi kafin ta fita ta kaiwa Antin wayar.

"Me zan dafa?" Ta katse Anti Bilkisun dake kokarin daga wayar mijinta, cikin maida hankali ga wayar a gaggauce ta amsamata.

"Duk abinda kike so ki dafa kawai. Hello."

Ta ƙarashe da daga wayar Munir. Cikin sauri Ramlat ta yi gaba tana ji Anti Bilkin na ba shi hakuri da cewa ba ita ke amfani da wayar ba, can kuma ta ji tsakinta da masifa. Taɓe baki Ramlat ta yi don ta san kaɗan daga aikinta kenan. Ko a jikinta don tana da tabbacin zai wahala Yaya Munir ya isketa cikin gidan.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull