Kenza eBookz

L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 33

L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 33

L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 33: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 33. "Me yasa kike da rawar kai har haka falaak?,yaushe ya…

3,370 words

"Me yasa kike da rawar kai har haka falaak?,yaushe ya zama yayanki?" Tayi maganar haka kawai tana jin furucin falaak din yana tabata. Bata wani damu ba,zuwa yanzu halayen akhnan din duka ba baqinta bane,sannan uwa uba tana sanya ran lokaci yayi da akhnan din zata sake janta a jiki,don zata tafi gidan aurenta ne,zata fara wata rayuwa ta daban ba wadda sukeyi ba a yanzu,dole komai zai canza.

"Tunda kina nuna min careless,na sani koshi zai daukeni a matsayin qanwarsa ta gaske,irin abinda na rasa a tare da ke" Sosai maganan ya ratsata,amma duk da haka saita dauke idanunta daga kan falaak din taci gaba da sanya takalmanta a hankali,kafin ta soma nufar qofa,birra buhaina bushira barratu bara'atu dama falaak suna biye da ita.

*HAISAM*

Yau din tun daga nesan nesa da gidan ya sanya salaana ya ajiyesu. Akwai nazari da yakeso ya sakeyi na unguwar duka dama anihin ginin katangun masarautar. Tare da maleek suke takawa,wanda dukkaninsu suna maqale ne da Bluetooth suna hira a tsakaninsu ta conference call din da suka hada da mutallab....khadeem....amjad.....naseeb. Duk da maganarsa qalilanne cikin hirar tasu,amma hakan bai hana masa jin dadin hirar ba,wadda ta gauraya da yanayin garin daya bada lullumi na hadari. Jikinsa har yanzu bayajin qwarinsa sam,amma kuma hakan dai bai kauda wannan jarumtar qarfin halin da qarfin zuciya da qawazucin dake tattare dashi ba.

Surutu ko dogon magana ba dabi'ar maleek bane,suna dan kamanceceniya ta wannan fannin,duk da wani lokaci maleek idan da zurfin sabo tsakaninku yana dogon hira,kamar dai a cikinsu su bakwai din,to amma yau tunda suka taho yake basu labarin agadez.

"Nan kusa zakuzo guys....don nikam har nayi farin kamu" Maganan yaja hankalin haisam,amma sai baice komai ba da wannan salon basarwar tasa,yayi kaman baiji ba,yaci gaba da takawa abinsa yana nazarin ginin katangar masarautar da suka fara cimmata.

Yanajin ihun khadeem,dan rud'u ne na gasken da kusan yafi kowa rudu a cikinsu,wannan ya sanya yafi kowa tara 'yammata.

"Me nakeji kana fadi maleek?,yau kuma an biyo ta kanka?" Idanu maleek ya lumshe yana shafa qirjinsa murmushi yana qwace masa.

"Wata princess tayi wuf da zuciyata daga shigowata......kuma bazan tsaya kallon ruwa ba kwado yayimin qafa.....zan zauna,zan jira mahaifinta ya dawo na nema aurenta da kaina Allah khadeem" Still haisam yaji maganan ta masa ba zata,duk da cewa yayi hasashen haka dama tun wancan ranar,amma kuma issues din da suka sakoshi a gaba ya sanya bai maida hankali ba akai.

"Amma mutumina.....ya akayi ka riga dan gari yin farinjini?" Naseeb ya fadi da alamun yana danne dariya qasan ranshi.

Sarai maleek yasan da waye yake,saiya saci kallon haisam sannan ya janye idanun nasa da sauri kafin ya masa wannan kallon nasa yana dariya qasa qasa.

"Ya qaryata zuciyarsa ne kawai.....ina kuma masa fatan kada nan gaba kadan na sake kiranku kuzo kuyi jinyar me ci......" Qit! Haisam ya yanke kiran gaba daya,kowannensu take wayarsa tayi disconnecting,abinda ya sanya kowa dariya a cikinsu daga shiyyar da yake. Sunsan halinsa,sunsan aikinsa ne,kuma shi daya yake iya musu wannan yankar qaunar idan hira batayi masa ba,don shi kadai ne a cikinsu ya karanci sanin ilimin sanin na'ura ciki da bai dinta.

Harara yadan watsawa maleek sannan yace

"Ashe dama ba don Allah ko zumunci kace zaka zauna ba?....."

"Ba haka bane captain......"

"Haka ne.....kuma zanga waye zai baka auren....badai falaak ba?" Hannu maleek ya dora saman qirjinsa yana marairaicewa haisam.

"Tsaf zaa maidawa motii ni unconscious.....a haka ma nayi kara ne ban tareta ba,inaso nabi komai bisa tsarin addini.....mahaifanta kafin ita" Kai haisam yake jinjinawa,ya sani dukkaninsu har yanzu ba wanda ya sauka daga kan tarbiyya mutunci kima da martabarsa,saidai isowarsu bakin babban qofar shiga masarautar ya sanya suka aje zancan a nan.

Duk wani hadimi dake bakin kowacce qofa da zai wuce zuwa hanyar ciki rusunamasa yakeyi cikin GIRMAMAWA. Irin girman da sultane ne kawai ya cancanceshi,abun har ya fara bawa maleek mamaki.

Su kansu wani jin dadin dawowarsa sukeyi,hakanan sukejin rashin karsashi na gabatar da aikinsu,da wani irin salam da gidan yayi musu a tafiyar da akace musu yayi na kwanakin.

Daidai sanda suka iso farfajiya ta biyu data hada sassa da dama na gidan,daidai lokacin da falaak ke takawa gefan akhnan tana mata magana qasa qasa.

"Kinyi kyau yaa biftu,kayan sun miki kyan da duk wanda ya kalleki yasan amarya ce". Wani abu taji ya sauka a qirjinta,taji kamar falaak ta qara sauke mata nauyi saman zuciyarta,abinda ya sanyata daga idanunta kenan ta saukewa falaak harara. Kan fuskarta idanunshi suka sauka,fararen idanunta dake dauke da blue din qwayar idanu da haskensu ya fita tsakiyar blue din sosai. SAK amarya saboda yanayin gown din dake jikinta wadda birra ke dage mata ita daga baya.

Wani harbawa zuciyarsa dake cikin qirjinsa yaji tayi,a hankali ya janye qwayar idanunsa daga kanta yana jin yadda zuciyarsa taci gaba da bugawa kadan kadan.

A lissafinsa yanzun ba lokaci bane a al'adarsu na kai amarya ba,baya kuma zaton hakan,don inda hakanne zai kasance tabbas sai an sanar dashi. Tunaninsa ya sake dawowa jikinsa.......WAYE ALMAZ bayan kasancewarsa wanda aka dauko daga gidan marayu na YATAAMA.....shin ya cancanci ya bari sultane da damqa gudan jininsa a hannun da yayi imani SHIRYAYYEN SHIRI ne da manufa da akeson cimmawa?.

"Zanji da wannan tabbas" Ya samu kansa da bawa kansa da kansa yaqini.

Damqo hannun maleek yayi sosai yana tsareshi da idanu.

"Ina zaka?"

"Ko sau daya ne ka bari nayi magana da ita mana" Maleek din ya fada cikin bawa haisam tabbaci akan abinda yake fadi. Idanunsa ya tsaurara akan fuskar maleek dim sannan ya girgiza kai.

"Ba inda zakaje yanzu maleek.....tana tare da matar mutane ne,matar aure ce a gefanta,ta yaya zakaga adon daba naka ba?". Sosai maleek ya tsare haisam da kallo,sai ya zame hannunsa daga cikin na haisam din,wata irin dariya tana qwace masa.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Meye naka na kishin matar wani?" Cak yaji maganar ta tsaya masa a rai,sannu a hankali ya dauke dubansa daga kan maleek,yaci gaba da takawa zuwa ciki kafin yace

"Saika dawo"

"Ba inda zani,na fasa nima,zanci gaba da daurewa har sultane ya qara so,na kuma nemi izini daga gareshi,hakan sai yafi kima a idanunshi". Maleek ya fadi yana bin bayansa,still murmushin dake kan fuskarsa bai bace ba.

*MAMMINA*

Murmushi ne kawai yake fita saman fuskarta kadan kadan,tana jin wani nishadi yana ratsata,tana kuma hangen nesanta tana dab da zuwa kusa.

Tana hangen ranakun dariyarta,ranakun walwalarta,da ranakun jin dadinta suna dab da riskarta.

Hankali kwance kuma cikin nutsuwa tayi zaune saman sofa,ta dora qafarta daya kan daya tana girgizata a hankali. Tana ji ne kamar an mata kyautar duniya da abinda yake cikinta. Tana jinta a wata sabuwar duniya sabuwar rayuwa da zatazo mata da FANSA akan dukka wanda ya taba yiwa rayuwarta katsalandan,ya kuma jefata a dawwamammen baqinciki.

Bata da wani haufi,bata kuma da wata sauran matsala akan masaniyar abinda yake gudana tsakanin akhnan da almaz,don ta zuba dukkanin mutanenta da zasu bata labarin koda motsa yatsa ne almaz ko shehnaz sukayi.

"Allah ya baki yawan rai.......tamim yanason ganawa dake,saidai dokoki da iyakoki basu bashi daman shigowa ba kamar yadda aka saba" Raliya daya daga cikin hadimanta kenan dake iya karbar aiki sanda yalwa ke nesa.

Wayarta dake hannu ta dakata da dannawa,ta xubawa raliya idanu. Har tsakiyar ranta da zuciyarta tana jin yadda wadannan dokokin suke caccakar ranta. Har cikin ruhinta tana jin zafin yadda suke sake karo da muradanta,suke kuma kawo mata rauni wajen samun dukkanin wani information da take da buqatar samu.

"Ya dakata a sansanun ganawa,zan fito yanzu" Ta amsawa raliya din. Cikin ranta tana jin ba normal abu bane ya sanya tamim nemanta a irin wannan lokacin ba,don haka ta miqe tsam tana gyara alkyabbarta.

*AKHNAN*

Dukkanin hadiman da suka mata rakiya dama wadanda ke gurin tuni sukayi biyayya suka tsaya bisa sahu da tsarin na umarni cikin salo na sarauta da akhnan ta basu. Akwai hadimai sosai a gurin,wadanda suka samu a gun suna aikin gyara shukokin gurin yankesu daidaitasu da kuma rage musu tsaho. Sai kuma nata data taho dasu wadanda suka yiwa kansu gurin tsaiwa nesa kadan da ita,ta yadda zasu iya ji da ganin komai dake gudana kamar yadda ta zabi hakan.

Idanunta fes akan fuskarsa,fuskar data gaza tantance bambancinta da wancan fuskar ta waccan ranar. Ci gaba tayi da takawa a qasaice tana duban idanunsa,idanun da bata iya hangen komai ta cikinsu. Shima ita yake kallo,ya kuma qureta da dukkan kallonsa daya quntata zuciyar akhnan,sannu a hankali ta hadiye wani abu me kama da bacin rai,tana zama hannun kujerar dake kusa da ita,ta tsani yawan kallo,ta tsani a zuba mata idanu,batason a fiya kallonta,wannan ya sanya kamar ya zama doka akan dukkan wani bawa ko hadimi da zai sanya idanunsa cikin nata.

Cikin izza ta motsa labbanta tana dubansa bayan tadan kalli agogo.

"Kazo a makare,ina faran zaka fadi duk abinda ke ranka akan lokaci,ina da abunyi a gaba me yawa" Sosai maganar ta sauka akan kunne da zuciyar almaz,maganganun tamim kuma suna dawo masa tarwai cikin kansa kamar lokacin yake gaya masa su.

"Bata da kunya,bata iya girmama kowa". Maganar kuwa ta motsashi,ya tashi ya zauna sosai yana dubanta duk kuwa da yadda yakejin kansa ya masa wani irin nauyi.

Idanunsa dake lullumshewa ya waresu kadan a kanta,ware idanun kuma daya sanya akhnan din taji wani abu kadan ya fusgeta,taci gaba da barin idanunta a kansa.

Tana da kyau da gaske ne,wani irin sassanyan kyau me burge idanun me kallo. Sabgar mata tana daya daga cikin sabgogin da basa cikin tsarinsa sam. Bai taba tarayya da kowacce diya mace ba ko soyayya,saboda kayan mayensa kadai sunfi masa kowacce mace a gurinsa. Amma baisan me yasa ya kasa jin komai a kanta ba,wani abu me kama da soyayya ko sha'awa sam baiji ya masa tasiri a rai ba.

"Ke!" Ya kirata a dan tsawace,abinda yayi matuqar saukarwa da akhnan mamaki ta daga kanta tana dubansa kai tsaye.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261 KO 08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 57*

"Haka ake girmama......miji.....ki shigo ki sameni amma.....ba zaki....ddurd.....durqusa ki gaidanai ba?" Yayi maganar jimlar tana tsintsinkewa yana hadata da qyar.

Wani zallar mamaki ne yaso kasheta daga zaunen. Mamakin farki na batun gaisuwar da yakeyi,dubansa takeyi da kyau tana son gasgata kunnenta ko kuma qaryatashi. Ita akhnan yakema batun ta durqusa ta gaidashi?. Bayan sultane ba wata halitta guda daya data samu wanna girma martaba da mutuncin.

"Kana da hankali kuwa?" Ta tambayeshi fushinta yana motsawa a hankali. Idanunsa ya fidda sosai a kanta.

"Ni kikeso ki kira da mahaukaci kai tsaye?...ina matsayin mijinki?" Ya fadi yana nuna qirjinsa da alama maganan ya masa zafi sosai data fadi din.

"Bana daukan raini fa......ina zaman zamana bazan dauki iskanci ba......ahhhht...m.toooo,auren banza auren wofi" Ya qarasa fada yana watsa hannayensa. Mamakinta sake ninkuwa yayi,ta sake zuba masa idanu tana qare masa kallo da gasken gaske. Wanne irin mutum ne mammina ta zaba mata?,akwai hankali cikin maganganunsa da nutsuwarsa kuwa?. Idan har idanunta sun gane mata da kyau ma kamar cikin yanayin maye yake maganar,idanunsa sun nuna mata haka,hakanan dukkan wani acting nasa da yakeyi. Fidda idanunsa sosai yayi waje yana son ganinta da kyau,don ta fara yi masa dishi dishi,so yake ya nuna mata da gaske shine sama da ita. So yake ta gane shine gaba da ita,bazai yarda da yadda take wulaqata kowa ba,yana jin haka a jikinsa cewar shi din ba wulaqantacce bane.

"Ni bana daukarrrrrr......raini kome za'a bani......zan iya babbbbbballlaki ko kece sarkin" Sosai zuciyarta tazo mata iya wuya,wannan narkakken bacin ran da ya dade cikin qirjinta da zuciyarta ta yunqoro mata.

Tsawa ta sakar masa tana bude dukka blue eyes dinta waje,ta miqe tsam tana dubansa sanda yake miqewa tsaye shima yana dafa daya daga cikin hadiman da mammina ta bashi fa suke koya masa abubuwan da zai saje da gidan sarauta sosai,tun zuwansu kuma yana tsaye daga gefan nasa saboda nuna girmamawa.

"Kabi a sannu,ka iya bakinka....koda kai din waye idan kayi kuskuren fadin wani abu mara kyau akan mahaifina zan sanya a batar dakai ne cikin agadez,za'a kuma shafe babinka,ba za'a sake jin labarinka ba" Tayi furucin tana nunashi da yatsa.

Wata dariya ya saki idanunsa suna jujjuyawa gami da shanyewa,girmansu yana raguwa sosai.

"Gimbiya ko?...." Ya fadi yana shammatarta,bata ankara ba ta tsinceshi dab da ita. Wani irin ja baya tayi da zafin naman da ita kanta batasan tana dashi ba. Ya sake zuba mata ido na wasu mintuna kafin ya saki wata irin dariya.

"Tsammani kike zan miki wani abu?,tab.....wannan ai ba matar aure bace...ni dama can ba damuna kukayi ba" Sai ya daga hannu yana nunata da yatsa gami da fara tafiya da baya da baya yana tangal tangal kamar zai zube a gurin

"Mara kunyar banza kawai....kije na sakeki.....na sakeki......na sakeki.....na sakeki....." Ya yita maimaitawa kaman wanda aka baiwa aikin ibada wata qaramar dariya kuma tana kubce masa.

Bai gaji da maimaitawa ba yana kuma yunqurin fita a gurin,yana jin kamar qasar tana juyawa dashi saboda wani irin mahaukacin nauyi da yaji kansa ya masa.

*HAISAM*

Kebantaccen dakinsa ya wuce kai tsaye yabar omar da maleek a sitting room din farko,idanunsa saman duka na'urorinsa,ya qarasa a hankali cikin qwarewa ya fara hadasu. Wasu irin qananun device ne da idan ka kallesu ba zaka dauka suna da wani alfanu ba,dauka zakayi abun wasan yara ne kawai idan ka dauke system qwaya daya dake gurin.

A nutse ya hada komai,connection ne tsakanin mutanensu dake aiki cikin gidan,location hudu,bakin babbar qofar shigowa gidan dame binta,sassan bangaren mammina,sai kuma babban kitchen na dafe dafe na gidan.

Green din haske ya kama,abinda yake alamta masa kowa yana kusa. Kujera yana yana shirin zama,wayarsa tayi blinking haske kadan,ya dakata kadan yana dubawa,sai yaga nanay ce,sai ya zauna saman kujerara nutse yana furta.

"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Dukka sassan hudu ya aikewa hold on sign,sannan ya katse kiran nanay yabi kiran nanay din. Bugu daya ta daga,abinda ke tabbatar masa tana bakin wayar tana jiransa,tana kuma qagauce ta gaya masa koma mene

"Muhammad" Ta kirashi da wani irin yanayi muryarta tana rawa,abinda ya sanya duk wani jijiyar jikinsa tayi relax. Da husky and deep voice dinnan mash ya kira sunanta.

"Nanay.....Tasgabbaa'i .(calm down).......of gadhiisuu(relax)nanay........ki fadamin a hankali" Ya furta da wani irin coolness,don tuni jikinsa da zuciyarsa sun gama gaya mishi sakamakon.

"tole(okay)" Nanay ta fada da wannan nutsuwartata me cike da dattijantaka da harshensa da ya riga ya narke cikin yaren oromo.

Idanunsa a lumshe,zuciyarsa na wani irin gudu yayin da zuciyarsa ke sauraron sautin muryar nanay dinsa. Yadda take masa bayani daki daki,muryarta na karyewa gami da yin rawa a gurare masu yawa.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Muhammad.......Nama tokko natti fakkaata,inaji a jikina mutum daya ce......zeenatun ajani itace zeenatun lamaan dina....aikin mutum daya ne muhammad wannan tabbas.....inajin shi yasanya na kasa daina mafarkin safiyyah ta.....shi yasa na kasa daina ganinta tsahon lokaci cikin mafarkaina.....safeena ina hangenta acan nesa dani,wani irin nesa da yake ban tsoro......ko ina da rabon sake ganinsu?" Nanay ta furta dukka dauriyarta tana yankewa,wani irin qauna irin na 'yan uwantaka yana ratsata.

"Nanay" Ya kirata da tausasawa

"Na'am muhammad" Ta kirashi da wani rauni sosai da me saurare ke iyaji cikin muryarta.

"Na miki alqawari,koda ban kawo miki safeena ba,koda ban hadaki da safeena ba,zan hadaki da safiyya" Wuta ta daukewa nanay,tunaninta yana yin nauyi.

"Muhammad......ta yaya?"

"Nanay karki tambaya,karki tambayi yaushe,karki tambayi ta yaya,amma wannan din alqawari ne na miki,koda shine abu na qarshe daya ragemin da zanyi cikin rayuwata" Yayi furucin yanajin abinda ya fada da gasken gaske har cikin zuciyarsa.

"Allah yayi maka albarka......addu'ata tana tare daku muddin numfashina"

"Ameen nanay" Ya amsa yana jin wani qwarin gwiwa yana ratsashi,sannan ya yanke kiran.

Dukkanin hankalinsa ya maida ya kuma tattara akan kiran da ya yiwa kowanne,ya danna madannin daya dawo da connection din daya hada da farko.

"Ina buqatar tashin gobara cikin darennan daga madafa......sannan tayi kaman zata taba sasssannin matan gidan nan......amma bana buqatar ayi asarar rai ko daya.....kafin sannan,abeer....." Ya kira sunansa yana duban signal din abeer din.

"Yes obbo"

"Ina buqatar analysis na dukkan abinda ya halaka cikin gobarar bayan komai ya kammala,ina buqatar kuma a siya komai a maidashi muhallinsa kamar komai bai faru ba,koda tsintsiya banaso wani yayi asara"

"An gama obbo" Abeer ya amsa cikin matuqar girmamawa. Kai haisam din ya jinjina yana duban lafiyayyen agogon Rolex me tsadar gaske dake daure a tsintsiyar hannunsa

"Ina buqatar ta fara qarfr biyu na dare,banaso kuma ta haura awa biyu ayi a gamata" Ya qarasa fada yana sauke agogon daga fuskarsa gami da janye manyan idanun nan nasa da suka rusuna sosai.

"Vous pouvez reprendre votre travail(zaku iya komawa bakin aikinku)" Ya fadi cikin harshen faransanci daya sanya kowa ya koya qarfi da yaji cikin qanqanin lokaci.

Window din da iska ke kada curtains dinsa a hankali yake kalla,yanajin wani yaqini da qarfin gwiwa a tattare dashi,yana jin a yau abinda zai shiga tsakaninsa da shiga dakin ajiyar mammina shine fitar numfashi daga gangar jikinsa.

*MAMMINA*

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261 KO 08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 58*

*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________

Dukkanin wanda yake a muhallin.....kunnuwansa kuma suna iya dauko masa jirkitaccen sautin dake fita daga bakin almaz sai daya rasa numfashinsa na wadansu daqiqu. Da yawansu da qyar suka iya controlling iskar da suke shaqa cikin hunhunsu wadda take iya sarrafa komai na jikinsu yake aiki daidai.

Ba akhnan ba da jinta da ganinta ya dakata na wucin gadi ba......hatta da birra ji tayi a lokacin kamar idan aka tsaga jikinta ba za'a samu jini ba.

Da wani irin kallo da batasan wanne iri bane.....da wani irin yanayi da take jin kamar gangar jikinta bata tare da ita.....da wani irin yanayi data gaza bambance wanne iri ne take duban hanyar da almaz yabi ya wuce,hadimansa na biye dashi ba tare da kowa a cikinsu ya iya cewa komai dashi ko da ita ba.

A hankali ta daga hannunta tana shafa fuskarta zuwa kafadarta,tanason taji idan idanunta biyu ne,tanason taji idan da gaske ne.....itace akhnan,idanu biyu take tsaye da qafafunta ba cikin bacci ba,ba kuma cikin mafarki ba.

Itace hamshaqiyar GIMBIYAR QASAR AGADEZ itace d'a namiji a yau ya tsaya gabanta kansa tsaye yake furta ya saketa. Ya saketa a gaban BAYI ya saketa a gaban HADIMAN da suke bauta a garesu. Ya saketa ba tare da damuwa ba,ya saketa yana me juyawa ya kuma fice abinsa hankali kwance.

Idanunta ta daga a hankali tana saukewa saman fuskar kowanne hadimi. Kowa yana tsaye a muhallinsa ba tare da qwaqwaqwaran motsi ba. Ba wanda yake iya daga koda yatsarsa guda daya a cikinsu. Saidai hakan tasan bawai yana nufin basuji komai ba.....hakan bawai yana nufin komai bai faru ba,hakan kuma bawai yana nufin komai zai canza daga muhallinsa zuwa inda yake ba.

SAKI UKU?,CIKIN KWANA UKU KACAL?,taji wani sashe na zuciyarsa yana jaddada tambayarsa a gareta,tambayar da batasan ita dince ko zuciyartata bane zasu baiwa kanta da kanta amsa ba.

Wanne irin aure mammina tayi mata?,ta samu kanta da tambayar kanta.

Readers Also Read

More by Huguma