Kenza eBookz

Kawar zuciya Book 2 by takori - Chapter 5

Kawar zuciya Book 2 by takori - Chapter 5

Kawar zuciya Book 2 by takori Chapter 5: Kawar zuciya Book 2 by takori Chapter 5. Rayyah dai dariya take tana jinsu. Sabah ta kara cewa “Saboda Allah…

4,443 words

Rayyah dai dariya take tana jinsu. Sabah ta kara cewa “Saboda Allah Rayyah nida nake da sarbadeden saurayi irin Jabir a gefe, yaro matashi me jini a jika, dan late twenties, me zan yi da Yaya Zayyan? Wannan kayan tsufan ai sai Nana Safiyyah”.

Zayyan ya tuntsure da dariya harda bugun sityari yace “amma kin yankeni! Saina gayawa Sophie, kina kira ma darling dinta tsufa tun yanzu”.

Tunda su Sabah suka zo gidan suke wani irin kula da Safiyyah da komai na kulawar gidan ya koma wuyansu, ko tsinke basa bari ta kawar, ko abinci taci nan zasu kawo mata ruwa ta wanke hannu daga zaune. Zayyan kuma ya wadatasu da kayan dadi suke ta fama, duk fitar da yayi ya dawo sai ya riko musu abinmotsa baki, musamman Rufaida Yughurt da Rufaidah Shawarma da Pizza din Dominos da suke matukar so.

Yanzu kam kowa yaga Sophie ya san dan cikin ta ya gama duk wani shirye-shiryensa na isowa duniya. Tashi sai da dabara kwanciya ma haka.

**** ***** ****

Safiyyah ta fara wata irin naquda mai matukar wahala ranar wata Litinin, Zayyan baya gida yaje supervising ginin wani sabon Estate da yake ginawa a unguwar Jahi. Kasancewar tunda watan haihuwar Sophie ya kama baya yarda yayi nisa da tsakiyar Abuja.

Sabah ta kira shi a waya ta gaya masa yazo su tafi asibiti Aunty Safiyyah fa ta fara nakuda.

Nan da nan daa inda yake ya kira asibitinta suka tura motarsu ta daukosu daga gida, shikuma ya bar komai da yake yi a Jahi, ya karya kan motarsa yayi kwana zuwa asibitin. Suka iso kusan a tare da motar asibitin data dauko su Safiyyah.

Har da shi aka hadu aka gungura gadon Safiyyah zuwa dakin haihuwa.

A cikin awannin da basu gaza uku ba Safiyyah ta haifo santalelen yaron ta namiji mai kama da shi sak. Akan idanunsa, kanta bisa cinyoyinsa, yana mai tayata nishin haihuwar cike da tausayi kamar tare da shi suke labour, yana karanto addu’a yana tofa mata. ganin halin da Sophie ke ciki a wannan lokacin ya kara masa son Mamansa Haj. Fatu, yau ya yarda haihuwa ba karamin al’amari bace ga mata, gashin kanta ya wargaje akan cinyoyinsa yana supporting dinta da kalamai na karfafawa, bai gushe ba yana mata addu’a har ta haifo masa Danliti, kuma photocopy dinsa, bulelen yaro lafiyayye mai kama dashi sak.

Amma me? Likitoci sun yi sun yi yaron yayi kuka bayan isowarsa abu ya faskara, stillbirth!

***** **** ****

Zayyan sai ya rintse idanunsa a hankali, daidai sanda tunaninsa ya zo nan, yana mai tuno kyakkyawar fuskar jaririn da ya gani a ranar, dan su shi da Sophie, sai ya ji komai na memories din wancan lokacin ya dawo masa sabo. Wato lokacin rayuwarsu daga shi sai Safiyyah a gefensa. Amma a hakan ya daure ya cigaba da tunano al’amuran da suka gabata din, a kokarinsa na nemo maslaha da warwara, wadanda duk ba masu dadin tunawa bane a gareshi.

Abin kunya da bakin cikin da yafi kowanne girma a gareshi shine, daga Mama har yaranta duka aka rasa wanda zai zo ya duba Safiyyah a asibiti, balle su jajanta ko yi musu ta’aziyyah na yaron da suka rasa, alhalin sunfi kowa sanin halin da suka shiga da wahalar da suka sha akan cikin wadda bazata lissafu ba kafin samunsa, da wadda suka sha bayan samuwarshi, in ka cire Yaya Zubaina da ta kira su a waya, tayi ta lallashinsu, ta kuma tunasar dasu muhimmancin yarda da kaddara da tawakkali akan jarrabawar Ubangiji kowacce iri ce.

Saboda Baban Muntaqa baya barinta tafiye-tafiye sosai, amma kwarai taso zuwa har Abuja din, har lokacin Zubaina a garin Kano take aure. Kullum sai ta doko musu waya ta bata lokaci ta lallashesu, tana tunatar da su muhimmancin yin hakuri, da tagomashin da Allah ya tanadarwa wadanda suka rasa ‘ya’yansu suna kanana, tace kada susa damuwar hakan a ransu. Allah da ya basu wannan din, a lokacin da suka riga suka fidda rai da samun haihuwa, shi zai kuma basu wani kota IVF dinne cikin kudura da buwayarsa.

Daga shi har Safiyyah a wannan dan tsukun kusan zautuwa sukayi a zuci da zahiri, saboda duk wata soyayyarsu da burinsu da kawar zuciyoyinsu ya koma ga zuwan Babyn nan duniya, sun gama tanadin irin tattalinsa da zasuyi cike da soyayya da kauna na iyaye, da kuma tarbiyyar da zasu bashi duk sun gama tsarawa. Kai har makarantar da zasu kai yaron sun zaba tun bai zo duniya ba saboda tsabar dokinsu ga isowarsa.

Kwarai su kadai suka san irin wahalar da suka sha kafin Allah ya basu shi ta hanyar ‘In-Vitro Fertilization’. Da irin spending din da sukayi akan samuwar cikin da rainonsa. Hakika tattalin arzikinsa ya girgiza akan haihuwar babyn nan da shirin tarbarsa.

To ina ruwan Allah! Kana naka shima yana nashi. Kuma nasa shine gaskiya. Duk jarrabawar da yayi nufi ga bayinsa shi ya san ladan daya tanadar musu akanta, zai kuma baiwa bayinsa wannan ladan a duniya ko a kiyama, akan hakurin da suka yi, in har sun yi hakurin dominsa ne sun tsarkake shi.

In kaga wadannan ma’auratan a wannan lokacin na makokin jaririnsu, sai sun yi matukar baka tausayin da nan da nan zai saka ka zubda musu hawaye.

Domin sun rasa duk wani karsashi na jikin dan adam, da kuzarin su na cikin gida da waje. Can zaka hango su tsakiyar makeken gadon su manne cikin jikin juna, suna faman sauke ajiyar zuciya ba mai iya baiwa dan uwansa baki. Ba mijin ba, ba kuma matar ba, ba mai iya lallashin dan uwansa koda da kalmar “sannu” ta fatar baki ne. Wannan ya faru bayan an sallami Safiyyah daga gadon asibiti.

Babban bacin ransa yadda Mama dasu Ya Zubaida duk suka yi shakulatin bangaro dasu. Abun yayi matukar bashi mamaki da tsoro, bai yi zaton kiyayyarsu da Sophie ta kai haka ba, tunda in akan haihuwa ne ai gashi ta haifa musu Allah ne bai barshi ba. Tun daga lokacin ya fahimci kiyayyarsu da Sophie maras dalili ce, amma ya zaiyi?

Abun ya tsaye masa a rai kwarai. Ya san tun fil azal jinin Mama bai hadu dana Sophie ba, amma bai taba tunanin abun ya rikide zuwa tsana tsagwaro irin wannan ba har a gun kannensa da babbar Yayarsa, da har zata dau ciki watanni tara ta haife dan babu rai, amma su kasa ko jajanta mata su kasa zuwa su kuma kasa kiran waya wannan abun ya tsaye masa a rai fiyeda zatonsu.

Abinda shi bai sani ba, tun daga lokacin da Safiyyah ta yanke shawarar yin Dashen haihuwa saboda gorinsu da tsangwamarsu, daga lokacinne kuma ta samu rashin son da suke yi mata ya rikide ya kara matsayi zuwa tsagwaron tsana, dama kuma sun sha alwashin koda ta haifi dan da rai tunda ta hanyar IVF ne ta samu cikinsa bazasu taba rika mata shi a matsayin Da kamar sauran ‘ya’yansu kuma jikokin Baba Bello ba. Saidai ta kai Dandume su Alaramma su goya mata.

Bai manta da lokacin da ya kira Mama ba, tun suna asibitin da Safiyyah ta haihu kafin a sallameta, ya gaya mata Safiyyah ta sauka, amma yaron ko shurawa bai yi ba.

Yasa hankaci ya tsane idanunsa ba tareda Mama ta san idonsa ruwa yake fiddawa ba, budar bakin Mama sai cewa tayi, “yo daman wannan dan nata irin sauran ‘ya’yan mutane ne da za’a zaci dole zai rayu? Dasa mata shi fa akayi ta karfi da yaji, to meye abun mamaki ko damuwa don ya zo babu rai?

Shin in tambayeku; ku duka kaida Safiyyahr, wai ana yiwa Ubangiji dole ne akan abinda bai ga damar bayarwa ba? Matarnan taka Safiyyah ‘juya’ ce Baffa, na kara fadi gaskiya juya ce, ku yarda ko kada ku yarda kuma ya rage naku.

Da zata haihu da tuni ta haihu kamar yadda kowacce mace ke haihuwa naturally. Idan ka sake yarda aka yi Dashen haihuwar Da da maniyyinka Baffa Allah ya isa ban yafe maka ba!

Tunda dai mata masu haihuwar nan ta gaske ba karewa suka yi a duniya ba!”.

Wannan maganar ba karamin firgita shi da gigita shi ta yi ba, da sauri ya cire wayar a kunnensa ya duba yana tantamar anya Mamansa Haj. Fatu ce wannan? Kodai wrong number ya kira?

Sai a lokacin ma ya tuna cewa ai ko sau daya Mama Fatu tun samun cikin Safiyyah haka siddan bata taba kiransu tace Allah ya inganta ba, ko Allah ya sauki Safiyyah lafiya, a lokacin da take goyon cikin.

Ance ba’a fushi da iyaye, amma hakika Zayyan ransa ya sosu sosai da attitude din mahaifiyarsa, abunda Mama Fatu tayi ga iyalinsa bai taba zaton uwa zata yi shi ga dan data haifa ba. Har hakan yasa ya dan dauke kafa daga Katsina, na dan wani lokaci.

Ya maida hankali ga taya su Sabah kula da lafiyar Sophie, su su kula da ita daga safe zuwa dare, shikuma ya yi nasa jegon daga dare zuwa safe.

A lokacin da Sophie take jegonnan ne kuma ya fahimci wani abu a halittarsa, wato jikinsa baida jimirin hakuri da rashin matarsa na lokaci mai tsaho.

Kusan kullum Safiyyah na barci irinna masu jego, shi kuma yana fama da shan ruwan kanwa, domin kwantar da sha’awarsa ta da namiji, kwarai ya kan gaza hakuri da ita cikin dare, baya kuma son ketare iyakar Ubangiji don har lokacin jinin biki Safiyyah take yi.

Ga Safiyyah da kunya, ire-iren hanyoyin nan na kwantar da hankalin miji a yayin biki ko al’ada nauyinsu take ji, wani irin nauyi abun yake yi mata, sosai take jin kunya in ya nuna mata irin abubuwan da yake so tayi masa wadanda su kadai zasu iya kwantar da hankalinsa, duk kokarinsa na fahimtar da ita shida ita babu sauran kunya ta wannan fannin, shekara goma ba wasa ba, ta bude idonta suyi irin rayuwar data dace dasu amma Safiyyah kunya da nauyi da gidadanci basa barinta, irin dai upbringing na gidan manya data riga samu da kuma rashin good socialization da zai bata damar samun exposure akan kula da miji, ko irin ‘yan karance-karancennan na zamani da ake daukar ilmin rayuwar aure a cikinsu Safiyyah bata yi. Kaidai barta a karance-karancen da zai zurfafa ilmin ta na Architecture.

Ganin karatun hikayoyin soyayyah take a matsayin bata lokaci ko rashin tarbiyyah. Not because she doesn’t love him. Amma ta gaza sanin hanyoyin kula da bukatunshi na aure yadda ya kamata, alhalin karshen duk wani so da soyayyarta ta diya mace a duniya tasan na mijinta Zayyan Rafindadi ne.

A’ah ita dabi’arta na kunya, russunar da ido, da kana’a, nature dinta ne da Allah ya halicceta dasu tun fil azal, kunya da kawaici da rashin zaqewa akan sexual relationship dinsu. Komai shi yake yi a gadon aurensu. Ita saidai ya barta dasu rufe ido da ji masa kunya, da kiran sunansa. Wannan ba zai zamo abun mamaki ba, in aka yi la’akari da irin (decent upbringing) din da Safiyyah ta samu a gida.

Har Sophie ta yada wanka Zayyan bai je Katsina ba, ya kuma gama shirya surprising dinta da tarewarsu a sabon gidansu dake cikin shahararren Estate dinsa da ya kammala, wanda sai yanzu Allah yayi kammaluwarshi, watau SUNSET ESTATE, Estate dinsu shida Safiyyah dake GUZAPE. A ranar data yada wanka wato ranar da ta kwana 40 da haihuwa ya shirya komawarsu gidan.

Cikin ikon Allah a ranar sai ga mahaifinta Malam Usman da kansa a gidansu ranar da suke shirye-shiryen tashi. Haroun ya kawo shi har Abuja tun daga Dandume, a motar Haroun din.

Nan suka shiga hidima da bakuntar babban bakonsu Malam, Zayyan da Safiyyah da su Sabah kowa hidima yake da zuwan Malam, su dora wannan tukunya su sauke wannan, ana wadata malam da cimaka ta alfarma. Ya wuni sur tare dasu cikin kauna da soyayyahr Uba mai girma, ya yi musu nasiha da wa’azi sosai akan muhimmancin karbar jarrabawar Ubangiji kowacce iri ce, komai dacin ta, da ribar dake cikin hakan watarana.

Ya tunasar dasu tanadin da Ubangiji yayiwa iyayen da suka haifi da ya koma. Tare dashi aka tare ranar da yamma SUNSET ESTATE. Ya kwana tare dasu a sabon gidan a ‘guest wing’ Haroun kuma a hotel ya kwana, kusan kwanan zaune sukayi ranar suka raba dare a falon Safiyyah shida Zayyan da Safiyyah, yana mai basu sirrin addu’oin neman biyan bukata, abinda ya tadowa Zayyan kewar Baba Bello. Suka kasa tafiya suje su kwanta har asubah suna like da Mallam.

Zayyan ya kara jin kansa maraya sosai da soyayyar da Malam kema Safiyyah, sai yanzu yafi jin kewar Baba Bello, ya san da Baba yana raye da abubwan dake faruwa da yawa basu faru ba, da tuni shi da Safiyyah sun ga gata a wannan haihuwar tasu, da kauna da tattali, a wannan lokacin da ba abunda suka fi bukata fiyeda kaunar iyaye da support dinsu.

Tabbas da Baba Bello na raye, ba zai watsar masa da iyali yadda Mama tayi ba, alhalin tana ikirarin tana sonsa tana kuma kaunarsa, a matsayin tilon dan data haifa namiji ta kasa taya shi son iyalinsa. Sai yaji idanunsa sun kawo ruwa da hamma a lokaci guda, har Malam ya lura yace su tashi su je su kwanta haka.

Da malam zai koma a washegari yace tunda Safiyyah ta yada wanka, ta kuma samu lafiya zai wuce da Sabah da Rayyah Dandume.

Karon ta na farko da sake haduwa da Haroun kenan, tun bayan aurenta da yazo washegari daukar Malam zasu wuce. Gabadaya Haroun din Malam ya canza mata, ya zama babban mutum, Haroun ya samu cigaba sosai ta kowanne fanni na rayuwarsa, harkar danyen man fetur yake yi yanzu da ‘Dangote Refinery’, saboda abinda ya karanta kenan a jami’ar Maiduguri wato (Petro-chemical Engineering).

Bayan gaisuwarta da Haroun ya amsa ya kuma yi mata ta’aziyyah bai bar wata kalma ta kara shiga tsakaninsu ba. Bai ko kalleta ba, abin ya tsaye mata don kuwa Haroun a can baya yafi kowa shiga sha’aninta ita ke basar dashi. Sanda akayi aurenta kuma ya koma Nsukka yana hada kwalin karatunsa na biyu kuma tun bayan aurenta in zata iya tunawa Haroun bai taba kiranta a waya ko sau daya ba.

Al’amarinta da Yayanta Ridhwan (Yaya Shaikh) shi yafi komai bata mamaki akan na Haroun din Ammi, don in Haroun kishi yake tayi aure ta barshi, alhalin an san yana sonta tun tana karama, itama kuma ta san yana sonata koda bai taba furta mata ba. To Yaya Shaikh kuma fa?

Kalmar so ko kwalli daya bata taba gittawa a tsakaninta dashi ba. Gara Haroun zata ce hatta Ammi ta sha gaya mata son ta yake yi, tun tana karama, amma yana kallon kansa a wanda bai isa ya aureta din ba, kasancewasa almajiri ga Mallam.

A wannan zuwan da Malam yayi ne yake gaya mata cewa anyi auren Yaya Sheikh a Doha (Qatar), ya auri wata Shuwa Arab haifaffiyar Maiduguri da suka hadu a karatu mai suna Assafe.

Da Malam yace zasu tafi tare dasu Sabah Zayyan ki yayi, don yaga yadda zaman nasu ya zamewa Safiyyah abin debe kewa, bata shiga damuwa da tunani saboda kullum suna gefenta suna kwasarta da hirar Ammi, sai ya shigo falon suke musu sallama su shiga dakinsu data basu. Don haka zamansu tare da ita ya taimaka ainun wajen dawowar walwalarta.

Sai ya roki Malam alfarmar ya bar su Sabah su cigaba da zama tare dasu zuwa bayan sallah, don a lokacin an kusa shiga watan Ramadan saura sati guda wata mai alfarma ya kama.

Da kyar Malam ya yarda ya barsu, amma yace sallah da kwana uku lallai-lallai ya gansu sun dawo Dandume.

Malam da Haroun suka kama hanyar komawa Dandume washegari.

Kulawar mijin kwarai irin Arch. Zayyan Bello Rafindadi, da addu’ar caring iyaye masu riko da addini irin nata, sun taimaka matuka gaya wajen dawowar nutsuwar Safiyyah, bayan rashin IVF babyn da suka yi. A kullum yana karfafata da cewa “data haihu, da bata haihu ba shifa yana sonta a haka, she will forever remain his ALTER EGO, sa’annan the only partner da yake son ya rayu da ita a duniyarsa da lahirarsa.

Ba wani abu wai shi rashin haihuwa da zaisa ya juya mata baya. Yana rokon Allah ya taya shi akan hakan. Shi ita ya aura ba abinda zata haifa masa ba da baima sanshi ba.

Cikin kalaman sa na koyaushe Zayyan ya kan ce mata “koda zasu mutu basu haihu ba, bazai taba amfani da hakan ya wulakantata ko ya goranta mata ba, ko ya juya mata baya ba wai dalilin rashin haihuwa.

Ire-iren kalamansa masu dadi kenan da suka taru suka farfado da Safiyyah, ta soma komawa harkokin ta na yau da kullum, bayan rasa dan da suka haifa ta hanyar Dashe (IVF).

A wannan gabar ne kuma bayan dawowarsu SUNSET ESTATE Zayyan ya bata gwaggawaban jari, yace ta soma business din duk da take so, duk don ta kwantar da hankalinta, da kokarinsa na faranta mata, a bisa wuyar data sha wajen samun ciki da haihuwar In Vitro Fertilized Baby dinsu, wanda ya kira da suna a cikin zuciyarsa “Areef”.

***** ***** ****

Kudin project din wani Estate da yayiwa gwamnati ne ya fito a goman karshe na watan Ramadhan, ya samu kudi masu kauri a hannunsa, aljihunsa yayi nauyi sosai. Abinki da Da nagari, ba wanda ya fara tunawa as usual idan ya samu kudi masu kauri a lokacin sai mahaifiyarsa, Mama Fatu.

Tuni ya manta da bacin ran da Mama ta saka shi a ciki watanni kadan baya da suka gabata, don shi duk wata nasararsa a rayuwa, yana fara dangantata ne da iyayensa.

Don haka sune na farko da yake tunawa idan alkhairi irin wannan ya same shi. Yayi ma Baba Bello Sadaqah sannan yayiwa Mama Fatu hidima. Gashi ya jima bai je Katsina ba yayi kewar Mama. Don haka ya samu Safiyyah har daki yake gaya mata cikin farin ciki.

“Sophie kina ina ne? Zo daga kusa ki ji?”

Ta fito daga daki tana daura kallabinta, “gani nan Habiby, wani abu?”

Suka game a karamin falonta, da rabi-rabin runguma, saboda ya taho da sassarfa ne itama ta fito da sauri, ya riko kugunta ya zagayeta da hannayensa biyu yana murmushi irin na namijin da aljihunsa ya cika da albarka a gaban iyalinsa. Yace ma Safiyyah.

“Wannan sallahr so nake zan gwangwaje Mama da wani abu mai daraja, wane kaya ne na kwalliyar mata suka fi kowanne daraja?”

Safiyyah na murmushi ta sakalo hannayenta a wuyansa itama, tace “Gold! (Zinare). Shine karshen kwalliyar mata mai daraja”.

Yace “to Alhamdulillah. Zan sayama Mama sarka da dan kunne da zobe da warwaro na zinare don in gwangwajeta ba zatonta. Na san Mama da son kwalliya. Kudinnan dana gaya miki inata jira su fito na project din Bwari, yau sun fito cikin ikon Allah.

Yace “bana taba manta wata sallah ina dan shekara goma. Baba yazo bashi da kudi isasshe a hannunsa, yace iyalinshi mu hakura da kayan sallah, saboda ya samu yayi wasu abubuwan muhimmai da ‘yan kudin hannunsa.

Mama sai tace “ai ba komai Babansu, Allah ya dada rufa mana asiri Baban Baffa.

Sai ta dauki sarkarta ta zinare ta siyar, tayi mana kayan sallah, ta baiwa Baba ragowar kudin tace,

“kayi duk hidimarka da sauran kudinnan Babansu Baffa”.

Tun lokacin abun ya tsaya min a rai. Don naga wani irin feeling na godiya da bazan taba mantawa ba a fuskar Baba ga Mama. Na kudurce nikuma sai na biya Mama ‘gold’ dinta duk sanda Allah ya bani gwaggwabar dama.

Ya rubuta cheque na kudi masu yawa ya baiwa Safiyyah wadanda har saida suka bata tsoro, yace “Sophie, so nake Mama na tayi gayu da babban Zinare, ta fito kamar tauraruwa Zahra a cikin mata a wannan sallahr”.

Safiyyah ta karba tana jinjinawa halarcin Zayyan akan son iyayensa, tace “amma Habiby, tare da kai zamuje mu zabo ko? Yace “a’ah ni mace ne? Ina nasan design mai kyau? Kawai kije ki zabo, sannan ki sayawa su Zahra suma duka kanana da bai kai na Mama girma ba. Da kuma amaryata Sabah da kanwata ta kaina, Rayyah”.

Nan suka zauna bisa doguwar kujera three seater, yayi mata bayanin yadda yakeson na kowa ya kasance, da sauran mutanen da zasu yiwa kayan sallah a cikin kudin bayan sakon Mama, dama duk shekara ya saba hakan, ‘yan uwanshi kaf da nata, da iyayenta da nashi babu wanda baya yima kayan sallah na gani na fada. Kai hatta dan almajirin gidansu Safiyyah wani yaron dake zama gidansu yana zuwarma Ammi aike mai suna Saminu, ya shaida soyayyar Zayyan ga ahalin Safiyyah, don duk shekara bandirin shaddah baya wuceshi shima, duk sallah karama Zayyan bai mantawa dashi. Balle kuma kannenta uku, wato Sabah da Rayyah da Rayha, koda ba’a hannunsu zasu yi sallah ba ya maida yi musu kayan sallah cikin obligations dinsa (hakkinsa), tun bayan dawowarsu Abuja.

Sosai Safiyyah ta yi masa addu’ar karin budi da nasara cikin al’amuransa, tayi godiya yadda ya dace macen kwarai ta godema mijinta in yayi hidima ta bajinta irin wannan, ta kuma kara alfahari da Habiby dinta domin ya cika dan halas din da kowacce Uwa zata yi fatan haifar mai kaunarta da yi mata halarci kamarshi.

Baya taba iya yin dogon fushi da Mama Fatu (no matter how) yadda zata bakanta masa da halinta.

A kullum fatanta shine na samun ‘ya’yan da zasu yo gadon wadannan nagartattun halayen nasa, Zayyan Bello ya cika dan halas, uwa da ubanshi babu sama dasu a komai, tana addu’ar Allah ya bata ‘ya’ya daga gareshi su gado komai nasa, itama su ji kanta a tsufanta, ko ba don bata da shi ba.

A washegarin ranar suka je wani dankareren shagon zinare suka zabi latest design na set din wani white gold saukar jiya-jiya daga Dubai. Ya lashe miliyoyin kudin da Zayyan ya warewa Mama har da dori. Ta kuma sayawa sauran kannensa dan kunne kowacce yadda yace tayi. Sannan suka zarce kasuwar Wuse market tayi siyayyar komai da ya lissafa mata na kayan sallar jama’arsu, karkashin rakiyar kannenta su Rayyah, kaya ta zabowa su Zaitoon na gani na fada, masu tsada da quality, ta hada ma Mama da saitin turarukan (Aventus for Her) da ya taba gaya mata cewa dashi kadai Mama Fatu take amfani a matsayin nata neman albarkar, ta sayi wani tsadaddden akwati dan karami mai kyau, ta zauna ta jera turarukan nan da saitin (white gold) din a cikin akwatin gwanin ban sha’awa sukayi kyau a cikinsa. Kai kace wata yarinya budurwa za’a kaiwa toshin sallah.

Sannan ta siyowa dukkan kannenshi da kannenta kaya kamar yadda ya tsara.

Da Zayyan ya dawo gida ta nuna masa sayayyar duka tayi masa bayanin na kowa, yayi murna sosai da ganin sakon Mama da kannenshi, ya jinjina ma fasaharta da iya zaben design din zinare. Amma yana bude na su Sabah ya dauki atamfar yana juyawa a hannun shi, ko daga kalarta da rashin nauyinta ya san bata fi atamfar dubu takwas ba, ya dubi Sophie sama da kasa ya hade rai yace.

“Safiyya menene haka? Me kike nufi da hakan?”

Hankalinta ya tashi, ta dauka wani abu ne tayi masa ba daidai ba, sai taji yace yanzu don me zaki siyowa su Sabah kaya masu arha, su Hatoon ki siyo Swiss laces masu tsada, shin akwai bambamci tsakaninsu ne a gurina? Ban ji dadin abinnan da kika yi ba ko kadan, baki kyauta min ba”.

Sai ta soma bashi hakuri, tace “ba haka bane Habiby, kudin ne sunyi kasa sosai, sai naga cewa su Zahra yafi dacewa da wannan, su din kannenka ne da kuke ciki daya, hakkinka ne ka yi musu komai yanzu, musamman da hakkinsu kamar a wuyanka yake, su Sabah kuwa Ihsani ne tsakaninku wanda bai zame maka dole ba”.

Cikin takaicin kalamanta yace “sannu Mrs. Right, Gwanin na iya sarkin iyawa, toh canjin da kika dawo mun dashi me zanyi dashi? Idan har na isa dake ki koma kasuwar nan, abinda kikayi wa su Hatoon, shi nake so inga anyi wa su Sabah…”.

Dolenta suka koma kasuwa washegari aka sake siyo kayansu Sabah, don ransa ya baci sosai a ranar, ya dauke mata wuta da wannan abinda tayi, har saida ta gyara kuskurenta, ta kawo ta nuna masa ta bashi hakuri. Sannan ya sauko, ta hadawa kowa nashi aka aika kayan Katsina. Infact duk kannensa da aka kai musu kayan sun yaba, kowa yayi murna ana ta bugo waya ana yima Yaya Baffa godiya don sun dauka shi da kansa yaje ya sayo masu.

Mama kam kuka ta saka, tace wai yau Baffa ya tuna mata Baba Bello, komai Baba zai saya mata sai ya zabo na kerewa sa’a, don ya san ta da son special abu da basu cika gari ba, Mama tun asalinta mace ce mai son gayu da kashe kala, tana matukar son kayan ado na yayi, tana harka ta jiki sosai da manyan matan ‘yan bokon Katsina, saboda farin jinin Baba Bello.

Da sallah tazo, Zayyan da Safiyyah dasu Sabah suka yi shiri suka wuce Katsina don halartar shagalin bikin sallah kamar yadda mafi akasarin mazauna birnin tarayyah ke yin sallah a garuruwansu na haihuwa.

Gidan marigayi Prof. Bello Rafindadi gida ne da ake yin hidimar abinci ta alfarma duk ranar sallah, gate dinsu a bude yake. Wannan ya shiga wannan ya fita. Ana dafa abinci kala-kala ana bayarwa ga baki da makwabta. Haka ake yi duk sallah tun Baba Bello yana raye. To yau ma hakan ce ta kasance a gidan.

Ya kasance a kowanne washegarin sallah Mama Fatu tana gayyatar matan abokan Baba da kawayenta, suzo gidanta a ci a sha da cimaka ta alfarma da snacks, su wuni sur har yamma suna hira, zaki gansu duka hamshakan mata ne kusan su goma a falon Mama, ana hira ana nishadi, to ko bayan rasuwarshi Haj. Fatu ta cigaba da al’adar tata, ta gayyato mutanenta ranar sallah.

Wannan shekarar ma kamar ko wacce, kawayen Mama sun zo harda matar VC mai ci a yanzu na jami’ar Umaru Musa ‘Yar adua, Safiyyah tazo falon ita da kannenta zasu yiwa mutanen Mama gaisuwar sallah, Sophie ta sha ‘swiss lace’ dinta ‘purple’ me kyau, kannenta Sabah da Rayyah dake biye bayanta sun sako kayan da Zayyan ya siya musu na sallah iri daya sak da na yaran Mama wato su Hatoon, su Sabah sun yi kwalliyar sallah da kayan ne saboda Uncle Zayyan yana gidan, suna so su nuna mishi godiyarsu, ta hanyar saka kayan.

Don yace dasu da yamma in sha Allah idan ya dawo daga cikin gari za’a yi (family picture) harda su kafin ya maidasu Dandume gobe kamar yadda ya alqawartawa Malam. Idan su Zahra da Zaitoon sun iso daga gidajensu. Shiyasa suka saka kayan ba tareda sun kawo tunanin komai a ran su ba.

Readers Also Read