Kurkukun ƙaddara takun farko by by boss bature - Chapter 59
Kurkukun ƙaddara takun farko by by boss bature Chapter 59: Kurkukun ƙaddara takun farko by by boss bature Chapter 59. "It seems like we're not welcome at…
3,371 words
"It seems like we're not welcome at all" Jin wannan maganar yasa Danish Yin ƙoƙarin yi mata magana
"it's not like that, We welcome you with open arms. We are excited to have you here and look forward to getting to know you. You are highly welcome here"
Fuskar shi ɗauke da murmushi ya ƙarasa maganar, Yana yi musu nuni da gadajen su, don su shugo ciki su zauna.
shu'umin murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, irin na tatattun ƴan iska, Ba zato ba tsammani, su angel suka ga ta nufi Danish Tana ƙarasawa gabanshi Ta sanya hannu biyu Tayi hugging ɗinshi ajikinta, Cikin harshen turancin dake nuni da ƙwarewar ta ta furta"Tayi matuƙar jin daɗin haɗuwa da shi, tana fata za'a kar6e su hannu bibbiyu,"
Ran angel ya 6aci da sauri ta nufi inda suke atsaye, Suma sauran suka bi bayanta, Tana ƙarasawa gabansu ta sanya hannu Ta ruƙo damtsen hannun Danish Ta janye shi daga Jikin yarinyar, ta dinga jefa mata harara, Amma ko ajikinta sai ma ta sakar mata ƙayataccen murmushi tare da miƙa mata hannu don su gaisa
"Hi, Am unaizah ƴar gidan daddy, can i know u"? Ta jefa ma angel tambayar, Yatsina fuska angel ta yi, Kamar bazata tanka mata ba, Sai kuma tace"My name is Unaisah, Amma daddyna Yana kira na Angel, shine sunan da kowa Yake kira na" Dariya su ka ga ta saki tare da cewa"Wow, sunan mu yae shige dana juna, banbancin kawai harafin ƙarshe ne, ina fata zamu zama abokai" Da hausa tayi maganar amma sai ka rantse da Allah da turanci tayi ta, Saboda Yadda take furta ta, daga gani baturiyace amma ta iya hausa ba laifi,'
Murmushin yaƙe angel ta sakar mata tare da cewa"why not, tun da zama ya haɗu mu wuri ɗaya" murmushi ta kuma saki tana kallon fuskokin su Tace Idan ba damu tana son su gabatar mata da kansu, batare da sun Yi mata musu ba, ɗaya bayan ɗaya Kowannan su Ya gabatar mata da kanshi, koda a kazo kan Danish Yana yi mata bayani dangane dashi har wani lumshe ido take yi tana kallonshi, ran angel ya gama 6aci gani take kamar an kawo musu annoba ne, saboda babu natsuwa atare da yarinyar, bayan sun gama da kansu, Haris ya kalli sauran sabbin prisoners ɗin yace"saura ku ya rage ku faɗa mana sunayen ku, sannan muna son musan daga ina ku ke"_
Ƙaramar yarinyar nan ce ta fara Yi musu magana tace sunanta *JAMIMAH* Itama Prisoner ce a gidan kurkukun ta taso shekararta Goma cuf aduniya," Bayan Jamima Ta kammala gabatar musu da kanta, Wannan Doguwar mai zubin Taliyar indomi Ta faɗa musu cewa"ita Sunanta *SARAH* shekararta, Sha bakwai, Itama rainon kurkukun ƙaddara ce" Jinjina kai su kayi yayin da suka maida dubansu ga kirista ɗin nan suka ce mashi Ya faɗa musu wanene shi, Cikin sanyin murya yace musu Sunan shi*GABRIEL* twin sister ɗin shi kuma sunanta *GABRIELA* shekararsu goma sha bakwai," su angel sun yi mamakin jin shekarun su ashe duk Yara ne, Girman Jikine kawai, Naufal yace"rainon kurkukune ku ma Ko kuwa daga waje aka kawo ku"? Gabriel yace mishi bazai iya tuna komai dangane da rayuwarsu ta baya ba, shi dai kawai a bunda zai iya tunawa twins ne su, yana matuƙar ƙaunar ƴar uwarshi itama tana son shi, tare suka taso basu ta6a rabuwa ba"
Maganar shi ta ɗaurewa Angel kai, ga dukkan alamu suma tagwayen ba rainon kurkuku bane, daga waje aka zo su, Saboda babu addini agidan kurkukun ƙaddara, Su kuma Akwai sarƙar cross a wuyansu, hakan na nufin An canza musu tunaninsu ne,
Gaba ɗaya sun manta da mutun ɗaya daya rage basu su tambayi wanene shi ba, Kowa ya shafa'a da ɗan ta halikin nan, Sai da Parveen ta tuna da Abincinsu, Da sauri ta waiwaya baya don ta kalli Kayan abinci, Ras taji gaban ta ya faɗi ganin Mahaukacin yaron nan zuƙunne gaban faranti Ya ɗauki Chicken shawarma Yana turawa abaki, rabi na shiga rabi na zubewa ƙasa duk ya cakalkala ta, ga kuma Bargunansu daya wurgo ƙasa da fululluka, Da ƙarfi Ta ambaci"Innalallahi! " gaba ɗaya suka kalle ta, Ganin Tana kallon saitin dining carpet ɗinsu Yasa suma suka kalli wurin, Da gudun gaske parveen ta nufi yaron ta shaƙo wuyan rigarshi Ta wurgar dashi gefe ɗaya, Ya faɗi ƙasa kanshi ya bugu, Maimakon yayi kuka sai ya kama Dariya Yana Wuntsila ƙafafuwanshi, Rai a6ace Parveen ta shaƙo wuyanshi tana faɗin"Wanene kai?daga zuwa yau zaka fara Yi mana hauka? kana da hankali Kuwa....." bata kai ƙarshen maganar ba, sakamakon jin saukar Yawun daya watsa mata akan fuskarta, tsabar fusata yasa ta kikkifa mishi maru ka, ya dinga dariya ba ƙaƙƙautawa, daga gani jaki ne bai jin bugu.
Hankalinsu yae matuƙar tashi, saboda sun fahimci cewa Yaron yana da ta6in hankali, Mahaukaci ne aka kawo musu,
"Parveen ki daina bugun shi, Baki ga yaro bane"? Azeeza ce tai mata magana, Rai a6ace tace"Babu ruwana da yaro ne, Ubanshi zanci, har ni zai watsa wa miyau a fuska"? Da alama ta fusata, Rigarshi ta damƙo ta goge miyan daya watsa mata a face ɗinta, duk da haka bata ƙyale shi ba, sai da ta sanya hannu ta dunguri kanshi, Kafin ta miƙe ta nufi toilet don ta wanke fuskarta, badajimawa ba Sai ga parveen ta dawo Cikin ɗakin fuskarta ɗauke da lemar ruwa, Sai Jifar yaron take yi da harara kamar ƙwayar idon zasu faɗo ƙasa.
Deeja tace"Mun shiga uku, tamu ta same mu, Yanzu haka zamu rayu da wannan Ta6a66an? Naufal yace"Bazamu zuba mishi ido ba, Dole mu koya mishi hankali," tsoki haris yaja batare daya ce komai ba,
Danish ne yace da sauran"Idan kuna jin yunwa ga abinci nan, Idan zaku huta ga beds ɗinku nan, sannan......." bai ƙarasa ba yaɗan kalli ƙopar shiga sashen toilet ɗinsu yace"Game buƙatar watsa ruwa ko yin wani uziri wannan ƙopar zaku bi, Anan toilets ɗin mu su ke" Yana magana hankalin shi na akan Matashiyar yarinyar nan, dake ta kallon shi tana faman cizon pink lips ɗinta, ran angel idan yai dubu ya 6aci, bakomai yafi ƙona mata rai ba face ganin yadda take kallon Danish tana cizon le6e, tarasa gane me hakan ke nufi, to ko dai halittarta ce ahaka? Ko kuwa wani sabon salon iskancin ne"?
"Bana jin yunwa, I need to take bath, before in kwanta In huta" Ƴar gidan daddy ce tayi maganar tana ƙoƙarin sauke School bag ɗinta, Idon kowa na akanta, Miƙa ma Danish Backpack ɗin tai tare da cewa"Ka ajiye min ita, sannan ka raka ki toilet ɗin, bazan iya ganewa ba" Wani irin kallon harara angel take jefa ma Danish, duk yasha jinin jikin shi, Sam ya kasa kar6ar jakar Unaiza, Sai angel ce ta kar6e jakar tace"Zan ajiye maki ita, sannan zan raka ki toilet ɗin, idan ma kinaso har cuɗa maki baya zan Iya yi" Girgiza kai Unaiza tae tana fadin"No, bana so, ki dai ajiye min back pack ɗin, Shi sai ya raka ni toilet ɗin" mamaki ne ya kama angel, aranta tace"that's impossible, kinzo da bidi'a," Kar6ar jakar tayi daga hannun unaiza taje ta ajiye mata ita gefen donta mai ɗauke da no 16, juyowar da za ta yi, karaf idanuwanta suka sauka akan Unaiza da ke ƙoƙarin cire Coat ɗinta, Bakomai ne ya faɗar mata da gaba ba, face Ƙirjin Unaiza, Musamman da ta ƙarasa Cire rigar Hankalin Kowa Ya koma kansu, Kamar babu riga ajikinta saboda Yadda surar su ta bayyana ajikin vest din, Manya manya dasu kamar balan balan, shatun nipples ɗin sun fito sosai, kamar zasu huda ta, gata yarinya amma tubarkalla, Allah yayita da boobs, "
Kwanciyar hankali ya ƙarewa angel, Kishi ne ya addabi zuciyarta, kodan hada ƙarin ita bata da su ne, Oho dai,
Bayan Unaiza ta ɗebe Coat ɗin Ta miƙa ma Danish tace Ya ruƙe mata, Hannun shi na kerma ya ruƙeta, wani irin ƙamshi ne ke fita jikin coat ɗinta," hannayenta ta ɗaura saman gajeran skirt ɗinta, Waro ido angel tae baki a sake take kallon ikon Allah, Cire shi tae ya rage daga ita sai Short na mata, "
duk su naufal suna a tsaye suna kallon ikon Allah, Miƙe ma Danish Skirt ɗin ta yi"Ka ajiye min su" Kafin yai yunƙurin kar6ar skirt ɗin angel tai saurin komawa wurinsu ta sanya hannu ta kar6i skirt din ta kuma ƙwaci coat ɗin dake a hannun Danish, Fuskarta a ɗaure ta nufi akwatinsu ta sanya mata su a ciki, Kafin ta dawo ta tsaya agefen Danish,
"Muje ka raka ni toile ɗin" ta yi maganar tana ƙoƙarin ruƙo hannunshi, Angel tae saurin ka6e mata hannun"Ni zan raka ki," Bata jira amsar da unaiza zata bata ba, Taja hannunta, ta wuce da ita zuwa sashen toilet ɗinsu, sai bayan da suka shige, azeeza da parveen suka kalli juna, Alamar mamaki, sufa sunga abunda basu ta6a ganin irin shi ba, tun da ko tsohuwa nata azube suke kamar silifas, Cikinsu kuwa ba wadda ta ke da su irin na ƴar gidan daddy, har ƙwara waɗan da suka fara manyanta, Sune ya fara fito mawa, amma ita ko wannan ƴar shilan ƙirjinta sunfi ƙarfin jikinta da shekarunta.
"Gabriel, banji kace komai ba"? Danish ne yae mishi magana ganin yayi tsaye bai motsa ba shi da sauran ƴan uwan nashi, Cikin sanyin murya yace"Inaso na kwanta, saboda kaina ciwo yake yi min" Nuna mashi gadonshi danish yae da hannu, Yace mashi thanks kafin Ya nufi gadon, Sai da ya fara cire coat ɗinsa, Ya ɗaura ta gefe, Sannan ya haye gadon ya kwanta,
Kallon Jamima su kayi ƴar ƙaramar yarinyar nan, parveen ta raya aranta cewa"Wannan dai rainonta zamuyi da alama" Haris ne yace da ita"Kefa? Zaki kwanta ko xaki ci abinci" Ta6e baki ta ɗanyi kafin tace"Yunwa nake ji," Deeja tace"amma ke kike yin wanka da kanki"? Ɗaga mata kai tayi"Eh, inayi yanzu, amma sai ana cuta min bayana saboda hannu na bai kai wa" Murmushine ya bayyana akan fuskokinsu, don ba ƙaramin burgesu tayi ba, gata ƴar kyakkyawa da ita, Hibba tace"idan ma kinaso har wankan sai muyi maki," dariya tasaki tare da sanya tafin hannayenta ta rufe fuskarta, alamar taji kunya.
Ruƙo hannunta Haris yae acikin nashi yace"muje muci abinci ko"? Tace mishi eh, " mubeen yace"to itafa Wannan bamu ji ra'ayinta ba, " yae maganar yana nuna Sarah dake atsaye Ta ruƙe qugu, Yatsina fuska Ta ɗanyi can kuma saita ƙaƙaro murmushi tace"Nima bana Jin yunwa, zan kwanta na huta ne" tae maganar tare da juya ta nufi gadajensu, Ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallo, a sukwane Ta juyo ta kalle su Deeja tace"wai a ina zata kwanta ne"?
Nan take su ka fahimci cewa Ta raino gadon ne, Wato yayi mata ƙanƙanta, Hannah tace"Acan inda kuka Baro, a saman Ina ki ke kwana ne"? ta6e baki Sarah ta yi Ba tare da ta bata amsa ba, Ta maida idonta kan gadon, Ta curo bargon saman shi, Ta shimfiɗashi a ƙasa, ta ɗauko pillow ta jefa, Kafin ta cire coat ɗin Jikinta ta ɗaura a ƙasa, Ta faɗa sama gadon ta kwanta.
A bunda ya faru bayan Angel ta raka ƴar gidan daddy toilet, suna shiga ciki taja burki ta tsaya Tana faman zazzare blue eyes ɗinta haɗi da yatsina fuska, Angel tace"Ni xan Koma, ayi wanka lafiya" har zata juya muryar Unaiza ta dakatar da ita
"Nifa ban fahimta ba, Ina bathtub yake ne? tana nufin (kwamin wanka) Wannan wani irin toilet ne kamar na Marasa galihu" Tsabar mamaki yasa angel sakin baki kamar sakarya tana kallonta, Daƙyar ta iya buɗe baki tace"ba mu da bathtub, Iya a bunda idonki suka gane maki acikin toilet din su muke dasu, Ga Shower nan, Sai kuma bokiti, can kuma Soso ne da sabulu," aruɗe unaiza tace"that's Impossible, ae ni bana sharing soson wanka, Kuma bana wanka in ba a cikin bathtub ba, I can't stay here i wanna go home, cos daddy ba haka Ya kwatanta min school ɗin ba, Yace min fa komai irin na Gidan mu ne, but why naga banbanci"? tamkar zata fashe da kuka tayi maganar, har saida gaban angel ya faɗi jin abunda tace, Wato ita duk a tunaninta School ce aka kawota batasan cewa Prison bane, To me hakan ke nufi? Kodai mahaifinta ne ya yi mata ƙarya kan cewa za'a kawo ta makaranta! Tashin hankali Sai lokacin angel ta tuna da irin uniform ɗinta na gayu, dama ta yi mamakin ganinta da haɗaɗɗun takalma ƴan ƙwaras ƙwaras, Ga gajeran skirt na gayu, Ga kuma ƙatuwar School bag Ta goyo, Tabɗijancan, In dai a bunda take hasashe ya tabbata to kuwa Iyayenta sun Cuce ta, Mamaki Ya hana angel cewa komai, taya akai basu gusar mata da hankalinta ba? Kamar yarda aka yi ma Gabriel? Ko kuwa sihirin ne bai kama Jikinta ba?
ta yi zurfi acikin tunaninta muryar unaiza ta katse ta"Pls talk to me! Ni ban fahimci komai ba, game da school din nan," tashin hankali ne Ya bayyana ƙarara akan fuskar angel, miryarta na ɗan rawa tace da unaiza"wacece ke? Dama ke ba rainon Kurkuku bace"? Waro ido tae tare da maimaita sunan prison da angel ta faɗi, Ba don ta fahimci me hakan ke nufi ba,
"Ban fahimce ki ba, Naji kince prison, Nifa daddyna yace dani xai sanya ni a high school Na south korea, saboda inason kallon drama ɗin su komai nasu yana ƙayatar dani, Daddyna yana yi min komai nake so, shi ne Da kanshi, Ya sama min admission a school ɗin nan, a gida aka kawo min uniform na sanya ajiki na......" unaiza bata ƙarasa maganarta ba, Angel ta ɗaura hannunta akai,! Irin ta shiga ukun nan, fito wa ta yi daga Cikin toilet ɗin Ta tsaya daga waje tana ambaton"Innallahi wa'inna ilaihirraji'un"! da sauri ƴar gidan daddy ta biyo bayan angel, baiwar Allah duk ta ruɗe ta rasa gane me angel ke nufi,
"Pls tell me the truth Ko ba school bane nan ɗin? I ave to know" wani irin kallon tausayi angel ke binta dashi, muryarta kamar ta mashayin giya tace"Zaki iya tuna Ta ina aka kawo ki Nan" girgiza kai tayi"I can't remember, Ni dai nasan time da masu aikin gidan mu, suka taimaka min nayi wanka na sanya uniform da daddyna ya bani, so bayan nan sun rakoni zuwa wurin da motocin bodyguards ɗina su ke, sun buɗe min mota, Na shiga Ciki na zauna, ina ta farin ciki, duk na qagara mu ƙarasa Airport sai bacci ya ɗauke ni, daga nan ban ƙara tuna komai ba, sai dai na ganni Acikin School ɗin nan tare da sauran students din da muka zo da su" Tana magana tana yatsina fuska daga gani ɗabi'arta ce yin hakan,
Jinjina kai angel tae yayin da take kallonta, haƙika ta yi mamakin da basu canza mata tunaninta ba, tun da har ta iya faɗin yadda aka kawota Cikinsu, tabbas kowanene Ubanta ba ƙaramin Mugu bane, Azzalumi, Wato shi wayau yayi mata ya fake da cewa za'a kaita Sk don ta yi karatu batasan cewa Sadaukar da ita ya yi ba zuwa Gidan Kurkukun ƙaddara, don biyan wata buƙata tashi, Rayuwarta abun tausayi baiwar Allah, Sai da aka gama sangartata, Daga gani an gama jiyar da ita duk wani daɗi na duniyar nan kafin aka tsamota daga aljannar duniya aka kawota gidan kurkukun ƙaddara,
Ganin irin kallon da angel take binta dashi ne yasa tace"Pls Ke nake jira ki bani amsa," A ƙagare tayi maganar,
"Ya sunan mahaifinki? Kuma wanene shi"? Muryarta A disashe tace"Ae ni bansan real name nashi ba, na dai san ana kiran shi Jan wuya..." bata ƙarasa maganar ba angel ta katse ta da cewa"Ba ki ta6a zuwa school bane? Da wani suna kike amfani"? Ta bata amsa da cewa"ni tunda na taso ban ta6a zuwa school ba, daddyna bayaso ina shan wahala, A gida ake koya min karatu, yanzu ma don na kwallafa raine akan inason zuwa south korea karatu shine yace zai sani...."
Jinjina kai angel tae kafin tace"Amma awace ƙasa ku ke zaune duk da naji kina magana da yare biyu, hausa da turanci so na kasa gane wani jinsi kike"
Wannan karan tamkar zata fashe mata da kuka ta yi maganar don ta gaji da tsayuwa,
"My dad is from Nigeria and my mom is from England. I've never been to Nigeria, and I don't know my dad's hometown or his job, Ni da Mommyna ne kawai muke rayuwa a england sai ƴan Aikin gidan mu, amma yana yawan zuwa kawo min ziyara daga Nigeria"
Hankalin angel ya ƙara tashi, daƙyar tace mata yanzu kiyi haƙuri kiyi wankan idan kin kammala zanyi maki bayanin komai" Girgiza kai tayi"ae bazan iya wanka awannan toilet din ba, saboda ba irin na gidanmu bane, ni nasaba acikin bathtub nake yi, kuma masu aikin gidan mu ne suke taimaka min wurin yin wankan"
Kallon ta kawai angel ke yi, Iya cutuwa dai an Cuci yarinyar nan, tama rasa taya zata fahimtar da ita cewa Nan kurkuku ne, ba high school ta ƙasar korea ba? Zaiyi wuya ta fahimce ta, babbar matsalar irinsu Suna da ƙarancin imani, sannan basu da tawakkali, Tana iya ta faɗa mata azo asamu matsala, Ya za tayi da ita?
Yayin da su Angel suke a sashen toilet dinsu ita da ƴar gidan daddy, Su kuma can ɗaki suna fama da wannan mahaukacin Yaron, abunda ya faru Suna ƙoƙarin zuwa suci abinci, Eve tace dasu,
"Wai nikam Ina Yaron nan yake ne"? Kafin wani ya buɗe baki ya bata amsa suka Ji ƙarar karyewar wani abu acikin kunnuwansu, Agigice suka kai idanuwansu wurin da suka Jiyo sautin ƙarar, ransu yae mutuƙar 6aci ganin Irin uwar 6arnar da Yaron yayi musu, Gaba ɗaya Ya kado da cake ɗinsu ƙasa, Table ɗin Ya 6alle, Cake ɗin ya ƙundumo kasa Ya tarwatse, hakan bai ishe shi ba, sai da ya hau saman Cake ɗin Ya dinga duma hannuwanshi aciki Yana Kwaso shi Yana turawa abakinsa, duk ya 6ata uniform ɗin jikin shi da cake ɗin, A ƙarshe ma sai ya hau saman Cake ɗin ya dinga burgima yana dariya, a fusace parveen ta nufi inda yake, Haris da Danish suna ta ƙoƙarin dakatar da ita akan kada ta buge shi, amma ina ko waiwayon su bata yi ba, wata irin damƙa takai ma wuyan rigar shi, ta ɗago dashi ta daddage ta buga kanshi a ƙasa, azabar zafi yasa shi fashewa da kuka mai tsiwar gaske, tana huci tace"Shege ashe kana jin bugu, ae nayi tunanin kurma ne kai" Sautin kukan yaron ne ya karaɗe kunnuwansu angel dake a sashen toilet ɗinsu, da gudu suka nufi ɗakin suna shugowa suka ci burki suna kallon Yaron dake ta kuka, Hatta gabriel dake kwance yana bacci shi da Sarah sai da suka farka saboda sautin kukan fitinannan Yaron, An rasa me lallashin shi acikin su, haushin shi suke Ji, Ya baƙanta musu rai, duk irin yadda suka ƙwalla fa ransu ga son cin cake ɗin nan ya tarwatsa komai, Farin Cikinsu Ya gushe, Har ga Allah basu Ji daɗin zuwan prisoners ɗin nan ba, Saboda mutun biyun nan dake acikinsu, Mahaukacin yaron nan da Angel ta sanyawa suna Majnun saboda Yaƙi faɗa musu sunanshi, Sai kuma Unaiza ƴar gidan daddy, A ranar Bayan Danish ya lallashi Yaron Yaje dashi toilet ya wanke mishi Jikin shi Da uniform ɗinshi da ya 6ata da cake, Ya shanya su saman igiyar toilet ɗinsu, ya ɗauko bargo Ya ƙudundune shi ajiki yakai shi Daki ya kwantar dashi saman gadon shi, Cikin ƙanƙani lokaci bacci yayi awon gaba dashi, Hankalinsu har ya kwanta, ashe ƙura bata lafa ba, Sun gama shan wahalar gyara ɗakin nasu da ya 6ata musu ya hargitsa komai, Suna ƙoƙarin zama su huta, Unaiza tace musu Yunwa take ji, Suka ce mata Ga abinci can saman dining carpet ɗinsu taje taci, Saboda damuwa ma yasa babu wanda ya waiwayi abinci acikin su, Sai wannan ƙaramar yarinyar jamimah ita kaɗai ta zauna tana ci.
Ita ko Unaiza ƴar gidan daddy ta ce musu ba zata ci ba saboda a gidansu saman dining table ake jera mata abinci kala goma sha biyar, sai ta za6a ta darje, hatta abincin ma abaki masu aikin gidansu suke bata tana ci" gaba ɗaya ta rikita su da maganganunta, sun gaza gane inda ta dosa,