Kenza eBookz

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 - Chapter 50

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 - Chapter 50

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 Chapter 50: Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 Chapter 50. Yatsun hannun parveen har karma suke yi wurin…

2,718 words

Yatsun hannun parveen har karma suke yi wurin ɗaukar cup din tea, duka ta kur6e shi, ta soma cin wainar kwai hannu baka hannu ƙurya.

Batul kuwa wani sabon salon ƙauyanci, tunda ta dafi plate din noodles tasha romo da kayan haɗi, da hannu take ɗaukar indomie din tana Jujjuyata kafin ta turata abaki, ɗaya bayan ɗaya Angel ke kallonsu, Kunya duk ta kamata, koda ta daura idonta kan Jamimah robar zuma ta ɗauka ta dinga matsata a tafin hannunta ta sanya harshe tana lasa hada tanɗar baki, Angel ji take kamar ta fasa ihu.

Ummin america da boss man duk suna kallonsu sai faman sakin murmushi suke Yi.

Gyaran murya ya yi masu jamimah ta dago tana kallon shi yace"kidaina shan zumar ita kadai, ga mahaɗinta nan ki zuba asama sai ki ci" ya faɗa yana nuna mata plate din pancakes da robar yougurt' washe mashi baki tayi tana fadin"wallahi zaƙi gareta, kunnuwana har motsi suke yi" gaba daya suka sanya dariya, Ummi kamar zata shaƙe tsabar dariya, Angel dai abin duniya ya isheta, ita ala dole mai aji kada a zubda mata mutunci su kuwa ba ruwansu bayin Allah basu san ma menene ƙauyancin ba.

"Malama, ki dauki spork da shi zakiyi amfani ki ci noodles din ba hannu ba" ummi ce tayi maganar tana nuna batul da spoon din hannunta, bata Iya cin abinci da cokali ba cos sunfi sabawa da hannu, jiki asanyaye batul ta ke faman ƴan kame kame ta rasa ina zata ɗauki cokali, Angel ce ta ɗauko shi ta miƙa mata, ta kar6a ta tsoma shi cikin indomie din batasan yadda zata kwasota ba, ganin yadda ummi take yi masu dariyar shaƙiyanci yasa ran Angel ya 6aci ta haɗe rai, muryarta aƙula tace da batul"idan bazaki Iya ci da shi ba, Ki ajiye shi ba dole" kallonta ummi tayi aikuwa ta galla mata harara, mamaki ya kama ummi ganin abun da Angel tayi mata.

Batul kuwa ta ajiye cokalin taci gaba da ci da hannunta, Maganar Angel ta burge boss man, sai ƙara dubanta yake yi, abinci yake ci amma hankalin shi na akanta.

Haris dai tun da ya dafi chips babu maijin motsinshi, sai idan anyi magana ya ɗago da ido Ya dube su. Mutun ɗayane baya cin abinci, Ya rasa sukuninsa, saboda mutun biyu dake zaune acikinsu, bayason baƙuwar fuska, uwa uba ummi dake ta kallon shi jefi jefi take bin shi da kallo kamar zata haɗiye shi.

Sam Angel bata lura da yanayin da yake aciki ba, sai da Boss Man ya furta"meyasa baka cin abinci ne"? Tukunna ta ɗago ta dubi Danish don ta gane dashi yake magana.

"Bakomai yake iya ci ba, danish me kake son ci"? Ta jefa mashi tambayar, shiru bai bata amsa ba, kamar tayi magana da kurma. Ummi tana yamutsa fuska tace"ai na lura kamar mune muka takura mashi, ƙwarama ka saki jikin ka, saboda atare zamu cigaba da rayuwa acikin gidan nan"

Boss man yace"baya son baƙin fuska ne, amma tunda naga yafi sakewa da shi, Ki jaraba bashi wannan muga idan zaici" yai maganar tare da ruƙo plate din farfesu ya miƙa mata, bayan ta kar6a ta furta mashi"thank u" ta tura plate din agaban Danish.

Cikin muryar raɗa tace"pls ka saki jiki ka ci, tunda gani atare dakai, banason kana damuwa" jinjina mata kai yai alamar toh, duk don ya saki jikin shi yasa ta sanya hannu a plate din ta soma ci shima ya sanya hannun shi suka cigaba da ci atare. Sun dauki lokaci suna cin abincin, sunyi kulu wash rabu hani'an kafin daga bisani ɗaya bayan ɗaya suka fara miƙewa,

Masu aikin gidanne suka tattara kayan abinci, bayan sun kwashe komai suka gyara dining room din tamkar ba'a ta6a 6ata shi ba.

Falo suka koma, kowannansu ya zamu wuri saman sofa ya zauna, kamar yadda Man Ya basu Umarni, yana daga zaune shida ummi suna fuskantar su, sanyin A.c sai ratsa fatar jikin su ya ke.

Sun natsu suna jiran jin me zaice"da farko dai Ina yi maku barka da zuwa gidan nan, ina fata kunji daɗin kasancewa acikin shi" ya faɗa yana dubansu. Amsa mashi suka yi da eh, yace "good, ina fata zaku bamu haɗin kai, mu zauna peacefully babu faɗa babu cacar baki," ɗaga mashi kai sukayi alamar eh.

Ya ƙara da cewa"na fahimci bakomai ne kuka sani ba, to duk abunda baku gane ba kada kuce zakuyi gamon kanku, hakan zai iya haifa maku matsalar da bama fata, idan kunga abu kunaso kuyi amfani dashi baku san yarda akeyi ba, Ga auntyn ku nan yai maganar yana nuna ummi dake zaune saman sofa ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya.

"Ku tambayeta zata koya maku, kada kuji shakkar komai, ku ɗauke mu tamkar iyayenku ko yayyanku, ina fata kuna jina"? Jinjina mashi kai su ka yi, Angel tayi shiru tana kallonshi, muryarshi ta tsaya mata aranta, ji take kamar tasan me irin muryar sai dai takasa gano komai.

"Zaku Iya tambayar Ƴar uwarku Angel itama, don na fahimci kamar tafi ku sanin wasu abubuwan" amsa mashi su ka yi da toh.

"Sannan duk abunda kuke buƙata ta 6angaren aike ni zaku yi ma magana, in sha Allah zanyi maku shi, Idan time din sallah yayi zanzo in tafi da mazan dake acikin ku muyi sallah akwai wurin da muke yin ibada acikin gidan nan, ina fata gaba ɗayan ku musulmai ne" ya faɗa yana dubansu Parveen tai karaf tace"banda Danish da Gabriel sunƙi kar6ar shahada" zaro ido ya ɗanyi yana duban fuskar Danish daya haɗe rai babu annuri.

Gabriel Yace"nifa ƙarya take yi min, Nima musulmin ne"

Da zolaya boss man yace"idan har dagaske kai musulmi ne to ya akai naji sunanka bana musulmai ba"?sunnar dakai ƙasa Yai yana faman sakin murmushi.

Angel tace"nice namanta ban biya mashi shahada ba, ya faɗamin yana so ya musulunta shima" jinjina kai boss man yai, ya dawo da dubanshi gareta"shifa danish? Wani addini yake yi"?

"Bashi da addini" dafe kai boss man yai"Eyyah banji daɗin jin hakan ba, kuma bashi da ra'ayin ya musulunta kamar Gabriel"? Girgiza mashi kai Angel tayi"bayasoma anayi mashi maganar ai, ranshi 6aci yake yi, shiyasa muka ƙyale shi"

"Okey, kada hakan ya dameku, in sha Allah asannu zamuja ra'ayin shi" ta6e baki Danish yai jin abunda boss man yace.

"Gabriel na dawo gareka, tunda kana so ka musulunta, babu buƙatar 6ata lokaci, Zan biya maka kalmar shahada saika maimaita da kyakkyawar niya" murmushi gabriel yasaki bashi ba hatta sauran ƴan uwanshi sunji daɗi, ba tare da 6ata lokaci ba, Ya biya mashi kalamar shahada, wani irin daɗine ya lullu6e su Angel, shima Gabriel din daɗin yake ji sai faman washe baki yake yi.

"Ina taya ka murnar shiga addininmu, ko kana buƙatar na canza maka suna? tun kafin gabriel ya bashi amsa su Batul su ka yi saurin cewa"Eh wallahi acanza mashi, sunan shi wahalar faɗi yake yi mana," dariya boss man yasaki jin abunda suka ce. "Okey, daga yau zamu dinga kiranshi da....."bai ƙarasa sunan ba yai shiru yana kallon fuskar Gabriel duk sun ƙagara da suji wani suna za'a sanya mashi.

"SAJEED" wani irin ihun farin ciki suka saki, Sunan yayi bala'en yi masu daɗi musamman Azeeza.

"Ina fata sunan yayi maka"? Jinjina mashi kai Gabriel yai"eh, nagode sosai" Boss man yace"okey, daga yanzu sunan da zaku dinga kiran shi da shi kenan wato Sajeed, Kefa Angel meye asalin sunanki" farfari tayi mashi da ido kafin ta bashi amsa da cewa"Unaisah" Tamkar baisan sunan ba yace"wow suna mai daɗi, mai zai hana kema mu dinga kiranki da asalin sunanki" zumbura mashi baki tayi ba tare data furta komai ba, tana son asalin sunanta sai dai tafi son sunan Angel saboda daddynta ne ya za6a mata shi.

"Dan Allah Angel ki amince mu dinga kiranki da Unaisah Yafi daɗi Allah" Batul ce tayi maganar, Hannah tace"nima nafison Unaisah din yana da daɗi" Haris ma yace"nima shine za6ina, Unaisah" Ta6e baki Angel tayi tare da kallon fuskar Danish don taji me zaice, batasan boss man na kallon ta ba, Ya fahimci tafi ƙaunar Danish akan sauran ƴan uwanta, saboda yadda take bashi muhimmanci.

Da ido tayi mashi alamar ta amince da sunan ko kuwa"? Ɗaga mata gira yai alamar eh. Dawo da dubanta tayi akan fuskar Boss man"shikenan na amince, adinga kirana da Unaisah" Murmushi ya saki ba tare da sun gani ba saboda mask din fuskarshi. Javed ne yace "um sallah ma Angel ta koya mana amma bamu taba yi ba dama tace in muka zo zamu rinqa sallah da karatu"

Jinjina kai yayi tare da fadin "karku damu zamu rinƙa karatu tare in sha Allah komai zaku iya wanda ya shafi addinin muslunci" Da alama sunji dadin maganar Jemimahh tace"wai kai ba zaka cire abun fuskarka ba"? Girgiza mata kai yai"a'a" tace "to meyasa baka son mu ganka? Ko dai mummuna ne kai baka da kyau"? Dariya ce ta kubce mashi.

Azeeza tace"bakya jin magana jemimah ina ruwanki da shi? Ke komai sai kin nuna zaƙewa" harara jemimah ta watsa mata"Ni ki ƙyale ni," ta faɗa tana duban shi"dan Allah ka cire muga fuskarka" Javed yace"nima inason naganka, tun da kace atare zamu rayu agidan nan, please ka cire mu ga fuskar ka.

Girga mashi kai yai"Ku yi haƙuri ba yanzu ba, tunda muna atare wata rana zaku ganni" Angel tace"babu komai, Allah ya nuna mana lokacin, Ni sai na ke jima kamar nasan muryarka don dai kace ba yanzu zaka buɗe fuskarka ba ni kuma da saina gane wanene kai" hakanan ta faɗa bada wata manufa ba, tasan batasan shi ba.

Murmushi yai ba tare daya tanka mata ba, kallon Ummi yai, tun da ta zauna tana sauraron su bata ce komai ba "Ba abunda zaki faɗa masu ne"? Yamutsa fuska tayi kamar bata son furta magana tace"naso yau in taimaka masu su gyara kansu, amma nabari sai zuwa gobe ko jibi, idan na ƙara hutawa"

Yace"okey, ku tashi mu tafi inaso zan nuna maku ko'ina na cikin part dinku, duk abunda kuka gani wanda kuke neman ƙarin bayani akanshi Ni zaku tambaya" suka amsa mashi da toh. Miƙewa sukayi Ummi ma ta miƙe don tana son itama ta ƙarema ko'ina na part din kallo, cikinsa da wajensa. Yinin Ranar sunsha yawo, Sunga abubuwan ban mamaki dana Al'ajabi, ido ya samu abinci, kamar karsu dawo cikin gidan, Boss man yasha tambayoyi kamar ƴan jarida, duk abunda basu gane ba sai sun tambayeshi ba ƙaramar wahala yasha ba, itama ummi tana taimaka mashi wurin amsa masu tambayarsu, duk yawon da suka sha basu leƙa wajen gidan ba, kuma basu shiga sauran part din ba.

*JOS CITY*

Idan muka koma 6angaren Alhaji ubaid, tunda garin Allah Ya waye da sassafe Benazir ta farka tana sambatu akan mijinta da ƴarta, Alhaji ubaid Ya jira kiran Dr.shureim sai dai shiru, har kiran layin wayarshi yai amma bai ɗaga ba, ya kira Alhaji musa akaci sa'a kiran ya shiga kusan sau goma tana ringing ba'ayi picking ba, gashi lokaci yana ta tafiya babu alamun zuwan Shureim, daga bisani suka kira likita domin duba lafiyar benazir, bayan ya duddubata ya faɗa masu cewa lafiyarta ƙalau, sai dai akwai abun da ta ƙwallafa rai akanshi yaji tana fadin mijinta da ƴarta yace to kada su kuskura suce zasu faɗa mata zancen babu su, don a halin da take aciki yanzu bazata Iya jurewa ba, zata Iya samun ta6in hankali, zaifi suja baki suyi shiru, sannan suci gaba da kwantar mata da hankali har zuwa lokacin da zata samu natsuwa sosai, tukunna su faɗa mata, sunji dadin shawarwarin da likitan ya basu, bayan tafiyarshi cikin ikon Allah, Benazir ta dawo hayyacinta a lokacin da basu yi tsammani ba, ganin Iyayenta a gefe da gefen gadon da take akwance yasa ta rushe da kukan farin ciki tana ambaton sunayensu haɗi da roƙon yafiyarsu akan babban laifin da ta aikata na guduwar da tayi ba tare da sanin su ba, tayi mamakin jin suna kwantar mata da hankalinta, sukace su basu ruƙeta aransu ba, sun yafe mata, ta daina kuka komai ya riga daya wuce, tuna baya baida amfani tun da ya riga da ya faru, ƙaddarace da babu wanda ya isa ya canza ta, haƙiƙa taji daɗin kyakkyawar tarbar da ta samu awurinsu tayi tsammanin zasu koreta ne idan sun ganta, saima suka koma suna lallashinta haɗi da tarairayarta, abinci ma abaki hajiya layla ta bata shi, duk bayan ƴan mintuna sai ta tambayesu ina mijinta da jinjirar data bari a cikin kwamin wanka? tana son tagansu, idan suna agida dan Allah su taimaka su kaita wurin su, hajiya layla ta bata haƙuri da cewa sunyi tafiya basa a ƙasar amma tana da tabbacin sun kusa dawowa, sai lokacin tace toh ita yarinyar ta rayu? Waye ya rene ta harta girma? Kuma ya sunanta"? Hajiya layla tace"ta rayu mana, kyakkyawar budurwa ta ɗauko hasken fatarki, kamannin fuskarta ne dai ta ɗauko na daddynta, hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba, tana ta faman sauke ajiyar zuciya tace"baki faɗa min sunanta ba? Kuma tasan ni? An faɗa mata sunan mahaifiyarta? Kuma Kuna nuna mata hotona"? Shiru hajiya layla tayi don batasan amsar da zata bata ba, ita kanta ba zumunci take yi da tajuddeen ba, saboda bada son ranta ya auri Benazir ba, shiyasa ko zuwa gidan bata ta6a yi ba, tun lokacin da suka koma dubai da zama, a hotone ma ta ta6a ganin Angel din, taji nauyin amsar da zata ba benazir, daƙyar ta Iya furta mata sunanta Angel, tana faman murmushin yaƙe tace ai tasanki ya za'ai mu ƙi nuna mata hotonki, duk in tajudden ya kawota gidan nan sai mun nuna mata hotunanki, Yarinyar tana sonki sosai, kullum maganarta ina mamanta take? Yaushe zata dawo? Meyasa kika tafi baki waiwaye ta ba' jin hakan yasa benazir ta fashe da kuka, Hajiya layla duk tasha jinin jikinta, fargabarta ranar da Allah zai haɗa benazir da ƴarta idan har tana araye tabbas zaiyi wuya yarinyar ta amince da ita, ga kuma ƙaryar data faɗa mata.

Cikin shessheƙar kuka benazir tace"amma dai baku fada mata a yanayin da na tafi nabarta ba ko"? Hajiya layla tace eh bamu faɗa mata ba, mun dai ce mata kin 6ace ne ba'asan inda kika tafi ba, to dayake yarinyar tana da tawakkali kuma tana samun kulawar tajo da kuma kulawar da muke bata hakan bai dameta sosai ba" baiwar Allah benazir jikinta duk yai sanyi, tace Ina aneelerh da mijinta"? Hajiya layla tace ai mijin aneelerh baya nan shima tare suka yi tafiyar, ta matsa lamba akan tana son akaita gidansu Aneelerh don taganta, Alhaji ubaid ya sanar da ita cewa ai basa garin jos sun koma abuja da zama, badan taso ba ta haƙura, damuwar hajiyar laila ɗaya kada tace su nuna mata hoton ƴarta saboda babu maishi acikinsu, har ƙwara Alhaji ubaid wata'ƙil asamu hutunanta na yarinyata saboda yana son yarinyar, cikin ikon Allah benazir bata tambayesu game da hoton Angel ba, saboda halin damuwar data shiga gani take kamar bazata ta6a ganin mijinta da ƴarta ba, duk da mommynta ta kwantar mata da hankalinta. Masu gadin gidan kusan sau uku suna shigowa cikin gidan domin duba lafiyar benazir, duk sun damu da ita, haka zalika zainab takasa samun sukuni duk bayan ƴan mintuna saita leƙo ta dubata, hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba ganin yadda kowa ya damu da ita. Tana akwance saman gadonta, hajiya layla tana a gefenta, a lokacin Alhaji ubaid Ya koma dakinshi, damuwar duniya ta ishe shi, tun da ya jaraba kiran layin shureim dana Alhaji ubaid basu ɗaga ba, ya rasa sukuni, sai faman yin zarya yake yi acikin ɗakin shi, kaf family dinsu babu wanda yasan da dawowar benazir, saboda bai sanar da su ba, hatta mutanan da suke zumunci da su bai faɗamawa ba, saboda mai gemu ya basu shawarar su dan jinkirta tunda ba'asan wanene yai silar yi mata asirin ba, zasu Iya ƙara cutar da ita idan suka ji cewa tana araye kuma ta dawo gida, da ace Iyayensu na araye da kuwa sune mutun na farko da zai fara sanarmawa donsu taya shi murna sai dai babu su, mutum biyu ne yafi yarda dasu ƙanin shi Alhaji musa sai ƙanwarsu autar gidansu Hajiya Laurat, second wife din mai girma sharafuddeen obinna, itama ya jaraba kiran layin wayarta bata yi picking ba, abun duniya duk ya ishe shi.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull