Kenza eBookz

Kurkukun ƙaddara takun farko by by boss bature - Chapter 75

Kurkukun ƙaddara takun farko by by boss bature - Chapter 75

Kurkukun ƙaddara takun farko by by boss bature Chapter 75: Kurkukun ƙaddara takun farko by by boss bature Chapter 75. Angel, Hannah, Hibba, Deeja, Parveen,…

3,247 words

Angel, Hannah, Hibba, Deeja, Parveen, Eve, Yasmin, Rubina," tsabar farin ciki yasa suka fasa ihu Jin ta kira sunayen su hakan na nufin Tana acikin hayyacinta, wani irin farin ciki ne ya lullu6e Su, kamar waɗanda akayiwa albishir da mukullin fita daga cikin kurkukun ƙaddara.

Tana so ta bayyana masu irin kewarsu da tayi sai dai takasa magana, saboda hawayen da suka ciko idanuwanta, daƙyar ta iya buɗe masu hannayen ta tare da yi masu alamar su matso kusa da ita, da sauri suka matsa ta haɗa azeeza da parveen da deeja ta rungumesu, sai lokacin ta samu damar fitar da kukan da take 6oyewa, sosai ta fashe masu sa ku ka, suma kukan suke yi an rasa me lallashin wani acikin su, ta ɗauki tsawon lokacin kafin ta saki su deeja, ta miƙa masu Hibba hannu suka matso suma ta rungume su a ƙirjinta, dukkan su saida suka ji ɗumin jikinta, da hannayensu suka dinga share mata hawayen dake akan fuskarta, itama ta sanya hannunta tana share ma kowannansu na kan fuskarshi.

Cikin sanyin murya ta furta"ashe da rabon mu sake ganin juna nida ƴan uwana! ashe mafarkina zai zama gaskiya na sake yin rayuwa a cikin ku? Jan numfashi tai kafin taci gaba da cewa"duk yadda zan faɗa maku irin kewarku da nayi ba zaku fahimta ba, haukane kawai banyi ba, amma naji jiki na rashin ku atare dani, na zubar da hawayena kamar bazan rayu ba, Allah ne kaɗai yasan irin raɗaɗi da ƙuncin da na shiga........" kasa ƙarasa maganar ta yi saboda kukan daya ciyota, da sauri Angel ta sanya hannayenta biyu ta dafa shoulders ɗinta tana lallashinta.

"Batul ki daina kuka dan Allah, kuma ku daina zubar da hawayen ku, godiya yakamata mu yi ma Allah daya dawo mana dake lafiya, duk da naga sauyi atattare dake, bamu san ina aka kaiki ba! Me a ka yi maki na tsawon watannin nan! Na yi maki tambayoyin nan ne saboda su ne damuwar mu, amma bamu buƙatar amsar su ayanzu, saboda kwanciyar hankalin ki mu ke so, ashirye mu ke da mu sanyaki farin ciki, wanda zaisa ki manta da duk wata damu da kika shiga na rashin mu atare dake,"

Kalaman Angel ba ƙaramin sanyaya mata zuciya su ka yi ba, atare suka ɗaga hannayensu sama suna yiwa Allah godiya haɗi da yi ma ƴar uwarsu batul addu'a, duk tana sauraronsu, wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta, bayan sun kammala yi mata addu'ar ne, ta ɗago da kanta daga jikin Angel, Ganin tana kallon gadajensu Danish yasa duk suka sha jinin jikin su, aruɗe take ƙare masu kallo, abun da basu ta6a tsammanin zata tambayesu ba, sai ji su ka yi tace"Ina Danish!" shine mutun na farko da ta fara tambayarsu, sun yi mamakin hakan duk irin abunda yayi mata, cigaba da tambayarsu ta yi cikin ruɗu.

"Meyasa bangan su asaman gadajen su ba? Ina Haris ina Javed da Mubeen da Naufal? Ina su ka je ne? Ko sun shiga toilet ne"?

Angel ce ta yi mata magana"ki yi haƙuri batul, zuwa gobe da safe zamu faɗa maki komai, yanzu dare yayi sosai, ki kwanta ki huta ," ta yi maganar tare da ruƙota, ta kwantar da ita tare da janyo bargo ta lullu6a mata shi saman jikinta zuwa ƙirjin ta.

Ta yi mata hakan ne duk don ta kawar mata da tunaninta, na tambayarsu agame da su Haris.

Mayar da dubanta ta yi gasu Deeja"Ku je ku kwanta, Zuwa gobe za mu yi magana da ita" Ba don sunso ba suka miƙe kowa ya nufi tsohon gadon shi, duk don saboda ita suka kwanta saman su yau, itama sarah ta nufi shimfiɗarta ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe saƙe dangane da ƴar uwarsu batul da ta gani yau, da alama akwai wani abu daya ɗan sha mata kai.

Mutun biyu ne ya rage Azeeza dake zaune saman gadon batul, sai jamimah dake zaune gefen gadon sai gyangyaɗi ta ke yi kamar zata faɗo ƙasa.

"Azeeza taso muje in raka ki ki kwanta," maƙe kafaɗa Azeeza tayi tare da cewa"Inaso na kwana a gefen batul" shiru Angel ta ɗanyi tana kallon fuskarta, taci burin ta kwana tare da batul dinta, ga Azeeza ta nuna tanaso.

Ita kanta batul ɗin, bata son Angel tabar gadon nata, sai satar kallon juna su ke yi, da alama akwai wani abu daya ɗaure masu kai agame da canjin da kowan nan su ya yi, Sai da Angel ta ruƙo azeeza ta kwantar da ita gefen batul, tukunna ta sauko daga saman gadon, still idon batul akan fuskarta.

"Zanje na kwanta, ki kulamin da kanki, gobe zamu yi magana" ta ƙarasa maganar tana sakar mata murmushi. lumshe ido batul ta yi tare da ɗan jinjina mata kai, hawaye ne masu ɗumi suka soma gangarowa ta cikin idanuwan nata, nan take Angel taji gabanta ya faɗi, sai dai bata tambayeta hawayen menene ba, ta bari sai zuwa gobe su yi magana.

kasa tafiya tayi, komawa tayi daga gefen gadon ta ɗan zauna tare da duƙar da kanta saitin fuskar batul, ta manna mata kiss saman forehead ɗinta da cheek nata, a hankali batul ta ɗan ware idanuwanta tana duban Angel wadda tuni ta miƙe daga gefen gadon, sai da ta fara ɗaukar jamimah, kafin ta juya ta kwantar da ita saman gadon Danish itama ta kwanta daga gefenta tare da rungume jamimah a jikinta, sai kallon juna suke yi ita da batul da ke akwance saman gadonta, Da yake suna fuskantar juna.

Tsawon lokaci sunata ta kallon juna, ɗakin yai tsit baka jin sautin komai, sun ƙi bari bacci ya ɗauke su, gani su ke yi kamar in suka runtsa za'a ƙara zuwa a ɗauke masu ita, zuciyoyinsu a cike suke da tambayoyi iri iri da suke son su yi mata, idan gari ya ware, sun kwana da wadataccen farin ciki acikin zukatansu saboda dawowar ƴar uwarsu batul, kaɗan daga cikinsu ne suka samu damar tuntsawa.

❤PRISONERS💖

A washe garin ranar tun da sassafe, ta soma jin hayaniyarsu a cikin kunnanta, muryoyinsu da alamun farin ciki atattare da su, a hankali ta ɗan buɗe idanuwanta, biji biji ta fara ganinsu a kewaye da gadonta, har saida ta ɗan firgita, daga bisani ne idanuwanta suka dawo normal taga fuskokinsu a washe sai murmushi suke sakar mata, azeeza da ke a gefenta kwance, ta ɗan tada kanta saman gwiwar hannunta, ta ƙura mata ido sai kallonta ta ke kamar zata lashe ta.

"Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah! Allah mun gode maka daka dawo mana da ƴar uwar mu batul, Nifa jiya da daddare dana kwanta, gabana ya dinga faɗuwa gani nake kamar in na runtse idanuwana zan farka inga babu batul ɗin mu" Deeja ce ta yi maganar fuskarta ɗauke da murmushin farin ciki.

Parveen tace"wlh nima haka naji araina, shiyasa yau da safe ina farkawa nai wuff nazo gaban gadonki don in duba in ga ko kina nan" ƙayataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskar batul, ta rasa akan wa zata tsayar da idanuwanta, sai faman jujjuya eye balls ɗinta ta ke yi akan faces ɗin su.

"Ni kaina da mafarkin ki na kwana, ƴar uwata rabin raina" da sauri ta wurga eye balls ɗinta kan fuskar Angel wadda zuwanta kenan, Tana agefen Hibba, wani murmushin ne ya ƙara bayyana akan fuskarta, wanda ke nuni da irin farin cikin da take a ciki.

"Fatan ba mu takura maki ba, mun tada ki daga bacci, wlh mun yi kewarki ne kamar mu zauce" acewar hibba, calmy ta soma magana"Nafi so ku takura min hibba, aini abunso ne a wurina, in gan ku atare dani, ko na minti ɗaya bana son wani a cikin ku ya nisanta dani, ba dan ƙaddara ta rabani da ku ba, ku kan ku kun sani, da ƙafafuwana bazan ta6a yin nesa da ku ba" muryarta na ɗan rawa ta ƙarasa maganar, tuni idanuwanta suka cicciko da ƙwalla, ita kaɗai tasan irin raɗaɗin da ta ke ji a cikin zuciyarta.

"Batul pls don't cry, idan har ba so kike zuciyoyin mu su raunata ba, mun fi buƙatar farin cikin ki ayanzu, ki daure pls," Deeja ce tai maganar, lumshe idanuwanta ta ɗanyi yayin da take binsu da kallo, su kansu sun fahimci akwai wani abu dake damunta.

"Azeeza irin wannan kallo haka, " daƙyar ta furta maganar, tana kallon azeeza, murmushi ta sakar mata tare da cewa"Ƙaunarki nake yi batul, dole in kalle ki don baki san irin kewarki da nayi ba. Kamar in haɗiye ki" tayi maganar tana wage bakinta, Hakan da ta yi ba ƙaramin dariya ta basu ba.

Ita kanta batul ɗin saida ta ɗan murmusa, a hankali ta yunƙura ta miƙe, itama azeeza ta miƙe zaune saman mattress ɗin, Saukowa ta yi daga saman gadon taci gaba da tafiya tana bin ɗakin nasu da kallo, ganin irin sauye sauyen da a ka yi mashi, gaba ɗaya suka bi bayanta suna tafiya atare da ita, dakatawa tayi da yin tafiyar tare da juyowa ta kallesu tace"Jiya na tambaye ku amma ba ku bani amsa ba, ina Danish dasu haris su ke ne"? Deeja ce tai ƙarfin halin faɗa mata cewa anzo an tafi dasu almost one week, An riga tafiya da Danish," iya abunda ta sanar da ita kenan, bata faɗa mata awani hali aka tafi da shi ba, jinjina kanta ta yi ba tare da tace komai ba, sai dai fuskarta ta nuna alamun damuwa, kuma idanuwanta hawaye ne acike dasu.

"An kawo mana sabbin prisoners ne? Jiya kamar naso inga wata ƙaramar yarinya," tai tambayar tana kallonsu "naga kuma sabbin gadaje, kusan goma sha biyar" yasmin ce ta bata amsa dacewa"Eh, bayan tafiyarki aka kawo su, Amma mutun biyar ne prisoners ɗin, sai dai daga cikinsu Giants sun tafi da mutun uku, yanzu biyune atare damu. jamimah itace ƙaramar sai Sarah," ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa"ku bani labari mana, dame dame ya faru bayan bana nan"? A taƙaice Angel ta sanar da ita duk wani abu da ya faru bayan bata nan sai dai bata faɗa mata wanda zai sanyata damuwa ba.

"Mu koma mu zauna batul," yasmin ce tai mata maganar, ganin sai yawo su ke yi cikin ɗakin, ga shi daga gani jikin nata babu ƙwari, ga ƴar guntuwar rigar dake a jikinta sai ɗagewa ta ke yi.

"Kina jin yunwa" parveen ce tai mata tambayar, ɗaga mata kai ta yi alamar eh, langwa6e kai parveen"wayyo Allah, ga shi babu abinci sai giants sun kawo mana" ƴar dariya Batul ta saki kafin tace"Ki kwantar da hankalin ki, kallon ku da na ke yasa naji na ƙoshi, babu wani yunwa atare dani,"

"Batul baki bamu labarin ina aka kai ki ba tsawon wata uku? Sannan waye ya dawo mana dake ko giant ne, mun ga kin canza mana sosai, kin rame kamar babu ƙoshin lafiya atare da ke" rubina ce tayi maganar,

Shiru ta ɗanyi kamar bazata amsa mata tambayoyin ta ba, duk su ka tsareta da ido suna kallonta, tun kafin ta fara magana Angel ta raya aranta cewa batul baza ta faɗa masu gaskiyar abunda ya faru da ita ba, ko dan kada ta sanya su damuwa.

A tsanake ta soma magana"bakomai ne zan iya tunawa ba, tun time da aka tafi dani, na dai san ba a cutar dani ba, ramar da ku ka gani a jikina bata komai bace face rashin ku atare dani, na tsinci kaina acikin wani ɗaki ina rayuwa ni kaɗai, ban rasa ci da sha ba, ana kawo min lafiyayyen abinci, ina yin wanka har ma in kwanta in yi bacci, mafi yawancin lokutta, ina yawan yin kukan rashin ku, in dinga ihu ina ambaton sunayen ku don kuzo ku ɗauke ni sai dai shiru babu mai jina........." iya abinda ta faɗa masu kenan, kuma sun yarda da maganarta, banda Angel, don koda tana basu labarin idonta akan Angel don tasan bazata yarda da ita ba, abunda yasa su deeja suka yarda da labarin da ta basu, saboda an dawo masu da ita ba kamar yarda aka saba dawowa dasu ba, Cikin mawuyacin hali, wasu ma basa a cikin hayyacin su.

"Batul yakamata kije ki yi wanka, akwai sabbin kaya da muka fada maki tsohuwa tamira ta bamu zamu ɗauko maki naki ki sanya, sannan muna so zamu gyara maki gashin kan ki" fuskarta ɗauke da murmushi tace masu toh, Eve tace"wai ina Uniform ɗin ki su ke ne? Ya akai aka sanya maki wannan guntuwar rigar launin Ja"? Muryarta da en ina tace"am..in..nima bansani ba, bansan waye ya canza min ita ba, kawai rana ɗaya na farka na ganni da ita a jikina" wani irin kallo Angel take binta dashi, kallon ban yarda da maganar ki ba, sai faman wurwurga ƙwayar idanuwanta ta ke yi, da zarar sun haɗa ido da Angel saita kawar da kanta gefe.

Ganin hakan yasa Angel ta ruƙo hannunta a cikin nata sosai ta damƙe shi tare da cewa"Muje na taimaka maki kiyi wankan" da sauri ta girgiza kai tare da cewa"Zan iya Angel, ki bari zanje nayi da kaina" a ruɗe tayi maganar, hakan ya ƙara tabbatar ma Angel abunda ta ke hasashe akanta, ta 6oye masu abunda ya faru da ita.

Gyaɗa kai Angel tayi"Its ok, amma mu fara shiga toilet ɗin, mu wanke maki kanki, In yaso daga bisani saimu fito mu barki ki yi wankan" muryarta adarare ta amsa mata da toh.

Mutun uku ne suka haɗu wurin wanke mata gashin kanta saboda yawanshi, Angel da Hanna sai Seeja, Sosai suka murje gashin kan nata, Bayan sun kammala wanke mata kan, suka barta cikin toilet din don tayi wanka, Angel fa jikinta duk ya yi sanyi, a ƙagare take da su samu damar da zasu ke6e da ita don suyi magana, sai dai ga dukkan alamu ita batul ɗin bata son su yi magana, shiyasa take kakkauce mata, Bayan wasu ƴan mintuna, Batul ta fito daga wakan, dama tun kafin fitowarta Angel ta ɗauko mata sabbin kayanta, ba tare da 6ata lokaci ba, ta zura uniform din a jikinta, Masha Allah, zayyana irin kyan da batul tayi a cikin kayan nata 6ata baki ne, abunka ga fara sol, Sun ƙara fiddo mata da kyanta, don ma ta ɗanyi rama.

daga ciki ta sanya red vest dinta, sama ta ɗaura wrap coat dinta, kafin ta sanya black trouser din, Angel ce ta taimaka mata wurin ɗaure igiyar coat ɗin, ta ɗaura mata Cotton scarves ɗinta saman wuyanta, Bayan ta kammala gyara mata su tsaf a jikinta.

Su Parveen sai santin kyanta su ke yi, Hannu biyu angel ta sanya wurin janyota a jikinta, sosai ta rungumeta, tana ɗan bubbuga bayanta, in a low voice ta furta mata"Ina son magana da ke, amma na lura kamar baki so why"? Muryarta na ɗan rawa tace"Angel, banason tuna abunda ya faru dani, pls kada ki matsa min kada ki tambaye ni komai, na roƙe ki, kuma bana so hakan ya 6ata maki rai" suna yin maganar ne ba tare da sun raba jikinsu daga na juna ba.

"Shikenan batul, bazan tambaye ki ba, ni kaina bana son na takura maki, zan jira ki har zuwa time da kika ji zaki iya sanar dani sai ki faɗa min" ta amsa mata da toh," Deeja dake ta kallonsu manne da juna ta fahimci cewa magana su ke yi, bayan sun raba jikinsu, ta dinga bin su azeeza tana rungume su a jikinta tana faɗa masu irin kewarsu da ta yi, Deeja kuma taja hannun Angel su ka koma gefe ɗaya,

Tambayarta ta yi me suka tattauna da batul, ta sanar da ita cewa ta tambaye ta ne game da abunda ya faru da ita amma bata faɗa mata komai ba, Deeja tace"kada mu takura mata, tunda ta nuna bata son mu sani, mu ƙyale ta kawai, wata kil hakan zaifi mana kwanciyar hankali," Angel ta gamsu da maganar deeja.

Badajimawa ba, Giants suka kawo masu lafiyayyan abinci, Saboda tsabar ƙauna, a baki suka dinga ba batul tana ci, sunƙi bari ta sanya hannunta taci, hakan ba ƙaramin karya mata zuciya yayi ba, tabbas an zalunce ta da aka raba ta da ƴan uwanta, amma yanzu Alhamdulillah tunda gata a cikinsu, da ranta da lafiyarta.

Bayan sun kammala Cin abincin, Giants suka tattara Farantan suka tafi dasu, A saman shimfidar sarah, suka zazzauna suna fira tare da batul, Angel tana zuƙunne gaban akwatinansu, Ta buɗe ta ɗauko Nail cutter da nail filler tare da madubi, ta dawo ta miƙe ma Sarah tace gashi ta gyara ma ƴar uwarsu akaifa, Murmushi sarah tasaki, tare da sanya hannu ta kar6a, Kafin su fara gyaran akaifar, Angel tace ta ɗan dakata, tana so su kalli faces ɗinsu a cikin madubi, ita da ƴar uwarta batul, Gefen batul ta zauna tare da ɗaga madubin, Ta haɗa fuskokinsu wuri ɗaya, Suka natsu suna kallon juna, hakanan Angel ta dinga jin faɗuwar gaba a yayin da take kallon fuskar batul ta cikin mirror, su azeeza sai faman leƙo da fuskokinsu suke yi suna kallon su.

"An ta6a faɗa maku cewa, Kuna bala'en kama da juna" Sarah ce tai maganar, parveen tace"wlh kuwa nima saida ki ka yi maganar nan tukunna na lura da hakan, Angel da batul suna kama sosai, musamman ta wurin shape ɗin bakinsu, duk da ba launi ɗaya bane, da kuma hasken fatarsu, gashin kansu ma Ya yi shige, hatta tsawonsu iri ɗaya,"

Deeja tace"ae hatta Yatsun hannuwansu dana ƙafafuwansu iri ɗaya ne sak babu bambanci, najima da sanin wannan ban ta6a faɗi bane" sarah tace"to kodai ƴan gida ɗaya ne"? Girgiza kai Yasmin tai tare da cewa"A labarin da Angel ta bamu, ita kaɗaice Awurin daddynta, mommynta ma, tun tana yarinya ta gudu tabarta, bata da ƴar uwa mace tun da ta taso a rayuwarta,"

Sarah tace"hmmm adai yi shiru kawai amma fa ni akwai abunda nake zargi, ina da wata baiwa da ku ba ku sani ba, tun kasancewa ta a prison, nake wannan hasashen, nasha ganin masu kama da juna wanda su basu lura da hakan ba, sai dai ina tunanin zaman tare ne yasa muke kamanceceniya da juna, yanzu a cikin ku nan, kaf ɗinku Naga kamanceceniya atsakaninku da junan ku, Hatta wannan yarinyar da aka kawo mu tare da ita, Me take da suna....." Eve ce ta ƙarasa mata maganar da cewa"Kina nufin Ƴar gidan daddy" jinjina kai tayi "eh ita nake nufi, akwai kamanceceniyarta da wani acikin ku, amma bazan faɗi ba" tana ƴar dariya ta yi maganar,

"Ko kina nufin azeeza? Don kinga kalar gashinsu yayi shige da launin fatarsu," girgiza kai tayi"a'a, ba azeeza ba, bana so na faɗi maku ne"

Roƙon ta su ka dinga yi haɗi da yi mata magiya akan ta faɗa masu da wa take kama, da kuma sauran waɗanda ta ke hasashen suna da kamanceceniya a tsakaninsu, tace masu itafa su daina yarda da maganarta, Ƙarya ta ke yi masu"

Haushin da suka ji ne yasa suka dunƙule hannu suna yi mata dundu abayanta, Abun saiya koma wasa, duk wannan abun da suke yi Angel da batul suna sauraronsu, sai dai hankalinsu ba akansu Ya ke ba, Yana akan junansu, Sai kallon fuskokinsu suke yi ta cikin madubi kamar zasu lashe juna, Sai da suka gama ƴar buge bugen da sarah, kafin daga bisani, kowannansu Ya natsu, suna ta nishi kamar waɗanda suka sha gudu.

Bayan sun samu natsuwa, Sarah ta soma gyarama batul akaifarta, Allah yayi mata baiwar Iya gyara akaifa, Batul taji daɗin ganin yadda ta gyara mata akaifarta, ta dinga yi mata godiya, Sarah tace tadaina yi mata godiya, domin kuwa babu godiya a tsakanin prisoners,"

Readers Also Read