Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 12

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 12

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 12: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 12. Bashi kadai ba......ita kanta taji.....taji reaction na…

3,320 words

Bashi kadai ba......ita kanta taji.....taji reaction na jikinsa,saidai tsoron daya saukar mata itama ya sanya bata fahimci komai ba,sai daukewar da numfashinta yayi na daqiqu.

Komawa yayi ya zauna sosai saman seat dinsa yana qoqarin saita nutsuwarsa. Idanunsa sukayi laushi sosai lissafin abubuwa yana cika kansa. Ya sani.....akwai manufar aurenta. TARKO.....tarko ne ga mammina da zuwa yanzu ya kammala da babinta......zuwan wa'adin fashewar nakiyoyin daya dasa kadai yake jira. Nakiyoyin da ya sani......da kanta zata sanya abu me qarfi ta dinga fashesu daya bayan daya.....a yanzun a qulle take cikin wani irin dabaibayi sasari dama sarqoqin da ita kanta bata sani ba.......to amma wannan auren fa?.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 21*

"YA DAURU.....NA DINDINDIN NE!" Daga can wani sashe na zuciyarsa ya bashi amsa. Bai sani ba,amma ya jima yana hasashe. Tabbas akwai qaddarorin da muke saqasu da farko,amma qarshensu saisu qwace daga sarrafawarmu su shiga saqa kansu da kansu.......ko wannan shiryayyar qaddarar zata qwace daga hannunsa ne?......ta fara saqa kanta da kanta?.

Tunaninsa ya yanke sanda ya soma jin wani abu......wani abu kaman sheshsheqar kuka can qasa,sheshsheqar da ake boyeta ba tare da buqatar kowa ya jita ba. Saidai shi din na dabanne,yana da wani irin kakkaifan ji,wanda zaiyi wahala kayi magana komai qanqantarta ba tare da yajika ba.

Sanda idanunta ke kallon yadda jirginsu yakeyin nisa da niger.......yakeyin nisa da qasar Niamey gaba daya,sai takejin kamar tanayin wani nisa ne na har abada. Kamar tana barin niger ne bari na har abada,kamar akwai nisa da sultane zaiyi mata nisa na har abada. Kamar zata barshi ne na har abada.....shima zai barta bari na har abada din. Sai taji gaba daya zuciyarta ta karye,sai taji kaman tana da buqatar wani a kusa da ita,wanin da zatayi kuka sosai a sake a gabansa kamar sultane. Ba gaban kowa take kuka ba......ba kowa yake ganin hawayenta ba idan ka debe mutum biyun,sultane da mammina,saidai a yanzun sultane kadai take dashi wanda zatayi kuka a gabansa ta more,a ina zata samu madadi?,ta qarashe da tambayarta mara amsa.

A hankali taji lallausan tafin hannun nan nasa yana kutsawa zuwa cikin nata......a hankali da wani irin yanayi ta tafiyar maciji taji yana kutsa yatsunsa biyar tsakiyar nasa yanzun.......a hankali kuma taji ya game hannuwansu guri daya yadan matse cikin nasa ta yadda suka fara musayar dumin hannuwan juna.

Wani irin shuru.....shuru me cakude da nutsuwa shine abinda ya wanxu a tsakaninsu,shine abinda ya mamaye jirgin iyakar inda suke.

Duk da kukan bai tsaya ba,amma wani irin sassauci takeji yana sauka a hankali cikin zuciyarta. Wani irin sanyi da ya sanya hatta da hawayen dake fita daga cikin idanunta suke fita da wani irin sanyi. Lokaci lokaci tana jin yadda yake dan matsa hannunta dake cikin nasa,kamar dai yanason yayi magana ne,kaman dai lallashinta yakeyi ta hanyar motsa yatsunsu dake guri daya da dan matsasu kadan.

Tsahon wasu mintuna,kafin a hankali wannan muryar tasa me laushi da zurfi ta motsa a hankali zuwa cikin kunnenta,cikin yarenta,cikin harshen faransanci da wannnan accent din nasa dake bugar da ita,yake sake saka mata jin tsananin dadin yaren French wanda a baya batasan yana dashi ba sai a bakinsa

"Kiyi kuka idan kinaso,ba rauni bane......amma bame cutarwa ba" Sai taji kalaman sun sauka a kunnuwanta da wani irin banbanci me yawan gaske. Maimakon kuma kukan yaci gaba,a hankali sai taji hawayen suna raguwa suna ja baya da kansu. Yaji komai,duk da baya ganin fuskarta amma yaji yadda ta soma daidaita kanta,yana jin nauyin wannan amanar dake saman kansa......yana kuma fatan ya sauketa har zuwa sanda Allah zaiyi ikonsa cikin lamarinsu gaba daya shi da ita.

“Wani lokaci… dole ne mutum ya bar wuri… domin ya gano inda ya kamata ya kasance.” yayi maganar da nazari masu yawa cikin magananunsa,wanda ya sani,a wannan lokaci ba lallai bane ta fahimci ma'anonin maganarsa ba.

Sosai maganan ya tsaya mata a rai,amma kuma ta gaza sarrafa maganar cikin ranta. Tana jin sanda ya zame tattausan tafin hannunsa daga cikin nata,sai taji yatsunta suna motsi a hankali.....suna motsawa kaman suna shirin riqe nasa yatsun da suke dab da ficewa daga cikin nata.

"Ungo" Ya fada a hankali yana ajiye mata tissue. A hankali ta juyo da fuskar ta don ganin me yake miqa matan,kai tsaye idanunta suka zarce kan fuskarsa suka fada cikin idanunsa.

Ita yake kalla da wadannan idanun da har abada suke tuna mata wadancan ranakun na farko. Wani lokaci idan ta motsa labbanta,sai taji tanason tambayarsa.

"Kaine wannan mutumin?,na wancan ranar daya fara sanyawa na zama mara nasara karo na farko a rayuwata?." Saidai kuma kwarjininsa da izzarta suna cakuduwa su tayar da alfaharinta na diya mace,kaman yanzu saita zare idanunta daga kansa sanda ta fahimci shima ya dauke kansa daga gareta.

"Assalamu alaikum sir....akwai abinda kake buqata?" Ta sake jin muryar wannan matashiyar crew din. Wani abu ta shaqa sosai cikin hancinta,ya kuma tsaye mata a qirjinta cak kaman tsaiwar mashi.

"Me kuma take nema?" Taji tambayar ta zarta cikin kanta. Kadan ta matse yatsunta tanason kauda hankalinta akan komai ma,don batasan abinda yake jan hankalinta ba ga duk motsi da maganan da yarinyar zatayi masa ba.

Ba tare daya amsa mata ba,ya juya kansa a hankali zuwa sashen da take.

"Kina buqatar wani abu?" Ya tambayeta da wani irin softness da yaren French din nan nasa da kullum xai magana dashi sai taji kamar nasa yaran daban yake da wanda ta saba ji. Kai kawai ta girgiza masa,cikin izzarnan tata da sanyin jiki,sannan a hankali ta motsa labbanta tana cewa

"Ba komai" Kaman bazai janye idanunsa daga kanta ba,kafin ya janye din,ba tare kuma daya sake duban crew din ba ya furta.

"Ruwa.......coffee,in akwai buqata sama da haka zaa sanar miki" Ya fada da salon iya taqaice magana irin nashi.

Kai ta gyada,sannan a ladabce ta juya tana barin gurin don cika umarninsa.

Komai daya shafi jirgin.....komai daya shafi tafiyar tasu tana nuna zallar alfarma ne da wata irin tarin izza da dukiya. Wani irin yanayi da tunda take hawa jirgi bata taba riskar yanayi irinsa ba. Shuru ya wadaci gurin.........sanda jirgin ke sake kutsawa cikin sararin subhana. Pilot da crew din da basu da yawa dukka suna bangarorinsu suna ayyukansu.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Ta gaza controlling zuciyarta,ta gaza tsaida zuciyarta daga nanata tambayar SHI WAYE?......WAYESHI A AGADEZ......KO NIAMEY da yake da irin wannan alfarmar?.

Private jet.....private pilot.......private crew?. Komai private ne.....komai kuma me kima tsada da alfarma ne.

Tun bayan da ta kawo ruwan,ya tura mata gabanta......ya hada da tissue dukka ya ajiye mata,duk da cewar bata buqaci komai ba. Sai ya gyara kujerar da yake kai zuwa yanayin da zaifi masa dadin relaxing bayansa sosai.

Yayi relaxing din cikin wata nutsuwa yana miqe dogayen qafafunsa dake sanye cikin socks charcoal color da suka dace da shigar jikinsa.

A nutse ya bude briefcase din dake gefansa,ya zaro wani qaramin littafi da duka duka a qiyasinta shafukansa ba zasu haura hamsin ba. Daga kwancen ya sake ragewa gurin da yafi kama da parlor haske,ya koma yayi relaxing sosai yana bude littafin.

Shuru ya ziyarci gurin,wani irin shuru da bai bar mata komai ba sai qamshin turarensa da kuma satar kallonsa da bata shirya ba. Tun bai jima ba ta fahimci karatun yana mata dadi,tun basuyi nisa ba ta gane yadda karatu ke matuqar dauke masa hankali da sakashi a nishadi. Sannu a hankali saita samu kanta da satar kallonsa,satar kallon data zarce mata zuwa wani kalar satar kallo na minti daya zuwa rabin minti sannan ta zare idanunta da sauri a duk sanda taga yayi motsi. Yadda fararen manyan qwayar idanunsa suka rusuna kamar wanda bacci ke son qwacewa.......ta saukar da idanunta a hankali zuwa ga lips dinsa. Wani abu daya fusgi hankalinta.....wani abu data sani ya taba burgeta sau daya tak game da wani jarumi cikin fina finan soyayyan da takan kalla. Wasu irin lips ne masu wani irin shape me daukan hankali,lips din da zai wahala kaga sun bushe,suna da wani irin yanayi dake nuna sulbin da suke dashi koda daga nesa kake,nisan da zaka dauka ma mamallakinsu yana using lips gloss ne saboda qawatashi. Ta saukar da duban nata cikin dabara zuwa ga habarsa. Wani irin beard,kwantaccen saje da gemu daya zama cikakken ado wa fuskarsa. Wasu irin gashi marasa tauri sune kwance sama da qasan labban nasa,suka kuma zagayesu sannan suka hade da kuncinsa zuwa qasan habarsa. Wani irin baqin gashi me daukan idanu da kuma sulbi a idanu ma.....sulbin da haka kawai taji zuciyarta lokaci daya na fusgarta dason taji yanayinsu cikin hannunta. Ta sake maida idanunsa ga cikakkiyar girar dake barazanar hadewa da juna,sai taji wani abu ya zarce ta cikin maqogoranta,ya kuma harba saqon.

"Anya bai fini kyau ba?" Tambayar da ita kanta tasan ta sakata a shakka......shakkar da tabbaci yakeso ya rinjayeta. Ba bala'e'en kyau ya mallaka ba......amma Allah ya yiwa zubin halitta da tsarinsa baiwa da KWARJINI. Komai nasa idan ka kalla yana da wata irin cika da kamala da kwarjini.

Sanda ta dora idanunta kan hannunsa dake riqe da littafin sai taji bugun numfashinta ya sauya na wucin gadi,ta janye idanunta saboda zuciyarta dake gaya mata.

"Kallon bai yawa ba?.....idan yaji a jikinsa fa?" Amma haka kawai minti daya kacal sai taji tanaso ta kalla,tanason ta kalli dogayen yatsun nan da ayau suka ratsa tafukan hannayenta sama da kullum. Tanason taga yatsun da sune na farko da suka fara gauraya da nata yatsun da sunan d'a namiji ya taba hannuwan nata.

Saidai a wannan karon tana shirin janye idanun nata ya kamata da nasa idanun da wani irin sauri da bazata da bata taba kawowa ba. Wani irin kunya...kunya me nauyi da wani irin sanyi taji yana bin kowacce gaba ta jikinta. Zagayayyun fararen idanun da bata taba ganin wani d'a namiji da fararen idanuwa irin haka ba.

Kafeta yayi da wadannan mayatattun idanuwan nasa,idanuwan da suke da wani irin tasiri,ba iya kan mata kawai ba hatta da maza. Yana da wani irin shape ne idanunsa da wani irin tasiri da yawanci ma'abota yawan kallon alqur'ani da hadith kawai ke samunsa saboda kwarjini da albarkar da litattafan ke dasu.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 22*

"Kici gaba" Ya furta a nutse yana motsa wadannan kyawawan labban nasa bayan data dauke dubanta kwata kwata daga sashen. Ita sam ba zata bari ba......ba zata aminta ya fahimci koda sau daya ta saci kallonsa ba. Maganar saita tsananta bugawar da zuciyarta takeyi bayan wadda ta tsinci kanta a ciki a dazu,sanda yayi mata kamun ba zata.

Tsuke fuska tayi kadan,sosai takejin ba zata aminta kai tsaye ba.

"Me?" Ta furta cikin qarfin hali da dakiya bayan ta waiwayo tana dubansa,saidai duban bai kasance nakai tsaye ba,don ta sani.....a yanayin ba zata iya kallon qwayar idanunsa ba.

"Kallon" Shima ya bata amsa a yanayi nakai tsaye yana kuma sake kafeta da idanun nan nasa. Yadda ta soma amsa masan da wannan izzar.....da wannan k'i fadin.....da wannan jin isar sai yaja ra'ayinsa.

Yadda zuciyarta ta sake bugawa tare da bata tabbacin ya ganta.....tabbas ya gagganta tana kallonsa. Tun yaushe?,tun kallon farko?,ko ana qarshe ne?. Rasa me zatace tayi.....rasa amsar bashi tayi,saboda ita din kanta tana mamakin ita khadeeja muhammad hammud?,......itace da satar kallon wani d'a namiji?,why?.....me yasa?. Cikin son kariyar mutuncinta da jin izza ta dauke kallonta daga sashen data ajiye kanta ta maida ga window ba tare da tace komai ba,tana kallon yadda suke keta gajimare da girgije suna sake nisa cikin sararin samaniya.

Haka kawai yaji bayason maganan ya tsaya iya haka,ya motsa kadan ya gyara zamansa yana aza qafarsa daya saman daya,wani yanayin zama dake masa kyau,yana kuma sake fidda wata shimfidaddiyar izza dake tattare dashi wanda shi kansa baisan yana da ita ba.

"Me kike kalla?" Ya sake tambayarta yanayin haka kawai yana sanyashi nishadi,saidai ko ga saman fuskarsa ba zaka fahimci hakan ba.

Sake tsananta bugu zuciyarta tayi,ta sake tsuke fuska tana girgiza kai.

"Ba komai" Ta fada cikin yanayi na basarwa,can qasan ranta cike da tuhuma. Boyayyen murmushi ya saki. Ba itace mace ta farko da irin haka ta faru tsakaninsu ba,saidai nata yanayin cike yake da wani irin izza jin kai da kiyaye pride irin na diya mace. Yanason wannan dabi'ar.......kare alfahari da izza ba,karon farko daya fara ganinta tattare da wata diya mace a kansa.

"Kici gaba......amma kuma....." Sai yadan dakata. Dukka kunnuwanta suna gurin,dukka kunnuwanta suna tare da fitar lafazin daga bakinsa. Tsaiwar tasa sai tasa mata wani irin qaguauta taji abinda zaya qarasa fada,amma kuma sai ya yanke maganan daga nan.

"Idan kika kalleni na dan lokaci......" Ya sake dakatawa kaman bayason ya qarasa maganan.

"Bazan qyaleki ki daina ba" Da sauri ta juyo.....wani irin saurin da bata shirya ba. Hakan yakeso dama.......sosai ya riqe qwayar idanunta cikin nasa,akwai abinda yakeso ya gani,kuma ya samu ya gani din,kafin a hankali ya zame idanun nasa.

Numfashi take saukewa a hankali bayan ta maida idanunta ga window,tana jin wata gajiya da tsoro suna shigarta a hankali. Qirjinta yana dagawa,haka numfashinta yana fita da wani irin yanayi kamar wadda tayi gudu.

"Waye shi?,wanna irin mutum ne shi?" Tambayoyi biyun da takejin qaguwar samu amsa sosai a kansu,saidai ta sani a nan kusa bata da wannan amsar......bata dame sanar da ita.

Ya kama ta tana kallonsa… amma maimakon ya dakatar da ita,ya sanya ta son sake kallonsa ne kawai......amma tana tsoron maganansa na qarshe BAZAN QYALEKI KI DAINA BA.....

Cikin qasa da awa daya wani mutum daban take gani ba sheikh haisam ba......ba sheikh muhammad haisam da yake zaune a masarautarsu qarqashin alfarmar mahaifinta ba. Sanda ta farka daga baccin daya dauketa bayan shurun daya ratsa tsakaninsu,shurun da yafi mata sauqin wanzuwa tsakaninsu akan ya sake kamata tana kallonsa......ta farka ta samu kanta lullube da wani tattausan baro,kanta kuma jingine da madaidaicin pillow me taushi,kaman yadda aka sauya fasalin kujerar nata zuwa yanayin da zaiyi supporting kwanciyartata.

Koda ta bude idanun nata a gabanta ta ganshi,ta waiwaya tana duban window din wanda ya gaya mata a tsaye jirgin yake. Koda ta duba lokaci sai taga sun qara kusan mintuna goma sha biyar akan ainihin lokacin da akace zasu sauka.

Ya sauka jirgin tuntuni,ta sani,inde ba babbar lalura ko wata damuwa ba,jirgi baya sab'a lokacin tashinsa ko saukarsa........zaman da sukayi kenan kawai ana jira ta tashi a barcinta ne ko kuma yaya?.

Ta sauke idanunta a hankali a gabanta sanda ya tsugunna da nutsuwa yana daidaita mata takalmanta a gabanta. Wani irin nauyi taji.....nauyi taji sosai ya aza mata. Anya batayi kuskuren fahimtarsa ba?, ba kowanne d'a namiji bane zai yarda yayi lowering kansa.......ya tsugunna a gabanki ya daidaita takalmanki zuwa saitin qafarki don kawai kisa ba. To me tayi masa data cancanci wannan girmamawar?.

"Koyi yake.....koyi yake da fiyayyen halitta" Wani sashe na zuciyarta ya bata amsa sanda yake tuna mata da wani sashe na littafin nan data karanta. Yadda yake hidimawa iyalinsa......yadda yake iya durqusawa matarsa ta takashi ta hau abun hawa S A W.

Idanunta ta lumshe tana jan siririn numfashi tana saukewa. A karon farko ta bishi da kallo,kallon dake narke da wani kalan emotion daga zuciyarta.......kallo me nauyi dake dauke da sinadaran BURGEWA......karon farko daya juya yana takawa tabi faffadan bayansa da kallo tana jin har qasan zuciyarta wata qwayar halitta me suna BURGEWA tana sauka tsakiyar naman zuciyarta.

Welcome to jidda......ta gani a rubuce b'aro b'aro,sanda suke takawa ita dashi kafada da kafada kamar wanda aka bashi gadinta. Ta sauke numfashi me sanyi a karo na babu adadi. Ta dauka a Riyadh zasu sauka......su sake bin mota su shigo makka,saiga wasu irin shimfida shimfidan motoci qirar Rolls Royce Cullinan guda biyu,da tarin Mercedes Benz S-class da suka kusa guda biyar. Jerin motocin alfarma guda shida da suke tsaye cikin tsari.......baya ga mutanen da take hange. Sanye da baqaqen suits kamar yadda aka taresu a airport na Niamey.....sai larabawan da take hanga sanye da farin thobe daya dace da shigar jikinsu sosai tare da bayyana asalin gadon shigar da sukayi.

Koda ba'a gaya mata ba ta gani.......tsaiwar jiransa sukeyi. Duk wanda ke tsaye a gurin dama motocin dake gurin suna jiran isowarsa ne.

Kaman dazun.....kamar a Niamey,yayi taku biyu yasha gabanta,ya kuma rufeta da faffadan qirjinsa ta yadda bame iya ganinta,ya sanya hannuwansa ya gyara yafen mayafinta,ya kuma gyara mata abayar jikinta sosai. Da wani irin sanyi a muryarsa......yana jin kamar yana hadiye wani abu da qyar ya furta.

"Boundaries please" Kaman dai dazun,amma a yanzun tana jin wani abu deep cikin muryar tasa. Bata sani ba.....batasan dalilin duka wannan ba.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

A hankali ya sake ratsa yatsunsa da nata......a hankali ya sake game tafukan hannunsu da wannan yanayin da yake sakawa tsigar jikinta tayi wani irin zubawa har taji kaman karsashinta yana raguwa. Takunsu kusan daidai yake tafiya,suna sake kusantar mutanen da dukkaninsu ke murmushiwa haisam din.

"Assalamu alaikum warahmatullah......welcome your royal highness" Balarabe na farko ya fara fada fuskarsa dauke da wani irin murmushi da zai nuna zallar sabo dake tsakaninsa da haisam din.

Wannan miskilin murmushin......wannan miskilin yanayin dashi ya amsa masa yana bashi hannu shima.

"Royal highness?" Ta maimaita Kalmar cikin kanta tana satar kallon fuskar haisam,wanda yadan taka gaba kadan da ita yana gaisawa da sauran mutanen dake tsaye,fuskar da bata samu cikakkiyar damar kallonta ba sai kwantaccen gashin gefan fuskarsa dake glowing a hasken fitilun da suka cika king abdul'aziz international airport din tamkar allurarka ta fadi ka dauka.

A hankali takejin wannan nutsatsiyar muryar tasa da tasha banban data dukka mazan dake gurin tana ratsa kunnuwanta. Idanunta suna kafe a qasa,tana jin gaisuwarsu tana kuma amsawa a hankali saidai bata daga kai ta kalli koda mutum daya a cikinsu ba,muryarsa da yadda yake magana da yaren da ta rasa gane wanne yare ne kawai ke mata tasiri cikin kunnuwa. Yaren da taji yana mata wani dadi,yana mata kuma kamanceceniya da yaren fullatanci,saidai yafi fulatancin tsari da dadi a kunnuwanta.

Cikin girmamawa daya daga cikin mutanen dake sanye da suit dinnan ya bude masa murfin rolls Royce din yaja da baya da girmamawa. Saidai kuma ya waiwayo gefansa,inda take tsage zuciyarta da kwanyarta suna zurfi da nisa a tunani.

"Bismillah" Yace da ita yana sake bude mata murfin sosai da wani yanayi da taji ya saukar mata da wani izza da girma.

Kowa ya dakata.....komai ya tsaya saboda jiran shigarta mota kawai?,.....kamar a masarautarta ta agadez inda akasan tarin girma da kimarta?.

A hankali ta taka da yanayin takunnan nata dake cakude da qasaita,ta taka motar tana shiga a nutse,ya tsugunna a hankali yana gyara mata abayarta data fito waje,muryarsa da taushi yace.

"Kiyi addu'a......koda bismillah ce" Sannan ya maida murfin ya rufe mata. Ta cikin glass na window din ta bishi da kallo,sanda yake zagayawa zuwa daya side din,da dan murmushi kadan saman fuskarsa yana magana da balaraben.

Ta cikin motar taci gaba da monitoring komai.....motsinsa da yadda yaci gaba da magana dasu. Yadda suke magana dashi cikin girmamawa da qanqan da kai......yadda yake magana dasu da wani yanayi......yanayin da yafi mata kama da yanayin mutumin da ya saba da iko tun daga haihuwarsa.

"Ya salam......wayeshi?" Ta fadi wannan karon a sarari tana jin shakka da kokwanto suna cikata a kanshi.

"Ina buqatar na sani......dole,ba malami bane kawai.....wannan fuskar da muke gani a agadez ba ita bace ta gaske.....wannan mutumin......bashi bane na gaske" Ta fadiwa kanta tana jin qwarin gwiwa. Tana jin zuciyarta na tunzurata......tana jin ya zama dole tayi bincike a kansa.

Readers Also Read

More by Huguma