Kenza eBookz

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 - Chapter 32

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 - Chapter 32

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 Chapter 32: Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 Chapter 32. "Pls ka tafi pravin na roƙe ka" Da kasalalliyar…

3,278 words

"Pls ka tafi pravin na roƙe ka" Da kasalalliyar muryarshi yake yi mata magana"zanyi kewarki nasan idan Owais ya dawo gidan nan ba ƙaramin takura zan yi ba, amma duk da hakan zanyi ƙoƙari ina satar hanya ba tare da kowa ya sani ba zan dinga zuwa ɗakin ki kina rage min zafi' harara hajjaty ta ɗan jefa masa"matarka fa? har mamaki nakeyi irin yarda kake liƙe min bayan matarka tafi ni komai"

Ta6e lips dinsa yai'kada ki ce haka, arziƙi kawai zata nuna maki bayan haka bana tunanin akwai wani abu da zata Iya finki dashi, sai dai ma ki fita.

"Amma kafi sonta akaina? Saboda Ta haifa maka ƴa'ƴa"

"Waya faɗa maki? Kema ai na samu ƙaruwa dake, sai dai Allah bai nufa zai yi tsawaicin kwana ba, Ya rasu amma zamu sake haifar wasu idan kina so"

Tamkar ya fama mata raunin dake acikin zuciyarta, kifa kanta tayi saman pillow, Hannu ɗaya ya ɗaura saman sumar kanta yaci gaba da shafa lallausan gashin kanta.

"Its ok, kada Ki yi min kuka kinsan banaso My honey, "

Cikin shessheƙar Kuka take faɗin"Pravin na gaji da irin rayuwar nan, bana jin daɗin kasancewata a matsayin ƴar aiki agidan nan saboda matarka saratu, ta tsane ni bata sona, har Gori ta ke Yi min tana kirana da sunan karuwa, wai ina shisshigema babansu wai ni pravin...' sautin kukanta ba ƙaramin ta6a mashi zuciya yai ba

Lallashinta ya soma Yi"am sorry nasan ba daɗi but ki yi haƙuri, in sha Allah zan nema maki mafita, idan bakya son zama gidan zan siya maki wani ki koma ki zauna can Hakan Yayi maki"?

Ya yi tambayar yana leƙen fuskarta

Ba tare da ta ɗago da kanta daga saman pillow ba tace"A'a, ai ni bana son inyi nesa da kai, Idan ka siya min gida na koma zaka Yi min wuyar gani, amma idan anan ne zan dinga ganinka akai akai, koda ba za mu yi magana ba idan ka gifta ina jin sanyi araina.

Lumshe ido yai, muryarta na ƙara jefa shi cikin Yanayi na jin shauƙinta.

"Shiyasa nake ƙara sonki My heart beat, kin fiye min kowace mace a duniya divya, kinyi haƙuri dani da daɗi da ba daɗi kin zauna dani, Inason ki sosai, kema kin sani, saratu bata fiye min ke ba, zan Iya rabuwa da ita amma ke bazan Iya rabuwa dake ba saboda ke Jinina Ce kuma amanace ke agare ni.

Kalaman pravin sun sanyaya mata zuciyarta sosai, bata ta6a kokwanto akan abunda yake faɗa mata ba. Idanuwanta jawur take duban fuskarshi

"I love u so much, My life partner," murmushi ya sakar mata.

"Idan akwai abunda kike buƙata Ki sanar dani zanyi maki shi"

Girgiza mashi kai tayi"a'a ai ni ka gama min komai pravin, ka haɗani da mutanen kirki waɗanda har yau ina alfaharin kasancewa ta acikin su, sun ɗauki nauyin komai na rayuwata ci na shana da suturar sanyawata, kaine sila pravin, bayan Albashi da nake samu awurinsu kaima kana turamin kuɗi duk ƙarshen wata masu yawan gaske, bansan ina zan kaisu ba, Tun da bani da buƙatarsu da ace Yaronmu yana araye kaga sai mu dinga siya mashi abubuwan wasan Yara, da sutura masu kyau ....."da rawar murya takai ƙarshen maganar, sosai ta sanya mashi kuka. Cikin shessheƙar Kuka tace"Pravin bazan 6oye maka ba, Inason na haihu ko dan na samu madadin shi" "Ki kwantar da hankalinki, Zanyi shawara akan hakan" jinjina mashi kai Tayi Yunƙurawa yai tare da miƙewa Ya sanya hannu Biyu ya cuccu6eta duk girman jikinta baya jin nauyin ɗaukarta, Saukowa yai daga saman gadon Ya nufi toilet da ita, wayarshi da ya bari acikin aljihun short dinsa dake yashe ƙasa sai ringing take Yi, da zarar kiran ya katse wani ke shigowa.

****************❤

A ƙalla ta shafe sama da mintuna 30 tana zarya A cikin ɗakinta, Hannunta ruƙe da I phone dinta, Yayin da idanuwanta ke kallon Haɗaɗɗiyar agogan bangon ɗakinta Ƙarfe 6 na marece, Lamarin Ya ɗaure mata kai, damuwa ce ƙarara akan fuskarta, Tun ɗazu da ta kammala Yin waya da Gimbiya mujeedat, Hankalinta ya dawo kan Mijinta, Ganin time ɗin dawowarshi daga aiki har Ya zarce babu shi babu alamar shi, saboda damuwar rashinsa ta manta da zancen Kiran Zahra, Hatta P.A dinsa Ta kira awaya ta tambaye shi ina pravin? Yace mata ai shi tun wuraren ƙarfe sha Biyu na safe rabon shi da pravin, Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba, hakan na nufin ko aiki baiyi a office ba, to ina Ya shiga? Tun ɗazu take kiran layin shi ba'a picking, abun duniya ya isheta, saboda ta damu da pravin tayi kewarshi sosai, bata tunanin ko abincin zata Iya ci idan bai dawo ba.

Guntun tsoki taja A fili ta furta"ya Salam, Ya Allah ga bawanka nan, Ka tsare min shi a duk Inda Yake, " ta ambaci hakan tare da jefa wayarta saman Gado, da sauri ta nufi tafkeken closet na kayansu ta buɗe ta ɗauki Mayafi ta Yafa a kafaɗa, tsabar sauri takalman da ta zura a ƙafarta daban daban, adai dai baƙin ƙofar fita daga ɗakin Suka yi kicibus da Twins Bakunansu ɗauke da sallama, Wankan suit ne a jikinsu, sun bi shape ɗinsu, Masha Allah, wrist watch dinsu mai Kyan gaske, Wani irin daddaɗan ƙamshi ke fita daga Jikinsu.

Hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba ganin mommyn nasu fuskarta babu walwala.

Har suna haɗa baki wurin furta"Mom Lafiya? Meke damunki ne" girgiza kai Tayi"inafa lafiya, daddynku tun ƙarfe shabiyu yabar office, har yanzu bai dawo ba, Na kira Layin shi wayar tana ringing ba'a ɗayawa.

Atare suka kalli juna, babu alamun damuwa akan fuskokinsu. Kwantar mata da hankali suka soma Yi"mommy ki kwantar da hankalinki, daddy fa ba wani ƙaramin yaro bane da zaki tashi hankali akanshi, Yasan inda Yaje kuma zai dawo ne in sha Allah"

Fuskarta babu walwala take dubansu"pls ku bani Hanya in wuce inaso Naje na faɗa ma baba" har suna haɗa baki wurin furta sunan baba

"Haba Mommy, Akan wani dalili zaki je ki faɗa mashi? So kike ki tashi hankalin shi, Gaskiya a'a ki koma ki zauna, zamuje mu nemo daddy duk In da ya shiga"

Ruƙo Hannunta Zayn yai, Suka koma Cikin ɗakin, Gefen gado ya zaunar da ita,

"Zayn pls, Ku duba daddynku, Ni damuwata kada ace wani abunne ya same shi dama jiya ya faɗamin baya jin daɗin jikinshi" muryarta tamkar zata fashe da kuka ta yi masu maganar.

Zaid Yace"in sha Allah ba abunda ya same shi mommy, yanzu zamuje mu nemo shi" ya ambaci hakan Tare da ruƙo hannun ɗan uwansa suka fuce daga ɗakin.

Ransu ya 6aci matuƙa, daga gaban ƙofar ɗakin suka tsaya suna kallon juna "Mutumin nan ɗan rainin wayau ne, wlh Zaid zan tona mashi asiri awurin mommy, Ta ya ya zai bar mahaifiyarmu cikin damuwa, Yana can Yana sharholiyar shi, dama zuba mashi ido nakeyi ina tara shi...." duk yadda zaid yaso ya dakatar da Zayn Akan Yai shiru yaƙi rufe baki saida Yakai ƙarshen Aya

"Ka daina ɗaga murya bro, Ni bawai ina goyan bayan abunda yake yi ba ne, just ka yi tunani mana, muddin ka tona ma daddy asiri wlh mu zaka ja ma bala'e, Kana ganin irin gorin da ake yi mana a family, akan mahaifinmu yana zama gidan surukansu Yanzu idan ka faɗama Mommy cewa daddy Yana bin matan banza me kake tunanin zai Biyo baya"?

Sassauta fushin fuskarshi Yai"Hakane Zaid amma abun Yana ƙona min rai, why ya ke son ja mana baƙin jini? Dame mommy ta rage shi da har yagaza kama mutuncin kansa, wai shi so yake dole saiya 6ata mana suna" tuni idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla

Ya ci gaba da cewa"Shine silar komai dake faruwa arayuwarmu, Zaid Ina kishin mahaifiyata sosai, Ina jin takaici da ƙululun baƙin Cikin mutumin nan, wlh duk ranar da mommy taji labarin abunda Yake aikatawa tabbas zuciyarta zata Iya bugawa saboda tana da kishi kuma Tana son daddy, ni har kokwanto nakeyi anya daddy yana son mommy kuwa? Ko dai Abunda mutane suke hasashe akanshi gaskiya ne? ya aureta saboda dukiyar family dinmu' yana magana hawaye naci gaba da taruwa acikin idanuwanshi.

Dafa kafaɗarshi Zaid Yai"duk abunda ka ke ji zayn nima inajin shi, Amma Ya zamuyi? Mu tamu ƙaddarar ahaka tazo mana, Muyi haƙuri wata rana sai labari Sannan Yakamata muna tayashi da addu'a akan Allah ya shirye shi, saboda shi mahaifinmu ne duk inda za'aje adawo mu jininsa ne kuma ba zamu so mutuncinsa ya zube a idon jama'a ba.

Lallashin junansu su ka yi, Hannunsu ruƙe cikin na juna suka Nufi Babban falon gidan, masu aikine keta kai komo.

Suna dab da zasu fuce daga falon, Kwatsam Pravin Ya faɗo Sai faman zumbula sauri Yake Yi, Jikinshi sanye da Suit dinsa light brown, ƙiris Ya rage su ban gaji juna da shi, duk da faɗin ƙofar kasancewar Kowan nan su Hankalinshi ba a kwance yake ba Har zasu gifta shi, suka ci wani uban burki agabanshi, Tun daga Kan Yarda suke jefa mashi kallo yasa shi kame kanshi.

"Har kun dawo daga aikin"? Tambayar daya jefa masu kenan.

Zayn tamkar ya shaƙe baban nasu haka Yake ji, takaici Ya hana su yi magana.

"Lafiya? Baku ji ina magana ba"? Saida suka taushi zuciyoyinsu tukunna suka Iya yi mashi magana,

Zaid yace"Sannu da dawowa daddy, Ya office din? Naga yau ka yi marece ko duk Aikin ne ya ruƙe ka"?

Basarwa Yai tare da cewa"Eh, " daga haka bai ƙara tanka masu ba, Sai bi da yai ta gefen su Ya wuce, kamar sakarkaru haka suka Bi bayanshi da kallo, Sam baisan cewa sun san abunda yake aikatawa ba.

Kusan atare suka girgiza kawunan su.

"Zayn tunda Ya dawo mu koma ɗaki, dama Ni agajiye nake wlh, inaso na ɗan kwanta In huta" Juyawa sukayi Atare suka nufi part dinsu.

Hajiya saratu na zaune gefe gadonta, baiwar Allah damuwar duniya ta isheta Hannu biyu ta zabga uban tagumi, gabanta sai faɗuwa yake yi gani take yi kamar wani abunne Ya faru da mijinta, Kasa samun natsuwa tayi zumbur ta miƙe kamar an zungureta da sanda, safa da marwa taci gaba da yi acikin ɗakin tana ƙarewa agogon bango kallo.

Ba zato ba tsammani muryar Pravin ta ratsa kunnuwanta"Assalamu alaikum" tunkafin Ta juyo ta kalleshi ta soma sauke nauyayyar ajiyar zuciya, tsabar farin ciki da sauri ta nufeshi, hannu biyu ya rungumeta a ƙirjinsa.

Sai faman sauke ajiyar zuciya take Yi, yayin da take ƙara shaƙar ƙamashin turaren jikinsa.

"Am sorry My wife, nasan ban kyauta maki ba...."tunkan Ya ƙarasa maganar, Hajiya saratu ta dago da fuskarta, babu annuri ko misƙala zarratin tuni yasha jinin jikinshi.

Da kakkausar Murya ta furta"PRAVIN DAGA INA KAKE"!? Rass Yaji gabanshi Ya faɗi "Na kira p.A dinka Awaya ya sanar dani cewa tun ƙarfe 12 kabar office, Inason Jin ya akai kabar office ina kuma kaje"? Rai a6ace take Yi mashi magana, Hannunta ruƙe da qugunta. Ya tsareta da Ido batare daya furta kalma ba, hakan ba ƙaramin Ƙona mata rai ba, Tsawa ta daka mashi kamar mahaukaciya Ta cakumi Gaban rigarshi.

"Nace ka faɗamin Ina kaje pravin? Saboda ka maidani shashasha ban da amfani awurinka shine zaka kama Hanya kabar office tun ƙarfe sha Biyu baka kirani awaya ka sanar dani ba, Kasa duk nabi na tashin hankalina akanka, ni na ɗaukama wani abunne ya same ka sai gashi ka dawomun lafiyarka qalou"

Ƴan hanjin cikinsa tuni sun soma kaɗawa, Abunka ga shu'umin namijin wanda yasan takan mace, runtse idonshi yai tare da kai hannu ya dafe gefen cikinsa.

Nan take Hankalinta yai matuƙar tashi la66anta na rawa take faɗin"pr...pravin? Lafiya? Meke damunka" Da wata irin kasalalliyar murya ya furta"My stomach, bana jin daɗi ai tun Jiya na faɗa maki," ya ƙarasa maganar yana faman cizon la66ansa, lokaci ɗaya fushin fuskarta ya sassauto, tsananin tausayin shine Ya kamata, ganin yana tangal tangal kamar zai faɗi yasa tayi saurin talla6e waist ɗinsa, da taimakon ta suka ƙarasa gaban Gado Ya hau Ya kanta Yana fuskantar ceilling, daga gefen gadon ta zauna daga gefenshi tana kallon shi

"Pravin am sorry nayi maka faɗa bansan baka da lafiya ba, kaine kaƙi Yi min magana, why pravin kasan baka da lafiya meyasa baka kira awaya ka sanar dani ba? Cikin kulawa take yi mashi magana, har ta manta da zancen tambayarshi Ina yaje.

Wahalallan Yawu ya haɗiya, Cikin mawuyacin Hali Ya furta"wayar bata a hannuna ne a mota nabarta, Ina Cikin Yin draving zan dawo gida, Ciwon ciki Ya takura min, draving dinma na gagara Yi, shine na wuce gidan abokina dake anan kusa, to acan bacci ya kwashe ni,

"Pravin why baka je asibitin Gida ba? ai da komai yazo maka da sauki, yanzu ka tashi ka shirya In kaika asibiti da kaina inyaso sai in dubaka acan"

Tana Ƙoƙarin miƙewa yai saurin fusgo hannunta, gaba ɗaya ta faɗa saman jikinsa, Ƙanƙame ta yai da hannayenshi biyu

Yana faman cizon le6e ya furta"rashin lafiyata bata asibiti bace, My wife kece kike damuna saboda rashin bani haƙƙina da bakya yi akai akai, shiyasa nake fama da ciwon cikin nan, ko da yaushe Aikinki ne agabanki, idan dare yai nayi maki magana kina danna laptop sai kice min In jira ki kammala daga nan har bacci ya ɗauke ni baki gama ba......"

Pravin Ya kashe mata Jiki da kalamansa, ta yarda da abunda ya faɗa mata saboda tasan bata kyauta mashi ta 6angaren nan mafi yawan time idan Ya matsa mata tana Yin aiki bata kula shi saita kammala.

"Am sorry dear, indai nice zan gyara, kayi haƙuri nayi kuskure but bazan ƙara Ba, tun da abun Yana affecting dinka". Lumshe ido Yai, har cikin zuciyarshi ba ƙaramin daɗi Yaji ba, ganin yai nasara akanta.

"Yanzu ka faɗamin me kakeso? Za ka yi wanka in taimaka? Ko zaka fara Cin abinci ne"

Yana faman sakin nishi Ya furta"nafi buƙatar wankan, amma idan kin amince muyi atare" Murmushi tasakar mashi"is Okey, shine kaɗai abunda kakeso"? Ɗaga mata Gira yai alamar eh, A hankali ta ɗaura yatsun hannayenta saman coat din jikinsa Ta cire mashi ita, kafin ta zame mashi belt din wandonsa, yunƙura yai tare da miƙewa ya sauko daga saman gadon Ya ƙarasa zame wandon ya rage daga shi sai short da singlet dinsa, Yaja hannunta suka nufi toilet, da gudu nabi bayansu sai dai kafin in ƙarasa Pravin Ya kulle ƙofa.

*EX-PRISONERS❤*

Idan muka koma 6angaren Prisoners, sai dai muce Alhamdulillah, tun bayan da Dr laura davis ta tattauna da Sojoji bata ƙara Ji daga gare su ba, An dai samu damar Kammala Yi masu injections ɗinsu kuma kullum sai sunsha magani na safe daban na rana daban na dare daban, injection ɗin duk mutun ɗaya uku suke Yi mashi arana, Likitoci sun ci kwakwa Wurin ma Matan allura, Musamman Azeeza da Jamimah, mugun tsoron Allura su ke ji, idan za'ayi masu sai an kira Angel ta ruƙesu, tukunna ake samun sauƙin yi masu allurar, Mazan dai da sauki basu tsoron Allura tamkar basu son ana tsira masu ita a jikinsu ba, cikin kwanaki huɗu da su ka Yi a Texas Rayuwarsu ta fara canzawa, saboda kyakkyawar kulawar da suke samu tarairayarsu ake Yi kamar new born babies, abinci sau uku ake basu, Breakfast, lunch and dinner, Lafiyayyan abinci mai gina jiki, sau ɗaya ake sanyasu yin wanka, su canza Kayan Jikin su, Su Angel an dage da yin sallah da addu'a, har tsakar dare tana tashi yin night prayers, yawanci addu'o'inta akan Danish ne, ta roƙi Allah da ya kare mata shi, idan farkawarshi Alkhairi ce Allah Yasa ya tashi cikin amince, idan kuma farkawarshi ba Alkhairi bace Allah yasa yaita sharar baccina har zuwa su koma Nigeria zaifi masu sauƙin su Yi control dinshi, duk da yanzu ta fara fargaban kada su zo Nigeria A nemi Ruwan zam zam arasa tabbas ba ƙaramar matsala za'a samu ba, damuwarta yanzu akan Sojojin ce shiru basu dawo ba, Kuma bata Ji daga bakin dr laura Ya ake ciki ba, Shin za'a maidasu ƙasarsu ne ko kuwa a'a, Ta dai zubawa sarautar Allah Ido 👀

Sam ta kasa runtsawa, tun wuraren ƙarfe tara na dare ta farka, saboda mugun bugun da ƙirjinta ke yi mata, tabbas tana ji aranta wani abun ne ke shirin faruwa. Miƙewa Tayi zaune saman gadonta, ta jingina Bayanta Jikin pillow, idanuwanta suna a lumshe, sanyin A.c sai ratsa fatar jikinta Yake yi wata irin kasala take Ji da matsanancin faɗuwae gaba. "Masoyiya Angel, Lafiya kika farka daga bacci? Na lura kamar wani abu ke damunki" Muryar Nurse Jessica ce ta fargar da ita, har saida ta ɗan zabura don bata yi tsammanin jin Muryar mutun a kusa da ita ba. Slowly ta wurga eye balls ɗinta akan fuskar nurse ɗin, tana daga zaune saman chair ta kusa da gadonta, hannunta ruƙe da wayarta, fara ce sol, uniform ɗin jikinta light blue ne kalar nasu, ta ɗaure jar sumar kanta da ribbom. Nauyayyar ajiyar zuciya Angel ta sauke tare da cewa"sister, nagode da kulawarki agareni, nakasa runtsawane saboda inason ganin yan uwana ko zaki Iya taimaka min"? Smiling gently nurse jessica tace"Na lura kina son ƴan uwan nan naki, cos tun ranar dana fara kula da ke, sau uku kike zuwa room ɗinsu Kina duba su, faɗamin ko dai akwai damuwane? Ko tsoro kike ji kada mu sace maki su"? Da zolaya nurce jessica tayi mata maganar Cikin jin kunya Angel takama ƴan kame kame tana faɗin"am.... Ba haka bane just inason su sosai, mun shaƙu da juna, shiyasa bana samun natsuwa idan ban gansu akai akai ba"

Nurse jessice tace"Kuna burgeni sosai, inaso Inga ƴan uwan masu son junansu, masu haɗin kai, ta hakanne ake cin ribar zaman duniya, idan har kana da ɗan uwa mai share maka hawayenka, mai nuna maka ƙauna wanda baya gajiya dakai tabbas ka gode ma Allah, zai yi wuya ka rasa madafa a duniyar nan, babu wanda zai yi gigin cutar dakai muddin kuna da haɗin kai a tsakaninku, amma idan Ya kasance kuna ƴan uwa baku da haɗin kai, danasani zai biyo baya cos dayawa rashin kulawa keja har damuwa tayi ma ɗan uwanka Illa, ya akaita abunda zakuyi danasani gaba dayanku"

Angel ta natsu Tana sauraron Kalaman Nurse Jessica, Haƙika kalamanta sun ta6a mata zuciya, sai taji ta ƙara ƙaunar ƴan uwanta, ta ɗanyi mamakin yarda nurse ɗin take sakar mata fuska suke Yin fira, saboda ta ta6a Jin ana faɗin turawa sun tsani baƙar fata suna nuna masu wariyar launin fata, sai dai tayi tunanin ba duka aka taru aka zama ɗaya ba, sannan kuma su basu da banbanci dasu, hasken fata, launin ido da kuma sumar kai, shiyasa suka zama ɗaya.

"Ki tashi muje in raka Ki ɗakunan ƴan uwan naki, Nima Inason ganin su, musamman twins ɗin nan" murmushine Ya bayyana akan fuskar Angel jin abunda nurse ɗin tace, tuntuni ta faɗa mata, ba twins bane Jamimah da azeeza ɗaya ta girma ɗaya amma taƙi yarda, ba ita kaɗai ba hatta sauran nurses ɗin da likitocin kallon twins suke Yi masu acewarsu Basu da banbanci, Komai nasu kala ɗaya.

da zumuɗi Angel ta sauko daga saman gadon, light blue uniform ɗinta ne a jikinta, sai da ta fara zuwa gaban closet ɗin ɗakin ta buɗe ta ɗauko Hijabin da aka bata Nayin sallah ta zura a jikinta.

Hannunsu ruƙe cikin na juna ita da nurse ɗin suka fito daga ɗakin, hasken electric bulbs Ya haskaka Asibitin tamar da rana, a tsanake suke Yin tafiya suna tattaunawa a tsakaninsu, ɗakin Gabriel suka Fara shiga, tayi mamakin ganinshi idon shi biyu Shida nurse rebecca, ta kunna masu kallo sun natsu abunsu.

Jin motsin shigowar Mutun yasa suka kai eyes dinsu ga ƙofar, murmushi ne ya bayyana akan faces dinsu

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull