L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 32
L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 32: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 32. "Ina sake jin tsoro akan abinfa na aikata domin jin…
3,327 words
"Ina sake jin tsoro akan abinfa na aikata domin jin dadinki akhnan,kamar ba za'a dauki tsahon lokaci ba zaki nunawa duniya ko ki gaya mata da bakinki cewa almaz ba zabinki bane".
Wani yanayi ne a fuskar mammina da yake nunawa akhnan raunin mammina da fargabar tata da gaske,sai takejin idan tayi mata hakan bata kyauta ba,bayan da qyar tasha kanta ta aminta ta zaba mata mijin auren don kubutar da ita daga fushin sultane.....bata cancanci wannan sakamakon ba,ita ta maidata cikin damuwar data kubuta ba.
"Na amince zan gana dashi,saidai ba'a wani kebantaccen guri ba......ba cikin wani kebantaccen daki ko muhalli ba,zan ganshi cikin lambu na.....zagaye da hadimai da suka saba aiki a gurin,da kuma nawa hadiman da suka saba yimin rakiya" Can qasan zuciyar mammina murmushi ne ya subuce mata. Dukkan wani tsari,dukkan wani karatu da zuciyar akhnan keyi ta gama baje lissafinsa. Kai take jinjinawa a hankali,tanason gujewa qaddararta ne.....qaddarar da ita ta riga data sani ba makawa saita sameta a kurkusa ma.....saita tilastata mallakawa almaz wannana abun....wannan tutiyar wannan alfaharin.....wannan taqamar.....mallakawar kuma zata zama matakin farko ne,zataci gaba da mallaka masa ba tare data sani ba,har xuwa lokacin da adadin data shatawa qaddararsu kan ta TSAYA!.
"Na gode da fahimtata da kikayi.....na gode da biyayyarki a gareni,zanci gaba da zama UWA wadda zata tsaya akan matsalolin d'iyarta. Duk qunci duk wuya. Duk tsanani,zanci gaba da tsaiwa dake a kowanne mataki ko rukuni na rayuwa har abada" Saita matsa a hankali tana rungume akhnan cikin jikinta,duk da yadda zuciyarta ke qyamtar hakan,gangar jikin keji tamkar tana hada gangar jikin nata ne dana safeena,kamar tana nutsa ruhinta tsakiyar abokan adawa masu tarin yawa.
Ta gefan akhnan ajiyar zuciya take saukewa,duk sanda mammina rungumeta saita ji kamar qarshen kowacce matsalarta ne yazo,tana jin wani sassauci a tare da ita,saidai still batasan me yasa wannan EMPTINESS din da takeji a ruhinta har yanzu ba wani abu da taji ya cike GURBINSA ba.
*NANAY*
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
A hankali ta shafa addu'ar data kammala bayan sallar walaha tana sauke idanunta akan saamee dake shigowa dauke da turaren wuta kamar kullum.
Tausayin yarinyar ya sake tsargawa nanay,zuwa yanzu tana jin yadda kwanakin ke qara nisa,haisam da take sanyan ran hankalinsa zai kawo kanta yayi musu nisan da basu dauka zaikai har haka ba. A hankali take karantar yanayinta,kamar ta soma sarewa,kamar ta soma cire rai daga dukkan zato da kuma tsammaninta.
Zuwa yanzu a wannan gabar kuma tana jin anya ba zata shiga maganar ba ko yaya ne?,anya ba zatayi wani yunquri ba don samawa marainiyar cikakkiyar nutsuwa da makoma mai inganci.
"Saamee" Nanay ta kirata a hankali.
"Na'am" Ta amsawa nanay din tana waiwayowa,saidai kuma tana gujewa hada idanu da ita.
"Zo nan ki bani aron wayarki in kira obbo dinku". Wani faduwar gaba tayi daga kiran sunansa kawai,yayin da nanay dake karantarta a nutse ta fahimci sauyawar yanayinta daga sanda ta kira sunansa.
A hankali take takowa zuwa ga nanay,tana kuma zuba numbers dinsa dake haddace a kanta,duk da cewa tayi saving nata a rubuce. Nanay ta zubawa hannunta idanu,tana rubuta number dinne da sauri sannan still hannunta yana rawa har sanda ta qaraso gabanta,ta tsugunna ta miqa mata wayar,nanay ta sanya hannu ta karba tana mata kuma alama data zauna.
Duban screen din wayar tayi,sunan data masa saving dashi kaman sauran yadda 'yan uwansa suke masa ne,sai ta zare idanunta tana maidawa kan saamee wadda tayi qasa da idanunta.
*HAISAM*
Kacokam ya aza idanunsa akan qunshin bayanan daya kammala tattarawa,tun daga safiyar yau zuwa yanzu yammacin ranar litinin. Abu biyu yake dagashi daga gurin sallah sai kuma dauko coffee,don ba wanda ya bawa daman shigowa dakin kwata kwata a yinin ranar.
Daidai da wayoyinsa dukka a kashe suke,sai bayan sallar la'asar dinnan ya kunnasu don ya kira masarauta yaji yanayin da ake ciki,ya kammala wayar kuma ya barta a silent don baya buqatar wani disturbance.
Wani irin kullewa kanshi yakeyi da yadda lissafinsa da bayanan daya tattara gaba daya da bincikensa suke kaishi da direction daya. Ya sanya mutane da yawa a sahu sahu saidai duk inda ya fara bin salsalar zaren kan mutum daya suke kaishi ZAITUNA/ZEENATU/MAMMINA daya gama imanin mutum daya ne da suna uku......mutum daya ne cikin gangar jiki uku.....mutum daya ne da aikin mutum uku.
"Rabbi yassir wala'ta'asir wa tammin bilkhair" Abinda ya dinga maimaitawa kenan yana zubawa allon system din idanu kaman iya aikin da aka aikoshi a yau yayi kenan cikin duniya. Idanunsa da suka nuna gajiya a fili ya janye yana maidawa saman wayarsa dake ringing,sunan nanay ne,kiran da yake jira tun kwanaki uku da suka shude,saidai yanayin rashin lafiya da kwashe wayoyin da omar yayi masa yasa dole ya daga qafa.
Jawo wayar yayi,ya yanke kiran kamar yadda ya saba sannan yabi bayan kiran. Tana ringing ya sakata a handsfree ya maida bayansa jikin kujera yayi relaxing yana jin yadda qwaqwalarsa ke ninka aikinta da wani irin gudu da sauri daya wuce iyaka,har yanajin ciwon kansa kamar yana shirin motsawa,sai ya sanya hannun nasa ya dafe kansa a hankali yana lumshe manyan idanunsa da a yau suka dan canza launi kadan.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 55*
Sallamar nanay dinne ta sanyashi bude idanunsa a hankali yana amsa sallamar gami da bude idanunshi. A nutse nanay ta miqawa saamee wayar sannan ta yunqura a hankali tana fadin
"Ki sameni a parlor idan kin gama". Kanta a qasa tana jin takun ficewar nanay din,sai ta koma ta zauna sosai saman carpet tana jin qafafunta kamar ba zasu iya daukarta ba.
Muryar nanay yake jiran sake ji,sai yaji muryar saamee ta maye gurbinta da sallamar nan tata cikin yanayinta me sanyi.
Numfashi ya aje a hankali yana amsa mata sallamar,husky voice dinnan nashi ya ratsata ya shiga kunnenta yana motsa wani abu dake boye can saqon zuciyarta.
"akkam jirta obbo(barka da warhaka,kana lafiya yaaya)" Ta fadi a hankali tana ganin kamar xai iya jiyo bugun zuciyarta daga nan inda take zaune.
"Ani gaarii dha,akkamitti?(lafiya nake,kefa?) Ya tambayeta tana qoqarin kwatanta kyautatawa a gareta kamar yadda yasan tana qoqarin yin hakan ga nanay dinsa.
"Alhamdulillah" Ta amsa duk wani sauran magana kuma yana dauke mata gami da tsaya mata a maqogaronta. Wani irin kwarjini yake mata koda a bayan idanunta ne,ta jima da sanin shi din wani irin namiji ne daban da sai zallar sa'a zata sanya mace ta samu damar mallakarsa.
"Makaranta fa?" Yayi qoqarin tambaya don kada ta dauka ya wofantar da qoqarinta.
"Komai lafiya alhamdulillah" Ta furta a hankali,har qasan ranta tana son tambayarsa sai yaushe zai shigo jimma?....don tayi wata muguwar kewarsa,amma takejin ba zata iya ba.
"Ma sha Allah,Allah ya taimaka,nanay fa?"
"Zan kai mata yanzun" Ta fadi a sanyaye,tana sanya rai ne hirarsu ta zarta haka,tana sanya ran maganarsu ta wuce haka,amma sai gashi da wurwuri ya gajarta maganar.
A nutse ta miqawa Nanay sannan ta taka tana fita a parlor din. Nanay ta bita da kallo sanda take sanya wayar a kunnenta.
"Barka da warhaka nanay"
"Barka kade muhammad.....fatan ka yini cikin aminci"
"Alhamdulillah nanay.....komai da kowa lafiya?"
"Lafiya Muhammad,inata tunaninka omar yace wani aikin daban ka shiga,shi ya sanya ba'a samunka" Idanunsa ya lumshe a hankali yana gyada kai,cikin ransa yana jin dadin yadda omar ya boyewa nanay rashin lafiyarsa.
"Na fito alhamdulillah nanay.....ko kin samu sunan abokiyar zaman Obbolettii n ki?" Kai ta gyada a hankali.
"Eh muhammad.....na samu amma da qyar,na rubuta don kada na manta,duk da nasan mantuw tayi kadan ta goge sunan azzalumin mutum irinta a kaina....."
"Meye sunan nanay?" Ya tambaya cikin tattarawa Nanay hankalinsa.
"ZEENATU" Wuta ce ta daukewa haisam na wasu daqiqu,kafin a hankali wani murmushi me cike da madaukakin mamaki ya mamayeshi. Zeenatu a Ethiopia......zaituna a agadez? Ya tambayi kansa da kansa yana kuma sake jinjina kansa.
"Matar ajani da ake zargi ZEENATU.......matar data fidda Obbolettii (sister) dinki daga gidanta ZEENATU.....ba wani alaqa tsakanin mutanen nan biyu?". Dif wuta ta daukewa nanay,tunaninta yana yin zurfi da kuma nisa.
" Ajani ya taba aure shima!.....na shekara daya muhammad kamar yadda safeenata tayi!!" Nanay ta fuusgi kalaman cikin wani irin rudani.
"Good nanay......zan iya samun wani abu game da rayuwar gidan ajani.....kaman ta hannun uwargidansa?"
"Ta rasu muhammad.....sati daya da suka wuce.....amma,bari na kira safuura" Nanay ta fadi tana yanke kiran. Ko ina na jikinta kyarma yakeyi,tanaji jikinta kamar taga Obbolettii dinta har guda biyu,tana jin kamar an gano ind sisters dinta suke,tanajin kamar an gano bakin zaren ne.
Kai kawai haisam yake juyawa a hankali,maimakon bacin rai ya mamayi fuskar nan tasa ma'abociyar Kwarjini,kawai sai wani qaramin murmushi ne yake fita a fuskarsa. Ganin komai yake tarwai.....kowanne lissafi nasa da yake sarqewa a baya a yanzun ya fara zuwa masa da warwara......yan hangen komai kamar an saka rariya ana taceshi.
Hujja daya tak yake nema da zata sake bashi tabbaci itace MATAR AJANI......hujja daya tak da yakejin a yanzu ya shirya shiga kowanne sashe kowanne lungu na masarautar agadez don ya fiddo ta. Idan ya tabbata INA MAKASHIN?.....waye wanda ya aikata kisan da shima yayi batan dabo?. Ta yaya lokaci bayan lokaci suke iya aiwatar da bazaranarsu ga motii aba jifar?,ta yaya?,su waye rassansu?,su waye mataimakansu?.
Yatsunsa kawai yake murzawa a hankali yana sake baje sabon lissafi. Kebantaccen dakin ajiyar mammina.....shi kadai ne abinda ke masa yawo a ransa da kansa....kebantaccen dakin da jikinsa ya bashi tabbacin lallai akwai BOYAYYUN SIRRIKA. TAMIM har guda biyu dake da alhakin kula dashi,da masu jin yaren oromo da yake da lissafin sunayensu yanzu haka fes dama fuskokinsu gaba daya!..
Turqashi......ya zuwa yanzu nasan me karatu yana tunanin KOMAI YAZO QARSHE......QARYA TA GAMA QAREWA......GASKIYA KUMA TA GAMA BAYYANA......SAIDAI NACE KUXO MUJE
MAJI MA GANI
Maleek ne ya shigo a nutse bayansa daya daga cikin hadiman haisam ne. Dauke da wani kyakkyawan royal tray da aka jera masa qananun bowls masu kyau.
Idanunsa ya zare ya maida kan maleek,shima maleek din shi yake kalla.
"Ina fata wannan aikin ya kammalu?" Tashi haisam din yayi ya zauna sosai yana duban maleek sanda hadimin ya ajiye abinda ke hannunsa yana fita.
"Yadai kusa......inaso na shiga masarauta,yau zanyi kwana uku ko biyu kuma kafin na fito.....ka kira likitan nan yazo ya ciremin wannan abun" Ya fadi yana daga hannunsa dake dauke da Canular.
Kai maleek ya girgiza yana zama saman sofa.
"Amma kasan akwai ragowan drip da zaka sake sha?"
"Ya isheni haka maleek,ina buqatar kammala wani abu dole.....inaso na gama komai qasa da sati daya". Ya amsa masa yana yarfar da hannun nasa,don har yadan fara tasawa saboda zaman allurar na kwanaki a jikinsa.
"Okay " Ya fadi yana lalubar wayarsa don kiran hadiminsa da suke agadez din tare.
*TAMIM*
A nutse ya miqawa almaz alkyabbar data zama sutura ta qarshe da zai sanya a jikinsa,bayan tarin kayan ado da qawar daya fara sanyawa a jikinsa na tsadaddar suturar ALHARIR.
Shi kansa tamim din a yau yana hangen wani irin kyau da biyayya da suturar tayi a jikin almaz din,tamkar dai dama ya saba da ire iren wadannan tufafin a jikinsa. Duk da haka ba abinda ya rage qudirinsa a zuciyarsa,ba abinda ya rage kaifin abinda yakeji a zuciyarsa.....hakanan ba abinda ya sauya daga aikata abinda yayi niyyar aikatawar.
A nutse almaz ya taka cikin wani salon izza da yaji ya saukar masa,ya matsa gaban tamfatsetsen madubin dake ajiye a wani bangare na daban na dakin.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Duban kansa yakeyi cikin madubin,yana jin wani izza tana shigarsa. Tsahon rayuwarsa bai taba ganin inda yayi kyau har haka ba,koda sau daya kuwa,duk da cewa yana rayuwa cikin sutura me kyau da kuma cima me kyau,amma ba sutura irin wannan ba....ba tufafi irin wannan ba me cike da nuna qarfin izzar wanda ya sanyasu. Sosai yakeji kansa yana sake shiga charge,abinda ya qara fadada nishadin da yakeji kenan,don tun daga daren jiya ya baje dukkan kayan mayensa da aka dakatar dashi daga sha,yasha me isarsa,ya kuma dora da wani da safen nan bayan wadancan sun sakeshi. Yana jin wani banbanci da wadannan kayan da wadanda ya saba sha. Wadannan din masu taada ne sosai data sanya aka tanadar masa kwali kwali kawai don jin dadinsa,ta kuma yi masa alqawari daman,ta kuma cika,abinda ya sake saka masa nutsuwa da bin dukkan sharudda da qa'idojinta. Basa sakashi yayi mankas ya manta da abinda yakeyi,amma suna fiddashi daga duniyarsa,suna kuma fitar dashi daga ainihin duniyar da yake rayuwa a cikin ta,suna sakashi ya jishi daidai yake da kowa,yana kuma daidai da tarar kowa da komai.
Waiwayowa yayi yana murmushi yana duba tamim,abinda ya sanya tamim dauke kansa daga mummunan kallon da yakewa almaz din,kallon dake cike da hassada qyashi kishi da baqinciki.
"Wai nine almaz a haka?.....nine na mallaki matar aure d'iya mafi girman daraja a yankin africa......gida irin wanda nake mafarki da rayuwa cikin izza mulki da qasaita.......amma kasan meye tamim?" Yayi tambayar yana duban fuskarsa yana kuma takowa zuwa gaban tamim din. Qoqarin gaske tamim yayi wajen maye murmushi saman fuskarsa.
"Na rasa wanne dalili ne ya sanya uwargijiyarka ta zaboni a cikin tarin matasan qasar Ethiopia.....a baya nayi tunanin don tana mahaifiyata ne,amma a yanzu tunanina ya gagara cafko komai" Almaz yayi maganar da tarin mamakin dake ransa daya bayyana cikin muryarsa.
Murmushi tamim ya saki,yana takawa a hankali gaban wani babban glass cup daya cikashi da tataccen lemon inibi wanda ya cakudashi da sinadarai daban daban.
"Kaidai ungo wannan kasha mu tafi.....yanzu ba lokaci bane na tunanin wannan.....tunda harka yadda ka shiga cikin masu sa'a ai shikenan,ba abinda ya rage maka saika zuba idanu kaci gaba da irgen lokutan sa'arka". Dan shuru almaz din yayi,kafin kuma ya saki murmushi yana miqa hannunsa ya karbi lemon hannun tamim din.
"Inason lemon nan sosai,inajin dadinsa" Ya furta a hankali sannna kuma yakai cup din bakinsa.
Tas ya shanye lemon a kurba daya,sannan ya miqawa tamim cup din yana cewa.
"Kamar zai bani freshness din da nakeso,na gode tamim" Ya damqa masa cup din yana juyawa. Da wani kalar shu'umin murmushi yabi almaz din,rabin aikinsa ya kammala saura rabi,yana duban takunsa da yakeyi cikin wani yanayi daya bayyanar da b'urbushin qasaita.
"Matsiyaci ya samu guri,wai har ya iya yanayi na masu mulki da saruta" Ya fada a fili can qasa yana jifan hanyar da almaz yabi da harara.
Jerin gwanon motocin alfarmar guda shida ne cass suka takewa motor din da almaz ke ciki baya. Ya saki wani irin murmushi sanda dukkan wani hadi dake cikin lemon ya fara zagaya sassan jikinsa,ya kuma soma jinsa a sama,uwa uba yadda yaga manyan motocin alfarma irin wannan na take masa baya sai ya sake sanya yanayin yabi jikinsa sosai
"Shege almaz,yau shine kamar gomna?" Ya tambayi kansa da kansa yana dariya. Sam a rayuwarsa ya rayu cikin wani madaukakin yanayi ba burinsa bane,damuwarsa daya shine ya rayu cikin 'YANCI. Bayason UMARNI,yafison ya rayu cikin sakewa da kuma zabawa kansa duk kalar rayuwar da yakeso,ba tare da an bashi umarni ba,ba tare da an sanyashi ko an hanashi ba. Ya sani......yanajin wata izza da girma a cikin jininsa da baisan wacce iri bace,wannan ya sanya sau tari yafi zabar kebance kansa tare da qin amincewa ya shiga taron jama'a.
Duba daya tamim yayi masa ya tabbatar ya fara fita daga hayyacinsa,ya fara buguwa,sai ya gyara zamansa sosai yana dubansa.
"Kasan meye almaz?" Kai ya girgiza yana duban tamim da idanun nan nasa da tamim din yake ganin suna masa kama da wasu idanu.
"Akhnan matarka.....tana da tsananin girman kai....bata girmamawa kowa saboda tana ganin mahaifinta shine sarki a wannan yankin....."
"Ashe?" Almaz ya fadi da wata irin murya yana bude idanunsa da kyau. Kai tamim ya jinjina cikin bashi tabbaci da son isar da saqonshi
"Qwarai da gaske.....kai baka lura ba?,a matsayinka na namiji kuma mijin dake aurenta.....ta taba gaidaka?,kota taba zuwa gurinka nemanka?,kota taba nemanka din koda a waya ne?" Shuru almaz yayi,wasu abubuwa suna cakudewa cikin kansa tsakanin maganganun tamim da kuma abinda tamim din ya bashi yasha. Gefe daya wata izza tana huruwa cikin ransa,yana jin kansa yana girma da fadi.
"Ba ko daya" Almaz ya fada muryarsa tana kaduwa da wani irin yanayi na wanda ya fara buguwa.
"Ahto....to kai kuma saika bari aci gaba da tafiya a haka?"
"Inaaaa......daga yau zan fara nuna mata ina da iko a kanta" Ya fada yana ji a ransa dole ya zama tsayayyen namiji.
A hankali tamim ke buda masa wasu abubuwa,yana kuma sake karanta masa abubuwan da ya tabbatar zasuyi tsananin tasiri a kansa game da akhnan din. So samu komai ya fada jagule musu a yau,shi yasa ya fara da horashi da kadan daga cikin kayan mayen dana tanada,wanda wannan shine zai bashi damar dorawa kan tsarinsa d'od'ar ba tare da sunansa ko alamar ayar tambaya ta hau kansa ba.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 56*
Yanaji a ransa,daga sanda auren almaz ya sauka daga kan akhnan,daga sannan zaiyi dukkan me yuwuwa don ganin ya mallaketa,koda meye zai faru a shirye yake,idan ta kama ma yana jin cewa a shirye yake ya dauketa cancankat ya rabata da ganin kowa ya kaita wata duniya ta daban,inda zai samu damar mallakarta ba tare da wani tarnaqi ba.
*AKHNAN*
Tana tsaye ne kawai tana jin yadda birra ke shiryata cikin wasu qawatattun kaya na alfarma da mammina ta aiko dasu. Iya akwatin da aka sanya kayan kawai abun kallo ne ballantana akai ga kyansa da kuma tsadar da suke da shi. Tana ji ne kamar ta sanya hannu ta ciro zuciyarta daga qirjinta,tana jin wani irin qunci da suya da zuciyarta takeyi kamar zata babbake.
Maganganun mammina kawai suke bata dauriya da qwarin gwiwa.....addu'ar da sultane ya kirata jiya yayi mata wadda ta bata tabbacin ya huce da ita.....yana kuma dab da maidata BIFTU dinsa kamar yadda take a baya,su kadai ne abinda suka sanya take iya tsaiwa da qafafunta a yanzu haka. To amma yaya rayuwar zata kasance?,ta yaya zata iya carrying identity na matar aure da mutumin da shi da ZERO daya suke a wajenta.
"An kammala ranki ya dade" Birra ta fadi cikin tsananin girmamawa tana komawa baya. Batako waiwaya ta kalli kanta a madubi ba kamar yadda ta saba ba ta fara matsawa inda birra ta ajiye mata takalmanta ta fara zurawa.
Falaak ce tayi sallama a nutse tana shigowa,fuskarta qunshe da murmushi tana duban akhnan din. Ita kanta idan ta kalli akhnan.....ta tuna a yanzu tana amsa sunan matar aure ne saita dinga jin abun wani abu na daban. Wani al'amari ne da dukkaninsu basu kawo wanzuwarsa a kusa ba.
"Ya biftu" Ta qaraso gabanta tayi kiranta da yanayin kira irin na tsakanin qanwa da yayarta.
Kyawawan blue eyes dinta da kwallin da birra ta zizara mata ya qara yiwa kyau ta daga ta dubeta.
"Yayanmu ya qaraso.....zan iya shiga sahun 'yan rakiya?" Ta tambaya tana dage dukka girarta sama.
"Yayanmu?" Ta maimaita sunan cikin kanta,saita ware idanunta akan falaak