Kenza eBookz

Kida a ruwa book 1 by bilyn abdull - Chapter 17

Kida a ruwa book 1 by bilyn abdull - Chapter 17

Kida a ruwa book 1 by bilyn abdull Chapter 17: Kida a ruwa book 1 by bilyn abdull Chapter 17. ★Su Zak-Shadow na Enugu cikin sabuwar rayuwar aikin soja,…

4,153 words

★Su Zak-Shadow na Enugu cikin sabuwar rayuwar aikin soja, anan rayuwar Mammah da marayun ƴaƴanta na neman canja salo da fuskantar sabuwar jarabawar rayuwa. Domin kuwa Zak-Shadow bai wuce watanni uku a Enugu ba Tasi'u ƙanin Mammah ya zo kwatsam. Zuwan daya saka Mammah a farin ciki dan tayi tsammanin har abada ta rasa dukkan ƴan uwa a duniya. Da farko dai kamar abin arziƙi tsakaninta da Tasi'u, dan harda zama ya bata labarin rayuwar da yake ciki ta tashin hankali. Yarinyar daya aura basu ko ƙulla shekara ɗaya ba a rayuwar aure suka rabu, ya shiga halin rayuwa mai tsanani a sabuwar ƙasar da bai san kowa ba, haka ya jure saboda karatun da yake yi. To zuwa yanzu ya kammala, acewarsa har ya samu aiki, yanzu ma yazo gida ne domin wani aiki da zai yi na wata uku ya koma. Mammah ta jajanta masa ta kuma tayashi farin ciki. Sunyi sati kamar uku a wannan farin cikin kwatsam rana tsaka sai ga Tasi'u da lauyoyi har biyu da wasu mutane, wai yana son a raba gida a bashi nashi kaso. Mamaki ya kama Mammah, ta kalla gida ta sake kallo, tabbas gidansu babba ne, gashi a bakin titi, kusan a yanzu ma gidan yafi duk wani gida na layin ƙyau saboda gyaran da Alhaji Nura yay masa lokacin daya aureta. Da farko ta ɗan so tirzawa tai masa faɗa, ya nuna mata shifa ba yaro bane, sannan gidan nan dai yana da hakki ai kuma dolene a bashi nashi hakki. Ganin yana son su zubar da mutunci a anguwa tace ba damuwa yayi duk yanda yaso, ko ɗaki ɗaya ta samu ALLAH ya amfana zata zauna da yaranta. Haka kuwa akai yayta shiga da fita batare daya bari tasan yaya komai yake tafiya ba. Kwatsam a cikin wata na biyu da zuwansa ta nemeshi ta rasa. Duk inda ya kamata ta bincika kuma tayi amma babu shi. Hankalinta yaso tashi kawunsu yace karta damu kanta, ta barshi duk ma inda yaje zai dawo tunda ba yaro bane. Haka dole ta haƙura ta share. Abin mamaki cikar wata ɗaya saiga wasu mutane wai sunzo gidan nan da take ciki nasu ne an sayar musu, suka nuna mata takardu harma da shaidun gani da ido da akai ciniki da su. Hankalin Mammah ya tashi kwarai da gaske, sai ta rasa inama zata saka kanta dan tashin hankali, kawai ta yanke jiki ta faɗi sai da aka kaita asibiti. Kwananta biyu aka sallamota, abu dai kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba Tasi'u ya saida gida ya gudu. Masu gida kuwa sun bata wata ɗaya kacal suna buƙatar gidan akwai abinda zasuyi da shi. Wannan tashin hankali ya saka Ma'aruff da Ja'afar sulalewa suka tafi Enugu suka sanar ma Zak-Shadow. Kwatsam babu zato ya gansu, mamaki ya kama shi ya balbalesu da faɗa domin a ganinsa ai kasada ce zasu kamo hanya batare da sanin gari ba su taho. Su dai haƙuri suke ta bashi, Imran dai ya kwacesu da ƙar, shine ya basu abinci sukaci ya basu wajen kwanciya. Zak-Shadow bai saurarensu ba sai dare, anan ne suka sanar masa abinda ke faruwa da halin da Mammah ke ciki, suka tabbatar masa a yanzu ma sunzo ne bada saninta ba, dan sun tabbatar tana can tana nemansu ƙilama hankali a tashe.. Jin wannan zance ya sake ɗaga hankalin Zak-Shadow, haka ya samu da ƙyar da kamun ƙafa aka bashi damar zuwa gida kwana uku kawai. Ya taso ƙanensa gaba suka nufi Kano. Aiko hasashen su ya tabbata, dan sun sami Mammah cikin tashin hankalin rashin sanin ina su Ja'afar ɗin suke, sai kuma gashi ta gansu harda uban gayya Haysam. Kukan dake danƙare da ƙirjinta sai a lokacin ne ta samu ta yi shi. Wannan al'amari ya sosa zuciyar Zak-Shadow matuƙa. Wanda ma bai san fushinsa ba a wannan karon ya gani kwarai da gaske. Ɗan kuɗin albashinsa da yake faman ajiyar taro da kwabo a account ya kwashe domin sayen fili, sai dai a karo na farko Kano ta fita masa a rai gaba ɗaya, yana son yin nesa da ita nisa mai yawa ko mahaifiyarsa zata samu salama tamkar yanda ta baro Bauchi, amma kuma bai san ina zai maidasu ba, dan haka ya nema shawarar Imran ta hanyar kiranshi a wayar landline. Babu wani ja'in-ja Imran ya bashi shawarar zuwa Abuja kawai, ya kuma haɗashi da yayansa. A ranar Haysam ya bar Kano zuwa Abuja. Inda da taimakon yayan Imran suka samu fili suka saya. Sauran kuɗin daya rage ya sayi siminti da bulo aka fara ginin ɗakuna ƙwara biyu kacal. Kwana uku aka bashi kawai a wajen aiki, dan haka dole ya koma Kano yabar sauran aikin wajen yayan Imran. Yana zuwa Kano ya sanar ma Mammah komai, mamaki ya kamata sai kuma ta shiga yi masa faɗa akan dammi zai yi hakan. Shi dai kansa a ƙasa kawai yana bata haƙuri ne. Sai da ta kammala yace su fara shiri kawai, nan da kwanaki kamar goma zasu koma can shi kuma ya shirya ya koma Enugu. Haka kuwa akayi, kwanaki goma bayan komawar Zak-Shadow yayan Imran yazo har Kano da mota ya kwashi su Mammah da yaranta. Tafiyar data sakata kuka sosai, jikin ƴan uwanta yay sanyi da rashin taimakonta da basuyi yunƙurin yi ba har Haysam ɗin ya yanke hukunci. Dan sun so hanata da nuna mata zasu ɗauki mataki tace ba komai zata koma Abujan kawai dan itama bata son zaman Kanon a yanzu. Wannan shine sanadi kuma mafarin barin Kano dasu Mammah sukai suka dawo Abuja. Ɗaki ne guda biyu kawai, sai aka zagaye gidan da kwanon langa-langa. Dan Zak-Shadow ya nuna baya son taimakon komai daga wani saboda Yayan Imran yaso yin hakan. Shima kuma Imran ɗin yaso yin hakan amma ya haƙura dan yasan wanene Zak-Shadow, idan yace baya son abu to kawai baya so ɗin da gaske. Yana sake ɗaukar albashin watan ya nufo Abuja, kuɗin yay amfani da su wajen maida ƙannensa duk makaranta, su Ammar ma da ba'a saka ba ya sanya su. Dama Mammah tunda suka dawo bata zauna ba, haka ta dinga shiga tana fita wajen nunama mutane kayan sana'arta ta koli. Sannu a hankali aka fara ganewa, kasancewar sabuwar anguwa ce kafin mutum yaje kasuwa sai yafi ganewa zuwa wajenta sayen abu a sauƙaƙe. Ganin haka ta fara haɗawa da kayan miya, da wannan sana'ar da albashin Zak-Shadow suka cigaba da rike rayuwarsu, idan an samu ɗan rarar kuɗi a sai siminti a ɗan ɗora gini. Kwatsam sai kuma ga wata ƙaddarar ta sake afkawa Zak-Shadow lokacin da yake shekara biyu da fara aikinsu, wai ya buɗe wata gaskiya wani ogansu yayi kutun-kutun an saka shi a prison. ALLAH sarki rayuwa, a wannan gaɓar ALLAH dai ya ƙaddara Mammah kam bazata rasa ranta ba. Dan bama ita kawai ba hatta su Ma'aruff sun shiga wata irin gigitar rayuwa. Haka Mammah ta dinga bin duk wanda ta sani cikin roƙo da magiya don ganin Haysam ya kuɓuta. Amma ina, Imran ma iya bakin ƙoƙarinsa yake amma al'amarin kamar da wani babban shiri a cikinsa. Hatta su Adetunji sunyi iya yinsu Zak-Shadow bai fito ba. Ga baƙar wahala suna bashi ta tashin hankali kamar sun sami criminal, duk mai hankali yaga wannan al'amari yasan akwai lauje cikin naɗi a ciki, sai dai kai tsaye basu san wa zasu fuskanta suce yayi ɗin ba..........✍🏼

_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_*

*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_*

*_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_*

*_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_*

*_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*

*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*

*_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

_Chapter 34_

__________________

https://chat.whatsapp.com/L3BXH7JYlBRHIkFRiOjeW3?mode=ems_copy_t

UMMU KHALIFA COLLECTION

Ina Mata Yan kwalisa ina mata masu san kayan ado kamar Egyptian abaya sleeping drees kids were shos bags musk dahara original.

To kukanku yazo karshe domin ummu khalifa sun zo muku da duk wadannnan kayan dierct suke order dinsu daga Egypt zuwa gida Nigeria kaidai kawai kashiga link dinsu domin gani ya kori jiii..

Ba nan ummuh khalifa suka tsaya ba suna nemawq mutane visa masu shaawar shugowa kasar ta Egypt karatu ko yawon bude ido ko kasuwanci ku tuntubeta a number dinta +201017018846/07048811474/

KO kuma shafinta na tiktok https://vt.tiktok.com/ZSU1FEkjc/ __________________

*_TELEGRAM GROUP_*

https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk

*_WHATSAPP CHANNEL_*

https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F

*_TIKTOK_*

https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/

*_INSTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

______________________

.........Lamarin kamar wasa sai da Zak-Shadow yay watanni shida sannan aka sake shi. Tsabar azabar da akai masa ana fiddoshi asibiti aka wuce da shi. Dan kai bazaka kallesa kace zai ƙara rayuwa ba a wannan duniyar ko moruwa. Da yake ita rayuwar ta UBANGIJI ce kuma sai gashi bayan jiyyar watanni kusan biyu ya miƙe. Miƙewar data sake canja Haysam Abdul-rasheed Shehu zuwa Zak-Shadow ɗin da yake a yau. Wanda baya ɗaukar raini, baya ɗaukar wasa daga kowa, koda kuwa kowan na sama da shi ne. A bisa bincike kuma aka gano Ogan nashi ne mai laifi ya kuma zaluncesa, dan haka aka ɗauki mataki a kansa aka maida Zak-Shadow bakin aiki tare da ƙarin girma. Ƙarin girman daya sashi wucewa mate ɗinsa a shiga soja su Imran. Ya fito a prison baifi da shekaru biyu ba ya kammala ginama Mammah muhallin zamanta. Gini mai ɗakuna huɗu dai-dai ƙarfin talaka, sai sauran fili babba kuma a gidan da za'a iya gina wasu parts ɗin ma. A wannan gaɓar ne kuma kwatsam Nasiru abokin Abdul-rasheed ya dawo gida Nigeria da iyalansa. Dawowar daya fuskanci matuƙar tashin hankali saboda jin halin da zuri'ar Abdul-rasheed suka shiga bayan wucewarsa. Da kuma saƙon daya dinga aiko musu da baya zuwa hannunsu. Kwanansa ɗaya a garin kano ya shiryo yazo Abuja. Ranar yaci kuka da takaici kwarai da gaske, ya rantse ya maya akan saƙon da ya dinga aikowa garesu ta hanyar wani abokinsa, saboda tunda ya tafi hankalinsa na kansu ne. Sai gashi koda yasa aka nemo wanda yake bama saƙo ashe shi yanata hidima ne da abinda yake aikoma marayun ALLAH, takaici ya saka shi sawa a rufe shi, sai da ƙyar daban haƙuri ya bari aka sake shi. Amma duk da haka sai da Zak-Shadow yasa aka cimasa ubansa ta bayan fage dai-dai gwargwado. Dawowar Uncle Nasiru ta sake canja rayuwar Mammah da ahalinta zuwa ni'imtacciyar rayuwa, duk da Alhamdullah dama zuwa yanzu basu tare da kowace damuwa. Dan sana'arta ma tayi girman da a yanzu har shago suke da shi a ƙofar gida da Zak-Shadow ya gyara musu. Karatun yaran kuma duk yana tafiya yanda ya kamata. A wani weekend da Zak-Shadow yazo ya samu babbar ɗiyar Uncle Nasiru a gidan tazo hutu. Yarinya ƙyaƙyƙyawa son kowa ƙin wanda bai samu ba, sunanta Nabiha, girman turai rainon biscuits da madara. Ga ilimi ga shagwaɓa ga gata. Tunda ta ƙyalla ido akan Zak-Shadow ta kafa ta tsare tace tayi mijin aure. Ko damuwa da sharetan da yake ma batayi, dan ita ba komai ma yaja hankalinta a kansa ba sai wannan jin kan nashi da tarin izza da nutsuwa. Harga ALLAH tana matuƙar son namiji maiji da kansa da kamun kai. Daɗin daɗawa ga jarumta, dan ko makaho ya shafa Zak-Shadow yasan sojan ne na gaske ba wasan yara ba. Ga ƙyawun ga gayu ga ilimin addini. Kannensa na girmamashi tamkar mahaifi a garesu. Mammah kanta na ji da shi sai dai bata nuna wa saboda kawaicin ɗan fari. Babu wani kunya ko tsayawa jan aji tace tana so shi. Shi kuma a take yace mata no. Shi bashi ma da burin aure nan kusa. Aiko ta sanya rigima harda kai ƙararsa wajen Mammah. Mammah kuwa najin wanga batu ta hau ta zauna abinta. Dan dama kullum cikin tunanin ta yanda Haysam zai nema auren mace take yi. Dan ta kula sam hankalinsa baya akan auren, ga Imran har an kai kuɗin nashi auren shi, hakama Ummi yayan Imran ya kafa ya tsare yana sonta. Ko tsayawa yin shawara da shi batai ba ta sanar ma Uncle Nasiru. Shima ba karamin farin ciki yayi ba da hakan, sai dai mahaifiyar yarinyar ta nuna bata so, a ganinta su Mammah talakawa ne sannan aikin soja ma kamar wani aikin wahala ne. Dama kuma a tsakanin tanata faman tafka tsiya da Uncle Nasiru ɗin akan su koma ƙasar waje ita bazata iya zaman Nigeria ba shi kuma yace ya dawo ƙasarsa kenan, sai kawai wannan batun auren Zak-Shadow da ƴarta ya ida tunzurata suka rikice har ya sake ta. Ya kuma aurama Zak-Shadow Nabeeha, dan itama dai ta bijirema uwar akan itafa babu gudu babu ja da baya. Haka takaici ya saka uwar tattarawa ta tafi ta barsu shi da ƴarsa, ta wuce da sauran ƙanen Nabeeha ɗin guda biyu. Shi ko Uncle Nasiru ya ƙara sabon aure. Anyi bikin harda na ƙanwarsa Ummi da Secondary kawai ta kammala, aka kaita gidan su Imran itama.. Matar Zak-Shadow kuwa anan gidan Mammah aka ajiye amarya, dan gefensu kaɗan aka yanki fili shima akai masa gini. Zak-Shadow bai fahimci son Nabeeha yake ba shima sai da akai musu aure, dan cikin ƙanƙanin lokaci suka ƙulle. Wata irin soyayya suke ma juna mai tsayawa a rai da zuciya. Sai dai a zahiri baka isa kace hakan ba saboda yanda shi gogan ke kame kansa. Shima Imran anyi nashi bikin da amaryarsa. Anan kuma cikin anguwar su Zak-Shadow yay ginin gidansa mai ƙyau aka sakata. Rayuwa ta cigaba da tafiya nasarori na cigaba da zagaye Zak-Shadow, ƙarin girma akai-akai har UBANGIJI ya ƙaddara a 2003 ya zama Captain, a Kuma lokacin wani sabon guguwar rikici ta taso a wani yankin ƙasar, an turasu matsayin nayaƙa, turawar data basu nasarori masu yawa har takai sun kada rundunar ƴan ta'addan wanwar, suka samu ƙarin girma kuwa Zak-Shadow ya zama Major. A 2006 kuma rikicin ya sake sauya salon da aka sake turasu wannan jejin dai sai dai a wani yankin ne daban, a inda suka haɗu da waɗan nan mata harda mace mai ciki da tai masa alƙawarin bama ɗanta. Ya kuma tabbatar mata zuwa ya amsa da hannunsa. Zak-Shadow ya matuƙar taka rawar gani a wannan jeji shi da mayaƙansa, dan kuwa ya hana ƴan ta'addan kowane irin motsin kirki koda na numfashi mai ƙarfi ne. Sannan ya daƙile haƙo ma'adanan da ake a tsakanin ƙauyukan wanda kowa ya tabbatar da saboda su ne ake haddasa rikicin dan masu ɗibarsu su samu damar diba cikin salama a lokacin da su al'ummar ƙauyukan yankin keta rayuwarsu. Sai kuma wata babbar kasuwa dake ata wajen data haɗa kasuwancin wasu ƙasashe itama aka tarwatsata domin cimma wani buri da manufa. Amma zaman Zak-Shadow da yaransa komai ya canja daga yanda yake. Ya sake samun ƙarin girma zuwa Lieutenant Colonel a 2010, har kuma a yanzu 2013 yake a matsayin tare da rundunar mayaƙa a wannan jejin dai da suka samar da zaman lafiya bisa girma da ƙudirar UBANGIJI. Zuwa yanzu kuma ƙanensa mata duk sunyi aure Biebah ce kawai a gabansu. Mazan dai bayan shi babu wanda ya sake aure, kuma har yanzu matarsa bata haihu ba....

Wannan kenan.

________________★

A CIGABA DA GASHI..... 2013...☺️🏃🏼‍♀️

Sosai Zak-Shadow yasha barcinsa, dan bai farka ba sai kusan goma da rabi. Har lokacin kuma da alama babu wanda yasan yana gidan bayan ƙaninsa Bilal. Wanka yay ya kimtsa cikin shigar kamala duk da kuwa ƙananun kaya ne na shan iska a cikin gida. Hankalinsa nakan mahaifiyarsa Mammah, dan haka bai ɓata lokaci ba ya fito. Gaba ɗaya falon ya kacame da surutu, yara ne ƴammata da zasu iya kaiwa shekaru 17-20-25. Suna akan dining table kowacce kayan barci ne a jikinta. Wata mata da ba tsohuwa ba kuma bazamuce yarinya bace tsaye a dining ɗin tana zuba musu abinci a plates ɗin gabansu. A mistake ta ɗan zubama yarinyar dake kusa da ita da zata iya kai shekaru 20 suger akan waya data ajiye saman table ɗin. Ji kake tasss saukar mari na bazata a fuskar matar, ba kowa bane kuwa da wannan aiki sai wannan yarinya. Cikin ɓacin rai da masifa ta ce, "Amma ke wawiya ce ko? Dan jakanta a kan wayata ma zaki zuba shuger salon ya shiga min speaker ɗin waya". Jikin mai aikin na rawa idannunta cike da ƙwalla ta shiga girgiza kai hannunta dafe da kumatu. "Dan ALLAH Aunty Amima kiyi haƙuri, wlhy kuskure aka samu...." "Uwar kuskure ba kuskure ba jaka kawai baƙauya. Dalla tashi min aka kona watsa miki ruwan shayin nan a wannan baƙar fuskar taki mai kama da daddawa". Da sauri mai-aikin da har hawaye sun fara ma gudu a fuska tai yunƙurin barin waje. Yayinda sauran ke dariyar ƙeta da izgili wai Amima ta kirata mai baƙar fuska kamar daddawa. "Koma ki rama!!". Razananniyar muryarsa dake a buɗe kuma a dake irin ta jaruman maza tsayayyu ta ratsa kunnuwansu. Ta kuma saka mai aikin sake rikicewa da daburcewa amma ta tsaya cak. Haka suma yaran a mugun zabure duk suka miƙe jikinsu na mazari, sai kuma duk suka zube ƙasa duƙe suna faɗin, "Dada sannu da zuwa". Idan kujerun dining ɗin sun tanka ya tanka, hasalima ko kallon inda suke baiyi ba. Mai-aikin ya sake tsarewa da idanu cike da bada umarni ya sake furta, "Baki jini bane?". Hawayenta ta share da sauri tana jinjina kai, ta ce, "Naji Dada kayi haƙuri, amma na yafe mata". "Ni kuma ban yafe ba, kar kuma ki bari na sake maimaita abinda na faɗa". Sosai Hinde mai aiki tasan wanene ubangidan nata, dan kuwa shekaru kusan huɗe kenan take zaune a gidan tana aiki. Ai baima gama rufe baki ba ta isa gaban Amama. Ji kake ɗauuuu! Tasss-tasss! Na saukar marin data rama, har sai da Amama ta tuntsura zata faɗi. "Ƙara mata". Ya sake faɗa cike da umarni. Haka Hinde ta sake saukema Amama mari na biyu daya sakata ƙwalla ƙarar azaba. Dan da alama itama dai Hinde ta daɗe tana fatan wannan ranar, shiyyasa ta buɗe kwanji ta sauke ma fuskar Amama duk wani takaicinta. Cike da sassarfa wata mata ta fito a wata hanya tana faɗin, "Mike faruwa? Wa yake kuk......" Cak ta tsaya batare data iya ƙarasa abinda ta faro faɗar ba sakamakon saukar idannunta akan wanda batai zaton gani ba. Shi ko tamkar ma bai san ALLAH yayi ruwanta a wajen ba yayi wani kicin-kicin da fuska yana danna waya hankali kwance. Ga Amama tasa hannu ta danne bakinta dan kar kukan da takeyi ya fito, dan inta bari hakan ta faru lallai zata gwammaci Hinde taita marinta fiye da hukuncinsa. Jiki a saɓule matar ta ƙaraso inda yake, itama dai bazata wuce 30years ba, sai dai daga gani kasan anaji da gayu sosai. Cikin kame kai da aro nutsuwar dole ta ce, "Sannu da zuwa My D! Shigowar yaushe haka babu labari?". Maimakon amsa maganarta ko kallonta ma baiyi ba. Sai da yaja iska tafi ta minti ɗaya batare da ya kalletan ba ya furta, "Su tattara su wuce gida". Daga haka ya miƙe abinsa ya fice a falon gaba ɗaya. Sororo ta bishi da kallo zuciyarta na bugawa da sauri-sauri, haka suma yaran gaba ɗaya firgici ya bayyana akan fuskar su. Balle Hinde da take jin har fitsari ya fara ɗiga mata a jiki, dan tasan uwar ɗakin nata sai ta huce a kanta, itace zata sha wahala bayan ya koma. Yana gama ficewa ta afka kitchen da tafiyar baya-baya. Su kuma ƴammatan suka zabura kan Nabiha suna hawaye.........✍🏼

_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_*

*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_*

*_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_*

*_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_*

*_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*

*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*

*_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

_Chapter 35_

__________________

🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾

https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH?mode=ems_copy_t

*_GYARA SHINE MACE_*

*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF 'YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾

*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327

*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula,

Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍

Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍

Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃

Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍

Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃

Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃

Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima

KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻

Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi

Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi

Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu

Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra

Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa

Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka

*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻

07069711327 call or Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍

Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊

__________________

*_TELEGRAM GROUP_*

https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk

*_WHATSAPP CHANNEL_*

https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F

*_TIKTOK_*

https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/

*_INSTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

______________________

.........ƘAUYEN BANKAURA.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull