Kurkukun kaddara book 1 - Chapter 31
Kurkukun kaddara book 1 Chapter 31: Kurkukun kaddara book 1 Chapter 31. tana kokari rufe idanuwanta, taga yana mutsu mutsu, ƙoƙarin juyowa ya yi, da sauri…
3,373 words
tana kokari rufe idanuwanta, taga yana mutsu mutsu, ƙoƙarin juyowa ya yi, da sauri ta rufe idanuwanta, don kar ya gane shi take kallo, natsuwa ya yi a yayin da yake kallonta, zuciyarshi cike fal da mamakin canza mashi da tayi, yafi tunanin taji tausayin shi ne saboda halin daya shiga, wata zuciyar kuma tana saƙa mashi cewa kada ka yarda da ita, so take ka saki jiki da ita, ta samu damar kashe ka cikin sauƙi, ta wani 6angaren kuma ba ƙaramin sanyi yaji ba, tun da ta karanta mashi wannan abun da baisan menene ba, Sai yaji duk duniya babu abunda yake kwaɗayin ya kasance yana sauraro acikin kunnanshi idan ba shi ba,
Tunani tayi ko yayi bacci yanzu, tana mutsu mutsun buɗe idanuwanta, yayi saurin rufe nashi eyes, shima baiso ta gane cewa Ita yake Kallo, ta jima tana kallon shi, da zarar taga xai buɗe ido sai ta rufe nata idon, shima haka idon yaga zata buɗe idonta sai yayi saurin rufe nashi, Sai da suka raba da dare suna wannan wasan, Kafin Allah ya kawo bacci 6arawo yayi awon gaba dasu
*ANEELERH*
A tsaye Take saman darduma ta kabbara sallah, Jikinta sanye da dogon Hijabi maroon colour har ƙasa ta sauko, tana ƙoƙarin yin sujjada Taji mutun saman bayanta Ya haye, Kasa ɗagowa tayi saboda gudun kada ya faɗo tasan bai wuci junaid bane, ba yau ya saba yi mata haka ba, a bedroom ɗin Mami ya kwana, har yasan ya tako daga ɗakin mami zuwa ɗakinta, a duk inda ya kwanta bacci ya ɗauke shi ko mun tsakiyar dare ne idan ya farka sai ya nemota duk inda ta shiga, Yadda kasan malamin duba,
Bubbuga bayanta taji yana yi tare da ambaton "Doki sukuta sukuta, doki sukuta sukuta!, yana magana yana sukuwa hada cewa Mommy, Ki tashi mu tafi yawo,' a hankali ta miƙa hannu ta ruƙo shi tare da janye shi daga saman bayanta, Ya faɗo daga gefe saman dardumar, bubbuga ƙafafunshi ya shiga yi, yana raira mata kuka, daurewa kawai take yi sam bata so taji yaron yana kuka, Tsananin tausayin shi taje ji,
Hannu ya miƙa ya ruko cazbaharta dake ajiye saman darduman, Ya miƙe zaune ya zura cazbahar saman wuyanshi, Allah Allah take ta kammala sallar kafin yayi tunanin ɗaukar qur'aninta da ta ajiye wurin daya ɗauki cazbahar, kura mata ido yayi jin taƙi tanka mashi ashagwa6e yake kiran sunanta"mommy! Ni ki tashi muyi wasan doki" yayi maganar da hausarshi da bata ƙarasa nuna ba, ya hanata sakat, daƙyar ta samu ta kammala yin sallar ta zauna zaman tahiya, Ya ɗaura kanshi saman laps ɗinta, Yana cigaba da yi mata shagwa6a, bayan sallame sallar ne ta samu damar kallon shi,
"Bansan meyasa kake yi mini haka ba junaid why? Bakaga sallah nake yi ba, bana hanaka in ina sallah kana hawar min bayana ba"? Wani kallo taga yana binta dashi, kamar wani mai hankali, a yanzu fa shekararshi biyu da rabi,
Sai daga baya ma ta lura da rigar dake ajikinshi, Singlet ce ta abie ya sanya, ta yi mashi yawa har ƙasan ƙafafun shi takai, cike da mamaki tace"kai! Waya sanya maka rigar abie"? Fuskarshi a tur6une yace"Ni na ta" hararar shi tayi"you're lying, ina kaga wayan da zaka iya ɗauko rigarshi ka sanya? tayi maganar tare da kai hannu tana jan kumatun shi,
"Faɗa mun gaskiya My baby boy, ko mamie ce ta sanya maka ita"? Girgiza mata kai yayi"kintan Allah wlh ni nata, in na miki ƙarya Allah ya ƙona......" bata bari yakai ƙarshen maganr ba, ta ɗan hambare bakinshi" Bana haka irin wannan rantsuwar ba?ba'ajin magana ta ko"? ashagwa6e yace"Ae ae nima musha naji yana yi," tsoki taja, shiyasa batason Junaid Yana zuwa wurin shi, duk a wurin shi yake koyan wannan rantse rantsen marasa kan gado, dole sai ta ja mashi kunne, Ya daina Yi agaban ɗanta, tun da yaron wayau ne dashi komai ɗauka yake yi acikin kanshi,
"Kadaina kaji babu kyau," amsa mata yae"Toh, in na daina zaki kai ni wurin Angela"? Murmushi tasaki tare da cewa"Da alama kana son ƴar uwar nan taka junaid, sai dai bansan ya za'ae in kaika wurinta ba, Nima nemanta nake yi...." cikin sanyin murya takai ƙarshen maganar, duk inta tuna su sai taji zuciyarta ta karaya, Almost 4 years kenan babu su babu labarinsu, '
Ɗaukar Junaid ta yi a hannunta ta miƙe ta ɗaura shi saman gadonsu, tana fadin"ka koma bacci dan Allah my baby boy, bana so kayi ta 6arna pls," amsa mata yayi"to" ya lumshe idanuwanshi alamar bacci zaiyi, ƙura mashi ido tayi tana kallonshi batare da ƙyaftawa ba,
Shafa fuskarshi tayi da hannunta, kafin ta zauna daga gefen gadon, takai hannu ta ɗauki wayarta dake ajiye saman bedside drawer,
Gallery ta shiga, ta lalubo tsoffin hotunansu tana kallo, Wani hoto ta buɗo wanda suka yi su uku, Ranar graduation ɗinsu akayi masu hoton a University of Hagen, dake a ƙasar germany, su uku su kayi hoton kowannasu yana asanye Cikin Graduation gown sunyi matuƙar yin kyau, Allah yayi halitta ta farko Aneelerh ce, A tsakiyarsu Benazir ce kyakkyawar balarabiya, Ta ƙarshe kuma wata aminiyarsu ce masha Allah, Matar akwai diri kamar ita ta ƙera kanta, kowacce da irin baiwar kyan da Allah yayi masu, sai dai kash gaba ɗayansu a halin yanzu ƙaddarar rayuwa tayi silar tarwatsewarsu,
A tsanake take kallon hotunan nasu, tayi matuƙar yin kewar aminnanta, bazata ta6a manta irin shaƙuwar da su kayi da juna ba, runtse idanuwanta tayi tana tuna wasu maganganun da suka jima suna yi mata yawo acikin kanta, ɗaya daga Cikin aminnan nata ne ta furta su a cikin text message da ta ta6a tura mata lokacin da take Cikin tashin hankali tace"Aneelerh bazan Iya jurewa ba, ko gaisuwata bai amsawa, bansan shi wani irin uba bane, ni dai banyi dacen iyaye ba, Yanzu haka da nake rubuta maki text ɗin nan, Ina akan hanyar zuwa airport wlh idan nabar ƙasar nan bazan sake dawowa Cikinta ba, tun da yace baison gani na, aneelerh agaban kowa Yaci mutunci na, agaban maids ɗin gidanmu, yayi mun korar kare hada tsine mun yayi kamar wani jahili shi baisan ƙaddara ba ne? Idan har na biyewa zuciya zansha poison ne in mutu........"
Sosai aneelerh ta fashe da kuka, lokacin da ta kammala tariyo abunda ya faru, A fili tace"Allah sarki Aisha! Bansan A ina zan ƙara ganinta ba, Allah ya kare ki aduk inda kike, ni shaida ce akanki, Ke mutuniyar kirkice, bana fata, ƙaddarar rayuwa tayi silar canzaki daga yadda nasanki, '
Cikin shessheƙar kuka aneelerh tace"Narasa Aisha saboda korar karan da mahaifinta yayi mata, na kuma zo narasa Benazir, duk da ita don san ranta ta gudu, daga baya kuma Narasa Mutun uku masu mahimmanci acikin rayuwata, " jefar da wayarta tayi saman mattress, Ta kifa kanta Jikin pillow, junaid tuni ya jima da komawa bacci,
Tasha kuka kafin bacci yayi awon gaba da ita, Wuraren ƙarfe 9 na safe, Mami ta shigo ɗakin Jikinta sanye da atampa , murmushi ta saki ganin yadda uwa da ɗanta suke ta sharar bacci, Girgiza kai ta ɗanyi "Jikana mai abun ban mamaki, dama nasan bai wuci nan ka gudo ba, wurin mommyn taka, bayan ka sace mun rigar mijina, Allah dai ya shirya mun kai,' Takai ƙarshen maganar, tare da ƙarasawa Cikin ɗakin agaban gadon aneeleerh ta tsaya tare dakai hannu tana ɗan bubbuga kafarta" Daughter baccin ya isa haka, Ki tashi muje muyi breakfast,"
Buɗe ido aneelerh tayi sun ɗan kumbura saboda kukan da tasha, koda ganin busassun hawaye akan fuskarta, sai mami ta ɗaure fuska"aneelerh when zaki daina kuka? Sai kace wata ƙaramar yarinya? Abu kaɗan sai kuka duk kin maida kanki wata sauna," rai aɗan 6ace tayi maganar, yayin da take zama gefen gadon idonta akan fuskar aneelerh,
Miƙewa zaune aneelerh ta yi, batare da tace komai ba,
"Fada mun me kuma ya saki kuka"? Muryarta a disashe tace"Mami kiyi hakuri idan kukana ya 6ata maki rai, nasan bakya son ganin zubar hawaye na, nima ba so nake yi ba, sai dai wani abunne ko nayi kokarin na danne saina kasa, idan ba hawayen na zubar ba, bana jin daɗi," yanayin yadda tayi maganar ba ƙaramin kashe ma mami jiki tayi ba ,
Ruƙo hannayen aneelerh tayi acikin nata"Aneelerh, kodai zaki ɗauki shawarar mahaifinki ne, ki koma abuja gidan Uncle ɗinki da zama? ina ganin kamar in kina acan zaki fi samun sauƙi acikin zuciyarki, amma zamanki anan sam babu cigaba," girgiza kai aneelerh tayi yi"Mami dan Allah kudaina yi mun maganar komawa gidan uncle da zama, ya kuke so nayi da rai na? A halin da nake Ciki, ku kaɗai nake gani inji sanyi acikin raina, indai nayi nesa da ku, bazan ta6a samun natsuwa ba" takai karshen maganar fuskarta a yamutse,
Mami ta fahimci halin da aneelerh take Ciki, dama tasan zaiyi wuya ta amince tayi nesa da su,
"Shikenan, bazan ƙara yi maki zancen komawa can ɗin ba, ina fata hakan yayi maki" jinjina kai aneelerh tayi alamar eh,
"Yanzu ki tashi ki shiga toilet ki wanke fuskarki sarkin kuka, Allah idan baki daina ba sai yaronki ya raina ki, ga shi nan yanzu shima ya fara zama irin ki, ko kallon banza mutun yayi mashi sai ya fara ta6e baki zaiyi ma mutane kuka," murmushi gefen fuska aneelerh ta saki, tare da juyawa tana kallon junaid dake kwance, har lokacin wuyanshi na sanye da cazbaharta daya sanya,
Dariya mami tayi don ita sai lokacin ta lura da cazbahar da ke sanye a wuyan junaid, "Wayaga ɗan Sarkin malamai," dariya sukayi atare, gwanin ban sha'awa,
Miƙewa mommy tayi"xan koma dining ki same ni acan ina jiranku,"
Amsa mata tayi da toh mami, kafin ta sauko daga saman gadon ta shige toilet, after some minutes ta fito tana gyara doguwar rigar material ɗin dake ajikinta,'
Har lokacin Junaid Bai farka ba, tasan dole yana jin yunwa, hannu takai tare da ɗauko shi, aikuwa kamar ta tsunkule shi, Yaita kuka yana fadin shi bai gaji da baccin ba, tana dariya tace"Am sorry My baby Boy, breakfast zamuyi da zarar mun kammala, Sai ka koma baccin ka, daƙyar ta samu ta shawo kanshi Ya daina kuka, Toilet ta shiga da shi, ta yi mashi wanka, ta fito dashi sa6e saman kafaɗarta, ta nado shi Cikin towel, Gyara mashi Jikin shi tayi kafin ta sanya mashi riga da wando, rungume dashi ta fito ta nufi dining table, Mami ta hango a zaune tana Shan tea, Kujera taja ta zauna suna fuskantar juna da mami tace"ɗazu ban gaishe ki ba, My first love, Ina kwana mamina, ina fata kin tashi cikin koshin lpy," fuskar mami dauke da murmushi ta amsa mata da cewa"Alhamdulillah, my lovely daughter, Ya grand son ɗin nawa naga yana ta tur6une fuska uwa alkubus, halan tashinsa ki kayi daga bacci"? Takai ƙarshen maganar idonta akan junaid, dake zaune saman cinyar mommynsa, sai shan mur yake yi, yana hura hanci, Shi an takura mashi,
"Mami saboda fa ya ci abinci na tada shi, amma da yake shi baisan abun arziki ba, shine yake ta hura mun hanci,"
Mami tace"kwantar da hankalin ki, ae da zarar yayi arba da noodles zai wartsake" hannu mami takai tare da ruƙo plate ɗin dake shaƙe da noodles ta tura ma aneelerh agabanta,
Hannunshi har kerma yake yi wurin kokarin tsoma shi Cikin taliyar, da sauri aneeleerh ta damƙi hannun nashi tare da cewa"Baka ga akwai zafi ba? So kake bakin ka ya ƙone"? ta6e baki ya soma yi alamar zaiyi kuka, lallashin shi ta shiga yi"haba my baby boy, Fushi ba naka bane bari na baka da hannu na" hannu ta sanya ta soma ɗibowa tana bashi abaki yana Ci,
"Mami Ina abie? Ko har sun tafi"? Jinjina kai mamie tayi"tun yaushe kuma, tun bayan sallar asuba yace mun bazai dawo gida ba, daga can zasu wuce, "
"Shi ne ko ya jira muyi sallama dashi" rai adan 6ace tayi maganar, mami tace"sauri yake yi ne, idan mun kammala cin abinci sai ki kira shi awaya ki yi mashi Allah ya kiyaye hanya," amsa mata tayi da toh, daga haka suka Cigaba da cin abincin su,
*south korea🌹*
Seoul City,
Hajiya adama ce zaune saman Sofa mai mazaunin mutun uku, A cikin katafaren Palourn gidansu, jikinta na sanye da doguwar cord lace milk colour, idanuwanta na a manne da farin glass medicated, Ta natsuwa tana daddana laptop ɗinta dake asaman Table ɗin gabanta, da alama Komai ya daidaita don yanayinta bai nuna tana acikin damuwa ba,
Gaba ɗaya ta tattara kwandon hankalinta akan aikin da take yi acikin laptop ɗinta,
Sautin Dirar motoci ta juyo acikin Apartment din nasu, dakatawa ta ɗanyi da daddana laptop din ta ɗago tana kallon bakin kofar shigowa falon, duk da tasan ba lallai In baƙin su bane tun da basu kaɗai bane akwai sauran mutanan dake Haya Acikin Ginin,
( mu haɗu next week on monday in Allah yakaimu da rai da lafiya, don jin yadda zata kaya, akwai fa sauran Rina akaba, domin neman ƙarin bayani 08103884440) [9/22, 7:10 PM] +234 803 216 9283: *💋KURKUKUN ƘADDARA💋*
*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*
*Dedicated to Aunty kubra❤*
*Gargarɗi!!!*
_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_
E24-25
💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫
*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K'ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K'ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327
*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*Hadin amarya budurwa ko zawara*
*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*
*Maijego package (virgin gain)* 📦
*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*
*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*
*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*
*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*
*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*
*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*
*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni'ima sha'awa da dandano* *Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki* *Kalolin Zuma masu saukar da ni'ima Nan take da gamsar da maigida* *Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni'ima da dandano irin wadda akeso* *Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano* *Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327
*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni'ima da jimawa sosai ajikin mace*
*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha'awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha'awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura* http://wa.me/+2347069711327
*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*
*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*
Uncel abdallah ne Ya shigo Falon, Hannun shi ruƙe da key ɗin motarshi, Suit ne ajikin shi, Miƙe wa Hajiya adama tayi fuskarta asake tace "Welcome back dear, I heard the sound of cars Coming in ko munyi baƙi ne"? sai da ya samu wuri ya zauna tukunna ya kalle ta fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Ni ne baƙon ae, fatan na same ki lafiya, Yau naga walwala atattare dake, Ga shi kin ɗau wanka kinyi kyau abunki,"
Ta6e baki ta yi "Ae tun da kayi mun albishir game da komawarmu gida, Nake ta sakin fara'a ni kaɗai abuna, Yanzu haka ma da kaganni a zaune, Ina duba kayayyakin da zan siyane na tsaraba da zanyiwa mutanan gida," takai ƙarshen maganar tare da kama hanyar zuwa kitchen tace"Bari na kawo maka Ruwa mai sanyi kasha"
"Da kanki Hajiyata? Ina mai aikin gidan take ne"? A sukwane ta Juyo tana bin shi da kallon bansan rainin wayau,
"Oh kamanta irin Korar da kayi ma Ajumma daga gidan nan, Saboda laifin da ba nata ba, ƴar baiwar Allah, dama burinka kaga ina shiga kitchen da girmana, ae yanzu hankalin ka ya kwanta, Hajiya adama ta zama kukun mijinta" Dariya Uncle abdalla Yayi"Matar nan kina sani nishaɗi, Abun alfahari ne mace ta girka ma mijinta abinci da hannunta yaci ya sanya mata albarka, Ta samu lada, Ni ae naga Cigaba sosai, da na kori wannan tsohuwar matar, Tun barinta gidan, kika daina shan Soju, gashi yanzu kin samu natsuwa kin dawo Hajiya adamar dana sani,"
Hararar wasa ta jefa mashi daga inda take a tsaye" korar ajumma da kayi ba shi ne yasa na daina shaye shaye ba, Da naso zan fita inje in siyo da kaina ne, Allah ne yayi silar shiryuwata, dama ba halina bane, tsautsayine da ƙaddara, da kuma damuwar da na shiga na rashin mutun uku masu mahimmanci acikin rayuwata.........." muryarta a karye takai ƙarshen maganar, da sauri tajuya ta shige Cikin kitchen,
Jingina bayan shi Yayi a jikin Sofa ɗin da yake zaune, Har ga Allah Shi kanshi yana acikin matsanaciyar damuwa na rashin ya'yan shi da ya yi, Yaji raɗaɗi sosai, sai dai ba yadda zai yi, daure wa kawai ya ke yi, A duk lokacin daya tuna rashin Da yayi, Na ɗan uwansa, Kuma yayansa Malam zahiru, da mahafiyarsu deeja, Sai ya dinga Jin kanshi tamkar marayan da baida mafaɗi aduniya, Dama wake gaya mashi gaskiya idan yay badai dai ba? malam zahiru ne, tun yana yaro shi yake zaunar dashi yayi mashi nasiha game da rayuwar duniyar nan, kalmar da yafi faɗa mashi itace "ABDALLAH KAJI TSORON ALLAH, ' tuna wannan yasa shi kai hannu ya dafe goshinsa, Idanuwanshi suka Cicciko tab da kwalla, haƙika yaji mutuwarsu, Hatta yahana su Mahaifiyar Tajuddeen, Yaji mutuwarta sosai, Mutanan kirkiki, Mutane masu ƙima da daraja,
Ajiyar zuciya ya sauke, tare da lumshe idanuwanshi, Bakomai yake tunawa ba face Tajudeen lokacin da zai raba shi da iyayenshi, Suna kuka yana kuka saboda basu son rabuwa da juna, Suna matuƙar ƙaunar ɗansu, Amma saboda son zuciya yabi ta ƙarfi da yaji don yana da arziƙi, ya ba mahaifiyarsu Cin hanci, aka damƙa mashi yaro, tun da yake bai ta6a danasanin raba tajudeen da iyayenshi ba, Sai bayan rasuwarsu, tsawon shekaru basu yi tozali da dansu ba, har sun koma ga mahaliccin su, Shi ma kuma ɗan nasu An neme shi ƙasa ko sama babu shi, Wannan wata irin ƙaddarar rayuwace? Yanzu idan Allah yasa aka ga su tajudden Taya zai Iya Sanar dashi game da mutuwar Iyayenshi!!? innallahi wa'inna ilaihirraji'un............
Tun ɗazu Hajiya adama ta fito daga cikin kitchen, hannunta ruƙe da plate mai ɗauke da glass cup na ruwa mai sanyi tare da snacks, ta jima a tsaye tana kallon Mijinta nata da ya yi zurfin Cikin tunani, Hawaye ta gani kwance a cikin idanuwanshi, Da alamun damuwa attare da shi ba kamar yadda ya shigo mata ba, A saman C table ta ɗaura plate ɗin dake hannunta,
Kwala mashi kira Tayi A firgice yakai idanuwanshi akanta yana kallonta
"wai lafiya dear, Ina ta kiran sunanka Amma hankalinka sam baya atare dakai, Meya faru ne? Yanzu fa nabarka fuskarka asake, amma kuma na dawo na taras dakai cikin damuwa" tayi maganar tare da kai hannu ta ɗauki Cup ɗin ruwan ta miƙa mashi,