Kenza eBookz

Kwai cikin kaya book 2 complete - Chapter 31

Kwai cikin kaya book 2 complete - Chapter 31

Kwai cikin kaya book 2 complete Chapter 31: Kwai cikin kaya book 2 complete Chapter 31. A safiyar yau nakejin wai za'a kai lefena gidan Dad ne, haka kawai…

3,979 words

A safiyar yau nakejin wai za'a kai lefena gidan Dad ne, haka kawai naji gabana ya faɗi, amma sai na danne zuciyata na cigaba da addu'oi, har yanzu Yah Qaseem na ƙasan raina, inason nasan halin da ya ke ciki shi da Dad fiye da kowa a gidanmu, sai dai hakan ta gagara dan boss ya toshe ko ina da ina da zan iya jinsu. Su Amaturrahman sunata shirin tafiya can gidan domin amsar lefen suma, sai a yau naga sauran manyan ƴaƴan Ummu ƴan uwan tagwaicin Amaturrahman. Abdul-Raheem da Abdur-rahman, sai Ameen ɗan uwan tagwaicin Meenal, sai Uncles ɗinsu huɗu, Sauban da matarsa ƙyaƙyƙyawa mai kirki da yaransu huɗu masha ALLAH, sai Aryaan shima da matarsa da yara biyu, Aiyaan ma matarsa da yarinyarsu ɗaya sai ciki ƙarami da matarsa keda shi, sai Khalil shima da tasa matar da yara biyu, dukansu suma a jiya suka iso daga India. Gida ya cika yanda akeso tamkar bikine daya shafesu na jini, washe gari sai ga wadda naji suna kira Aunty Samha itama da nata ƴaƴan, sai kuma babbar mace suna kiranta Aunty Mimi. Wlhy bansan sanda hawaye suka faramin gudu a kumatuba, duk wani kewar ahali sun toshemin ita ta ko ina, sun mayemin gurbin dangin da suka nisanceni. A wajen Amaturrahman nakejin wai Boss yazo masarauta wajen Ummu yau da safe, bai nemi inda nakeba har ya wuce, banji komai a rainaba game da hakan, sai daga baya suke bani labarin Ummu ce tace an daina ganina har da shi kansa bazai ganniba. Ni saida abinma yaso bani dariya amma na kanne.

_______________

A gidan Dad kam shirye-shiryen karɓar lefe suke, duk da dai ran Momy a ɓace yake matuƙa tana dai ƙoƙarin dannewane, shi dai Dad baka gane yanayinsa, dan yamafi maida hankali ga lallashin ƴar lelensa da suka cikama zuciya

da alƙawarin komawarta gidan Jay nan bada jimawaba. Kusan sha biyun rana su Amaturrahman suka iso gidansu Hudah, Hudah dai bata fitoba zamanta tai cikin ɗakinta, Aamilah kuma an fito ayi rainin wayo saita iske waɗanan sunci uwarta aduk iskancin da take taƙamar ta tara kota iya. Dole fa ta nutsu waje guda ta kama kanta, harta je ta ƙwanƙwasama Shahudah dake ɗaki gulma da cewar lallai Bily ta shahara a asirin nata har ƴan gidan sarki taimawa. Cikin takaici Shahudah tace, “Tsinanniya jikar matsafa, ai nayi alƙawarin randa na koma gidan Bb wlhy bazata kwana a gidanba, shi kansa saina sakashi yin nadama wlhy, kuma a banza zata shiga ta fito Hajiya (mama Atika) tamin alƙawarin ko hannunta bazai riƙeba dan Uban da ya haifeta”. Dariya Aamilah ta sanya da sake tunzurata akan hakan da zatai shine dai-dai, kuma taji daɗin matakin da mama Atika tace zata ɗauka akan kar Bilkisu ta raɓu Jawaad, (dan sufa har iyanzu tunaninsu nakan asiri Bilkisu taima Jay bawai sonta yakeba😂). “Mtsooww kamar kin manta da aikin matsafa kenan” cewar Shahudah cike da takaici. Haka dai sukaita aikin zagin Bilkisu da Alhaji Babba harda su Ummah basu tsiraba, kai gidan sarki ma saida suka samu rabonsu😂.

Oho su bama susan da zaman wata Hudah ba a duniya balle a cikin gidan, sun ɓararraje abinsu sunata harkokinsu tamkar gidansu (😂Wani aiki saisu Samha) hankalinsu kwancefa yake a gidan Dad dukda sunga cika da batsewar da Momy keyi basu nuna ta damesuba. Ƙarfe biyu da wasu mintuna na rana matan Uncles ɗin Jawaad dasu Ummah suka iso da lefen Bilkisu. Kayane gwargwadon iko na gani na faɗa babu fariyya a ciki balle nuna anfi kowa. Sai dai fa tsarin kayan da nagartarsu dolene ta girgiza zukatan mahassada da masu ganin wadda akai dominta bata cancancesu ba. Inna zainabu sai haɗiyar zuciya akeyi, hatta da Lawisa da ayanzun basa faɗa da bilkisun kuma itama mijinta Alhmdllh sun sami sauyi saida taji ɗaci a ranta, hakama sauran dangin kowa dai ta ciki na ciki, su kansu matan Uncles ɗin Jawaad da suka kawo kayan kowa dai sai murmushin saman fuska tunda suma sai yaune suke ganin kayan tunda su Ummah ne suka haɗa abinsu. To kowa dai ya danne an gama komai lafiya, an kuma bar kayan anan sai Dad ya gani sai a kaisu masarauta zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu suma su Gimbiya su gani. Tukuyci mai tsoka ƴan masarauta suka saukema su Ummah, wanda ya girgiza kowa hatta momy da take ganin wanda Dad ya bada a bayar yayi yawa da.

Aikam tunda su Safah suka koma masarauta babu abinda suke sai labarin lefe, suka addabama Bilkisu da tsokana musamman su Amaturrahman da matansu Aryaan da suke biye musu suma dayake mashiriritan ne. Sai da gimbiya ta fito da kanta ta korasu daga kan Bilkisu sannan suka sama mata lafiya.

_____________

Gayya taban mamaki su Jabeer sukayo a wannan biki, al'amarin har ba'a cewa komai, tun a yau baƙin nesa kuwa suka fara sauka, irin su Abbati ma duk yau suka kawo matansu gidan Ummah babba, su kuma suka yada zango a masaukin da su Hafiz suka tanada musu. Ango kuwa yau alhamis yana zuwa office Sir Ahmad ya korosa akan ya tafi sun bashi hutu, karya ƙara ganin ƙafarsa sai nan da sati biyu ciff, shidai murmushi kawai yayi baice komaiba. Ƴan station ɗinsu ma dai zuwa yanzu sunsan boss ya auri Bilkisu, masu gulmar dama soyayya yake da ita sai bakuna suka buɗe aka samu nayi, yayinda masu goyama Rose baya suketa angizata da maganganun ɓatanci ga Bilkisu da Jay ɗin kansa, masoyansu na ƙwarai kuwa murna suke tayasu da ganin sun dace da juna.

MASARAUTA

Tunda garin ALLAH ya waye an tashine cikin shirye-shiryen kamu da aka haɗashi da Hausa fulani day baki ɗaya, su Ummie, Nazifa, Zuhrah, Rebecca, Amina, Nabeelah, duk suna can suma tare dasu Amaturrahman, abin birgewa kuma duk ƙawayensu na Boarding skull sai da su Ummie suka gayyatosu suma duk sunata isowa masarauta a safiyar yau, hakan saiya saka Bilkisu hawaye da tuno iyayenta, inama da ransu wannan rana tazo mata, inama suna jingine da ita har zuwa yau ɗinta, ina firdausin ta, ƙawar amana ko tace ƴar uwa rabin jiki, kullum addu'arta ALLAH ya

sadata da Firdausi da iyayenta kafin tabar duniya.

Tunda safe dama mai ƙunshi tazo muka shige cikin ɗaki daga ni sai ita ta shiga zanamin na nutsuwa, zuwa azhar ya bushe yay shar kamar ka cinye dan baƙi da jaa aka ɗaɗara mani, kasancewar fashin salla nike dama sai kawai aka shigamin gyaran kai a nan gida dan Gimbiya nada dukkan kayan gyaran kai a gida da takema kanta, bayan an kammala nai wanka lokacin ƙarfe kusan uku. Kasancewar ba sallah zanyi ba sai ban damu da kwalliyar da ake shirin tsaramin ba, ni kaina basai an faɗaba nasan ina tsaruwa dai-dai gwargwadon iko, duk da ba'aimin kwalliyar dana canja kamanni baneba amma nayi ƙyau fiye da zato. Bayan an kammala kwalliyar aka shiryani cikin atamfa lass ƴar ubansu datasha stones work ɗan gaske, sket da riga akai da suka fidda ainahin tsarin jikina dukda basu matseni tsam ba, sundai zaunamin a jiki ɗas har ni kaina ban gaji da kallon kaina ba. An min naɗin ɗan kwali mai tsari aka ƙawata adon nawa da sauran kayan ƙawata kwalliya irinsu sarƙa da sauransu. Ƙamshina kam ai har hawa kan mutane yakeyi, daka ganni kaga cikakkaiyar bahaushiya jinin Fulani, tabbas a yau na sake yarda da babu mummuna a duniya sai wanda ya munana kansa, idan har zaka tashi ka gyara kanka tofa ka wuce a kiraka mai muni, dama can rashin gata da kulawane suka dadushe sihirtaccen ƙyawuna mai cike da kwarjini. Taron iya matane, dan acikin masarauta ma za'a yisa, su Ummah da danginsu duk sun iso masarautar, hakama danginna na ɓangaren Uwa su Inna Zainabu dasu Momy harda Aamilah, Aunty Shahudah dai ban gantaba, ƴan gidansu Boss ma kam inada tabbacin ƙwai da kwarkwata ne a wajen nan. Babu abinda da dai za'a cema UBANGIJI sai godiya a wannan al'amari, amma tabbas Bilkisu tazo da farin jini mai ban mamaki da tarin alkairi. Iyayen ƙawayenta su Ummie, matansu Aliyu, abokan aikinsu ƴan station ɗinsu, ƙawayenta na makaranta harma da waɗanda sukazo dalilin wane da wane duk suna a wajen. Sai ƙarfe huɗu da rabi Gimbiya Sarauniyar gagara badau Munayatul-muna ta fito riƙe da hannun amarya Bilkisu mai gadon zinari. Ai a take wajen ya ɗauki ƙannan magana musamman ma ƴan gidansu Jawaad da ada suke ɗaukar Bilkisu ba komaiba saboda yanda su Momy ke munanata da ƙasƙantar da ita a garesu. Wasu sunɗan santa sama-sama wasuko sai a yau suke ganinta. Ganin yanda ɗunbin mutane suka taru danni sai kawai naji hawaye sun zubomin a kumatu, Zuhrah ce ta duƙa gabana inda ya kasance mazaunina ta shareminsu da handkherchief tana murmushi, “Haba amarsu ai lokacin kuka baiyiba kinji, sai gobe idan ALLAH ya kaimu kina kusa da Boss, da sun zubo ya lashe kayansa”. ta ƙare maganar da kashemin ido. Hararta nayi ban iya cewa komaiba, sai dai fa maganar datai sai da naji gabana yaɗan faɗi, dana tuna kuma ma ina period saina ɗanji sauƙi a raina. Ba'a ɓata lokaci wajen fara gudanar da abinda ya tara mutane ba, komai kuma a nutse babu wata hayaniya, koda aka fara kiɗan ƙwarya ma a nutse ƴammata da matan aurenma masu jini a jika keyin rawa, ina tsakkiya nikam anata zubamin liƙi, Anum na liƙe dani wai tana gwagwaɗamin wai itama idan ta tashi aure zamuje Saudiyya da masu kiɗan su mat. Murmushi kawai nayi mata dan ta bani dariya. komai ya tafi cikin burgewa da kwanciyar hankali, kafin a koma yin hotuna da kowa ke fatan yi da amarya da gimbiyar gagara badau. Zuwa magriba aka tashi. Ni dai tunma kafin magriban muka bar wajen tare da Ummu da akoda yaushe tana kusa dani idanunta akan kowa da zai iya raɓata. Dan tace itafa bata wani yarda da kowa dake wajenba.

__________________

A ɓangaren su Jay suma sunacan suna nasu shagalin, sai dai su nasu sai bayan sallar isha'i suka fara, suma iyasune maza zalla a wajen abokansa, su Aryaan duk suna can dan kuwa dai sa'annine, sudai su Abdur-raheem, dasu Anuwar basu jeba kasancewar su Jay yayunsune wannan shigar ba tasu bace, suna buƙatar sakewa kuma, sunama can gidan Mami Munubiya suna shan shaftarsu hankali kwance.

Dauriya kawai Jay keyi, dan kansa ciwo yake masa matsanancin ciwo ma kuwa, amma kasancewar yasan duk ɗunbin mutanennan dan shi

suka taru sai ya daure har zuwa goma na dare kafin ya gudu ɗakin da zai kwana a hotel ɗin ya barsu, ko wanka baiyiba dan bai jima da yiba, kayansa kawai ya zame ya faɗa saman gadon ya kwanta yana sauke tagwayen ajiyar zuciya, cikin ransa ko mamakin Bilkisu ya keyi, ƙaramar yarinya da ita sai shegen jan aji da miskilanci, tunda ta tafi bata nemsaba, ta dawo ma haka. Wani ɓangare na zuciyarsa yace, ‘Kaida haƙƙin sanin lafiyarta ke a kanka ka nemeta ne?’. Kansa ya dafe kawai da lumshe idanu, kafin ya buɗe a hankali ya jawo wayarsa dan tunawa da saƙwanin da yasa a turo masa. Kasancewar datarsa a buɗe take duk sunma buɗe kansu da kansu, harda videos. Ya sauki wani lallausan murmushi maiban mamaki daya sakani tunanin wai shin mi yake kallo hakane?................✍

Jiya kun haɗan zafi yasin, waɗanda ban ɗaga kiransu ba suyi haƙuri man kaina ne ya tsiyaye😂🚴🏼.

BARKA DA JUMA'A.

Musha weekend lafiya

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭😭🙏🏻Billyn Abdul: Page 38

..................Shagulgulan biki sun cigaba da gudana a washe gari tamkar yanda aka tsara, su Ummah babba sunyi yinin biki suma matsayin iyayen ango, kafin zuwa la'asar su ɗunguma zuwa masarauta domin halartar walima da gimbiya ta shirya itama. Walima kam ta ƙayatar fiye da zato, amarya tasha ƙyau cikin shadda pink mai duhu. Inda malamai magada annabawa suka gudanar da wa'azi mai kashe jiki da ɓargo, bilkisu kam dai ansha kuka, idanu sun ƙara girma. Tun su Zuhrah dake zaune kusa da ita suna mata dariya har dai suka koma lallashinta suma suna sharar hawayen dan jikinsu duk sai yay sanyi ƙalau. An tashine gab da magriba, dan haka kowa yana yin salla shirin tafiya dinner ya fara. Amarya ma wanka aka sakata ta shiga. Gaba ɗaya jikina a sanyaye yake, tunani da fargaba duk sun cika zuciyata, yau ni Bilkisu nice za'a ɗauka akai gidan boss matsayin matarsa ta aure, aure ba yawo ba, idan naje shike nan natafi din din din, duk da nasan ba sonsa nakeba, shima kuma bason nawa ya keba na ɗaura ɗammarar masa biyyayya insha ALLAH, zanyi haƙuri tamkar yanda kowa ke faɗamin zaman aure haƙurine, zanyi biyayya a garesa matsayinsa na mijina shugabana, zanyi aiki da dukkan dabarun Umm-Anum da gambiya suka ɗorani akai domin samun zaman lafiya a gidana koda ace bazai soni ba. tausayinsa nakeji har cikin raina yanzun, dan a daren jiya munyi zama na musamman da Ummu inda muka tattauna game da kamanninsa da Anuwar harma da Umm-Anum ta abubuwa da dama. Ta tabbatar min nice ya dace nai wannan aikin na bincikar abinda ya shafesa ko tanan zasu iya fahimtar idan akwai alaƙar da duk muke zargi dan kamannin sun wuce kama akwai dangantakar jini dole, bansan komai na abinda ya shafi family nasa ba, sai ɗan abinda ba'a rasaba shima iyakarsa daga wajen su Mom ne da da rashin jituwa tsakaninsa da Yah Qaseem, amma a raina nima tunda muka haɗu da Umm-Anum nakeji abubuwa da dama nazomin a rai game da shi......... Da wannan tunane-tunanen na tsaftace jikina na fito, kasancewar ba salla zanyiba zaman min kwalliya akayi. Tun ina jiyo hayaniyar ƙawayena dake ɗakin su Amaturrahman suna shiryawa har naji tsit, alamar dai sun fice dan zuwa yanzu har anyi sallar isha'i. Basan yaya zan musalta muku irin ƙyawun da nayiba yauma, amma na bama kowa damar ya hasasoni cikin zuciyarsa, kwalliyata ta yau ta kasance harda alƙyabar da Mommah ta bani matsayin ƙyautarta, basai an faɗaba, a gani da ido kaɗai ya isa amsa ga mai kallo cewar an sayeta da kuɗaɗe masu nauyi da darajar gaske. Suna cikin gyaramin alƙyabbar da santin ƙyawun da nayi aunty Samha ta shigo. “Wow, masha ALLAH amaryar ƙamshi” ta faɗa tana rungumeni, ta ɗagoni tana kallona da cigaba da faɗin, “Wannan ai saiki rikita angon yace an fasa dinner ɗin”. Dariya waɗanda sukaimin kwalliyar sukayi, ni dai kaina a ƙasa ban yarda na kalleta bama dan tasa naji kunya, gashi kukane keta ƙoƙarin tasomin ina dannewa. Itace ta kama hannuna muka fice, ganin ba'a kaini wajen Ummu ba sai nayi tunanin za'a sake dawo dani nan kenan, ƙilama sai gobe idan ALLAH ya kaimu. A take naji farin ciki ya wani lulluɓeni. Ko ina ƙwanyar yake da haske a masarauta shiyyasa koda muka fito dukda kaina a ƙasa yake ina kallon inda muka nufa. Mun tsaya dai-dai motar da na hango Oga Jabeer jingine yana waya tun fitowarmu, yana sanye da shadda ƴar ubansu ruwan madara. Yana ganin mun ƙaraso ya ajiye wayar yana murmushi da faɗin, “Aunty Samha aini da har ina shirin bin bayanku, dan naga baƙwa son bamu amaryarnan kamar”. Murmushi tayi mai sauti tana gyaramin hular alƙyabar, “To gaskiya badan munasoba zamu baku, dan bamu gaji da ɗiyarmu ba, amma yaya muka iya, wannan shine girman”. Oga Jabeer na ƴar dariya ya buɗe ƙofar motar da cewa, “Aure yaƙin mata”. Tace, “Har mazan ma”. Daddaɗan ƙamshin turarensa da na sani daine ya fara tarbata da sallama, na shaƙa na lumshe idanu ina ƙoƙarin dai-daita bugun zuciyata da kalato yawun da zan jiƙa maƙoshina da ya bushe, sai da na zauna da ƙyau Mah-mah ta gyaramin alƙyabar sannan na tsinkayi muryarsa yana gaisheta cike da mutun tawa, sai da suka gama gaisuwar s

annan Oga Jabeer ya rufe motar ya shigo shima, itama motar da zasu tafi a ciki ta nufa ta shiga. “Ina yini?”. Na faɗa a hankali har banyi zaton zaima jini ba. Shiru banji ya amsaba, kuma tabbas inaji a jikina idonsa a kaina suke, dan ina jinsu har cikin ɓargona. kaɗan juya na kalli sashen da yake dan in tabbatar da bai jinin ba kokuwa ƴan wulaƙancinne a kusa..... Ina ɗagowa idanuna na shigewa cikin nasa, saurin maida kaina ƙasa nai ina ɗan ƙunƙuni a cikin raina batare da nasan bakina naɗan motsawaba ashe, ‘mutum babu abinda ya iya sai kallo, har sai an hango maka muni’. Jawaad dake kallon yanda bakinta dake ta shining na ɗan lipstick ɗin da aka sanya mata ya lumshe idanu a hankali yana sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya, maida kansa yay jikin sit ya kwantar yana maijin takaicin yarda da yay da zuwan wannan dinner ɗin banzar, yanzufa kowa sai yaga wannan ƙyawun da tai ko?. Ware idanunsa ya sakeyi a kanta yana binta da wani irin sassanyar kallo, gaba ɗaya ƙamshin turarenta ya saukarma gaɓɓansa da kasala......... “Ehhgy egeehhmm!”. Jabeer yay gyaran murya. Haɗe fuska jay yayi ya balla masa harara tare da ɗauke kansa ya maida gefe bai dai ce komaiba. Jabeer ya haɗiye dariyar dake cinsa daƙyar sannan ya tada motar suka fice.

Shiru motar tayi bakajin motsin komai sai na ac da ƙamshin turarukanmu, tunda na gaida Oga Jabeer nima ban sake ko ɗaga kai na kalli inda sukeba, dodon nawa kam tun gaisuwarsa da aunty Samha ban sakejin ya firta komai ba shima, anata kiran wayarsama yayi kunnen uwar shegu tamkar ba yaji ana kiran. Mintuna ƙalilan muka iso wajen taron, inda muka taras da abokansa dasu Ummie tsaitsaye alamar isowarmu suke jira. Jabeer da yay fakin ya juyo ya kalli Jay. “ku zama cikin shiri boss, bara na musu magana”. Kai kawai ya ɗaga masa, shi kuma ya fice. Kusan sakanni ashirin da fitar Oga Jabeer babu wanda ya motsa a cikinmu daga ni har shi, inata ɗan juya zoben yatsana ne dan gaba ɗaya a takure nakejin zaman namu kusa da juna. “Bana son rawa” na tsinkayi muryarsa ƙasa-ƙasa saitin kunnena, da sauri na juya garesa dan a bazata maganar tazomin. A karo na biyu muka sake haɗa ido, sai dai yanzun duk yanda naso janye nawa kamar ɗazun hakan ya gagara, kallo yakemin irin na tsakkiyar idonnan tamkar zai haɗiyeni dasu, bazan iya jurewa ba, amma na kasa janyewa dan tamkar yamin ɗaurin goro ne da mayun idanun nasa da a yau suke farare tas babu sirkin ja alamar dai baya tattare da ɓacin rai. Da ƙyar na samu nai ƙoƙarin yin ƙasa da kaina zuciyata na wani tsitstsinkewa tare da jinin jikina. Amma a bazata saijin tattausan hannunsa nai ya taro haɓata ya sake ɗago fuskar, tuni zuciyata ta sake wani zallo tamjar zata faso ƙirji ta fito, Farfar na farayi da idanuna da suka cika taf da ƙwalla lokacin da ya matso da fuskarsa daf da tawa har munajin saukar numfashin juna, lumshe idanun kawai nayi ganin bani da wata mafita kuma, ya kawo bakinsa daf da nawa. Yanda jikina ke tsuma zai tabbatar maka a matsanancin tsoro nake da yanayin, tsigar jikina duk ta miƙe. Jay dake kallon yanda bily ta rikice ya saki lallausan murmushi tare da goga hancinsa kan nata, murya can ƙasan maƙoshi yace, “Matsoraciya kawai, darajar matata tafi ƙarfin nayi kissing ɗinta anan wajen yariya, hakan bazai taɓa yuwuba sai a fadata insha ALLAH. badan girman alƙawari ba da bazan taɓa bari ki shiga wajen nanba, ni kaɗai yafi cancanta na shaida wannan ƙyawu naki a cikin gidana. Ina ƙara maimaita miki bana son rawa”. Ya ƙare maganar da ɗaura yatsansa babba saman lips ɗina ya kwashe ɗan lipstick ɗin da aka samin. Wata irin kunya naji ta lulluɓeni mai haɗe da tsoro da ɗan haushin gogen lipstick da yayi, nai ƙasa da kaina ina ɗan kumbura da faɗin, “Toni nama iya rawan ne ma.........” Saukar ɗalli kawai naji a saman laɓɓana mai azabar zafin, na ɗago idanuna da suka cika da ƙwalla a kansa. sassanyan murmushin mugunta ya sakarmin har dimples ɗinsa duka biyu na loɓawa, ya ɗage kafaɗunsa yana ɗage gira ɗaya da taɓe baki alamar ni naja. Kafin wani ya ƙara magana a ciki

nmu akai knocking glass ɗin motar, sauke gilas ɗin yayi, oga Hafiz ne yay masa magana akan mu fito. Banji amsar da ya bashiba, baice min komaiba nima ya fice, ina ƙoƙarin gyara alƙyabata nima na fita naji an buɗe ƙofar ɓangarena, na ɗago dan ganin wanene muka haɗa ido ashe shine ya zagayo tanan, hannunsa na dama ya miƙomin yana wani ɓata fuska da kallona ƙasa-ƙasa, a kunyace na ɗora nawa ya taimakamin na fita nima, hannunsa na haggu yasa yaja hular alƙyabar ya sake rufemin fuska da ƙyau. Ina jiyo wani cikin baƙin abokansa na faɗin, “Sarakin kishi muma ba kalla zamuyiba ai bar wahalar rurrufe mata fuska”. banji ya bashi amsaba sai dariyar da sauran sukayi. Inajin irin zafin da nakeji a duk lokacin da ya raɓu jikina, sai dai yau kaɗan nakejinsa cikin amincin ALLAH, dan haka nai jarumtar daurewa tamkar banajin komai ina addu'a cikin raina har muka shige abokansa da ƙawayena na biye damu a baya cikin ƙyaƙyƙyawan tsari babu wata hayaniya. Muna shiga da aunty Batool dake ƙofar tsaye tana jiranmu muka fara cin karo, ta shiga feso mana wani farin abu mai ƙyalƙyali da ƙamshi, masu hotuna kuwa nata ƙyalla mu.

Sauran mutanen duk suka miƙe idanun kowa na kan amarya da ango dake cike da birgewa, yayinda ƴanmatan family ɗin su Jay sukejin zafi a zukatansu dajin takaicin bilkisu da tazo daga sama tai musu wuf da shi, sai irinsu Rose da kallo ɗaya zakai musu ka hango tsagwaron kishi da tsanar bilkisun a cikin idanunsu. MC kuwa na zubama amarya da ango kirari. yayinda Ali jita ya sake gyara maƙogwaron nan nasa na zinari ya fara baitocin girma ga amaryar ƙamshi bilkisu mai gadon zinari cikin waƙarsa mai taken Bilkisu gimbiya.

(Bara naɗan raira muku kaɗan saura wani yace ban iyaba😣😚. lol)

🎸🎸🎶🎶BILKEESU zan faɗa dan ALLAH, mata ku bani dama duka. bilkisu gimbiya. BILKEESU mai gadon zinari waƙarki ta fita haka.🎸🎶🎶 BILKEESU sai gani sai nuni, kowa ya tabbata duka.🎸🎸🎸🎺🎺 BILKEESU gimbiya an baki, mata su dakata duka.🎸🎸🎺 BILKEESU sanya alƙyabar ki kaya mayalwata haka.🎸 Bilkisu gimbiya. BILKEESU za'a yiwa fada, ai mata fifita haka. 🎸 Jita kaja muje nai waƙar Bilkisu masu girma haka.🎸 Mata ku rausaya Ali jita nine na baku dama haka🎸🎶🎶 Komai yanada rana a gane dama tanada dama haka, Bilkisu gimbiya. Giwa ki rausaya BILKEESU ALLAH ya ƙara baiwa haka.🎸🎷🎷 Komai yaje ya dawo BILKEESU ku za'a tabbatarwa haka🎸 Ganga irin ta girma a miki waccan a mata garwa haka.🎸 BILKEESU za'a baiwa Number komai daren daɗewa duka Bilkisu gimbiya BILKEESU sannu mata irin na zamanin ɗebe kewa duka.🎸🎸 Kinsha aradu kinsha yasin, kin samu arziƙi duka.🎸🎷🎸🎷 Kin tsallakema tarkon maƙiya, ga ɗan abin biki haka.🎸 Kinzam sarauniya a cikin mata bar munafuka haka. Bilkisu gimbiya🎸 Ga zamani da daɗi wannan al'amarinkine duka🎸🎸🎸 Tsarki na zuciya bilkisu ya baki ɗaukaka haka. Kinsa kara a hanya BILKEESU wazata tsallakane🎸 Komai kina tunani Bilkisu baƙya abu daka haka🎸 Bilkisu gimbiya Ga ilimi da halin girma, ALLAH ya ɗaukaka haka.........🎸🎷🎸🎷🎸🎺🎺🎺🎺

(Kunema sauran kuji na gaji😂😜)

“Mawaƙin nan dolene yaci ƙyautar mota”. Oga Aliyu dake bayanmu shida matarsa ya faɗa yana ƴar dariya. Murmushi naga boss yayi a hankali lokacin da yake kama kafaɗuna yana zaunar da ni a ɗaya daga kujerar guda biyu da aka tanada danmu. Ni kaina waƙar tamin daɗi sosai, hakan ya sakani sakin murmushi da banyi niyyaba. Jay yaɗan lumshe idanu ya sake buɗewa a kanta sannan ya zauna a nashi mazaunin shima.

Babu ɓata lokaci aka fara gudanar da abinda ya tara mutane, an buɗe taro da addu'a kafin ai kiran Ummie tazo ta bada tarihin amarya a taƙaice, Hafiz ma ya bada tarihin ango tare da ɗorawa da shaƙiyancin randa suka fara gane Jawaad ya kamu da son amaryar tasa. Yanda yake faɗar wajen dole ya saka mutane dariya, masu baƙin ciki kuwa suka shiga zuba tsaki suna haɗiyar zuciya. Bily kanta sai da ta murmusa dukda tasan ba haka bane tunda ita

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull