Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 14

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 14

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 14: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 14. Maimaita maganan ta soma yi cikin kanta. Da waye zai…

3,359 words

Maimaita maganan ta soma yi cikin kanta. Da waye zai gana?,da waye zaiyi meeting?. Imams na haram?......inde daidai taji imams na haram ne.......WAYESHI? Tambayar ta sake dokawa cikin kanta,saita daga kan nata da sauri tana ajewa a kansa,daidai sanda ya juya harshe yana bawa hadiman amsa da harshen larabci maimakon turancin da suka masa magana dashi.

"Kuma?.....an kuma?" Ta furta a hankali tana jin wani tsoro nasa da mamakinsa yana kamata.

"Anya bame had'ari bane?" Ta sake tambayar kanta tana jin tana rikicewa kadan. Yare nawa ya iya?,harshe nawa yake iya sarrafawa. Da farko yana hausa duk da bata zauna a bakinsa sosai ba ta yadda idan yanayi saika gane ba yarensa bace.....English.......france..... Tuareg kadan kadan.....ga kuma larabcin da bata jin komai a cikinsa......a iya haka ya tsaya?,ko da ragowar yaruka?.....WAYESHI.......tabbas akwai wani lullubi cikin rayuwarsa......akwai abinda dukkaninsu basu sani ba,ita da sultane dama dukkan wanda yake tare dasu. ME YAKE BOYEWA?,Mene manufofinsa?,ta samu kanta da fada tana jin yadda larabcin ke fita tartar daga bakinsa,bashi da maraba da Accent na larabawan da suke musu jagora.

Hanya kawai taga ana buda musu duk da yawan mutanen dake gurin,suna sake gaba.....suna kusantar inda duk zuwanta bata samun daman isa gurin.

"Ta wannan hanyar sheikh" Jami'in ya sake fadi yana musu nuni da wata kebantacciyar hanya.

Cikin mintuna qalilan suka iso wani guri,kebantaccen gurin da bata taba zata za'a sameshi a guri me cike da cunkoson al'umma haka ba. A tsare yake,ba cunkoson mutane,sai shimfidu bisa tsari da tarin tsaro.

"VIP zone sheikh zamu qarasa" Ya sake fadi cikin girmamawa ganin ya danyi slow kadan da tafiyarsa.

"Ki jira a nan.....kiyi sallarki a nan" Ya fada a nutse sannan ya juya yana takawa jami'an suna biye dashi ta wata hanyar da take dab da inda zai kaika bakin ka'aba matsayar da liman yake tsayawa a duk sanda za'ayi sallah.

A hankali ta taka zuwa saman shimfidun. Tana duban matan dake zaune cikin nutsuwa samansu. Dukkaninsu kusan qabilu ne daban daban daga qasashe daban daban,saikin lura da gaske zaki gane banbancin yanayinsu,alamu kadan tasa ta iya gane daga gidan mulki ko sarauta suka fito suma. Nutsuwarsu da shigarsu ta daban ce.

"Ga guri nan" Taji wata sassanyan murya tayi magana daga bayanta. Hausar da taji ya sanyata waiwayawa da sauri tana neman me maganar.

Kyakkyawar matashiya ce,wadda aqalla zasuyi sa'annin juna ita da ita a qiyasin shekaru nakai tsaye datayi mata. Murmushi ta sakar mata tana sake nuna mata muhallin dake kusa da ita wanda babu kowa. A hankali ta tsinci kanta da maida mata murmushin,sannan ta soma takawa zuwa inda tayi mata tayin,ta zare takalminta a nutse tana hawa saman carpet din.

Samun kanta tayi dayin bismillah kafin ta zauna,abinda ya tsaye mata cikin zuciya.

"Yaushe kika fara koya?" Ta tambayi kanta,bata da amsa bata sani ba,kawai ta samu kanta dayi ne.

"Halan ke dayace kema.....ba abokan tafiya?" Matashiyar ta sake fadi tana murmushi da alamun dake nuna yawan murmushi yana cikin dabi'arta. Kai akhnan ta daga mata a hankali tana qoqarin sake aza murmushi akan fuskarta.

"Ni ni dame gidana ne......yana bangaren maza.... Kefa?" Tambayar sai ta yiwa akhnan nauyi,ita dawa zatace mata?.

"Ni sunana ameenatu muhammad jadda.....amma ana kirana da iffa......kefa?" Sosai sunan ya yiwa akhnan dadi,sannan kuma sai takejin kamar akwai inda ta taba jin sunan.

"Khadeeja muhammad hammud" Ta amsata a taqaice. Kai iffa ta jinjina

"Sunanki yayimin dadi.....daga nigeria nake......kekam nasan ba 'yar can bane....." Kai ta gyada a hankali murmushi yana sake subuce mata kadan. Karon farko da hira da wani ya burgeta,wanin da ba shehnaz ko aisa ba.

"Nijer.....agadez" Idanu iffa ta fidda kadan.

"Daga agadez palace?" Kai akhnan ta gyada a nutse

"Yeah........haba,kaman nasan sunan......daughter of sultane muhammad hammud.....right?" Iffa ta furta tana dan fidda idanunta waje tana nuna akhnan da yatsa.

Wannan karon dole murmushin akhnan ya sake qaruwa,ta sake daga mata kai a hankali,saidai tayar da iqama da aka fara qoqarin yi shine abinda ya katse wannan hirar tsakaninsu.

Cikin sahu da matsayin da Allah ke bawa bayin da suka samu daman yin sallah a gurin suka gabatar da sallar isha'i ta wannan rana. Sallar da suna sallameta basu samu daman yin wata maganar da iffa ba me gidanta ya kirata

"Save my number please prince khadeeja" Iffa ta fada tana murmushi. A nutse ta fidda wayarta ta karantawa akhnan numbers dinta ta dora da fadin.

"A swissotel muka sauka....zamu qara kwana bakwai kafin mu wuce,ina fatan zamu sake haduwa?"

"In sha Allah" Akhnan ta amsa mata. Tana jin kamar ta samu wani madadi,wani madadi nasu shehnaz da aisa data baro a agadez din. (One of jadda's family......sabreen namesake).

Duk da yawan mutanen dake kaiwa da kawowa amma hakan bai hana idanunta ganinsa ba. Daga nesa sanda yake takowa sanye da wannan farin ihram din data kyawun daya masa ya kasa dusashewa a idanunta da zuciyarta. Daga nesa kadan take hangensa,hannunsa cikin na sheikh abdurrahman assudais,gefansa kuma sheikh yasir aldosary. Dukkansu suna murmushi ne,da alama akwai magana me muhimmanci da sukeyi. Hanya ce da idan zasu wuce ake cikata da security,suna kuma wucewa ne da dan sassarfa saboda mutane masu daukan hoto da kuma masu son tsaidasu.

Ta lumshe idanunta tana sauke ajiyar zuciya don ragewa zuciyartata nauyi. Tantama shakka da kuma kokwanto a kansa sake cikata yakeyi. Da gasken gaske takeson sanin shi waye,ta kuma fara aika bayani a kansa......amma tana jin kamar amsar ba zatazo mata a sanda takeso ba.

Ta sake daga idanunta,sai ta hangeshi yana takowa da wani irin nutsuwa,haske ihram din jikinsa yana sake haske fuskar nan tasa data rasa wanne irin sirri ne kwance a cikinta. Sirrin da idan ka kalleta kwarjini nutsuwa da kamala sune abinda kawai zaka iya gani.

Da alama bai ganta ba,wannan ya bata daman sake shigewa mutane kadan tana kallonsa,tanaso taga ta yadda zai iya zaqulota,duk da tare suke da daya daga cikin askar na gurin suna magana kadan kadan. Sallama sukayi ya koma bakin aikinsa,shi kuma ya tsaya cak da alamun yana wara idanunsa ne don zaqulota.

Idanunta zube fes a kansa,ya danyi qasa da kansa kamar me kallon wani abu,sai kuma ya juyo cikin second daya saiga idanunsa cikin nata. Zare idanun nata tayi,tana jin alamun takunsa a jikinta,tana jin sanda ya iso dab da ita,tana jin muryar nan tasa me zurfi da wani kwarjini yana fadin.

"Ina fata kin dauki niyya?" Kai ta daga a hankali,sai ya juya yana fadin.

"Bismillah"

Biye take dashi a hankali,qafafuwansu suna sake musu jagoranci zuwa gaban ka'aba. Idanunta akan dakin,daki mafi tsarki,muhallin da yafi kowanne martaba tsarki da daukaka a duniya. Tana sake kusantarta tana jin yadda zuciyarta ke sake sanyi.....tana qara duka taku guda tana jin yadda nauyin dake saman zuciyarta yana raguwa.

Sanda ta tsaya a saitin inda zasu fara dawafi,girman dakin ya bayyana a gabanta,sai taji wani karayar zuciya. Ta sauke idanunta akan tarin mutanen dake dawafi a sannan. Yau din kamar akwai cikowar jama'a sosai,abinda tafi tsoro kenan yafi kuma bata wahala duk cikin umara ko aikin hajji,wannan turmutsutsun,wannan cikowar.

Takawa ya fara yi,tana daga gefansa,a hankali take ajiye takunta duk inda ya ajiye nasa,suka fara zagayen farko. Dukkaninsu zuciyoyinsu sunyi nisa wajen addu'o'i da jin kusanci da mahaliccinsu. Ta lumshe idanunta,tana jin yadda cunkuso yake qara daduwa,amma hakan bai hanata jin daddadan sautinsa ba. Sautinsa shi kadai yana fita da wata irin nutsuwa,sautinsa shi kadai duk da tarin muryoyin bayi dake cike da roqo da kuma fata kala daban daban,saidai batasan dalilin daya sanya kunnuwanta ke tsame iya nasa sautin kawai ba.

Wani buri ne da takejin a yau ya ninka yadda ta saba jinsa cikin zuciyarta.....burin kaiwa gaban ginin dakin ka'aba,ta sanya hannunta ta tabashi,ta kifa fuskarta a jiki tayi kuka ta kuma gayawa Allah buqatunta. Tunda take zuwa bata taba damuwa da yin hakan ba,hasalima yawan cunkuson shike firgitata,tafi zabar yin dawafinta a sama tayi ta kammala,amma a yau din sai takejin shine abu guda dayan da take buri wato ta isa ga ginin dakin ka'aba. Tanajin kamar buqatunta masu nauyi ne a wannan karon......tana jin kamar buqatunta sun rinjayi na kowanne lokaci. Wannan qawa zucin ya sanyata ta fara neman hanyar kutsawa ta tsakanin wani rukunin 'yan qasar Malaysia da alamu ke nuna ahali daya ne,saidai yadda suka matseta a cikinsu ya sanya numfashinta ya soma sama sama.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 26*

"H.....ha.....haisammmm" Ta fada da sauri tana qoqarin qwato numfashinta. Har tsakiyar kansa yaji saukar sunan cikin kunnuwashi da wani kebantaccen yanahi,wani baqon sauti da a yau ya fara jin fitar sunan a gurbin. Da wani irin Zafin nama ya miqa hannunsa ya damqe nata,sannan ya jawota daidai kafadarsa yana manne tafin hannunsa cikin nata da wannan yanayin dake zare mata kowacce laka ta jikinta ya maye gurbinsa da kasala.

Sosai ya mata gurbi kusa dashi,ya hade dukka tazarar dake tsakaninsu ta yadda ko zare bazai iya ratsawa ba. Idanunta ta daga tana qoqarin kallon fuskarsa. Zafin naman daya gwada mata kadai ya isa ya gaya mata qarfi da kuzarin daya mallaka. Ba ita yake kalla ba,idanunsa suna gabansa da yana lissafa yadda zasu samu isa gaban ka'aba cikin sauqi. Sai sautin sunansa daya fita a bakinta da yaketa maimaituwa cikin kanshi.

"Ki zauna kusa dani" Ya furta cikin wani salo na umarni kai tsaye. Ya fahimci abinda yasa aka matseta har haka,ya sani kuma a daidai wannan lokacin bata da qarfin da zata iyakai kanta gaban ka'aba din.

Da sauri ta sauke idanunta daga kansa zuwa qasa,zuciyarta ta soma motsawa.

"Ya Allah......" Ta fada tana jin wani faduwar gaba tana samunta. Me ya kamata ta fara roqa?wacce addu'a zatayi?. Kamar yasan tambayar dake ranta kenan,wannan muryar tasa ta sake shiga kunnuwanta da wasu addu'o'i da taji zuciyarta na kwanciya kaman an yayyafa mata ruwan sanyi,sai kawai ta dinga maimaita abinda yake fadi.

A duk sanda ta maimaita fadin kowanne harafi dake fita a bakinsa sai taji zuciyarta ta sake nutsuwa. Duk sanda ta maimaita sai taji wani irin nutsuwa da kwanciyar hankali. Abu daya data ga yanayi,sauya mata bangare wanda batasan adadin sau nawa yayi ba. Daga kafadar hagunsa zuwa ta dama,daga kuma kafadar damansa zuwa hagu.

Wani irin kariya takeji tako ina.....wani irin aminci da tsaro irin wanda bata taba jinsa ba tunda take zuwa umara,koda kuwa da hadimai guda nawa zatazo. Bata sake jin an matseta ba tun matsewar farko,bata sake maimaita kowacce addu'a ba sai addu'o'in da suke fita daga bakinsa cike da wata irin nutsuwa,addu'o'in da koda batasan ma'anarsu ba......amma tana jin wani gamsuwa da aminci a cikin maimaitasu.

Zagaye bakwai me cike da wani irin yanayi.....zagaye bakwai me cike da wani sirrin aminci da nutsuwa da bata taba sanin akwai irinsa ba.

Suka tsaya cak,tsill hannunsa cikin nata. Akwai rangwamen cunkos zuwa sannan,saidai hakan bai hana cunkuson masu son zuwa gaban ka'aba. Hannunta ya saki a hankali,sai ya riqe tsintsiyar hannunta yana zagayo da ita gabansa.

Qugunta ya riqe da hannunsa guda daya,a hankali ya sanya idanunsa cikin nata,sai itama ta daga blue eyes dinta tana ajesu a nasa. Wani irin abu ya sauka saman zuciyar kowannensu,wani abu me nauyi taji yana taba zuciyarta da wani irin yanayi data gaza fassarashi. Kallon ido cikin ido da qaramar tazara irin wannan.....tazarar da hatta da numfashin junansu musayarsa sukeyi,tazarar da take iyajin yadda jikinsa yake gogar nata,tazarar da ta fara gaban babban daki.....babban gurin da babu irinsa,tazarar da ta sanya wata nutsuwa a ruhinta....wannan tazarar da taji a karo na farko ba wata tazara mai qaranci da muhimmanci irinta.

"Es-tu prête?(kin shirya?)" Ya furta yana motsa labbansa da suka janye hankalin Akhnan sosai,sannan cikakkiyar girarsa guda daya tana dagewa sama. Sai data lumshe idanunta a hankali,tana jin wani yanayi na daban yana ratsata. Tayi qoqarin motsa labbanta amma ta gaza cewa komai,sai kai ta daga masa a hankali.

Shima da idanu ya amsa mata,kallon daya sanya taji wani abu yana narkewa tun daga zuciyarta yana kwaranya a gangar jikinta gaba daya.

Ba zato taji yasa hannuwansa biyu ya rabata da qasa. Tadan tsorata har batasan sanda ta riqe faffadar kafadarsa ba. Hannunta ya sauka saman lallausar fatar kafadarsa......laushinta ya hadu da taushin nata tafin hannun. Saman qafafunsa taji ya dora tafukan qafafunta bayan ya juyata,bayanta yana cikin qirjinsa,ya saka hannuwansa ya zagayesu saman cikinta,ya mata kyakkyawar garkuwa da dukkan jikinsa. Ta yadda ba wani abu da ya isa ya tabata.......a yanayin da ba wani abu da zai kusanceta muddin ba gangar jikinsa ba. Habarsa ya dora saman kafadarta,da wani kusanci sosai cikin muryarsa a tausashe yake fadin.

"Zaki tafiya saman qafafuna....zamu qarasa gaban ka'aba kiyi addu'a.....gurine me muhimmanci sosai.....gurine na amsa addu'a da dukkan buqatu.......zakiyi alqawari?". Sauka kowacce kalma take daga bakinsa kai tsaye zuwa kowane sashe na jikinta,saqon da dukka maganar suna ratsata. Alqawari daya fada ya sanyata bude idanunta dake lumshe tunda ya fara maganan,bata motsa ba,amma yaga alamun bude idanun nata.

"Zaki sakani cikin addu'arki?" Ya fadi maganan yana kaiwa qarshenta da wani irin numfashi me nauyi. Shuru kawai tayi.....tana jin sautin bugun zuciyarta ta cikin kunnuwanta. Zata sashi a addu'o'inta kamar yaya?,bata fahimta ba,ba kuma zata iya tambaya ba. Abu daya ta sani.....zai mata wani abu da zai shiga sahun tarihinta.

"Kinyi alqawari?" Ya fada yana dan matsa qashin qugunta kadan ba tare da yasan yayi hakan ba. Kai ta daga a hankali ba tare data shiryawa hakan ba.

Qafarsa ta farko ya cira,wani tsoro ya kamata taji kaman zata fadi,saita manne bayanta sosai da jikinsa tana riqe hannuwansa dake qugunta.

"Ki tsaya" Ya sake fadi kaman me rada a hankali muryarsa na sauka da wani irin sanyi.

"You're safe.......kina tare dani" Ya sake maimaitawa. Sai taji ta aminta dashi din.....ta aminta da maganarsa,sai taji ta saki jikinta hankali kwance. Yana takawa a hankali da ita,mutane na wucewa ta gefansu amma tana jin kamar komai ya tsaya. Da dukka jikinsa ya bata kariya,yana kutsawa da ita da wani irin qarfi na zuciya da hikima ba tare da cutar da kowa ba har suka isa gaban ka'abar.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Sauketa yayi a hankali daga saman qafafunsa,ta sake takawa ta matsa zuwa gaba,bai matsa daga bayanta ba,sai ya sanya hannuwansa ta gefe da gefan kafadunta yana dafe bangon ka'aba dashi,yayi mata wata ingarman rumfa da gangar jikinsa,ya lullube bayanta da kyau da jikinsa,ya kuma samar mata da space din da zai wadaceta tayi addu'a.

Hannunta ta dora itama saitin nasa tana dafe ka'aban. A karon farko kenan,duk da shekarun data dauka tana zuwa. A karom farko ta sanadinsa,da dukka wata kariya da zai iya bata ya sadata da dakin. Sai taji wani hawaye me dumi yana saukar mata,ta masa a hankali ta sumbaci hajarul aswad,ya sake matsawa da ita gefe kadan,ta saka bakinta fa sumbaci ka'aban,kafin ta dauke kanta ya sake manneta cikin jikinsa,ya kuma zuro kansa ta kafadarta,abinda ya hanata iya dagowa kenan,sai tabar fuskarta a jikin dakin tana sauraren fitar numfashinsa,dumin jikinsa,da sautin addu'o'in da ba zata iya tantance abinda yake roqa ba.

Wani yanayi ta jita a ciki,irin yanayin da yafi kowanne yanayi yi mata dadi cikin duniya. Ya zareta a hankali ya riqe qyam cikin jikinsa yana sake zareta daga turmutsitsin.

Sallah sukayi raka'a biyu daga nesa kadan da ka'aba din. Saita samu kanta da cikar hawaye a idanunta. Ta daga hannuwanta ta rasa me zata roqa?. Bayan addu'a data sakewa sultane,a yau saita samu kanta da yiwa mamarta addu'a.

"Ya Allah,kayi mata rahama.....ka shafe kurakuranta......ka yafe mata zunubanta Allah" Saita dakata,tana tuna me zata roqawa kanta.

"Allah......ka......" Kasa qarasawa tayi,tana juya abinda zuciyarta ta raya mata ta roqa din,ya cancanta?,ya kamata ta roqi wannan kuwa?. Wannw tabbaci take dashi?,wanne yaqini take dashi?. Bata da dukkan wata makama......bata da dukkan wani qwarin gwiwa nayin addu'a akan wannan.

Daga inda take zaune tana iya ganinsa. Tsaiwarsa a sallah......ruku'unsa dama sujjadarsa. Komai nasa sai take ganin yana da wani irin banbanci da wanda ta sani da kuma wanda ta saba gani.

Yadda ya zauna saman qafafunsa,cikin wani tawali'u da qanqan dakai,ya hade dukka tafukan hannayensa,ba wani sauran izza a tare dashi.....ba wata qasaita....sai zallar nuna miqa wuya ga ubangiji,sai taji itama tata zuciyar tana karyewa. Kuka kawai taji tana son tayi,ba tare da tasan dalili ba,sai kawai ta cure guri daya,ta cusa kanta tsakanin cinyoyinta tana bawa hawayenta daman sauka yadda sukeso.

Ta dauki mintuna aqalla ashirin a haka......a hankali taji kaman qamshinsa a kusa da ita.....a hankali takejin kamar akwai wani kusanci na daban a tare da ita,sai ta soma qoqarin daidaita kanta da sassauta kukan,kafin a hankali ta soma qoqarin daga kanta.

Shine a zaune a gabanta,da wani irin coolness ya zuba mata manyan idanun nan nasa. Kallon ya mata nauyin da ba zata iya jura ba.

"Kiyi addu'a......guri ne na bayyana dukkan damuwa da samun waraka". Sai ya miqe a hankali ba tare da yace komai ba. Maganar ta tsaya mata a rai,tayi qasa da kanta a hankali tana bawa zuciyarta daman ambatar dukkan abinda take buri da muradi.

Karo na biyu ta sake ganin an miqa mata cup,ta daga idanunta a hankali. Shine ya dawo,yana tsugunne saman qafafunsa da cups guda biyu masu cike da zamzam mai sanyi.

Batayi musu ba ta miqa masa hannun,yatsunsu suka hadu da juna,sai ya zare hannunsa a hankali. Kauda kanta tayi tana juya yadda zata sha ruwa a gabansa,yana zaune dab da ita,idanunsa ta tabbatar kuma suna cikin nasa. Kamar yasan me take tunani,kamar yasan abinda yake ranta,sai ya matsa gefe kadan yana zama sosai saman tiles din masallacin.

A nutse ta shanye gaba daya,sai taji wata nutsuwa tana saukar mata a hankali. Ta sake satar kallonsa,baya komai don ya nuna kansa.....amma komai qoqari yake ya nuna wayeshi. A yanzun tana jin kawai kamar binne kansa yakeyi......tana jin wani binnnan mutum ne kawai suke rayuwa dashi,ba ainihin haqiqanin sheikh haisam na agadez ba.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 27*

Ba a nan kawai ba.....sanda suke takawa a hankali ita dashi,tana daga gefansa.....iskar dare me tarin nutsuwa da wani irin sanyi tana kadasu. Kusan dukka inda sukebi kamar abun shiri,ma'aurata ne guri guri cikin yanayi na soyayya da zai dauki hankalin duk wanda ya gansu.

Wasu a kwance daya yayi pillow da cinyar daya......wasu a zaune suna hira......wasu karatun qur'ani.....wasu kuma dukkansu bacci suke kusa da kusa da juna,yayin da wasunsu kuma suke maqale da hannun juna suna tafiya zuwa gurarensu.

Idanunta yawo kawai yakeyi a kansu,haka kawai takejin komai yana burgeta,haka kawai takejin yanayin duk da take kalla yana burgeta.

Ba soyayya sam cikin tsarinta.....saboda ba kalan namijin da takejin yakai ya mallaketa......amma a yanzun batasan me yasa couples din suke burgeta ba.

Qarar da yaji wayarsa tayi ta Bluetooth din dake kunnensa shi ya sanyashi cirota daga qaramin wallet din hannunsa.

Beeno ne ya ajiye masa saqo,wanda ya tsara saqo kawai dama banda kira har sai sun kammala umara.

_muhammad ya damu.....yanason yaga 'yaruwarshi tunda ya rasa mamarsa_ shine kawai saqon. Wani nauyi yaji ya sauka a ransa,tausayin yaron ya kamashi,sai ya maidawa beeno din amsa a taqaice.

_ka bashi haquri,zasu hadu a Ethiopia_

Daga can wani sashe na daban take kallonsu,yana kwance saman cinyarta da alqur'ani a hannunsa,ita kuma ta tura yatsunta cikin sumarsa tana hargitsata a hankali tana kuma biye da sautin karatun nasa. Sautinsa ne sama da natan,amma dukka sound dinsu ya cakude ya bada wani launin qira'a me dadi.

Batasan me ya saukar da murmushi saman fuskarta ba......sannan ya fusgi hankalinta zuwa ga kallonsa don taga ko shima ya gani?. Still idonsa nakan waya,wani abu taji mara dadi ya tsaye mata,saita janye dubanta a kansa ta maida kansu,daidai sanda shi kuma ya juya a hankali yana dubanta da wani yanayi da zai wahala ka gane ita yake kalla.

Readers Also Read

More by Huguma